ads:::

BARIKI IYAWA

8[9/12, 8:25 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: [6/2, 5:38 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 1_Tafe take cikin tukun ta na masu isa,da takama,tamkar mai gudun taka kasa,,hasken solar,kadai ke haskata da walwalin net din jikin ta..duk wanda yaci karo da ita,,toh koh ya tsaya kallon ta,, ko kuma ya wuce yana waiwayen ta,,wata iriya ce ita.. Allah ya bata abu 3... Kwarjini... Kyau,dan akwai zubii. Sannan uwa uba Aji.. Duk ustazan cinka akaf unguwa da kewayen nan kasan da zaman ta., sanye take cikin Riga da skirt na wani rantsatsan farin net,da head blue, ta zuba wata uwar sarka ta Daham kirar Dubai,,ga wane shegen takalmi mai tsinin tsiya blue,.rike da karamar jakar ta blue,, sai katon net data rufa blue a matsayin gyale,,in ka ganta,zaka rantse da Allah ko wata yar shugaban kasar ce.. Ba yar Haj Ladi da Malam Abdu ba..."BARIKI"kenan..wanda take wa kanta kirari da "IYAWA. kai da ganin ta zaka gani wani take jira,domin tana kallon agogon hannun ta tana dan tsuka,,fuskar nan sai sheki take tasha make up tamkar wacce zata zaben sarauniyar kyau..harara ta kwada mishi,lokacin da yai parking din motar a gaban ta,, sanin hali yasa daga nesa ya fara bata hakuri "Hajiya amini afuwa, wlh go slow na samu, gashi mai goge motar ne aka kai Matar shi asibiti kuma ya hana baya nan a bada...tsaki taja kanta warce mukullin motar ta,," kai kana rasa karyar kare kanka ne..ji shi a gun,,wlh na kusa sauya ka...kasan kwa yau ranar nan yadda take a waje na??ya dukar da kai"Hajjaju ai hakuri..ta bude pose din ta da bashi dubu1 "kaban waje..tuni ya kauce ta shiga motar... Tana zama ta duba mudubin gaban motar, ta Wai waiga cikin motar,kan ta bude ta dakko air freshener ta feffesa.." Dan iska,duk ya loda min garadan banxa a mota tana wari.. Tai tsaki,kan ta daura belt ta bata key.. Motar ma kamar bata so take Jan ta..wayan ta ne yai kara..ta dauka,ita kanta wayan kasan ta manya ce.. "Haba "BARIKI"... wulakancin da zaki min kenan??8 da kwata fa yanxun... Da sauri ta katse ta" ee eehm...yi min a hankali.. Gani nan bisa hanya..tace"Dan ke muka maida abun nan fa 8,kowa yazo amma kujerar ki empty..sannan har yanxun.. Kit ta kashe wayan"jaraba..mutum sai mita ya tsohuwa.. Ta sanya CD na wakar Ashique ta taka totur mota ta kara gudu... 15 mint ya kaita harabar hotel din da zasuyi program din,,tai parking kan ta fara takun nata na isa..waje ya hargitse..tamkar wanda ake gidan bikin mata,don baa gama zama ba,,da Zee ta fara karo da Royal... Tuni suka hau mata kirarin da ita kadai suke wa a duk qawaye.. "Yeee...kaga manya a Baku naku daban... Kaga mai sai maza caroling mai sa mata su watse...kaga farar mace..Alkyabba ta mata..wai sukari bakai farin banza ba..tuni kanta ya fara fashe wa..dan mudin suka gamu da da qawayen ta yan qarya.. Mai kirari ta cigaba..ita kwa sai wani juyi take tana yatsina halamar mai tai lacking.."Dawusu ce ke..ta kowa dole a kalle ki..in dake a waje dukkan mata su kauce..Allah ja mana ran suka Sara mata tare da cewa"BARIKI... Tuni tai wani fari tare da rausayar da kai ta na kada keys..kan a hankali ta furta"IYAWA ba..ta barsu nan tai chan ciki ta zauna kujerar kusa da amarya..suka bita da kallo...tana kula da Yadda mutum 2 ke Binta da harara .. amarya da abokin ango..ta kalle shi ta tabe baki kan ta zauna.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/22, 4:59 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 2_Tamkar ita ake jira kuwa aka fara sanar da kowa ya zauna a mazaunin shi.. Suka danyi bayanan su..tana ta kula da har yanxun Harar da Hafeez yake mata.. Ta kada kai.. Lalle ya kamata tai gaggawar saita mutumin nan.. Tunda take babu wanda ya taba kokarin shiga hancin ta sai Hafeez,da kudundune ma ya shiga shi..tai kwafa dai dai lokacin da aka tashi amarya da ango zasu yanka cake, chan baya yai yadda shi kadai ne karshe,, a hankali itama ta tako,tare da daukar kwalin 5alive tai wajen da yake..da wannan takun nata, yana ganin ta ya kara hade rai,, tai murmushin mugun ta, a dai dai shi ta tsaya kamar zata gogi jikin shi,, yai tsaki,Yarinyar nan ba karamin tsanar halin ta yai ba..tunda ya gano ita wacece... Yasan duk macen kwarai bazata so a kirata da sunan BARIKI ba..yai tsaki tare da kara matsawa.. Bude kwalin tai,ta dai daita shi dai dai kafadar shi da gan gan ta kar kata shi a kafadar, tuni ya fara bulbula mishi cikin jiki..take yaja baya dan ya tsorata, ga lemon da sanyi..ya kalle ta ya kalli taron, ba wanda ke kallon su, an dukufa kallon yankan cake.. Baisan lokacin da ya sau mata mari ba.,ji kake"Tasssss,hall ya dauka..abun ka da Babban waje,tuni ya dauka,,zata dafe kunci da sauri lbrn wata ya fado mata.. Ana juyo wa ta nuna shi da hannu.."Wallahi in ka kara sai na maka Marin da yafi haka... Taja tsaki kan ta juya tai waje tana dagowa amarya hannu..da mamaki kowa yake binsu,musamman ango da amarya.. Shi kwa Hafeez dan tsabar takaici kasa ko motsi yai,..lalle ya yarda, yarinyar nan "BARIKIN ce da gaske.. Da sauri yai waje..motar ta yaga ta fita..da sauri ya shiga tashi,,Ita kwa tana fita data shiga mota ta sau kuka..tunda take ba mahalukin da ya taba Marin ta sai Hafeez,, duk da ta maida mishi Marin kanshi,,kuka take tamkar ranta zai fice..ita rasa mey zatai ta huce ne yasa tai mai haka... Waje ta samu tai parking a gefen hotel din ta daura kanta a stirring motar ta cigaba da kuka..mai ta tsare wa Hafeez a rayuwa ne?? Jiyan nan ya gama dizgata gaban mutane..sannan yau ya sakar mata mari a bainar jama a.. Jin an tsaya da mota a kanta yasa ta dago..shine kwa,da sauri ta fara kokarin tada mota taki tashi,, ganin yana kokarin bude mata kofa da sauri ta danna lock tana kallon shi,, ta tsorata matuka, tasan yau kam ya ritsata sai wata ba ita ba.. Glass din ya fara buga mata..tuni ta gigice,ganin yana kokarin fasawa..sai kokarin tada motar take,.Allah yaso ta ta tashi,,. Kallon motar yake da tsabar takaici..yau kam da ya far mata sai taga karyar BARIKI.. Ango da Amarya ne suka fito..suma a mota,suka karaso wajen,," Mey zakai Hafeez?Yasha gaban shi sai huci yake yana kallon motar harta kule..."Dan Allah yaushe ne zaku hadu Baku bar abin fada a waje ba?yanxu fa shikenan kun bata mana taro,,amaryar ta kallo Hafeez "kayi hakuri Hafeez, akan ido na komai ya wakana,da sauri suka kallo ta,tace" BARIKI fa ta wuce inda kake tsammanin ta wlh Hafeez,, kuma kai yadda ka dauke ta wlh ba haka take ba,,da sauri Hafeez ya tsayar su"kina nufin kinga lokacin da na mare ta ta dawo dashi kaina? Ta kada kai "tun zuwan ta wajen ka nake hankalce daku.. "Itama fa ramawa tayi,, in anbi ta Allah abinda kai mata jiya yafi haka.. Yai tsaki," kuban waje na wuce..kauce mishi sukai,,suka bishi da kallo har Shima motar shi ta kule. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/22, 5:00 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 3_Tana zuwa gida Maman su na waje suna fira da Abban su a kan taburma,,da sauri ta wuce daki ko magana bata musu ba tana hawaye.. Baki sake suka bita da kallo..dan ko su da suke iyayen ta rabon da suga hawayen ta tun tana karama..tashi sukai suka bita..lalle yau kam ba kanta..duk abinda yasa Sa'adatu toh mai girma ne.. A gefen gadon ta suka zauna.,in kaga dakin, tamkar irin na yar gatan nan..yasha kayan alatu,duk da rufin asiri ne dasu dai dai gwargwado.. "Sa'a lfy?mey ya same ki haka?ta kallo su.." Ba komai,,Abba mayi maganar gobe..suka kalli juna.."Toh toh shikenan.. Sai da safen,,ta daga musu kai,,kan suka fita..nan ta cigaba da kwance wa tana daura wa. Asalin lbrn..Sa'adatu yan asalin jahar Yobe ne,a karamar hukumar Nguru,, baban ta malamin makaranta ne na primary,,yana da rufin asiri dai dai gwargwado..duk da bai da ko gidan kansa a garin guru,,yana da mata 2,haj Ladi da Mairamu,,yaran shi 2 rak,Fadeela sai Sa'adatu..tun suna yara mairamu tasa maman su a gaba da kissa da kisisina sai da ta fidda Maman su gidan..dake mace ce ita mai hakuri,tunda ta kyalla taga ita haihuwa..ga amaryar ta harda yara 2,,tai mugun halin taga baci,sai ta koma kissa da BARIKI..inta fahimci mai gidan zai shigo saita fito tsakar gida ta fara kukan kissa,,"Nima ai Allah bai manta dani ba,da har zaki min gurin haihuwa Ladi,,koda yake laifin malam ne.. Tuni zai karaso yana "Subhanallah,, mairamu mai ne?mey ladin ta miki?sai ta cigaba da kukan ta,, Wai na aiki Sa'adatu yarinyar nan tace bazata ba,daga magana Ladi ta hau zagina,, dan ban Haifa kaza da kaza..tuni ya fara huci,,ya ban kada dakin Ladi.." Ke na fahimci kin fara sauya hali tun ba yau ba,, infa naga dama saina Debi ya'yan duka na bata,, a wannan lokacin Maman su Sa'adatu takan ji haushi,ganin gashi an fada mishi abu.,amma bai bincike ba ya hauta da masifa,,"toh ka bata su, sai kwa ya sake tunxuro wa..dan ita fa zaman gidan har ya ishe,lokacin bata fi yar shekara 22 ba,,amma ba bakin cikin da bata dauka na mairamu in ba idon mai gidan, sannan mairamu tasan ta kan Miji,shi yasa a kullum tafi Ladi Power a gun mai gidan,,ga tsabar iya barikanci,,agaban kowa sai tace zata rungumi malam.,ita ta matse ta zauna a tsakar gida bai zame mata komai ba,,duk abunda ya dace ladi tayi ita da take amarya kuma karama,amma mairamu ta amshe,kuma ita sam bai damun ta bare tai koyi da ita..akwai lokacin da malam ya kawo kifi,,yana rawar jiki yau girkin mairamu,,gaba daya tai farfesu ta watso musu kayuka a kwano..haka take ta hakuri da ladi,dan datai magana,malam zaice ta fiya kawo kara,,shi wlh ya gaji,ita kullum cikin korafi take??inkwa ranar yan muguntar suna kanta haka zata kama su Yaran tai ta nadar su.,uffan ladi bazata ce ba..sai dai in ta gama zakaji Sa'a na zuba mata Allah ya isa.. Sa'adatu ba kyal bace,,shekarar ta3,amma Allah ya bata bakar wayo,,ga baki na fitsara,,tuni ta fara karantar kishiyar uwar tata tun kan ta tafasa.. Ana haka ranar aikin mairamu ne,,sai tace wa fadeela taje ta kawo kwano a zuba musu,,fadeela tana bala'in tsoron mairamu kamar mey,lokacin shekarar ta 5.,ta zuba musu ta kai daki..chan saiga Ladi ta fito da abinci tazo kan mairamu.. A gaskiya mairamu kina jin tsoron Allah,, yanxu abincin nan ne zai ishe ni,har na bawa yara suci??kullum kina zuba haka bana magana, indai yara sun koshi sai dai ranar Girki na,,wane irin mugun ta ne wannan? Tuni dama da gaiya tayi,,jiya ta samo Sa'a,. Kiris take jira Ladi ta tanka,,"Haka naga damar zuba muku,,sai dai kar kici..tuni ta tunxuro.. Ba tasan sanda ta watsa mata abincin a jiki ba.. Yai dai dai da shigo war malam..tana ganin haka ta sau kuka.. "Nikam naga ta kaina a gidan nan,,Ladi ni zaki zubawa abinci a jiki daga abin kirki?? Bayan kin gama zage ni ban kula ki ba,,yau dole na bar gidan nan dan naga haka kike nema..tuni tai hanyar daki tana kuka,ta saci kallon malam din da yai kan Ladi..mari ya kifa mata,sai a idon su Sa'adatu,,tana kallo tai wa Maman tasu gwalo sannan ta cigaba da kukan karya..malam yace" Ashe rashin mutuncin naki yakai haka Ladi?tuni ta fara hawaye rike da kunci.. Toh kije gidan Ku saina neme ki..ta kada kai.,kan ta kallo mairamu..."In Allah ya yarda sharrin ki sai ya sauka a kanki..ta juyo kan malam din,,Ka dinga tsananta bincike a lamarin ka,,sannan ka zamo mai adalci a...hannu ya daga zai zuba mata wani mari yaran suka kan kame shi,,kuka suke suna bashi hakuri.. Duk tsiya,yana ji da yaran shi, musamman Sa'a.. Ya sauke hannu,,tuni taje ta fara hada kaya tana kuka.. Tunda ta bar gidan take gasa yaran,,wanka da ruwan sanyi,duka,,barin Sa'a, dan ta bala'in tsanar yarinyar.. Tana jibgar ta tana mata Allah ya isa..kuma in ta tashi saita fanshe., inta dai daici ta daura abinci taje ta zuba kasa ta gudu..ko ta zuba ruwa a murhun,yadda har baban su ya dawo bata gama Girki ba.. Nan zai hau fada..tuni Sa'a zata hau dariyar keta. Zancen Ladi kuwa,sai da yai wata 3 tukun ya Wai waye ta,,fir tace bazata dawo ba, ita saki take so..a lokacin mairamu ke gaban shi, ba musu ya mata 1,, baa jima ba tai auren ta. By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [6/2, 5:48 PM] Feenat Ja'afar: © Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 4_Yau shekara 5 da rabuwar Ladi da malam..Iyanxu babu wata kissar da Sa'adatu bata koya ba wajen Matar uban ta.. Dan tsaf ta zame mata tamkar makaranta.. Sharrin yau daban na gobe daban..ga Baban yana masifar son Sa'ar.. Yau da yamma ta zaunar da fadeela.. "Yau komai nace kicewa Baba haka ne,, ta harare ta." Saura ki tsaya tsoron ta..bulala ta dakko..tace ta da kar kare Iya karfin ta ta shauda mata a singalalin hannun ta.. Ido fadeela ta zaro,, "kina da kai kuwa..Sa'a tai tsaki.." Dallah ni ki daken nace,,fadeelan ta kada kai.,kan tai baya,,ta Dakar kare ta zula mata bulala,,da sauri ta hular ta,,harda hawayen ta Sa'an amma ta kara miko mata, ta daga kafar ta,, saura kafa,,tace"ke ni bazan Iya ba,, ta juyo da harara"ni nace kimin dallah.. A haka banxa ma wata katuwar duka na take, bare yau da zan ci uwar ta nima..tuni ta kara zaro ido "Sa'a wlh ba ruwana..haka kurin bazaki jamin masifa ba,,ta juyo kan ta kalli hannun ta, tuni har ya fara tashi.." Kar ki Iya din.,amma wlh Allah komai nace ba ruwan ki da karya tani, ke ko kishin uwar ki bakya yi..nan kishiyoyi sun hana ta zaman gidan aure..auren mama 2 harda na baba 3..kina nufin zuba ido zanyi wasu wanda basu isa komai ba suna maida ta bazawara??ta girgiza kai "wlh Allah zaman mairo a satin nan zai kare a gidan nan..kin ganni nan..shekara ta 7 ina Neman ta takwas.. Na koyi halin mairamu kaf harda kari..duk wata BARIKI na koya a wajen ta.. Kede naki ido..ta dau bulalar ta leka waje,,lokacin mairamu tana daki,,ta ajiye bulalar a kofar dakin nata kan tai waje..chan kwanar su ta nufa.. Tasan duk inda baban su yake yanxu yana hanya..dan su yan primary tun dazu suka dawo..shi kuma ya koma secondary.. Ta labe tana leken shi, in ka ganta taci uwar damara da hijab din islamiyar ta..ko minti 5 batai da tsayuwa ba ta hango shi yana ta howa shida malam kallah,, da gudu tai gida..dai dai mairamu ta fito zata duba abincin ta.. Ta dan leka.tana kallo lokacin da take dokawa dakin su harara..tai kwafa,da gudu ta shigo da gan gan ta mangaje ta,sai kwa tai taga taga ta dafe rumfar da take Girki a gun,,ta Dakar kare ta mako ashar,,ita kwa ta kama kugu tana murguda baki.. Dube ta fara sai kwa ta dau bulalar target din Sa'a,, tana ganin haka tai baya.." Wlh nifa ba jakar uban ki bace da zaki ta nadar mu kullum.. Tuni ta kara tunxuro ta"ni kika zaga saude?lalle yau zaki yaba wa aya zakin ta., tai kanta"shegu gadon tsiya..tai charaf"kece dai gadon tsiya wlh,, Tsohuwar yar BARIKI.. Ni wlh na fiki Iya ta..da gudu fadeela ta fito.. Ganin yadda ake danbe da Sa'a da mairamu,, ta rike bulalar tamau ita kwa kira take ta sake,,tana jin kilin kilin din besfar Baban ta sau wani uban ihu..."Wayyo Allah.. Wayyo Baba kazo ka taimake ni... Na shiga uku zata kashe ni.. Tuni ta hau burburwa a gaban Mairo..ita kwa da tsabar mamaki ta sau baki tana kallon ta.. Da gudu ya shigo.,ganin katuwar bulalar dake hannun mairamu yasa da sauri yai kan Sa'a.,"Badai da bulalar nan ta dake ki ba..tuni ta kan kame shi tana razgar kuka"Baba ta kusa awa 1 tana duka na da ita.,kawai dan nace yunwa nake ji,, Wai ta fara zagi na,fadi take Wai,dama da bin malamai ta kori uwar mu..mu kuma da duka zata kashe mu.. Da hanxari ya kallo mairamu.,wacce ta yar da bulalar ta daura hannu a ka,,ta yi mata gwalo tana dariya, da taga baban zai kallo ta sai ta hau matso hawaye...a fusace ya tashi yayo kanta., "wlh karya kike,,yanxu dama in bana nan haka kike cimin zalin ya'ya?? Tuni ya kwada mata mari,,kira take wlh karya take mata..yace" wannan yarinyar har tasan wani karya,ai ganau ne ni ba jiyau ba..saboda haka yau zaki dan Dana kudar ki..ganin ya juya zai dakko bulala da gudu tai dakin ta ta rufo da sakata tana"wlh Baja isa tsawan zaman mu yau kace zaka daken ba...ke kuma inna fito wlh saina ci uwar ki a gidan nan..gadon jaraba..tana kukan tace"mudai ba gadon jaraba bane ehe.. Baban ya juyo kanta,, "yi hakuri uwata..dama haka take muku?ta hararo fadeela,, kan ta karbe" Baba haka taje mana kullum, sai tace in mun fada maka sai ta kashe mu..ya zaro ido.. Kan ya kallo fadeela," zo nan yaya ta..ita kam duk jikin ta kar karwa yake..dan tasan yau Sa'a taja musu masifa a gum mairamu..wannan irin sharri, wlh ko ita bata Iya ba...Hawaye yake goge musu,,sai yanxu ya kula da hannun Sa'a., yayi ja jawur abunka da farar mace,ya tashi yai luhu luhu,yana tabawa tasau kara.. "Nidai Baba ka dawo mana da Maman mu,wlh kashe zatai kamar yadda tace" wayyo Allah hannu na..da tausayi ya kalle su,,amma Allah ya isa tsakanin shi da mairamu,,"Yi hakuri uwata..saina fanshe dukan nan datai muku yau..makota da tunda aka fara abun suka kasa kunne suna jin komai suka kalli juna.."lalle yarinyar nan BARIKI CE.. Dubi yadda tai..ta rike haba,dayar ta matso tana yi a hankali.. "Ai wlh tun yarinyar nan tana karama na kula ita zata kori Mairo a gidan nan,,ji ranar fa data zuba mata kasa a miya..ina ji uban yana ta bala'i.. Sai na fita naji tana fadawa yar tata ita ta zuba..ta kalle ta suka kwashe da dariya,,dan sarai sun San komai na rayuwar gidan,sama da mai gidan ma,tun zaman Ladi suka San kom..sai dai ita ladin batta wayo.. Sai yarta. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary BARIKI...IYAWA 5_Ranar sai su Sa'a ne sukai badaga da abinci, mairamu taki fitowa a daki,,ga malam yai Kane Kane sun zuba abinci suna ci har shi,,bai fita ba sai sallar la'asar,tafiya yake yana tunanin zancen Sa'a, tabbas ya zama dole ya dawo da Ladi, kodan yaran nan.. Toh amma ta ina zai fara?? Yana fita ta bude dakin ta, fadeela na ganin haka tai dakin su da gudu,,ita kwa Sa'a ta mike,,Kallon ta kawai take, tana mamakin yadda yar filillikar yarinyar nan tasan BARIKI?? Kai batajin sharrin da Sa'a tai mata yau ta taba yin Rabin shi,take taji ta fara shayin yarinyar.. Ta tsuguna ta bude tukunya da sauri ta rigata dauke tukunyar.. Ta taso a fusace "ke, mey kike ji dashi ne?? Ta yatsina fuska" Abun da kike ji dashi,,ai ni na karasa girkin, saboda haka,yadda kike zuba mana San rai wlh kema yau haka zaki ci..makota suna ji suka hau turmi suna lekowa a hankali..tayo kanta suka fara zaga gida,tubur tubur take Binta da uban ma zaune,,data zo dai dai kitchen din ta kwata bar da miyar a kasa,, ta kallo ta tana huci., "kika zubar min da miya?tai mata kallon banxa" kodai ba miyar ki ba?fadeela ta leko,, hannu take ta daga wa Sa'an Wai tai hakuri,, ta dallah mata harara,, "ai uban mu ne yai cefanen,ba Ubale ba,.ta murguda baki,. Datai wani kukan kura ta rarumo ta tuni ta hau jibga dukan ta take bakin ta yaki mutuwa.." Wlh kin daki Allah ya isa..tuni ta hau ramawa fadeela ta zo ta fara rike ta,,"dan Allah kiyi hakuri mama mairamu..data mangare fadeela sai tai kasa tare da rike baki,,"shegu,wlh yau sai na huce a kanku.. Da sauri makociyar daya ta sauka tai waje.,danta ta samu"maza jeka kira baban su fadeela, kace za ai kisa a gidan shi,, da gudu dan yai hanyar masallaci,ta dawo ta hau turmin tana tsurkutawa makociyar ta,suna hango baban su Sa'a da karfi suka ce "Sa'a, baban ki..ta kalli zaure sai gashi da gudun sa., tuni ta rike hannun ta ta daura aka" Wayyo ta karyan hannu,, zata kashe mu..tana ganin shi tai baya ta saki Sa'an.. Kanta yai,yana kama hannun ta kara sakar kara"wayyo Baba ta karya mu.,ya kalli fadeela da bakin ta jini..a tunzure ya yo kan mairamu.. "Kan ki kashen yara wlh ke zan fara kashe wa..tana ganin haka tai zaure..da sauri Sa'a tasa kafa ta tado ta..sai kwa raff ta fadi..tuni yahau jibgar kamar Allah ya aiko shi..makocin shi yazo shiga gida yaji kwakwazon Mairo.. Da sallama ya shiga,yaji shiru..ga nan Mairo a kasa sai jibgar ta yake..da sauri ya shiga.." Subhanallah, Malam Abdu, da girman ka,,kira yake"barni na kashe ta kan ta kashen ya'ya.. Dakyar ya ban bare shi..yana haki..malam kallah yace "mey ya faru haka?tuni Sa'a ta amshe" Wai dan zan kara miya a abinci shine ta fito, Wai munci rabon mu,,nace sai mun kara shine ta zubar da miyar, Wai in uban namu ya dawo yai abinda zai yi..makotan nan wannan ta kalli wannan., a fusace yace"nai abinda zanyi koh?toh na sake ki,, dan na Gaji da wannan bakar muguntar.. Da sauri makocin nashi yace"haba malam Abdu.. Ka yanke hukunci da sauri,, tuni Sa'a ta tashi ta karkade jiki tana murmushin mugun ta,, ya nuno ta "kar na dawo na same ki a gida na.,da sauri makocin ya janye shi sukai waje,,harda rangada guda Sa'a,, tai tsalle ta dire,." Wlh na fada,baza ki kuma kaiwa sati a gidan nan ba,gashi nan,sai a tattara ai gaba,a samu uwale da ubale achan, tuni makotan suka zago.."Mairamu lamarin sai hakuri.. A fusace ta kallo su..in banda nishi babu abinda take..Lalle BARIKI IYAWA ce..dubi yar karamar yarinyar nan tasha da ita?? Kokarin tashi take ta kasa,,makotan suka zo rike ta ta fusge."Dallah munafukai Ku cikani.. Ai duk ina kallon Ku.. Kuma ta Allah ba taku ba..zama daram dam.. Tuni suka hau shewa.. Harda bawa Sa'a hannu suka tafa"nan kikai kutunguilar da kika fidda baiwar Allah a dakin ta, gashi nan, dake Allah ba azzalumin sarki bane, yar filillikar yarta tai waje da ke..Ashe de Kano ba wata..tuni suka kara tafawa..kawai saita fashe da kuka..mey Sa'a zatai inba dariya ba.. Ta kallo fadeela da ta rakabe chan,,tai tsaki"meye kike rakabe mata?uwar mu ce zata dawo fa?kizo ma mui celebration. By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [12/23, 6:53 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 6_Haka mairamu tana ji tana gani ta bar gidan nan..da daddare sai ga uwar ta,,Wai saki nawa yai wa yarta,yai mata kallon banxa"saki 3,azo a Debi kayan ta, dan garin zamu bari, ta kallo su Sa'a, ta sau mata gwalo,,tace"ai shikenan nan,kan ka kaiwa, naga mai kula maka da yaran,,da sauri Sa'a tace"eh munji,muma uwar mu zata dawo,,baban ya kalli sa'a,, ya hannun? Tace"munje dasu zulai an gyara, ashe targade tamin.,ta hararo uwar mairamu, baki ta kama tana salati,"Yau taga BARIKI,, ashe dagaske ne,a fusace ya kallo ta,, "Hajiya yata ba BARIKI bace,tunda guntun mutunci a rabu lfy,ya tashi yai waje,tana ganin uban ya fita ta mike.." Kwarai BARIKI ce ni,ai rainon yarki ne.,daga inda ta tsaya na daura,,ta murguda baki,,ai a tattara, Allah yayi bazamu birni da wasu ba,.ta dau buta tai bandaki.. Tsohuwar ta bita da kallon mamaki,lalle ta yarda "BARIKI IYAWA ce,,ba sai an koya maka kake koya ba,,ko wacce mace da tata iyawar.. Amma ta yarinyar nan har tsoro yake bata,tun kan ta tafas har ta kone.. Sanadin rabuwar mairamu da malam Abdu kenan,,akwai uban gidan shi dan siyasa,a kano yake, shi ya bashi gida,yace ya koma chan yana kula mishi da wasu abubuwan shi achan,, dakyar da taimakon Sa'a, ladi ta yarda ta dawo,sati guda suka tattara sai kano,,farkon barin su Nguru kenan.. Tunda tazo unguwar aka san da zuwan sa'a, dan team guda gare ta, mai gidan Baban su ya sake musu makaranta ta kudi,,anan suka hadu da ummi,,da wasu daga cikin qawayen ta,, idan fada kake neman a tare maka,naira 2 kachal zaka bawa Sa'a,yanxu zaka ga cika aiki,,in kwa kishiyar uwa ce ta dame ku,,ba dabarar da bata ta saita mata zama,,ana haka sukai coming interest.,Sa'a taci,Turkish,,tace ita kam ta Jahar su take so,,Mamudo,,mai gidan baban haka yai cuku cuku ya kaita chan., Sa'a ko rigima.. A chan ta samo yan Duniya, ya'yan masu kudi da masu karamin karfi,, nan ne farin kara samun iyayi da kisisinar ta,,nan karya ta karu,,dadin ta daya? Kwanyar ta naja..dan hutun farko,saida malaman su suka zo gidan su Sa'a, dan ka'ida in anyi hutu suna kai ziyara gidan dalibai masu ilimi,,toh fa,akaga malaman larabawa a gidan su Sa'a, yara suka cika,, tuni ta fara dagun kai,, tun daga nan martabar Sa'a ta kara sama cikin yaran arear,,wannan ne ya kara sa qaunar ta a gun iyayen,,ita kam fadeela day take so,,nan take yi. Tana ss1.,amma in ka ganta,zaka rantse wata katuwar budurwa ce,,komai ya kan kama,,samari suka fara mata cha..tuni kai ya fara gilgilwa,,basu ke gaban ta ba,,burin ta da yawa,, musamman kanan samari,tafi raina su,, toh wanda take nema suma ba'a barsu a baya ba,,sai kaga Alhj babba dashi,amma yazo yana rawar jiki wa Sa'adatu,, ganin yadda take, yasa suke sau mata kudi,,da taci naci,ta fatattake ka,, da kudin samari ta kafu,, dan ita batajin nan da shekara 5 ma zatai aure,,tun baban na taka mata burki,har yai shiru,,yakai ya kawo kayan da Sa'a take sawa yanxun ko yar wani mai kudin albarka., Ga BARIKI sai abunda yai gaba,,akwai lokacin da taje super market ita da fadeela,, suna cikin siyayya saiga wani Alhj sunzo shida matar shi siyayya,,tunda yaga Sa'a,ya kasa sukuni,,tuni matar ta fara tsaki tana hararar su Sa'a,, Sa'a ta kallo ta ta watsar,,sai a lokacin ta kula da yanayin Alhjn,,tai murmushin mugun ta.. Tuni ta fara kwarkwasa,tana wani yauki,,tamkar bata san Alhjn nayi ba,,da taxo dai dai wajen shi da gan gan ta yarda kwalin corn flakes,, tana wani fari ta tsuguna zata dauka,da sauri Alhjn yarigata,, sai washe baki yake,, "sanun ku yan mata,, tai wani fari ta saci kallon matar,duk sai huci take,,tai wani far da ido" Yauwa Alhj,, tuni fara'ar shi ta karu,, har ya manta da matar shi na gun,,iya wuya matar nan ta kawo.. Da karfi ta katse shi.. "Wai Alhj meye haka?ya juyo,." Mey.. mey..mey nayi,,taja tsaki sai kaje ka biya ai,,ka wani tsaya a gaban yar cikin ka kana bari,,ya kallo Sa'a.. Ta sau mai wani shegen murmushi tana far fara ido..tuni ya sake washe baki,, dan takaici kira take"Alhj, magana nake,, amma ina,shi ya tafi,,ta kalli su fadeela da tsabar takaici.. Tace"shegu karuwan banza kawai., ta bangaje fadeela ta wuce tana huci..Sa'a tana ganin ta futa ta hade rai "Baba, mama na maka magana,,tuni yasha mur" haba yan mata,, tai gaba tana taku zuwa wajen biyan kudi,,da sauri ya shiga gaba.."Aa aa.,bari zan biya duka..tai wani murmushi, kai maza abar su,,ita duk dan matar tayi,kawai daga ganin su zata fara ya tsina musu fuska.bata san wace ni ba,,taja baya ya biya kudin..zata dau ledar ya dauka har tasun ya rike,,ta kauda kai tana dariya..suka fito daga super market din, matar tana ganin su ta fito amota. By Feenat JaJa'afar & Hauwa Damary [12/23, 7:49 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 7_Magana take amma shi hankalin shi yayi kan Sa'a.. Tuni ta kule ta tsaida Taxi,,Sa'a ta nuna mishi ita,,kan yai wajen tana dagawa matar yatsu cikin shakiyanci..tuni ta kara kuluwa..tace mai taxi yaja,,shikwa Alhj yana ganin haka ya koma wajen su Sa'a,, "Asma'u muje na sauke ku mana,, tai far da ido,, toh mun gode,, tuni ya hau rawar jiki,, suna tafe yana musu tadi,,ita duk ya ishe ta, amma ta maze,,a layin su ta nuna kofar wani gidan kasa,.nan ne gidan mu,,yasau baki yana kallon gidan, yace" toh sai kin ganni,,ta kada mai kai,,har yaja mota yana daga musu hannu,ita kam yake kawai take mishi,,yana kule wa tai tsuka,,"ji yadda yake rawar jiki,,yan wahala.. Ita dai fadeela binta take da kallo..suja dauka suna tafe,,saiga wani dan unguwar su Aminu,yace"BARIKI.. Tace"IYAWA.. Yai dariyar keta..kai Allah barmu da BARIKI.. Tai murmushi "Amin Aminu,,yace" Wane garan aka kara wanka, tai fari,"kasan ku maza,,sai a hankali.. Nasan zai dawo..zan sa yara suna min gadin kofar gidan nan,so nake tashin farko ya bani kudin gyaran gida..Aminu mutumin ta ne,a duk unguwar a maza dashi kadai take hulda,,duk a dalilin qawar ta ummi.. Yai dariya "BARIKI ba imani,,yai kuma tanan za'a fara,tace" nagaya fiya rawar kai ne wlh,, yace"a sassauta mana,,tai murmushi "wanda bai kawo kanshi ba ba..sukai dariya.. Kan chan ta wuce gida,,tuni fadeela tai gida ita kam,,da sallama ta shiga,,aka cire gyale,,"mama mun dawo,,ta kalle ta,," sannu,ta fara bude kaya,,ta ware wa su mama kayan shayin da ta siyo,ta dau nasu da kayan cosmetic,ita dai mama kallon ta take "wai ni Sa'a na tambaye ki,,ta kallo maman" toh,, "ina kike samo wannan uban kudin haka?tai murmushi" mama kullum tambaya 1 kike min,,"wlh ni ba wanda nake roka yake ban kudi,, fadeela sheda ce,,ta girgiza kai,, "ni dai kimawa Allah kar kice zaki saida mutuncin ki a banza,, dan wlh koni uwar ki lamarin ki ya fara bani tsoro.. tai wani murmushi "mama,ta kallo ta," wlh hannu wannan, ba saurayin da yaga fuska bare ya taban,,na kuma miki alkawari, indai nice,toh zan rike mutunci na.. Ta kada kai "Allah ya muku albarka,. Sukace " Amin. Washegari kuwa sai ga Alhj yazo gidan da ta nuna mishi jiya,,tuni dama tasa yara zaman jira..in wannan sun gaji su bawa wannan,, ya yafito daya,,"Nan gidan su Asma'u? Ya kada kai "amma bata nan,bari a kira ta,,dan har sunan karyar data bashi ta sanar da yaran,,da gudu yai gida,sai gata ta dawo a islamiya,," BARIKI., tace "ya akai Tj,,ya rada mata" mutumin yazo,,tai murmushi "ku tashi toh,an jima zan neme ku,,tai gida..tuni ta cire kayan islamiya tasa na karya,aka mitsika powder,, ta zari gyale" mama ina zuwa, tai waje,uwar ta girgiza kai,, Allah mai halitta,, ta rasa Sa'a halin wa ta biyo a duniya,,wlh bata da kaffara, ko yanxu akai wa Sa'a aure a gidan mata 4 tsaf zata zauna..ita kanta wani sa'en tsoron BARIKI irin na yarta take.. "Alhj sannu da zuwa,, ya washe baki," yauwa Asma'u, ya gajiyar ku ta jiya?tai fari,"Tabi lfy,, "ina aunty,,yai murmushi,, tuni yaji ta kara shiga ransa,, Ya zamo kusan kullum Alhj sai yazo,,wahalar yau daban ta gobe daban, Alhj har ya mallakawa BARIKI waya,lokacin rike mai kyau sai ya'yan manya,,ranar da ya cika sati,yazo da kudi,wai zai bata ai gyaran gida dan zai turo manyan shi tambaya.. Saida cikin ta yai kululu..amna ta wayen ce..ya dakko damin kudi kuwa ya bata. ana haka washegari suna tsaye sai ga wata yar BARIKIN gaske ta fito a gidan,ta kalli Sa'a"BARIKI,.. Tai mata banza,,tace" Sa'a, dake nake fa,,tai mata kallon banza.."Bance kifita harka ta ba ne? Alhj ya sau baki,,Sa'a kuma,.ta kallo shi da yake"Sa'a fa,,ta daga kai, "aa ni ba wannan bama,kamar BARIKI naji an kira ki,,ta hade rai" eh Suna na kenan, ya hadiyi yawu.. Anya kuwa tafiyar shi zata wu davyar BARIKI? Da gani wacce ta fito a gidan sun nan ba yar kirki bace,,take ta kallo shi, ganin tarkon ta ya danu"Alhj lfy?ya kada kai "a ba komai,inaga zan tafi,, tai murmushi.." Toh nagode..yaushe zan ce zasu zo..ya kallo ta "aa ki bari zamuyi waya.. Tai murmushi"a gaida aunty na..koh kulata bai ba. Tun daga nan bata kara ganin kafar Alhj ba,dan tunda ta fuskanci da gaske yake tahada plan na rabuwa dashi cikin sauki..saida ta sake layi kan ta koma makaranta. By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [6/2, 5:59 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 8_Gashi har ta kammala secondary school dinta a Mamudo..iyanxu kam, karya ta ninka ta da,,BARIKI da Yanga da kisisina ya gaba,, cikakken zubi kuwa ya da zati Allah ya bata,, shekarun ta 17,amma in ka ganta,zaka zata tai 20,dan komai yaji cif cif,,kugun nan tamkar dame shi akai,ga mazaune,, ta ko'ina tayi MashaAllah.. Shi yasa take zan zaren ta son rai,,tamkar in taje makaranta karatun yanga da Iya tafiya, salo da sauran su ake koya mata,, duk yan Matan unguwar nan so suke suyi kawance da bariki,,likafa ta ci gaba,,tun a ss2 ta bude account,,dan a yanxun Business take,bata saye da siyarwa ba,, no.,ta saita gidan aure,, Tunda mazan yankin suka gane tsoron BARIKI suke,sai su kuma suka samu abun yi.. Akwai lokacin da a wata unguwar gaba dasu,wani dan siyasa Matan shi sun hana shi sakat,,yai nasihar a banza,,sun maida mishi gida kamar filin dambe,,Ranar suna office yake bawa abokin shi lbr,,"yanxu duk dabara ta ta kare,, ya kallo shi,kan yai dariya,"kasan mey?ya girgiza kai "ina ga ina da dabara,,tuni ya gyara zama,," in baka manta ba gidan Dana zauna da,ya kada kai "a unguwar, akwai wata Yarinya,," BARIKI sunan ta,, ita indai da kudi,toh aikin ta saita mata ne,,ya kalle shi da halamar tambaya,, "ban fahimce ka ba?? Yai murmushi,"a unguwar kaf,ba wanda baisan BARIKI IYAWA ba,,yarinyar tayi,ga diri ga kwainane,, ya harare shi" toh ni kuma mai zai hadani da wata bariki??mtsww kai ana abin kirki ka sako mana wani zance..yai dariya "ka jira ni tukun,,waya ya dauka,kan yai dailing wata number, kan yasa a hands free,," Daga chan aka dauka,"Aboki ya akai??yai dariyar keta"kaga na BARIKI sai yayi,,Shima ya kyalkyale da dariya,,"kai baka mantuwa abokina,, yace"ya zan manta,,da fatan har yanxu komai normal?? Yai dariya,, "kai BARIKI Duniya ce wlh,banga mai Matan unguwar nan suke tsoro har yanxu sama da BARIKI ba,, madam dina lukus kake ji, tunda akai wannan batu..yai dariya" Ya kamata a koma a karawa BARIKI jari,, suka sake kyalkyale wa da dariya..bayan sunyi sallama shi dai Muktar da kallo yake binshi,, ya ajiye waya yana"BARIKI BARIKI,, "tukun kasan wace BARIKI kan kaje gare ta,, Mutumi na dan nace BARIKI ba ina nufin karuwa ce ba,,ya girgiza kai," Tasan takan Duniya ne,,wannan abokin nawa,shekara 1 data wuce Matar shi ta tsuro mishi da hali iri iri,,da halama da zigar kawaye,,ga ta kamar ta yana son ta,,tuni ta hau iskanci irin na kowa ya samu inuwa,Wai dole yai shanya,,har karar ta yakai wajen iyaye, amma ba abunda ya sauya,,Ranar muka hadu,nace yau a gidan shi zanci abinci,,bai min musu ba muka je,, a parlour muka tarar ta ita da qawaye,,suna firar shi abokin nawa, fadi suke"Wlh mazan Saida haka,,in ka nuna musu bakka mutunci anfi dai dai tawa dasu..ya kalle ni na kalke shi baki sake,,.mukai sallama tana ganin mu ta tabe baki,, qawaye kowa yai hanyar sa,,tana gani mun zauna tai tsaki ko gaisuwa babu ta tafi,, ya kallo ni duk kunya ta ishe shi,,nan yahau kame kame,,nace"Ku nan hala Baku San da zaman BARIKI ba? Ya girgiza kai "wace haka?nai murmushi,, biyo ni mu fita tukun,, tuni ya zari mukullin mota, By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [12/24, 12:08 AM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 9_Wato a unguwar mu akwai wata Yarinya BARIKI.. Ita aikin ta kawai a dauke ta sojan haya., indai zataji dumus,toh fa gidan ka ya gyaru ya gama,, yanxu wajen ta zamu,, ni zan ma iso,akwai wani Aminu Aboki na suna dasawa sosai,,. Suna zuwa ya nemi Aminu a waya,,sukaci saa kuwa tana gida,, Suka koma inuwa jiran ta,, chan sai gata ta fito tana taku tamkar hawainiya,,baki ya sake yana kallon BARIKI,, lalle taci sunan ta,, Ji yadda take wani yauki,,. Ta karaso da sallamar ta, cikin muryar nan ta masu Duniya"Sannun Ku,, Sukai yake,,"yauwa BARIKI,, Aminu yace "ganan Aboki na ya kawo abokin shi ai mishi gyara,,tai murmushi, tare da kallon su da wannan kallon nata,,sai suka zama kamar wasu sokaye a wajen ta,, Aminu ya kallo su" Ku karan to mata, "Ni zan wuce,ga nan bakin ki,tai murmushi, tare da daga mishi yatsun ta 2" see you,, ya gyada kai, sukai sallama ya tafi,,Duk abunda ke faruwa suka karanto mata,tai murmushi,, "yane toh,, tai musu wani kallon kasa.,tuni ya gano mai take nufi,,rafar dubu 10 ya bata,,"ki fara da wannan,, ta juya su tai murmushi,," bakka matsala,, "Abu 1 yanxu zaka min,ya gyara tsaiwa,," kasa min numbern ka,,sannan duk inda zata fita,ka sanar ni,ya gyada kai,, tai murmushi "Baka da damuwa,,ana haka saiga wata Qawar Matar wanda aka bada contract dinta tazo wuce wa,,da sauri ya kallo abokin,," tafa kwabe,,ganan Qawar ta,, suka kalli Sa'a, tai murmushi "ai tama taimaka min wajen aiki na,,Wai salma kake nufi? ya gyada kai,, tai murmushi," kai kamar baka ganta ba,, sannan yau,kar kaje gida sai karfe 10 dare,, nasan daga nan,gidan ka zata..zata sanar da Matar ka,cewar ta ganka tare da BARIKI.. Daga nan, zata fada mata koni wacece,, ina so in ka koma,ka sauya mata fuska,,da sauri ya kallo ta,, tai murmushi "I know what am doing,,, ok?ya gyada mata kai,,nasan zata fara tambayar a ina kakai dare?kasan amsar bata I guess.. Ya kada kai" ki sanar ni dai,,tai murmushi,. Zamuyi waya,,dan yanxun haka ina da wajen zuwa,,ni zanji da sauran aikin..sukai kada kai tare da mata sallama,,,. Direct kwa salma gidan Qawar ta tayi,,da mamaki ta bude ta shigo,dan dazun ta tafi,,"da fatan ba mantuwa kikai ba??Tace "hmm zakiga mantuwa,, kin San kwa ina naga mijin ki? Ta kada kai tare da gyara zama tana zaro ido,," Toh a wajen BARIKI,,Bakya ramin kanki sai na wata,,tuni ta fara tunanin ina take jin BARIKI? Ta cigaba. "Ke kinga damin kudin dake hannun ta?kuma wlh mijin ki ne ya bata,,.ta kallo ta" kinyi shiru ina miki magana, "ko zaki ce baki gane wa nake nufi ba?Kin manta Nazeer saurayin Mamy da suka hada soyayya da wata ta daga karshe ya kita ya koma gun ta?ko zakice Baki tuna wacce tasa aka mana A tule ba lokacin bikin Hafsa dan mamy tai mata tsaki??Ita tuni ta hau zufa,,dan tuno da wacece BARIKI,,tuni ta mike,,ta kade in har mijin ta ya auro mata BARIKI,,tasan koda kwarkwasa saita Kore ta a gidan nan,,ta zauna," Qawata meye abun yi??ta zam,,"ki fara tada mai wuta tukun na,,na 2,gobe yana fita muhadu muje har gida muci mata.. Dama wlh har yanxu ina cike da a tulen data sa aka mana. Haka ta barta kan sai goben. Sai 10da kwata ya shigo gidan,,kamar yadda BARIKI Tace kuwa tana ta zarya a parlour,, da Dane,ko 8 ya shigo tana daki a kwance,,tuni ta yai kicin kicin ya hade rai,, tana ganin haka gaban ta ya fadi,,kan tai magana wayar shi tai kara,ya kalle ta a wulakance yai tsaki kan ya zauna a kan kujera yana murmushi,, "BARIKI,.. Yai dariya tamkar ta fada mishi wata Kalmar mai dadi,," kai ke ai ta daban ce,,yanxun dawo wata,, yai dariya yana Shafa haba tare da kallon yadda Matar shi ta daura hannu aka,,"nima tamkar na dawo inajin wannan tattausan muryar taki mai mantar min da komai,..yai Jim halamar yana saurarar ta,,ya kyalkyale da dariya,..tuni Matar ta sau kuka,,ya kalle ta ya watsar,,"Dan Allah asa ranar auren nan da wuri,,..ji yai an warce wayar hannun shi,, ya bita da kallo,tuni ta fara ban bami "Wlh ta Allah ba taki ba,,Banza karuwa kawai,,daga chan tai murmushi kit ta kashe wayar..a razane ya tashi,ya warce wayar shi,," wlh in kika kuma zagin masoyiyata a gaba sainai mugun saba miki,,"mey kika Iya ke in banda kullum ki bata min?sannan na samu mai wanke min zuciya da tattausan lafazi ki zage ta?? Kai ta girgiza mai "Dan Allah baban Najib kai hakuri,,wlh na daina,, ka rabani da BARIKI,, gwiwa biyu ta zauna tana rokan sa..ya fizge rigan shi tare da wuce wa daki..,,yana shiga ya danna sakata ya hau dariya.. Yaushe rabon sa Aisha ta mai abu ta bashi hakuri?? Kai ya manta,sai yau a dalilin BARIKI.. Yana son Matar shi.. Amma duk ta sauya hali..zai juri ganin ta a haka har yarda BARIKI tace By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [12/24, 12:54 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 10_Ya danna kira ya sanar ta ya akai,"ka barta zuwa gobe da safe,,nasan zata ce zata zo wuri na,,ko tasa azo,, kai mata gargadin wannan kan ka fita,,. Washegari ma bai sauya ba,yau Aisha harda su gaisuwa, wanda rabon ta da yi tun Kan ta sauya hali,, yai mata banza,,zai fita cikin sanyi tace baka karya ba,,ya harari wajen abincin, "No zan karya a waje,,sannan ban yarda ki daga daga nan ba,zan Iya dawo wa kowanne lokaci.. Yai waje yana dariyar keta,,a kujera ta zube,,tunda take Abban Najib bai taba mata haka ba,,Wai har abinci bazai ci ba.,ta share hawaye,Kila ma wajen BARIKI zai ciwo,,kai amma su salma sun mata huduba marar kyau,, gashi ta kwabe mata,, waya ta dauka,kan ta kira salman," karki zomin gida,munafukai kawai,,kit ta kashe wayar ta,, yanxu ta ina zata fara? Acikin kwana 2 duk ya sauya mata hali,Waya da BARIKI, text kuwa ba'a magana, ranar yana wanka ta saci numbern bariki a wayan shi,da sauri ta fita,,sai sa ya yay kan ta kira BARIKI,, a yangance ta dauka,, "Amm Aisha ce,,tai far " wacce kenan? Duk ta rasa abun fadi, dan ji tai ta mata kwarjini tun a waya..sai kawai ta kashe,,.bashi ya dawo ba sai azahar,, kuka ya same ta tanayi reras,, tana ganin shi ta tashi,, dan dazun nan aka kara karanta mata wace BARIKI yar unguwar su,,"Baban Najib,,dan Allah ka auri kowa banda sa'a,, kayi hakuri bazan kara ba,, ya kallo ta kamar yai dariya.,a ranshi yana tunanin "Wai meye da BARIKI ne da yasa mata ke tsoron ta?? Ya basar" Gaskiya bazan Iya fasa auren Sa'a ba,, dan tun yanxu tai min alkawarin zaman lfy da kwanciyar hankali,, bazan fasa ki koma min yar gidan jiya ba.., tuni ta hau rantsuwa ta daina,inta kuma ya auri BARIKI,, da wannan ya samu lfy a gidan shi,,yace da yamma muje zan raka ka.. Yamma nayi suka je gidan su BARIKI,, a lokacin tana gida ana drama da ita,,wani kanin kakan su yazo daga Nguru,amma irin in za'a bi da aure tsakani,, yazo akan lalle lalle BARIKI ta fidda Miji,,tunda fadeela ta fitar,,tuni ta fitsare "Ni fa banni da tsayayye,, atoh ko ina da wallahi ba zanyi aure yanxu ba,,baki ya saki har iyayen suna kallon ta,, dake bala'eene yahau ta da masifa,," kedin wa?dama duk iskancin da kike tatawa a garin na samu lbr,toh dole ki tsaida haka ki samo na aure,,ta kalle shi, "toh na tsaida,,yai murmushi," ko ke fa,,a ina yake?ta hade rai,, "kai man,, ba shiba hatta iyayen sai da suka zaro ido,, ya tashi," ke banson iskancin banxa,,Tuni ta fara burburwa tana kukan gaske,,"ni wlh kai nake so,, kuma kai zan aura,,baban ta ya doka mata tsawa,"Sa'a bama son iskanci fa,, "ta kara jiniya" wlh shi zan aura,, ni shi nake so,,tuni tsoho ya sau kuka,,Lalle ya yarda BARIKI ce yan nan,, kuka yake yana"Allah ya isa saude,,ki kalle ni kice ni zaki aura?jikar jika ta?cikin kukan karya tace"Toh Haram ne?nidai kai za'a abani, ba shiri yai hanyar waje yana goge kwala, "InshaAllah anyi na karshe,,da sauri baban ya bishi," Baba kai hakuri ka dawo,,dole ta bi umarnin ka ai,,har suka fito kofar gida tsoho na kuka"ai ni ba ruwana da harkar yarka daga yau,,Ashe da gaske "BARIKI ce haka??Wai ni zata aura??Alhj Muktar suka kalli juna,tuni dariya tazo musu,,a karshe dole baban tasha ya raka shi ya koma inda ya fito..yana fita ta ware tana dirkar dariya.. Ladi ta fara tafa hannu,ta nuno ta da hannu" anya Sa'a,, ta kallo Maman tasu,"mama mey nai? Ta kar kade jikin ta,, ta sauke ajiyar zuciya "ba komai Sa'a,, Allah ya shirya mana ke.,tace " Amin.tai waje wajen kiran ta,,. Dariya ta samu suna dirka, tana ganin shi ta gane shi,,tuni ta hau murmushi, "yau an tuno Haj Ahmad? Yai murmushi" Manya a Baku naku daban,ttai wani fari,,tuni Alhj Muktar ya gyara tsaiwa, kai shikam BARIKI ta mishi,da aure ba contract ba. By FeenaJa'afar & Hauwa Damary [9/13, 8:10 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: BARIKI...IYAWA 11_Abinda ya kawo su suka sanar mata,tai murmushi, da gani mutumin zai sau hannu, tuni ta yarda,Alhj yace da daddare zai dawo,sai su tsadan ce,,tai murmushi, dan tuni ta harbo jirgin shi,,kai ta kada,,sukai sallama tai gida,,Maman su ta kalle ta, "Sa'a, ta zauna tana amsa wa,," In tambaye ki man?tai murmushi, "toh mama, tace" ke ko tsoro bakya ji wataran wata tai miki illah akan mazan su?tai murmushi, "mama Allah bazai bawa kowa galaba a kaina ba,,kedai kimin adu'a,.. Ta kada kai" Yauwa, dama ina son fada muku,makaranta zan shiga,,cikin satin nan,, Maman ta kalle ta da mamaki,,Wai yaa ita take wa kanta komai tamkar da namiji mai aiki,,in bata manta ba, kwanan nan aka kawo takardun gidan Sa'a data siya da kudin ta,, ta girgiza kai "Allah ya kara kare mata Sa'an ta a ko'ina. Washegari plan ya fara,Alhj Muktar ya sanar mata Matan shi zasu walima,ya gaya mata lokaci da venue,, tuni ta gama tsara komai,, a chan unguwar da ke gaba dasu ne,,Bikin na manya ne,,an ciki kowa ya zauna a kan kujera mai gaba tar da walima kawai ake jira,,filin gidan babba ne,yadda in mutum ya shigo sai ka kare mishi kallo bai karaso ba,, tunda mota ta tsaya ake kallon bakin kofar,, sanye take cikin wata bakar Riga da ratsin purple doguwa kirar Dubai,, ankai tela ya kara fito da shape dinta,,anyi tuntu a ka da gashi da rabons manya,, tai nadi tamkar balarabiyar asali,, ga wani katon glass fuskar nan ta Gaji da make up,,hand bag dinta da wayar ta tasa cover da takalmin ta duk iri daya,tana zuwa wasu samari sun sha bakaken suite,da ganin su kasan bodyguards din ta ne, da suka bude mata motar suka bude mata gate,, daya ya bata jakar ta ta makala a hannu, daya ya bata phone nata,,tuni ji kake tsit waje kallo ya koma gun BARIKI,,ta tako, suma bodyguards din suka biyo ta,, da hannu ta musu sign dasu jira ta waje,,wata a wajen ta zunguri daya,,"Ita kuma wannan Matar wani Alhjn ce?kamar rada dayar ta rada mata yadda na kusa da su zasu Iya jin su,,"ke,in kinji ana BARIKI..IYAWA, toh wannan ce,,Matan guda 4 dake kusa suka kara kallon Sa'a,, Matar ta cigaba "Bazawara ce, sai dai manyan zata aura,,Budurwar wani dan siyasa ce,koh Alhj mukhtar naji ne??tuni 2 kusa da ita suka juyo,,sai dai sun kasa cewa komai,, ta cigaba, "ta taba aure,tana shiga Saida ta fidda Matan da kissa da tsabar Iyah BARIKI,, dayar ta kallo ta,," toh ke ina kika Santa?ta rike haba"waye besan BARIKI ba a tsuku kun nan?ai in kin ganta a hanya kina tafe da mijin ki ko saurayin ki boye shi,,dan maza idon su,,idon BARIKI,.. Ta zungure ta kamar gaske,,"yi shiru gat nan zuwa,,in an fita zan baki komai in details.. Suka kada kai,, Sa'a ta zauna tare da daura kafa daya kan daya,, tuni wata ta kusa da kujerar da ta zauna taja wani mugun tsaki,kan ta dau kujerar ta ta sauya waje,,Sa'an ta bita da kallo a takaice, da sauri ta sake bin Matar da kallo,,kamar ta taba ganin ta.. Matan Alhj Muktar suka bita da kallo,,suda suka shigo suna hararar juna,yanxu duk sun ware jin an anbaci saurayin wannan da kamar sunan mijin su,, wata yar safasafa ce tazo da kujera kusa da BARIKI,, "Shege BARIKI.. Tai wani mayaudarin murmushi,, kan ta furta" IYAWA.. Suka tafa,,"Yayi mai gara kan yan maza,.ana haka mai walima tazo aka hau waazi. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/25, 12:19 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 12_Tun ana raba take away uwar gidan Alhj Muktar taje wajen Matar nan mai tsaki, Matar abokin mijin su ce,,suka kebe da kujera,bayan sun gaisa take tambayar ta"Ni Maman Abba kin San yarinyar chan ne??ta tabe baki "nasan ta, muguwar bakar kilaki kenan,,ni ai bazan manta fuskar ta ba,,duk da yanxu ta kara girma, tunda ma in kina Neman karuwar hanya,toh ki nemi waccan,ta sake kallo BARIKI, ita wayar ta take,tana ta wani lumshe ido,, ta dawo da kallon ta kan Maman Abba," mey ya hadaku? Tai murmushin takaice., kan tai kwafa "akwai wani lokaci da muka je super market nida Alhj siyayya,, anan muka ci karo da ita,,wlh Alhj baiya kallon mata barin a gaba na,amma yarinyar nan in kinga kwarkwasar data dinga mishi,,ke daga karshe mantawa yai dani,,tun daga ranar Yarinyar tai gaba dashi,,Asma'u waya.. Waya Asma'u,, inaga da ta gama tatike shi ta Kore shi,shine kwana 2 naji shiru,,tun daga lokacin na daina yawo da Alhj. Tai ajiyar zuciya, inko har da gaske Alhj ita yake nema dole taci uban yar nan,,ta gidan ma yata kare bare wannan yar BARIKIN?? Tashi tai ta koma wajen ta, kan BARIKI ta fita ta rigata fita,,tashin hankali, Wai gobarar gemu,,tabbas wannan CRV Alhj ce,,sabuwa da ko su ba'a kaisu unguwa a ita,,ta cije lebe" Tab, wato tun kan ta shiga har ta fisu ikoh?ana haka Drivern su yazo, dai dai BARIKI ta fito,, da sauri bodyguards dinta suka zo,suka karbi Jakarta da wayan ta,, da mamakin ta sai ta ga drivern nasu yayi wajen BARIKI yana kwasar gaisuwa,,amarya ta fito,,taga lokacin da Bala driver ke gaida BARIKI harda bata abu a Leda,,ta kalli uwar gidan nata a yatsine,, "nifa ban gane lamarin nan ba fa M Hafsa?? Ta kallo ta da takaici,, " zaki gane in munje gida,,sukai wajen mota amma Bala driver bai taho ba,,tai wajen tare da doka mishi tsawa"Wai baka ga fitowar mu bane??ya juyo da sauri,."yi hakuri Hajiya,Alhj ne ya aiko ni gun amarya,,da sauri ta kalli BARIKI wacce take kokarin shiga mota,,da sauri tai wajen,, "Amaryar wa?bodyguard 1 yace ta Alhj,,sannan kiyi hankali kar wani abu ya faru anan,,dan ya tabbatar mana tsaron ta..taja tsaki" Dallah rufen baki,,nida Tsohuwar yar BARIKIN nan nake,,karon farko BARIKI ta kallo ta a wulakance,,"eh kin San ai Alalar Gero ce,wanda bai Iya ba ta kwabe masa,, tai mata wani kallon banza kan ta ce ya suja ta bata da lokacin ta.. Tuni suka ja suka bar amaryar Alhj baki sake,,magana 1 ta mata mai harcen damo,, ji tai tamkar ta kwala ihu,,a bainar jama'a an toya ta,,jiki a salibe tai mota,,bayan ta shiga ta kallo Bala"mey ka bata a Leda?uwar gidan ta kallo ta,, "kina da karfin hali Halima,,zaki kwace ne komai ya bata?tai kwafa," lalle Alhj yaso musu wulakanci,, har ya fifita wata akan su tun kan aure?uwar gidan ta kalle ta,, "ki bari muje gida muji dalili,,ko aure zaiyi,toh wlh bada wannan yar BARIKIN ba,,dan irin wayen nan suke daura ma hawan jini..tai kwafa.. Ana dire su a parlour suka tsaya,,yau daya suka zauna Neman mafita,," Yanxu Hajiya meye abin yi?ta kallo ta da mamaki,,dan rabon da ta kirata da Hajiya tun tana amarya,,lalle BARIKI mai sa ladabin dole.. Waya ta dauka,tace "Alhjn zamu kira,,yazo muji ta bakin shi,,ta girgiza mata kai" kar ki kira shi,,barshi yazo da kanshi,,ba tace BARIKI IYAWA bace?toh mu muyi amfani da damar mu ta Matan sa mu nuna mata kuran ta.. Tuni ta rada wa uwar gida abinda zasu mai in ya dawo..tuni aka manta da kishi aka hau Neman mafita. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/25, 1:32 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 13_Bai dawo ba sai kusan Tara na dare,tuni suka kara kulewa,, yana shiga ya gansu zaune a kujera 1 suna ta huci,,ba wanda yai wa magana yai dakin shi,,da sauri suka tsayar shi, Wai Alhj mai kake nufi?yaci mur, "danayi mey? "Kazo ka wuce ba ko magana, yace" ita sallamar ba magana bace?ko kun amsa?sukai shiru,yace"Ku bani waje..amaryar ta kara tare kofa"ai wlh sai ka fada mana wace Sa'a a gun ka da har ta fara shiga lamarin dangin ku,,yai mata wani kallo,, "Sa'a kuke son Sani? Ta kada kai tare da Rike kugu,,yai murmushi" itace wacce tasan na Gaji a barni na huta,,ita ke maraba daku a matsayin kishiyoyin ta da zata samu,,Sa'a, ta wuce tunanin ki a waje na,,ta tabe baki,, "wannan kai kasani, abu daya muka Sani, mudin Zaka auro wannan yar BARIKIN, toh fa tafiya zamuyi,, koh Hajiya? Ita dai uwar gida tsabar takaici ta kasa cewa komai,,yai murmushi, " zaku Iya yin komai, amma Sa'a kamar ta shigo ta gama,,Hajiyan ta tare shi"Alhj bafa zan zauna da Wannan kilakin ba wlh,,saboda tsabar wulakanci, Wai ita zaka fifita akan mu tun yanxu? Ya harde hannu"da akai mey?tai mai banza,,ya gyada kai kan yai daki,,amarya ta kallo uwar gida,,"Hajiya. Gidan su kawai zamu mu kaddamar mata,, ki duba tun yanxu mun zama bola?ta kada kai, "Allah ya kaimu,,. Washegari yana fita suna fita,direct gidan su Sa'a sukace driver ya kaisu,.zai musu suka hayaiyako mai,, tuni jiki na bari ya kaisu,,Suka karewa gidan kallo,nanne Wai gidan su ma,,ciki sukai,lokacin tana brush a gindin famfo,, da doguwar Riga ta bacci mai silik,da Maman ta suka fara cin karo,,da mamaki take kallon su, ganin ko sallama sun shigo gidan,,amaryar ce mai karfin halin tambayar "BARIKI fa??ta kuskure baki ta juyo rai hade,, suna hada ido suka ga ta bala'in yi musu kwarjini,,a jinin ta yake,,mudin kaso mata wulakanci indai kuka hada ido, toh sai dai ita ta sauke maka,Allah yai mata baiwar Kwarjini... da niyar nadar ta suka zo ko su ci mutuncin ta,,suka sau baki kallon ta,, mace kira kamar ita tai kanta?ji uban gashi da fagon wani guri?hmm lalle kam Sa'a ta wuce tunanin su,,tuni ta wayan ce wa tayi,tuni ta sau fuska lokacin da ta gane ko su waye su,,ta ajiye cup din tana kade brush tare da daukar mouth wash din,," Sannun Ku da zuwa Aunty,..Hajiyan ta kalli amarya, amarya ta kalli Hajiya.. Hee hee... BARIKI Ake fada muku,,IYAWA,, ta kallo mama,."ina taburmar nan?baki sake ta nuna mata kitchen,, ta tafi tana girgiza jiki,da kallo suma suka bita..ta dakko ta shimfida musu,,ta kallo su da murmushi,, "ya Ku zauna man,,tamkar wasu masu bin umarnin ta suka dawo,, ta koma daki ta sako hijab,.ta zauna," ina kwanan Ku Aunty?a ciki suka amsa,badan sun so ba,,Ta kallo Maman nata,"mama, baki nane fa,,Matan Alhj Muktar mai naci Dana ke baki lbr...Ba suba,hatta maman tata baki sake take kalle ta da sauri,, sukwa tuni suka gyara zama tare da sakar fuska,, tana ganin haka ta kada kai da murmushin mugun ta,, a ranta tana "woo ni BARIKI. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [6/2, 6:09 PM] Feenat Ja'afar: Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 14_Sai lokacin suka gaida Maman,.da mamakin su itama ta amsa,,ikon Allah, da ganin Matan da rashin mutunci suka zo gidan,,amma dubi Sa'a cikin seconds da bai wuce 3 ba har ta shasu,,kai,al'amarin yarinyar nan ita kanta tsoro yake bata,,Hausa sunce Wai Barewa bata gudu danta yai rarrafe,,toh gaskiya a kanta ta Musa,,dan ta ko'ina halin ta bai kama da na Sa'a ba,,da de fadeela ce,,sai dai in ta tuno ance kowacce mace da irin tata kissar a ake haifar ta,,. Kai ta kada musu,,ta kallo Maman,,tai mata halamar ta dan basu waje,,ta gyada kai, "ni zan fita ma,zan leka gidan gaisuwar nan da baban Ku yaje dazun,, ta kada" sai kin dawo,, ganan abincin ki a flaks,fadeela tayi makaranta.. Ta dawo gun su,"sai anjiman Ku, Ku gaida gida,,suka washe baki,"a dawo lfy,,Kanta fita Sa'a ta tashi ta dakko musu drinks a fridge din tsakar gidan,,da cups, ta zauna,,"Bissmillahn Ku fa,.suka kalle ta., "anya kuwa,sanyi da safe,tai murmushi,"toh ya akai? nasan da magana a bakin Ku,, sukai shiru,,tai murmushi,,zama ta gyara kamar mai Tahiya,ta dafa kafafun su,," am Aunty,, bari na fada muku Gaskiya,, wlh ba son Alhj nake ba,,en kuma Ku gode Allah,, shidai yana matukar sona,,sai dai ina lallaba shine saboda abu 1,,ta nuno su da hannu,, "saboda Ku,,dan kune matsalar shi,,kuma nayi alkawarin taimakon shi,,amaryar ta tabe baki,, ta kalle ta,," amma kun San mey? Uwar gida ta girgiza kai,,"mijin Ku na kaunar Ku,,amma kun tsaya kishi,,Baku da aiki sai tada mishi hankali,, ni fa mata na bani mamaki matuka,,. Kuma musamman Matan mai arziki, a gidan shi anfi tashin hankali,, kufa kalle Ku,, da girman Ku,,ai wlh kun wuce wannan gurin,,Ku tsaya kuyi kishi akan mijin Ku,. Kwatan kwacin Matan Annabi (S A W),,Ku kanku zaku dinga rage jin haushin juna da saukaka kishin,,nan tai ta musu,tare da sanar su Alhj ya sanar ta kom,, kuma tana tausayin shi Gaskiya.. "Sai dai abu 1 zan Iya muku,,suka kallo ta tare da sauke ajiyar zuciya,,Ku gyara tsakanin Ku,,Ku zauna lfy,,idan har kukai haka,shi kan shi Alhjn zaiji aurena ya fita a ranshi,kunga kun taimake ni,, kun taimaki Alhaji,. Sannan kun taimaki kanku.. Ni kuma zanji da sauran,, tunda Alhaji ya taba fada min,mudin mace bata son shi ta furta bazai aure ta dole ba.. Suka sauke ajiyar zuciya,, amarya tace. "Hajiya,wlh sai yanxu na gano matsalar gidan mu,,Sa'adatu tai magana mai kyau,, ya kamata mu hada kai koba auren nan,,kuma dama chan matsalar taki ce,,da sauri ta kallo ta" matsalar ki dai,,ni nace ki shigo da fetsara? tace"Toh ai kema ke kika yadda girman ki,,.tuni magana zata dawo fada Sa'a ta tsayar su,, "kunga irin ta ai,,na lura duk din kune Baku hakuri,, ni dai in Baku gyara hali ba,wlh zana yarda da Alhaji ya turo ne kawai,koda bana son shi,,.Amarya ta kallo ta" ke kuma sai an gama magana ki sako wata,,ai munce munji,,ta daga kafada.. "Ku dauka ni banni matsala,, Yanxu matsalar ta Ku ce kuda mijin Ku,,in kunji bayani na kun gyara kuga mai kyau,,in kun cigaba ta kwabe muku..toh wlh Ku zargi kanku,ta mike,"zan shiga wanka,,suma suka mike.." Mun tafi, sai kin jimu,,tai musu yake,"a gaida gida,,duk jiki yai sanyi suka fice.. Dai dai fadeela ta dawo,,ta kare musu kallo har suka fita kan ta dawo kan Sa'a.., "su kuma daga ina kika yayimo su?ta tabe baki,," Wai su nan da rashin mutunci suka zo,,any way,naga sun russuna,,aikina zai zo da sauki da halama.. "So nake a siyasar nan nai motar kaina a wajen Alhajin nan,,fadeela ta zaro ido" mota??tai murmushi, "karamar Alhaki ba,,ke Wai da ina sakar wa kana nan Yan iskan Alhazan nan da yanxu ina da motoci wlh,,yanxu haka ina da alkawarin gida a kasa..fadeela ta kada kai" ai ni tsoro kike bani,,wlh wannan ba Sana'a bace Sa'a,, ina gudun kar wataran ki hadu da dai dai ke,ko ki samu mai lakada miki duka..tai mata wani kallo "duka?mtsww wlh kina ban haushi,,ko kin manta duk inda zansa kafa tare nake da sojojin daba?? Ta waro ido.." Daba Sa'a? Tai murmushi "lalle da sauran ki fadeela,, kin ganni nan.. Ta nuna kanta" wlh na Iya taku na,,duk inda nake akwai masu take min baya tun daga safe har yamma,.a lokacin yara su karbe,,kamar yadda ake biyan ma'aikata a wata,nima haka nake biyan su..kuma nasan ba wanda ya sani..kema sai yanxun..ta kada mata kai.. "Shi yasa nace tsoron ki nake ji nima.. Sa'a akwai masu mugun nufi,,masu jefo asiri..da sauri ta daga mata hannu" ke ni ban son jafa'i,, na rike Allah, babu wanda ya isa ya min komai wlh.. Tuni ta hau jaraba tai bandaki.. Fadeela ta girgiza kai.. Sa'a bazata gane ba,, amma tunda ta saka Allah, ta gama komai.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/26, 2:12 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 15_Sai bayan la'asar Alhaji ya koma gida,,yasan da zuwan Matan shi zuwa gidan su BARIKI a bakin Bala driver,, sai dai da mamakin shi da ya shigo gidan An hadu da yara ana kallon Namamajo ana ta cin dariya,,kowacce taci Ado,tunda yake,abinda bai taba gani ba kenan a gidan shi anyi,,Wai a hadu,uwar gida da ya'yan ta da amarya da Ya'yan ta a waje daya..tab lalle ya fara ganin sauyi,,dan Babban burin shi dama Matan su hada kai, ya samu ya'yan shi ma su hada,,amma ina,ya kasa tsawan shekara 6,.sai gashi a abinda baifi kwana 3 ba BARIKI ta fara saita gidan shi,,toh ita kwa mey ta fada musu haka?da wani harshe tai musu magana wanda shi baiyi ba?? Ya kada kai yai sallama,, da fara'a suka amsa yaran suka taho da gudu mishi sannu da zuwa,tare da karbar kayan hannun shi suka ajiye gaban iyayen,,.Matan suma suka mai,ya amsa da kyar,,dan dole ya ga sauyawar su koba yau ba,,yai daki,,amarya ta kallo Hajiyan,, "mu bishi muji.. Suka ran kaya daki,,yana kokarin cire babbar Riga suka karaso,.karba sukai dukan su suna cire mishi,,ya tsaya baki sake yana kallon su,, Uwar gida tai murmushi," Alhaji muna fa sannu da zuwa,.ya kalle su tukun ya tabe baki,, "Ku Wai nan campaign kuke ne komai?suka kalli juna" name Alhj? Yai murmushi "na karna auri Sa'a,, zasui magana ya tsayar su,, " Ba abunda zai hanani auren Sa'a in fada muku,.gobe ma za'a kai kayan tambaya.. Da dariya suka fashe mishi,harda tafawa., tuni ya fara muzurai,, kadde fa sunyi wa yarinyar mutane wani abu??suka kallo shi, "Na BARIKI manya,,inji amarya,kai kace mana tusa mata kanka kake bamu Sani ba? Ashe ma ba son ka ake ba.. Ya bata rai" inji wa?suka hada baki"BARIKI.. Yai murmushi,,"eh a haka zan aure ta,, indai zata bani farin ciki a gida na,, ya wuce bandaki ya barsu tsaye,,zama sukai jiran ya fito.."aha Wai Baku tafi bane?? Suka kalle shi,, uwar gida tai gyaran murya.. "Alhaji,, ya kallo ta" eheem,.ta gyara zama"wlh ko ba aure mun gyara zaman mu,, kuma koda aure baza mu saba ba,,kai hakuri, munsan mun bata ma a baya,, amma wlh gaba bazai kara faruwa ba,,kallon ta kawai yake ya harde hannu,,tunda suke.basu taba sanar shi haka ba,,. Amarya ce ta katse shi,. "Nifa dan Allah nayi,,wlh kama daina cewa dan zaka auro wata BARIKI.. Ehe,.inma ka auro ta in baka Sani ba Toh yanxu ka Sani,.uwar gida sai daga mata hannu take halamar tai shiru,amma ina,dan fa ita yar gaba gaba ce,, tace" in baka Sani ba ka Sani"MATA UKU.. GOBARA(Na Mrs Jabo)Ce,,ehe,,gwara ma kai Hudu,.atoh,. yace "kun gama??uwar gida ta kada kai,"toh koh aman Wuta ne saina auro Sa'a., tashi tai" Hajiya mu tafi,,kai kuma Allah ya taimake ka..yace"Amin,, Suna fita uwar gida tace"Amma kin kwafsa mana fa,,tai kicin kicin.."Hajiya yi hakuri, wlh haushi ya bani,, kamar muna ziga shi.. Yana jiyo su ta daki,,.. Da dare ya samu BARIKI.. Sai murna yake,yau kam ta biya shi,,yaga abinda bai taba gani ba a gidan shi,,tai murmushi,"toh Allah yasa sun gyara kenan,.yace"Amin,. Amma Sa'a, nifa da gaske nake son ki fa,, wlh jiya da tunanin ki nai bacci..ta kalle shi tare da yin fari da ido.."Aiya Alhaji,, ina da tsayayye, sai dai baya kasar nan,PHDn shi in ya dawo muna da alkawarin aure..yai murmushi "anya Sa'a? Ya kada kai" Any way,, yanxu dai bamu tsadan ce ba..nawa kike ga zan baki?ta rausayar da ido,, "Alhaji masu gari,,Ashe ana cini ki kuma daku?yai murmushi, itama tai,..su BARIKI anso yaudara,,, tace" Ai zamanin siyasar yanxu da abunda ke hannun Ku manya ake kyauta ba cini ki ba.. Yanxu muna da kamar Ku a centern nan amma Bariki bata ko motar hawa..bare na samu ta raly..ta kanne mai ido 1..tuni ya hau washe baki,, lalle BARIKI,harda ke a yan campaign din namu Ashe??tace "kai,sosai, ai partn mu daya..tuni ta hau tsara shi tana kara kwadaita mishi kujerar da yake nema ta senator.. Dan dadi bai San ya mata alkawarin mota ba indai ya hau mulki.. Kamar gaske ta kallo shi da mamaki baki sake.." Alhj daga wasa??yai murmushi.."karki damu.,ai irin ku muke nema,,bare gaki da mutane,.indai kuka mana campaign yan partn mu sukai jama'a zakiyi mota..inkwa banci ba,,akwai wani karamin gida na a bayan layin nan,daki 2 ne,.na mallaka miki kodan saita min iyali da kikai..Tuni tace"Auxubillah, In Allah ya yarda ma kaci ka gama..yai murmushi"Toh amin sa a,,"Allah dai ya ja mana zamanin Ku Alhaji,, ni kuwa indai haka ne,kar kaji komai, a duk arear nan kune zakui wining..ko baku sau kaya ba..yace "A zama musau kaya.. Kai a hannun ki ma zai sauka,ta dafe kirji. " Allah Alhaji?ya gyada kai.,"Alkawari ne..tai murmushi.. Bai bar wajen ba sai 9 da 15.. Da haka auren Alhj ya tabalbal ce,,in kaje gidan shi gwanin sha'awa.. Dai dai da abinci tare suke,,duk sun fatattaki qawayen su yan ziga.. Suda Kansu sunji dadin zaman nasu..yadai wayance a cewar ya fasa auren Sa'a dan bata son shi..suka hau kuwa. Sa'a ta shiga makaranta, inda take karantar Mass communications., lalle tana da sha'awar hakan tun ba yau ba,, kamar yadda Alhaji ya alkarwan ta lokacin campaign nayi saiga katuwar mota a kofar gidan su Sa'a da sassafe,,lokacin tana ta aikin bacci,,baban su ya shigo dakin nata.."Ke Sa'a,.. Sa'a.. Ta tashi a kan sallaya tana mistsike ido.."Naam baba,.ina kwana..yace"biyoni tukunna.. Tuni ta ware.."Baba Lfy?ya fita tana biyo shi,, turus tai a kofar daki,,ganin yadda ake shigo da kaya..su fridge kana na,keken dinki,keken saka..turaman Attamfa.. Buhu buhun su shinkafa da sugar da sauran tarkacen kayan campaign... Tace "Malam daga ina haka?ya kallo ta. " yauwa da drivern mai gida muka zo..Alhaji Muktar.. Shi yace a kawo miki..tuni ta sau baki,,har ga Allah bata dauki zancen da mahimmanci ba,asali ma ta manta da zancen tana ta aikin karatun ta..oh baki bai ba,, yanxu taga uban da zai koya mata campaign,,ita da ko zabe bata taba fita ba bare campaign...tab shiga 3,kishiya maiya,, Miji Barawo.. Baban ne ya katse ta, "mey kenan haka ke nufi Sa'a?? Ta kallo shi ta fara inda inda..ya dakatar ta" Kinsan bazan taba yarda da wannan halin ba koh? Siyasa a gida na?kuma Wai kece shugaba? mamata mey kike son zama da baki zama ba?har gida gare ki fa,,ta kallo shi,ta marai rai ce "Baba wlh ban zata da gaske yake ba,, amma bari zan mishi magana.. Amma koni baba mey ya kaini siyasa anan garin..kai hakuri.. Mama da ta fito itama ta sau baki..ganin uban kaya a gida..ya kada kai" ni zan fita.. Ta dan duka"a dawo lfy Baba.. Yai murmushi, "Amin,Allah muku albarka.. tai murmushi" Amin Baba..ya kallo mama.. Mu min tafi..da baki take nuno mata Wai ta raka shi zaure..Maman ta mata dakuwa "yar kare..kai Sa'a.. Allah shirye ki.. Komai zage wa take ta nunawa uwar ta..ko daki baba ya shiga in suna waje ta dinga," mama kije man,,inkwa zai fita ta dinga sai ta raka baba zaure..BARIKI Duniya...Lol. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [6/2, 6:19 PM] Feenat Ja'afar: [12/26, 11:40 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 16_Daki ta shiga ta kunna waya,kan ta danna calling.. "BARIKI a Baku naku daban,,tai murmushi, "Alhaji ina kwana," lfy lau,. Ya karatu? tace "Alhamdulillah, " ya kaya sun iso koh?ta kada kai,"sun iso,,Sai dai fa Alhaji da matsala,, yace"matsalar mey Sa'a?koh sunyi kadan ne a karo miki?Tai Jim"Alhaji ba haka ba ne,,ni fa Alhj da wasa nake,,wlh ban taba harkar siyasa ba,,kaga kar nazo nai muku ba dai dai ba..ya gyada kai,, "Bari zanzo anjima da yamma,,ta kada kai" Ok,,bye.. Tai ajiyar zuciya.. Bata Iya cuta ba,bare ace ta Saida tace tai campaign din,,gwara yazo yasan nayi dasu.. Da misalin karfe 5 yazo,,bayan sun gaisa ya dau waya ya kira wata mata tare da mata kwatancen inda yake,,ba'a jima ba tazo a motar ta ita da wata yar unguwar yar siyasa,,Ya gaba tar mata dasu,"sune mataimakan ki,,ganan shu gabar Ku ta unguwar nan duka,,zata tsara miki yadda ake komai,,karki damu,ba Wai za'a fita dake campaign bane fa,,I trust you ne kawai, so ki rike kayan a gidan nan,,naki kawai ki bawa wanda kika tabbatar bata da karbi,kuma tana da kuri'a,sannan kuma zata dangwala mana,, ta kada kai "Ok,nagode Alhaji,, ya Ciro kudi bandir 3,yaba Sa'a 1 mai motar 2,,dakyar in zamu kara haduwa,.. Dai dai nan su Aminu sunxo wuce wa suka tsaya,, suka fito tana ganin su ta hau fara'a, tai sallama da Alhaji,, "Oh Aminu manyan kasa,.yaushe a gari??oh sorry Assalam Alaikum,, yai murmushi" Walaikum salam,," BARIKI manya,.da sauri abokin nashi ya dago Tare da sake kallon ta,. Da tunda yai arba da ita yaji zuciyar shi ta tsanan ta bugawa,. Yanxun ana kiran ta da BARIKI yaji wani damm..yai tunanin ko ya dace da DREAM GIRL (na Deeja Abdull)din shi,,dan yana son mace mai Aji, kwarkwasa, da iyayi da kuma addini.. But tashin farko a kira ta da BARIKI? Lalle bata kwarai bace.. Katse shi tai"ina yini.."BARIKI sai kin jimu,Alhaji ya bamu numbern ki,,ta kada musu kai tare da dagawa Alhaji hannu.. Tuni abokin Aminu ya kara kulewa,.dan da ganin dayar kasan muguwar yar BARIKIN asali ce,,gaisuwar da bai amsa ba kenan yaci mur.,tamkar bai taba dariya ba,, itama bata bi ta kanshi ba ta koma ga Aminu,, "Lalle BARIKI, tana fa kai miki mutuniyar nan,harda Su Alhaji Muktar yau a gidan nan??,,tai murmushi karo na 2 ta kallo abokin nashi,, tuni ya dauke kai,,ta tabe baki,," wlh aiki na mishi,kadai gane,kuma sai ta rufta dani,, ta wani marai rai ce mishi,,n wlh i don't know what do?? Ganin yadda take wani marai rai ta ta kara bawa abokin nashi haushi,. Ya kallo Aminu, ka saman a mota,,ya kallo ta ya watsar tare da harara yai gaba,,take itama ta dauke shi ta yar,,harda dan tsakin ta kadan,,"ban San ya zanyi da baba ba,,Aminu daga wasa mutumin nan ya kawo min kayan campaign,, yanxu fisabilillahi ina ni ina siyasa 4 God sake,,dube ni fa,,ta fara gyara Riga, dama doguwar Riga ce a jikin ta sai mayafi data daura,,Aminu yai murmushi, "Yanxu da abinda zai gagare ki dama??ta kalle shi,," no ka gane, wannan da ban ne,en kasan bansan shudanya da kowa,.Shima wannan lallaba shi nake ya samu yaci ya sallame ni da mota..ya waro ido "mota Sa'a? Ta kada kai tana mishi wani feffekara,," hasko ni Kaidai,,"kuma kin yadda?ta kada kai "na yarda,.yai murmushi, "yan siyasa fa basu alkawari, da sunci suke manta da kai," No wlh wannan na daban ne...horn suka jiyo,,ya kallo ta "toh sai zuwa na 2,.tace" ina Qawata?ya kada kai,"chan muka nufa ai...tai murmushi, "da kyau..yace" au abokina ne,,tun satin chan ya dawo,bamu hadu ba sai yau,nasan baki san shi ba..munxo wuce wa na ganki nace mu tsaya mu gaisa..ta tabe baki,,Da" ganin shi dan raini ne wlh,.kai hakuri fa,atoh.. Yai murmushi,ai afuwa? Ke dai sai nazo karbar kaso na,ta raki shi har bakin motar.."Ok,see yaa,.ta dago mishi yatsun ta,, yai kwafa,,Aminu ya kallo shi,, "ya dai? Ya tabe baki"Amma dai yarinyar nan yar raini ce daga ganin ta? Take Aminu ya tariyo itama nata zancen" Da ganin shi dan raini ne..sai yai dariya,,.ya kallo shi tare da Harar shi"dariya na baka koh?ba kaga Harar da take min bane?ya kada kai, "na gani,,amma kai ka fara mata ai,,Sa'a na San tsaf,in an mata saita rama. Baka Santa bane,,amma Sa'a,, hmm ta kece raini ce wlh,,jin shi kawai yake, amma ya kasa tan kawa,, take yaji haushin yarinyar ya dadu,,wato har a kira ka da sunan BARIKI alfari ne ka amsa?? Mtsww yai tsaki,,Aminu ya kallo shi,," ya akai kuma? Indai Sa'a ce yi hakuri, abar zancen ta. "Yanxu muje na kaika wajen Ummi,kaga hadaddiyar Babyn da zan aura,,.ya kada kai, shikam bai fiya magana ba,,Aminu ne mai surutun tsiya. Ummi ta fito itama duk kusan kiwon Sa'a ne,. Dan tare suke schl yanxun,, itama akwai iyayi,sai dai bata kai Sa'an ba.." ya gaba tar mata da abokin shi Hafeez, da fara'ar ta tace"a yau kam naga Hafeez,, yau she a kasar?yai murmushi, satin chan.. Ya shirye shirye?biki ya karato,.ta kalli Aminu ta sunkuyar da kai kasa tana murmushi,.a toh da dan dama dama,tunda ita tana da kunya,a ganin shi sun ban banta da Sa'a Qawar ta, dan shi kam yana son mace mai kunya,,. Anyi siyasa lfy,dakyar baba yabar ta a gidan ma,,Allah cikin ikon shi Su Alhj Muktar sunci zabe,Shima ya samu hawa kujerar senator,, randa za ai walima har BARIKI Matan Alhj suka gaiyato,,.sai dai yau har wata da hawa kujerar senator ba mota ba lbrn ta,har ta fidda tsammani,,. Yau bikin su Aminu saura wata 3,.su Sa'a kirjin biki,,taje gidan su Ummi zatai mata rakiya siyayya super market,,. Suna tsaka da zabe zabe,tayi gefen cosmetics tana zaba Ummi na bata basket tana zubawa, sai dariya suke dirka,, gaba daya hankalin ta yayi kan zancen Ummi,, ta mika hannu zata dau turare bata kula da mutum a tsugune zai dau abuba takai hannu,,da tsautsayi,gwan gwanin turaren role on na nevea ya fado kanshi yana dagowa,, da sauri ta sa hannu a baki kan tace" am really sorry pleas..tai shiru,take ta hade rai, shi kwa ba tare da ya dago ba yace"No,it's Ok,.."Sa'a meya far..jin an ambaci sunan wace yake haushi,,tuni Shima ya hade rai"kina kallon ina kike jifo min abu kai,,tuni itama ta kankan ce ido,,"ina kallon ka ne,,yai tsaki, "au,haka ma zaki ce? Ta tabe baki,, zata wuce yasha gaban ta,, " na fiskanci yar rainin hankali ce ke,,inba haka ba..."Hafeez,, mey ya faru?Sa'a? Tuni ya ware,,"a Ummi,,ta kalle su duka"Naam,Hafeez, ya akai ne?meya faru,,yai murmushi, "no ba komai,,ya Aboki na,, Sa'a tace" uhmm,ta wuce gaba,,ya bita da kallo,."Ummi zan wuce, koh kin gama?tace"eh mun gama,bari mu biya,,suka jera suka je wajen biya,,ya ajiye nashi,,kan ya kalli wajen mai kirgen"nawa ne kudin nasu?ta kalli Sa'a "tare kuke har ita,. Ta kallo ta" wa?Allah sauka,hanyar jirgi daban ta mota daban,, tana mai wani kallon 9 saura kwata,tuni ya kule,,yace"da ke zan biya wa?ya kada kai, "u must be jocking,, yai mata wani kallon raini,, zata tanka Ummi ta sako baki" Wai kun San juna ne hala? By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/27, 12:34 AM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 17_Ta maka mishi harara kan ta koma kan mai kirge,,"ki fadan kudi na ko na bar muku kayan Ku,,mai kirge tai murmushi,, ganin fadan nasu abin dariya,,ta fada mata kan ta kallo Hafeez Shima ta fada mishi,, ta dakko kudi ta bata,. Ta suri kayan ta zatai gaba,mai kirgen kudi tace"hala dai fadan nan na masoya ne?? Ya kallo ta da sauri kan ya kalli Sa'an da ta juyo "dawa? da waccen ne masoya,,?yaja tsaki." Dan Allah ban chanji na kan ki Sani amai,,tuni ta kullo ta karaso.,ka kallen da kyau,,kasan ni ba irin Matar Ku bace,,ke kuma ki Iya bakin ki, dan he's not my type.. Ummi da tsabar takaici ya ishe ta,,ga shi har sun soma tada musu jama'a, tuni tai waje taja Sa'a,, da sai bambami take,,ya fito kan ya kalli Ummin "zo mu wuce man,,ta kallo sa'a" kiyi hakuri kizo ya sauke mu,,"kut,. Ummi,jeki,jeki kawai, na gode da rakiya,. Amma bazan shiga wannan akwarabar motar ba,,muka kalli mota nida Hauwa,,Lalle Sa'a, kin so kan ki,,shikam dariya ma ta bashi,, "Ummi,ki shigo kawai mu tafi,,ta kalle shi, ta kalli Sa'a, in ta shiga ta shiga 3 wajen Sa'a, ganin yadda take cika da batsewa,,." Kai hakuri Hafeez, inna barta ba dadi,ya daga kafada.."sai gani na 2..sukai sallama ta dawo gun Sa'a,, yazo zai wuce ya zuge glass,, "sai a hau ta haya,.tai mai gwalo" eh dai baza a shiga ba,.ya sauke glass ya wuce.. Tace"a sauka da nauyi..Ummi ta kallo ta,, "Sa'a, lfyr ki kuwa yau?meye ya hada ki da haffex har haka da zafi?wannan ai fadan yara ne wlh,..ta dallah mata harara," Dallah rufen baki kema,,Wai ke ga dadi saurayi,,. "Nan har hakuri na bashi,,ta shagwabe fuska kamar mai shirin kuka.." Wayyo haushi,, da nasan shine,da duk kayan wajen zan rikito mishi aka,,Ummi ta kallo ta lokacin tana tsaida mai taxi.."Toh naji muje,,zanji komai wajen Aminu ai,,amma dai kun bar abin fada, kuma shagon zuwan kine kinsan?tace"Toh ina ruwa na,, inna zo kar su siyar min..ta bude mota ta shiga.. Har akaje gida bambami take.. Kai ba wanda ta taba chachar baki dashi a girman ta sai wannan,,. Da dare akace ana sallama da Sa'a, ta kallo yaron da masifa, kace"Baza'a zo ba,, mama da fadeela suka kalle ta,,tun dazo take dacin rai,,yaro yace"kai,Aunty Sa'a,, dan bakiga waye bane, tace"waye,,"senator fa,. Da sauri ta zabura.."Khali ban son karya fa..yace"ba kince ince bazaki zo ba,ta harare shi,"dallah da wasa nake,,maza kace ina zuwa,gobe kazo in baka chocolate.., amma kamin nan, da mota nawa yazo??yace "2,ta doka tsalle ta dire," wayyo niii...tuni ya hau zigata kamar yadda suka saba yi mata a unguwa.."in kin ganta wata karama mey kyau,,ko pikanto naji ana ce mata..,tace " Toh naji,..da sauri tai daki,ta yayumo gyale,,ta gyara fuska.. Mama da fadeela yan kallo..fara'a kamar gonar audiga tace"mama bari na leka..kai kawai ta daga mata..Tana zuwa zaure ta nutsu,,ta dan leko,,ya hakimce a wata dalleliyar bakar jeep,ga wata karama a gefe,yana ganin ta ya hau fara'a, ta karaso, "badai Alhaji nake ga ba?yai murmushi, "BARIKI da kanta,,tai murmushi kan suka gaisa,,yadda bata nuna mai komai ba yaji dadi,.ko irin zalamar nan.." Ai hakuri an jimu shiru,, tai murmushi, "Ku yanxu aikun shiga sahun uziri,,Yace" haka ne,kika ji bayani shiru.?tai murmushi.. "Alhaji name fa?yai murmushi, wato sai an nuna mai hali?hannu yasa a aljihu,," Ga nan alkawarin ki,tun dazu take jiran ki,nine yanxu na iso,kan wanda ya kawo ya tafi,,baki sake take kallon shi kamar gaske,,"Wai Alhaji da gaske?ya sha mur,"na taba miki wasa? mu kullin ta karba,baki sake take kallon key in,,"Alhaji da wace kalma zan gode maka?yai murmushi.. "Sa'adatu, gode Allah kawai,,sai dai har yanxun na kasa fidda ki a raina,,tun ranar chan Dana ga saurayin ki yazo na saddaqar,, ta kada kai" Aiya Alhaji,,kai hakuri,ya girgiza mata kai,"no karki damu,,kin burge ni da kika rike mishi alkawari,, kodan hakan nima yasa na cika miki naki alkawarin, dan ina son mutum mai rike alkawari da mahimmanci,,. Sun dan jima sukai sallama ya tafi..tana gani yai kwana ta zufa da gudu gida.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/27, 12:05 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 18_"Wayyo Allah na, Mama, mama,tun a zaure take kwada mata kira,,da sauri suka mike dan sun tsorata,, tana shiga ta rukunkume Maman,,"wayyo Allah mama maidani ciki,, wayyo Duniya sabuwa.. Mama ta dago ta,,"Sa'a murnar meye wannan haka? Dagowa tai harda hawayen farin ciki,, ta miko mata mukulli tana tsalle, "mama mota,,wallahi mota nayi sabuwa dau a ledar ta,,da sauri Maman ta kai hannu baki ta rufe" Sa'adatu mota??da sauri tace "mama Ku leko kuga wlh,, fadeela da mama suka bita a baya,,ganin motar yasa mama kusan zube wa,,ita kam shikenan karyar ta ta kare,,acikin 2 dole da daya,,ko dai Sa'a ta yar da mutuncin ta? Ko kuma a yayime ya yimen ta ta kwaso dan yankan kai,,ganin Maman tayi shiru yasa ta dauka ko yadda ne batai ba, da sauri tace "mam ga nan takaddun malkakar ta in baki yarda ba.. Kai ta girgiza mata,. Kan tace"muje gida Sa'a,, ta kallo fadeela da sai zaga motar take da murna,,suka ran kaya gida,,dakin su taga Maman tayi suka bita chan,,ta zauna a kan gado"mama lfy?Maman ta sauke ajiyar zuciya, kan ta kallo Sa'an "Ku zauna ni kam,,suka zauna, ta sake kallon su" Sa'a, ki dubi Allah ki fadan Gaskiya, ta waro ido "wlh mama da gaske nake fa,ta girgiza kai, " Sa'a ba wannan ba,, kin tabbatar ba mutuncin ki kika yar aka baki mota ba koh?da sauri tace"Subhanallah mama,,wlh Tallahi alkawari yamin in sunci siyasa zai sai min mota,,da akwai aikin da na mishi,wlh mama,,ta girgiza kai, "yanxu Sa'a bama wannan ba, mey zan cewa Baban Ku in yazo?itama sai yanxun ta tuna da baban su,tai shiru,,ana haka sukaji sallamar shi,kowa yai tsam,daga inda yake y tsaya a kofar,a tunanin shi ko bako sukai,,Maman tace ya shigo ba kowa,,ya bude labule" lfy kukai tsumu haka?motar waye a kofar gida?ya zauna suna mishi sannu da zuwa,,kowa sa kallon juna yake,sai da ya kara tambaya "munyi baki ne? tukun fadeela tace" Baba ta Sa'a ce,, tuni ya dauke wuta,,ya kallo Sa'an,, "Toh a ina kuma ta samo mota? Sukai shiru,Yace" dake nake,ta hau inda inda,, "umm..amm,ba..bani akai fa Baba, ta wani marai rai ce mishi kamar zatai kuka,, yai murmushi" nasan wataran sai sun fashe dake Sa'adatu,, ta zaro ido "Mey za'a su fanshe dani Baba?? Ya sake murmushin takaici kan ya kallo Maman sun,," Bissmillah man,,ya tashi ya fita,, mama ma ta bishi,ta kallo fadeela. "Mey fanshe wa Wai take nufi fadeela? Wai kuna nufin haka banza ba'a kyauta sai anci moriyar ka?fadeela ta kada mata kai" ana yi Sa'a,, amma ba irin wannan ba,,fisabilillahi a wannan marar waye zai baka kyautar mota haka kawai?? Ta kada kai, "Ok na gane,,wato Baku San ma abunda zan Iya¿da wanda bazan Iya ba koh?,, tashi tai tai waje,,a bakin kofa ta tsaya tana sallama,, Maman tace ta shigo,,ta kalle su duk sun wani cirko cirko.. Ita abun ma dariya ya fara bata,,"ni kam dan Allah Baku yarda dani bane baba? Yai mata dakuwa" ungo naki,,yar kota,, kimin bayani ya akai kika samu motar nan mai tsada haka,tace "Baba bafa abun mamaki bane dan dan siyasa yai kyautar mota,, wlh ba abunda akai,,kuma bari na kira a gaban ka kaji komai,. Taje ta dakko waya,,ta bugawa Alhaji tasa a hands free,,"Assalam Alaikum.. ya akai Sa'a,, ta gyara murya,,dama godiya na bugo na maka,,yai murmushi, " kinfi gaban nan Sa'a, ina son halin rike alkawari,, tace"Wlh ban San haka kawai za'a Iya min kyautar mota sukutum ba ba tare da nayi wani aiki ba,,yai dariya,"ke kwa kikai aiki,,tunda kin gyara min Matan gida na,, sannan kun tafiyar da abun campaign bisa amana,kar ki damu,,.yi wa kai ne,,sai dai ina fatan baki samu matsala a gida ba??ta kalli su baba,,"Alhaji na samu,,dan basu yadda da wannan kyautar ba ta fisabilillahi,,Yace "kar ki damu,gobe da dare zan samu baban naki da maganar,, tace" aa ba sai kazo ba,gashi a kusa. Baban ya karba,ya mishi bayani,shi saboda Allah yai,da kuma ta gyara tsakanin iyalin shi,.sannan shi wannan bai dauke ta a wata kyauta da Sa'a ta fi karfi ba..dakyar ya yarda da Sa'a ta rike motar,da sharadin babu gantali sosai a mota.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/27, 2:01 PM] Feenat Ja'afar. BARIKI...IYAWA 19_Lalle Sa'a, yarsu tana daga cikin wayan da suka zo Duniya cikin Sa'a,, fatan shi Allah ya cigaba da kare mishi Sa'adatun shi..Lalle kam taci sunan masu sunan nata "SA'ADATU SA'AR MATA..(na Damary en Feenat).. Washegari gidan su Ummi aka fara sauka,, dan tunda ta sa rai da mota tai joining class inda ake training, cikin 4 days kwa ta Iya mota,,da mamakin ta data shiga taji tana zugar ta..." Wayyo dadi..da gudu ta shiga gidan su Ummi, ba ko sallama "Qawata...Ummi.,woo fito kisha kallo..ta fito daga kitchen da mamakin sammakon Sa'a yau,,,dan sai 9 suke da lectures,,suka ci karo" Sa'a,. Lfy?maman Ummin ma ta fito,,jin sun wani kwalla musu ihu a cikin gida.."Lfyn Ku kuwa yaran?ina ai har sunyi waje,.ta girgiza kai "Allah ka shiryi Sa'a da Ummi,.. Tai kitchen dan duba abinda Ummin ta bari a wuta..da karadi suka shigo gidan"kai shegiyar gari..kin Faso mu da yawa,yau dole mu tada kura a schl.. "Duk dan uban da bai tayamu celebration ba bamu bashi,..suka kyalkyala dariya., mama ta fito,," zanga ranar da zakuyi hankali yaran nan.. Suka kallo ta,kan ta gaida ta, tace"oh Wai murnar ta meye wannan? Da sauri Ummi tace"Mama mota fa mukai?wanda zai aure ta senator nan ne ya siya mata..da sauri Sa'a ta kallo ta, sai ta kanne mata ido, "tace mama karya take wlh,,ni saboda Allah ya ban dan na mishi campaign din partn su..ta kallo Ummi, " kullum sai na ce miki ban son karya,,ta kalli mama"mama nasan kin yarda dani tamkar wacce ta Haifa ko? Maman ta kada kai, ta kallo Ummi tare da Harar ta"ni zuba mana abinci in kin gama,,ta kalli mama tare da mata murmushi.. Sukai kitchen. Tuni karya ta karu wajen Sa'a,, ansa bikin fadeela itama,,tuni suka hau shirye shiryen biki,.za'a ai nata kan nasu Ummi,, Ranar ta fito a gida, tabi layin su Aminu a kafa sukaci karo dashi,,da abokin shi,, tuni ta hade rai, Shima yana ganin ta ya hade rai yaja ya tsaya,,tai mai wani kallo kan ta dawo kan Aminu, "angon mu,,ya akai? Yai murmushi bayan ya kare musu kallo duka,," lfy lau,, yau ina motar na ganki a kasa?ta yatsine fuska,, tana chan gidan da ake ajiye ta,, Da sauri Hafeez ya kallo su,ta maka mishi harara tare da kawar da kai.. Duk yana kallon su Aminu.. Hafeez yai dan tsaki,,"malam kazo mu wuce ni,,ta tabe baki "ai ni ban tsayar da wani ba anan., ta murguda baki ba tare da ta kalle shi ba,,ya kalli layin yaga ba jama'a kan ya dawo kanta" dallah rufen baki a wajen,,ke har kin kai ki tsayar ni da?.tuni ta kankance ido ta nuno shi da hannu "kar ka kara ce min dallah chan..ya zaburo kamar mai jira," ance dallah din,,mey zakiyi?ta matso itama"kaima Dallah chan toh,,Aminu mai zai inba dariya ba,,Bai san mey yasa jinin su bai hadu da juna ba,tun haduwar su ta farko,,kuma yasan duk din su ba masu son fada da jama'a bane.."sarkin yan tusa kai a mutum, ban damu da kai ba ka bi ka damu dani,yai murmushi "ke a fada miki tusa kai,, macen da tsabar rashin kamun kanta ba wanda bai Santa ba,,da sauri ta kallo shi,zata tanka Aminu ya shiga tsakanin su,," Wai Ku hala kuna ganin hanjin juna koh??taja baya,, "kaci Sa'a wlh yau Dana fada maka wacce har ka mutu bazaka manta ni ba.. Taja tsaki tare da daga wa Aminu yatsun ta ta wuce,,tuni ya cije lebe tare da rintse ido,, ya bala'in tsanar tsaki,,kan ya bude ido har tai nisa,," amma ya kamata kasan ba abu mey kyau kuke ba,,ache kullum kuka hadu sai kun bar abun fadi?kwanaki naji mey ya faru a super market ai a wajen Ummi,,na rasa mey ke damun ka kwana 2 nan..ya kallo shi,shi kanshi bazai ce mey ke samun shi ba,, shida maganar bakin shi ma gagarar shi take,,amma ya rasa indai suka hadu da Sa'a in basui ba baya ma jin dadi.. Haka akai bikin fadeela sukuku da ita,, idan ta tuno kalaman Hafeez,, ta tsani a sha da ita a rayuwa, gashi bata rama ba yazo abu na damun ta.. Sun samu hutun makaranta a dai dai lokaci,dan yau suka fara shirin biki,ranar Aminu yazo Yace suzo suje rakasu zabar kayan taron,ta tambayo mama suka fito,,da ganin Hafeez tace ta fasa zuwa,,Ummi ta kallo Aminu,, da sauri ya fito,,"kar ki mana haka Sa'a pls,,kin San dole sai da ke a lamarin nan,, ya kamata ace abokin na da ta Ummi sun hada kai a bikin nan,dan kusan kune kan taron nan,ya kallo Hafeez "Dan Allah Ku taimake ni a gama lfy,, ta hade rai kan ta shiga,.ya sauke ajiyar zuciya.. A wajen masu decoration tai tsaye taki zama ganin kujerar kusa da hafeez,,duk suka zauna aka kawo musu drinks,Hafeez ya dau mai strawberries da blue barriers,sai kallon shi take tana yatsina fuska kamar taga kashi,,yai murmushi kan ya tashi,,yazo zai wuce ta gaban ta ta Matsa tana tsaki,ya kar kada kwalin yaji da ragowar guntun,ya saita bayan ta ya watsa mata kan yai waje,,taje ta zauna.. Sun gama kenan zasu fita Matar cikin da mijin ta suka tsayar da su Sa'an, Aminu yai gaba" kinyi staining ta bayan ki fa,,ta nuno Sa'a, take gaban ta ya fadi,,tana mai rokon Allah yasa Aminu baiga ba da Hafeez, yau da karyar ta ta kare..,toh amma da mamaki fa,a satin nan ta gama period dinta,kuma a zuwan farko baici har ya bata ta haka ba,,Ya ilahi.,,Ummi ta juya,ta kalla,.kan ta kada kai, dan tana ganin lokacin da Hafeez din ya watso mata Jan lemon,,tace"Ke kwantar da hankalin ki,lemo ne fa,,da sauri ta kalli Ummin, "Lemo kuma?ta rintse ido, "wlh Hafeez ne ya zuban,indai lemo ne,, tai kwafa,mu zuba indai nice... Allah yaso ta Ummi after dress ta dauro,, ta kallo ta" bani abayar ki ki karbi gyale na..da sauri suka kebe a cikin shagon sukai musanye..dan kunya koh masu shagon bata kalla ba tai waje..a dai dai windown shi ta tsaya tana huci..kan ta nuno shi da hannu"wlh ka dau bashi ..ta bude mota tana ta huci,,Aminu ya kallo shi yaga sai murmushin mugun ta yake,,toh mey kuma ya faru? Dan yana zaune baiga mey Hafeez din yai ba..Ummi ta shiga tana kallon Aminu,,ta daga mishi kafada,,ya kada kai tare da cewa.. "Allah ya shirye Ku wlh,,kui ta abu kamar wasu yara kanana,, yai tsaki,,.har akaje gidan kunshi ba wanda ya tanka wa dan uwan sa,,basu suka gama ba sai kusan 5,aka karbo head din su da kayan sawa a wajen mai guga na sawar gobe.. Hafeez tunda yazo kwanciya yake tunanin abinda yai wa Sa'a dazun,sai yaji bai kyauta ba,,shi dan tsokana yai mata badan tozar ci ba,, duk da tana bashi mugun haushi in sun hadu amma yana son yaga sunyi fada..sai dai yai alkawarin bazai kulata ba gobe bare suyi abun fadi a wajen partn.. Yau tunda suka tashi aka shiga busy,,sunsha gyaran amare sai kyalli suke,, hannun nan yasha kunshi,, tamkar duk dun sune amaren,, qawayen su suma duk sunsha kyau,,tun 4 ta koma gida ta kira Ali mai kula da motar ta ya kai mata ita Wanki,tai latti bata bashi da wuri ba,ya karbi mukulli jiki na bari yai gaba,dan yasan zai fadata yau da motar da yamman nan,,ta buga wa Ummi waya cewar a gida zata shirya,,tace " Dan Allah toh Sa'a kar ki latti,,8 sharp,pls.ta kashe waya,dan tun jiya take ji da fada. By Feenat Ja'afar [10/27, 12:07 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG  BARIKI IYAWA 3  [10/2, 5:57 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 20_Har yau da abun da ya faru a party,,sai da tai kuka mai Isar ta kan ta tashi ta cire kayan ta,, tana mai kara tsanar Hafeez a rayuwa.. Mari??wlh ko uwar da ta haife ta bata taba mata ba,,ta Shafa wajen,, a hankali ta furta"Allah ya isa wlh,,badan ta nuna masa yau BARIKI ba da tuni an sha da ita ta warke,,wa ta isa gaba tai wa fa fa kuma?? Shima yana zuwa gida ya tarar da su Hajiyan tashi a parlour,Tasleem da Zahra,, gaba daya gefen rigar shi ya jike,,yai sallama ba wal wala a fuskar shi,,suka bishi da kallo har ya shige dakin shi,,. Direct bandaki ya shiga ya cire ya watsa ruwa,jikin shi har ya fara dankon exotic din,, ruwa na sauka a a kanshi kawai hasko yadda take ta kuka yake da kokarin tada mota,,"Anya kana da hurumin takura wa baiwar Allah nan kuwa Hafeez? Jiya ka mata 1,ta rama,mai ya kaika da Marin ta??Ba halin ka bane wannan,, ya kada kai,,shi kanshi bazai ce ga dalilin da yasa yake biye wa Sa'a ba har haka,, a Schl din su da mata da suka take Sa'a a iskanci, toh amma mey yasa yafi jin zafin nata??ya kada kai,. "Dis is d 1st,and InshaAllah d last,,ba zai kara yadda makamancin hakan ta kara hada shi da Sa'a ba kuma,tunda an gama biki, toh Alhamdulillah.. Hafeez Shehu Umar yan asalin Jigawa ne,,kakan su aiki ya kawo shi Kano,, anan yai aure mata 3,har ya haifi yara bai waiwayi komawa Jigawa ba,, Allah ya bashi yara guda 11,,Baban su Hafeez shine na 5 a gidan,,yana da kanne mata 4 da Yayye maza 6,,Familyn suna da matukar hadin kan da bazaka gane wannan dan wane daki bane,,duk Matan Sun zauna lfy cikin Aminci da juna,,sai dai dan abinda ba'a rasa na yau da kullum ba,,duk gidan mutane 2 ne sukai boko,sauran duk muhammadiya sukai,, Shehu da Sadiya aurar gidan.. Shehu yanxu da ya zama Alhaji Shehu,yana da mata 1 da yara 4,,Aunty Maryam,Umar,Hafeez da autar su Tasleem,, Su gidan su Hafeez gidan yan boko ne kamar yadda baban su yai boko har ya mallaki kujerar perm sect,,saboda haka rayuwar su ta tafi cikin waye wa,,kowa na kaunar kowa,,Haj Fati itace Maman su Hafeez,,Mace ce mai fada,musamman akan gaskiyar ta,,shi yasa yaran sunfi shayin ta akan baban su,, dan shi kam mai sanyi ne,, Hafeez tun tasowar shi ba mai shiga shirgin jama'a bane,asali ma Aboki 2 gare shi,daga Aminu sai kwa Zunnu,, Musamman mata basa gaban shi,,tun kan ya tafi makaranta a indai, cikin birnin Hyderabad,,Artist ne,, tun a secondary yake da burin zama,,Allah ya taimake shi akai wa Baban shi hanya a a Sarojoni Naidu school of Arts and Communication,,. Tunda ya dawo aka Matsa mishi da zancen aure,,ai shekaran shi 34,meye meye,Yace"shifa bai da Matar aure,,tuni Hajiya Maryam tace ga Zahra,yar gidan kanin Baban shi,,amma fir Yace "shi batai mai ba,,Haj Maryam tace kwa an gama magana,,tunda zance yaje gun Zahra ta kasa sukuni,,dan Allah ya zuba mata dama son shi,,komai nashi burge ta yake,, shikam a nashi bangaren baiga kalar mafarkin shi a Zahra ba,,duk da su duk dangin su ba laifi suna da kyau,musamman gidan su Hafeez din,,dan Baban su a Yola ya samo Maman su,,kakan su kuma fulanin Jigawa ne,,. Ranar ya samu baban shi da zancen Zahra, shifa batai mishi ba,, baban Yace yai hakuri,dan zance har ya shiga family.. Tun daga lokacin ya dauke kafa a gidan su Zahra, sai sai ya gaida baban su a waje ya arce,, ko kula tai da hakan,haka kawai sai ta wanko kafa tace tazo wajen Tasleem, ko bata ganshi ba sai ta kwana. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/28, 1:18 PM] BARIKI...IYAWA 21_Washegari ma bai fita ba sai 11 Aminu yazo ya raka shi da abokan shi Gaisuwar Sirikai,,.Aminu yai mamakin yadda yaga ya sau rai,tuni ya dawo Hafeez din shi na da,, sunsha shadda sai kamshi suke suka shiga,,Aminu Yace su fara zuwa gidan su tukun,.dai zasu karya kwana suka ga Hafeez ya tsayar da mota,, sanye take cikin hijab dogo kusan kasa ruwan kasa mai hannu, da nikaf,amma ta dage shi saman kanta,,rike take da Qur'ani da littafai na addini,tafe take fuskar ta babu walwala., ido ya kara kar kade wa,, Aminu ya kallo shi"kai ma wa Allah kar ka kulata, muje dan Allah tunda bata ganmu ba,..da sauri ya kallo Aminun, kan ya kalle shi da mamaki"Wai da gaske Sa'a nake gani??Aminu yai karamin tsaki,."Dan Allah ja muje,da wace in ba ita ba,,sauran abokan da basu San komai ba suka fara "ko dai ta tafi da shine? Aminu ya kallo shi, sai dai da mamakin shi yaga Hafeez din yai murmushi kan ya tada mota,. Sun dawo daga gaisuwa ya tsare Aminu da tambaya., " Wai dan Allah da gaske Sa'a na gani dazun??ya kyalkyale da dariya,,"Aa yan biyun ta ce,,.ya hararo shi, "Bar zancen wasa, Allah da gaske nake,, Wai ina amaryar ne?? Aminu yai murmushi, yana fatan abinda yake zai faru.. Ya kada kai yana murmushin mugun ta..dakwa wannan drama zatai dadin gani,.Ummi ce ta fito ita da Kanwar ta,. Da murmushi take musu sannu da dawo wa.." Yauwa amarya,. Itama da mamaki take kallon shi,, ganin jiya a wajen Dinner irin rabuwar da sukai,, Aminu ya kanne mata ido,,ta sukui da kai tana murmushi,, ya kallo ta,,"Amarya,dan Allah na tambaye ki man?ta kallo shi,, "ok, Allah sa na Sani,,ya gyara zama,, kan ya kallo Aminu," ba ruwan ka,,tashi ma ka bamu waje,,.yai murmushi,, "indai Sa'a ce,kasan ko Ummi bazata fada min ita ba...zaka neme ni nasan..ya tashi yai daki cire babbar Rigan shi,, dariya take ta ciki ciki," kufa haka kuke keda mijin kin nan,komai ma dariya ne,ta kunshe baki tana"I am sorry,, ina ji, ya kada kai "Wace Sa'a? Sai taji tambayar tazo mata a bazata,, tace" me kace pls¿? Yai murmushi,, "cewa nayi wace ce Sa'a?? Tai murmushi,." Sa'adatu.. BARIKI.. Oh whatever Dana Sani ta qwarai ce,,.Hafeez, kai ne baka San BARIKI ba, baka San rayuwar ta ba,,ni dai abinda na Sani Sa'a mai Sa'a ce cikin mata,,nan ta fara bashi lbrn ta wanda ta Sani,karaf kaf bana sharri,,"abu 1 na Sani da Sa'a, bata barin ta kwana,, sannan mace ce mai amfani da baiwar da Allah ya bata,,amma fa ta hanya tsaftachaciya Hafeez,, ya kada kai da gamsuwa da bayanin ta,,"Amma mey yasa ta zabi sunan BARIKI da kuma wannan sanaar? Ta kada kai "na fada maka tana amfani da baiwar ta wajen Gina kanta..bayan wannan ta girgiza kai" Ban San komai ba,,ya kada kai,, "dama Sa'a tana zuwa islamiya??what I mean,dama ta saba ko yau ta fara??dai dai Aminu ya fito,"Har yau tambayar nan ake?yau fa ka sauya abokina? Yau ranar hala ta Sa'a ce? By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/28, 3:45 PM] BARIKI...IYAWA 22_Tai murmushi kan ta tashi tai kitchen tana kiran Qanwar ta.. Ya kallo Aminu"Dan Allah kaban naka details din da ka Sani a kanta,,ni kaina bazan ce ga abinda yasa na damu da ita ba a yau kadai ba,,Aminu yai dariya"Ba yau kadai ka damu da ita ba,.ina kula da kai,,har Allah Allah kake Ku hadu da Sa'a I know u fa..Ya kada kai,, duk abinda Ummi ta sanar mishi haka Shima Aminu ya sanar mishi,,"tun zuwan su Sa'a unguwar mu na Santa,, a lokacin bata fi yar 7 to 8 yrs ba,,tun a wancan lokacin ina ganin ta a islamiyar unguwar mu har yau din nan Hafeez,, en u know what?? Ya girgiza mishi kai,, a shekara 6 ta gama tai sauka,,sannan ta haddace littafai da dama da kake ganin ta haka,,sosai tasan abinda take yi,,yanxu haka ta gama amma bata daina zuwa hadda ba da daura wa wasu duk ran weekend, shine yau lahadi ka ganta,toh chan ta nufa,,nayi imani Hafeez ba haka ka dau Sa'a ba,,shi yasa yana da kyau ka kyautata niyar ka akan mutum,, Ya kada kai,, tare da rintse ido,, bai son a daina bashi lbrn Sa'a, Dan yana sashi nishadi,,take yaji wani abu na yawo a kwakwalwar shi zuwa jikin shi.. Ya bude ido ya kalli Aminu da wani yanayi,, "yaushe take tashi a makarantar? Ya kallo shi ya kyalkyale da dariya,tuni ya kule,, "kaifa dan iska ne wlh,, ni ka fadan nai gaba malam,.ya tsagaita dariyar kan ya fada mishi lokaci,, tuni ya kalli agogon hannun shi ya mike,," sai mun hadu,,ya kwalawa Ummi kira"na wuce,,,ta fito tana dariya,"sai ina?ya hararo Aminu,kan Yace mata"inda kuka aike ni,,ya dau key din shi ya fita,,suka sheke da dariya,,sun San wataran za'a Rina haka,. Tana woo wa kwanar ta dage nikaf din ta,,sauri take dan wata irin yunwa take ji,,daga kan da zatai ta hango shi yana fito a mota yana tahowa wajen ta, da sauri ta sauke Nikaf din ta juya bayan ta tana salati da faduwar gaba..ta shiga 3 indai ta bari Hafeez ya ritsata a gun nan sai dai wata ba Sa'a ba,, gashi a ka'idar ta in zata islamiya ba mai Binta a baya a masu take mata baya,,ta waiga taga gidan su Tj a bude da sauri ta kule tare da turo kofa,,d sauri ya bita yana kira,, "Sa'a ki bude dan Allah,, magana zamu yi,,cikin tsiwa tace" ba a bude ba,,kasan dai ramako nai ai,,wlh kama kauce kan na Tara maka yaran unguwa suma Atule,, yai murmushi,, toh na tafi bude,,wlh ba abunda zan miki,,tace"waxaka maida Yarinya,,na San ka ai,,ka tafi kawai,ba maganar da zanyi da kai,,taji shiru,,sai da ta kusa minti 10 taji shiru kan a hankali ta zare sakata a hankali zata leka ya turo kai ciki da sauri,,taja baya tare da kwala ihu,,zatai cikin gidan da sauri ya ruko hijab dinta,,ganin hijab din zai matse mata wuya yasa ta tsaya,. "Cikan hijab,yai murmushi tare da sa dayan hannun ya cire nikaf din da sauri,,ido ta zaro kanta nuno shi da hannu" wani salon wulakancin ne wannan komai?ya girgiza kai, "ka cikan hijab toh,ban son iskanci,, ta warce nikaf din ta,.jin ihu yasa Tj da kanin shi suka leko,," su waye?,,ta dallah musu harara,,"Jisu a gun,,toh Aljanu ne,,kallon bakin ta kawai yake,,akwai Iya fadan gan gan ga tsoro,, Tj ya murguda baki, itama ta murguda mishi,,Yace"Kuje ba komai,,suka kada kai,, ya juyo kan ta da take hararar shi,, yai murmushi, duk da haka yaki sake mata hijab,, bata nufa kawai sai ganin shi tai ya zube mata a kasa yai kalar tausayi,, da sauri taja baya tare da zaro ido cikin mamaki,,. Da sauri tace "meye haka?ya kada mata kai,," I am really sorry Sa'a,,wlh Sa'adatu believe me,, ban taba daukar hannu na taba wata da sunan duka ba,,koda kwa Qanwata ta ce,,but thank God, ba wanda ya gani,daga ni sai ke,sai Ummi da Hafeez,, tuni ta fara hawaye,,dan tuno yadda taji a jiyan,,tare da rintse ido,, take wani karfi yazo mata ta kwace hijab din ta da karfi,, cikin kuka tace"how could you? Ko kasan ko iyayen da suka haifo ni basu taba mari na ba a rayuwa,,ta goge hawayen ta,,"no bama haka ba,, Hafeez, duk da ba wanda Ya gani, amma zubar mutunci nawa ne,,da sauri Yace,"I know,, but pls I am so sorry,,nasan na miki ba dai dai ba, amma in kin duba duk mun ma juna pls,,ta girgiza kai, "ka Sani kuka,ka Sani a bakin ciki,ka dauran tsanar da ban San lefi na ba,. Ta goge idon ta tare da nuno shi da masifa,."Ban waje na wuce kawai,,tashi yai,dan yasan ba kula shi zatai ba yanxun., yana kauce wa ta fita tana daura Nikaf.. Ya bita da kallo har ta sha kwanar gidan su. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:02 AM] Feenat Ja'afar: [12/29, 3:39 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 23_Tana zuwa kofa taga mota a kofar gidan wata mai kyau,, da mamaki yau kuma wata samu haka??ta shiga,suna tsakar gida an shimfida taburma a inuwa,,harda Baba da a ka'ida iyanxu baya gida,,ta cire Nikaf din tare da sallama,,baban Yace"Kaga yar halak, walaikum salam,ta kalli bakon, tuni ta hade rai,, baba Yace"kin dawo mama ta?ta daga kai,"Baba lfy?yau nagan ka a gida?da fara'a Yace"a, baki gane bakon namu bane?ta kallo shi, dan jaraba kuwa kirrr ya kafe ta da ido,."Ban gane shi ba Baba,, bakon yai murmushi,, "lalle Sa'a,, Duniya da alkawari kuwa?ta harare shi a takaice,, ta basar,, baban yai murmushi," shekara 3 kam baici ki manta Ali ba,,dan wajen mai gida na da ya tafi kasar waje karatu,,naga har gidan nan yana zuwa kan ya tafi?tace"au, na gane,.bari na shiga ciki,,baban Yace dama fita zamuyi yazo gaida su Maman ki ne,,ta kada kai, Baban yai waje,,zata shiga Ali ya bita da kallo,,lalle Sa'a ta sake girma da kyau, wlh karan nan bazai bi ta kanta ba,,baisan dame ya ragu da Sa'a take kinshi ba?ya girgiza kai lokacin da ya tuno rabuwar su ta karshe da ta furta mishi ba aure a gaban ta yanxu,..yai murmushi, yanxu kam yasan akwai,,shi a yanxu gani yake irin su Sa'a ne kadai ajin auren shi a garin,,gashi Wai dan tsabar takaice Wai bata ma gane shi ba..yai kwafa,yasan ta inda zai bullo mata ai,, inta San wata,bata San wata ba. Shi kwa Hafeez tunda dare yai ya nemi nutsuwar shi ya rasa,, jin wannan abun da ke yawo a jikin shi sai karuwa yake,,ya kasa sukuni sai tunanin Sa'a,,. Duk da bata yafe ba,but at least ta gano yai nadama,, ya hasko lokacin da ya cire mata Nikaf dinta,, Ya salam,Ashe Sa'an karshe ce,amma mey yasa da bai kula da kyan nutsuwar ta,,ga ba karamin kyau hijab din ya mata ba,, yai murmushi, "Hafeez mey ke kanka ne yau 4d first time?? Sa'adatu.. Kamar an tsikare shi ya tashi tare da lalumar wayan shi,, ya kalli agogo 9 ma batai ba,, Aminu ya kira,,bugun farko ya dauka,,"Nifa tsiyata da gauron mutum baiya sanin dare yayi masa,. Dan tsaki yai" commot ni temako zaka min,,ka nemi gauro kuma,dan nima na kusa aure,.ya kyalkyale mishi da wannan dariyar da take kulal da Hafeez,, kan ya tsagaita, "kai shegen kaya,har an dai daita da Zahra ne??Hafeez yai tsaki, "wace haka?dan Allah be serious, numbern Sa'a nake so kaban..yace"eyeee?mey kace?ya kara tsaki,"kai fa dan wulakanci ne,zakace bakaji mey nace bane? Aminu ya ci mur kamar yana kallon shi, "meye dan na tambaya, nasan mey zaka karta mata,haka kawai kasa gobe tazo ta sauken kwandon bala'i a gida..toh da sake,.ji yai kamar ya bishi ta wayar ya rufe shi da duka..sai dai yasan halin Aminu,sai ya hana shi tsaf,,tuni ya dawo lallami,," no wlh ba abinda kake tsammani bane pls, gaisawa kawai zamuyi,,pls,.ya kara kecewa da dariya,, "lalle Sa'a tai zarra,a takaice dai tai wining kenan?da sauri yace "eh,duk ya matso ya bashi,amma dan wulakancin sai ja mishi rai yake,." Ni in zaka ban kaban malam,,Yace"kai,wlh kai ladabi,tam,,lalle Mutumi na da magana a kasa.,bani 2mints yazo zan turo,,tuni ya sauke wata ajiyar zuciya,.kan ya kashe. "Toh in na kira ma mey zan fara ce mata??ya salam,,Wai mey hakan ke nufi ne dashi da ya kasa sukuni?kadai wannan fa shi ake kira da so?dan ya San ance so a zuciya yake,gashi shima tashi zuciyar sai tsanan ta bugawa take,,tun a ganin shi na farko da Sa'a Saida yaji haka..yai murmushi,, da ya tuno yadda in sun gamu suke rabuwa,,in tana zazzaga fada bakin ta kawai yake tuna wa, komai da gaske take yin shi,,.. shigo war text ne ya katse shi, da sauri ya duba,,editing kawai yai ya danna calling,ya sata a kunne tare da komawa da baya ya kwanta rigin gine,,caller tune ya fara ji na sheikh sudeis na Allahumma Aslihlana Duniyall....take ya lumshe ido,,a hankali ya furta" Sa'a "bai tsammani ba yaji ance " Yes,who's this? Ido ya lumshe,dan baima San ta dauka ba,,ita kwa ta bangaren ta tuni ta fara kulewa,,a tunanin ta ko yan iskan samarin tane yan naci,,tuni ta fara sababi"Malam in baka da tace wa bacci nake ji,,yai murmushi kan Yace" am sorry,, Hafeez din ki ne..tuni taji abun wani bankwara kwai,Wai Hafeez din ki,,"Hafeez dina?tace"Toh daga wace jahar?yai murmushi mai sautin da ya ratsa ranta,duk da ta gane wake magana kuwa..ya katse ta "Sa'a,tace" umm,,"nasan kin gane mai magana,,kiyi hakuri again,na nemi afuwa pls,,,ta lumshe ido,, ya cigaba"Sa'a,, da baki juyar da Marin nan kaina ba da bazan taba yafe wa kaina ba,, amma ki tsimaye ni gobe,zanzo in tsaya a titi ki Tara kema jama'a ki rama Marin ki,,Kila in munyi 1-0 nima nawa mutuncin ya zuba sai ki yafen.. Pls,,ta ja numfashi,"ni bance ba,,Yace"meye baki ce ba?tai shiru, Yace"Ok,yanxu kin yafe ni ba sai kin rama ba??cikin kaguwa tace"eh..yai murmushi, "Ok,tnks, bari na barki,. Sweet dreams,,.. Kit ya kashe,,tabi wayar da kallo,,har kwakwalwar ta taji Kalmar" sweet dreams din nan..samun kanta tai da murmushi,, kome ta tuno take ta keme fuska kamar yana ganin ta. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/29, 4:35 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 24_Yau kwana 2 da faruwar haka,Ummi ta kira ta harda fadan su,, dan wulakanci batazo an kawo ta da ita ba,sannan har yanxu taki ta leko ta,,toh wlh zata fadawa mama,, tana jin tace mama ta hau bata hakuri,,zata zo yau,,"uwar jaraba, ta ce"na kai ki?saura ki min lattin zuwa..sukai sallama, ita kanta tasan bata kyauta ba,,. Da yamma misalin karfe 4 kwa ta dau wanka cikin wani dakakken Orange din les da blue, yai bala'in mata kyau,tai ado da blue sarka ta fashion,,batai wata kwalliya ba,amma sai kyalli take na dilka,ga kunshin biki kamar yau akai mata..Mama ta kalle ta,,"ah gaskiya baki kauta ba,amma kunfi kusa,,tai murmushi, "mama zan wuce,ba sako?dan gidan fadeela zan fara zuwa,,tai murmushi," babu,Ki gaida ta kawai.,ta gyada kai kan ta fita,,. Tuki take tamkar bata so,,duk da tana dan gudu,,bata San meya sa haka kawai take jin nishadin yamma cin,, dake gari ne na damuna,, ko ina gwanin ban sha'awa,, minti 7 ya kaita gidan fadeela,, a waje ta parker motar ta,, kan ta fito tai bakin gate,,ta tura karamar kofar ta shiga,,ba laifi,gida ne madai dai ci mai kyau, rabon ta da gidan kusan sati 2,,tunda ta fuskanci kishiyar fadeelan yar rainin hankali ce,,.a parlour kwa ta tarar ta ta hakimce,,ba kowa sai ita kadai,tana shiga ta hade rai,, take ta kalle ta ta watsar, ba tasan dalili ba ta tsani yarinyar nan fiye da yayar tata da take kishiyar ta,,gata da dan banzan kwarjini bare ta tanka ma Sa'an,, ko kallo bata ishe ta ba daga sallama tai ciki., ta hada hannu da kumatu tai tagumi halamar tunani,,ta cire gyalen ta ta ajiye kamin ta tabe baki,, "fadeela,, da sauri ta kalle ta tare da goge hawaye,,dan bakin ciki Sa'a baki ta sake tana kallon ta,,kan tace" lalle kin gamu da aiki kuwa,,wlh kinyi asarar kudin Tara fadeela,, tai murmushi, "sannu da zuwa,,mey nai kuma daga zuwan ki,,Sa'a ta tabe baki kan ta zauna ta daura kafa daya kan daya,," Fadeela ba karamin haushi kike bani a rayuwa ba,,dama Saida nace wa mana karki auri mai mata,dan nasan babu abunda zaki Iya dauka a gidan sai dolanci,,take fadeelan ta hade rai "ke ban San wulakanci fa,,abun harda zagi?ta hararo ta,"jiki fa,,dan Allah kina kallon mudubi kuwa?kinga ramar da kikai a abinda baifi wata guda ba??tai wani murmushi,kan ta mike tsaye tana gyara Riga,," wlh na gode da ban tsamu guntu a abunda kika sha na karba ba,da tuni nima na rako mata duniyar nan,,ki dube ni da kyau,, "wlh nafi karfin gujewa kishiya,,nafi karfin kishiya ta juyani wlh ko ita wace ce,,da sauri fadeelan ta taso tana sa hannu a baki halamar tai shiru kar taji,,taja tsaki kan ta suri jakar ta,," ki same ni a parlour,solomiyo kawai,,duk abinda ake kishiyar tana ji,,tana fitowa direct kujerar dake facing din kishiyar ta zauna,,ta ajiye jakar ta a dayar tare da daura kafa daya kan daya,,kishiyar taja tsaki,dai fadeela ta fito,sai wani rakabe wa take,,Sa'a ta kallo ta,, "meye hakan?a gidan mijin ki kike sanda?ta kallo kishiyar ta ta,.ta dallah mata harara kan taja wani uban tsaki,," dama dan talaka haka yake ai,bai oya samun guri ba,,anzo an hau kujera da babu ita a gidan uba,..ta kara makowa fadeelan harara..a rakabe tazo zata zauna tuni Sa'a ta amshe,,"dadin ta mun San uwale mun San ubale,,sannan tsinke ubale bai kawo gidan ba,tsiya kuma ai duk mun ganta har ke,, gwara mu da rufin asirin Allah,, sannan auran So da kauna aka kula damu,bawai tushe ba..ta nuno ta da hannu,,"mun San kom ai,,so babu wata rufa rufa..ta dawo kan fadeela.. "Gidan mijin ki ne nan,,yadda uban ki bai kawo kujera ba haka nata,,so kowa yai zagi a Kasuwa yasan da wanda yake..tuni ta hazuko ta mike,,"ni zaki gwada wa BARIKIN da ake fadi,, wlh kije shan kiyi karuwancin ki ba a gida na ba,.yar BARIKI kawai,,Sa'a ta kallo ta, sai wani huci take kamar tayi gudun fallako,,tai wani shegen murmushi,, tare da rausayar da kai.." Fadi da ihu ki kara da wayyo Allah,,. Ta tashi tsaye"BARIKI ba IYAWA ake fada miki,ta na wani yauki tare da jujjuya wa a hankali..horn suka jiyo,halamar mai gidan ya dawo..ta nuno ta key din motar ta.."kuma kisha kallo,yau zakiga karuwanci ganin idon ki,,BARIKI ba?yau zan baki darasi. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [12/29, 6:22 AM] BARIKI...IYAWA 25_Ta kallo fadeela da har ta fara hawaye,, tai murmushi,,sai da ta dai daici Alhaji zai shigo ta zauna tare da rukunkumo fadeela,, ta daga murya "Taji ita yar talakwa ce,masu kwadayin abun Duniya,,Munji mu ya'yan masu da maula ne,,munji Uban mu baida halin siyan kujera dole ki zage mu,..da sauri Alhajin ya shigo,," Subhanallah, Sa'a mey ya faru,,tuni ta tashi,,"yauwa,gwara da kazo,,Yau in kaga na bar gidan nan toh anyi ta ta kare wlh,,Yace"Sa'a meya faru ne,,fadeela, me ya faru kike kuka?Sa'a ta kallo Matar tashi,kan ta nuno ta da hannu, "Matar kace,,samun ta nai a kanta tana ta Nada,,dake ita kuma doluwa ce ta tsaya ana dukan ta kamar jaka,, daga rabiya ta dawo kaina,,Wai mu ya'yan matsiyata,sai fadeela ta bar mata gida,,Dana tambayi fadeelan sai cewa tayi daga fitowa zata shiga kitchen ta tare hanya,,Wai ai ba chokalin ta a ciki,,.daga sake hanya ta hau ta da duka.. Gata nan ta Musa,,tuni ya hau 90,,yayo kanta zai mare ta ta kauce"Dama na fuskanci Rabi kullum yarinyar nan rama take,,kwata kwata taki sakewa da gidan nan,, ina tambaye ta baiwar Allah tace ba komai,, Ashe gori kike mata harda hadawa da duka?a gida na?ta kada kai zatai magana tuni ya kara tunxuro,, " karya na miki kenan??ta girgiza kai,,ya cigaba"kuma da kike kiran ba chokalin uban ta,ke da na naki uban,, tuni ta kallo Sa'a, Sa'an ta kanne mata ido daya,,kan ta kallo Alhaji, "ai zance ya kare,, yau kam zan fadi komai in naje gida,da sauri ya yo gun Sa'an jiki na bari" aa Qanwata,.kar muyi haka dake,,kar su dauke ni wanda ban isa da gida na ba,,zan dau mataki ai,,dole kowa tai hurumin ta,,wlh babu takura a gidana,,saboda haka Rabi ki kiyaye wlh,,so da kauna yasa na auro fadeela,,dole tai son ranta a gidan nan da itama nata ne..ta kallo shi "Toh Alhaji ba komai,,ta kallo Rabin,, " Aunty ni zan tafi,,Allah kiyaye gaba,ta kallo fadeela da Alhaji,, "na wuce,dama zan wuce ne na shigo mu gaisa,, ya wage baki" Atoh toh kin kyauta,,ya zaro kudi a aljihun shi,,"gashi Haj Sa'a asha mai,,ta kada kai "Alhaji harda wahala? Ta dan Durkusa" toh na gode,,Yace"mu rakata man fadeela koh?ta kada kai ya matso ba ko kunya yana goge mata ido,, Sa'a tai wani murmushin, kai da gani kasan na mugunta ne,ta kallo Haj Rabi,,tare da daga mata gira,,ta zuge jaka ta dakko wani katon glass su Alhaji sukai waje,tana kokarin sawa tace"Yato kika ga??ta dau jakar ta tai hanyar waje"ki gode Allah da yau banyi wanda zaki yi gida ba,,. Ta daga mata yatsu 2, "sai gani na 2,wlh ki gyara koh na gyara ki,..tai waje..Wai Saida ta fita tai yunkurin sha kota,sai sai kan ta kai kofa har ta fice,ba abin ta bita ba Alhaji na waje,..Sai yanxu taji hawaye na zubo mata,, lalle Alhaji, wato sirrin ta karafkaf ya kwasa ya kaiwa dangin amaryar sa..? Bayan Sunyi sallama da Alhaji ta kallo ta,zan kira ki,yanxu kibi mijin ki,,saura ki tsaya wannan Dolan cin naki.. Ta bude kofa ta fita,,fadeela ta bita da murmushi, dan uwa mai dadi,,Allah yaga tana son mijin ta,duk da badan Allah bai bashi haihuwa ba da yana da kusan kamar ta.. Ta kada kai, Ashe hakane abun,.kuka ta samu Haj Rabi nayi reras,dan Alhaji yace in fadeela ta shigo ta bata hakurin dukan da ta mata..Wai Alhaji yai mata wulakanci DAN bata haihu ba.. Yace" ke kika ce haka bani ba,abu 1 ne bazan dauka ba,,tuni fadeela tai ciki,.chan Shima yabi bayan ta ya barta parlour tana ta rasgar kuka,,gashi ba wanda take sakar wa a dangin mijin hatta Hajiyan shi ba dadin ta take ji ba bare ta kai kara. 5:08 tana gidan Ummi,, da gudu ummin ta rukunkume ta har suna shirin faduwa,, kan ta dago tare da ture ta kujera,,"Dallah na manta ma munyi fada,, wlh baki m Sa'a,, ta marai rai ce "yi hakuri, tace" na zata ko lefin ya shafe mu ne na ran dinner? Tai murmushi, "bar tuna min,ya wuce ai,.da mamaki ta kallo ta,, ta tashi,meye yake kamshi haka?kai shegiyar qawa,,ke ai bana shakkun ki,,ba kamar waccan ba,,tai daki," Wai ina angon ne?ta biyo ta, "yanxu zaki gansu,.tace" inye, qawata komai yaji,Allah sanya alkairi, sannan a dage, yanxu BARIKI zatai aiki..suka tafa..sun koma parlour taji wayan ta na kuka,, ta dauka,fadeela ce,."ya akai auntyn tsoro? Tai murmushi, kai wlh Sa'a baki da kyau,tai murmushi kan tace"kwarai kuwa,ko nai wanka ba..tace"ke kinga yadda yazo yana lallaba ta,harda Durkusawa fa a kasa, Wai shiga in kara baki hakuri kar ki fada a gida,,tai kwafa"ai kinga illar nunawa kishiya tsoron ta,, fir ke kenan kullum akaje gidan ki kina daki,,bazaki ware ki kama mijin ki ba,, bari kiji,idan har zakina tuna wa da wata a gida bazaki Iya komai ba a gidan Miji,,tukun ina kayan nan Dana kawo miki?tace"suna nan,"da fatan kina amfani da su?ta kada kai, gaskiya ban fara ba..ta kada kai "Toh in kin fara mayi maganar,,.dai dai nan taji hayaniyar su Aminu,,lokacin tana fadin "nidai ina fada miki kishiya ba abar tsoro bace,atoh u better wake up n shine ur eyes,,.ta tsaya da magana ganin da wanda Aminu ya shigo,.tace" bari inna je gida zan kira ki,da kallo itama ta bishi,,yayi kyau cikin kana nan kaya,,sai murmushi yake sakar wa,,fuskar ta ba yabo ba fallasa,,Aminu yace "Kaga Alalar Gero,, wato BARIKI.. IYAWA,, tuni fara'ar fuskar Hafeez ta kau.. Maimakon ta kalli Aminun sai ta ke kallon Hafeez din. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:06 AM] Feenat Ja'afar: [1/6, 12:34 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 26_Ta maida kallon ta kan Aminu,"Ango kasha kamshi,,ya Dan bata rai,"au,ai munyi fushi ma Ashe,tai murmushi ta dan sachi kallon Hafeez din,, duk yai kicin kicin,,tace "ai hakuri dai,gani nazo,,ya kalli Hafeez, ya sake kallon Sa'a,, yai murmushi, halin su sai su..tashi yai yabi Matar shi daki.. Ya bar kallon wayar ya kallo ta,.duk ranshi ba dadi, suka hada ido yai mata kirrr,,tana ganin haka itama ta cinkune fuska,.sun dan jima ba wanda Yace da wani uffan,, chan dai ya nisa,," Amma kin San BARIKI ba sunan azziki bane ba koh Sa'a?? Ta kallo shi da mamaki,,baki sake.,yaci gaba,,"Gaskiya Lamarin duk bai dace da ke ba..ta dallah mishi harara,.kaga karfin hali,Wai Barawo da sallama,."Toh,Abba na,,"meye ruwan ka da Lamari na toh??ganin ta fara daukar zafi yasa ya sakko.. "No, Sa'adatu,,BARIKIN ne ban son ana fada miki,ina tsananin jin zafi,..da sauri ta daga mishi hannu.,"Zafi?sai ta zata ko wani fadan yake nema..cikin fada tace"Ni dauka ta My professional life was my personal life,,ta hade girar sama da kasa..da lumana ta karasa fadin" stay out of it..ok?.ta fara kun kuni a hankali"kaji min mutum da karfin hali..ta daura kafa 1 kan 1,,yai murmushi,,"Allah ya huci zuciyar ki yan mata,," my mistake.. Tun daga lokacin bai sake ce mata komai ba ya dukufa a wayan shi,,ta dan kallo shi, jin yai shiru,,kanshi kasa,ta dan harare shi,.kan ta cigaba..lokaci lokaci tana dan Harar shi,kamar wanda laifin shi ke karuwa..Text taji ya shigo,,tai kamar karta bude tana chat.. Ta dai sauka,.abinda ta gani yasa ta kalle shi,,wai "Meye kike harara ta??ta murguda baki..taki reply..Chan wani text din ya shigo, " mey kuma nai na murguda baki??..ta kallo shi da niyar tace "anyi din,sai kawai taga Shima ya murguda mata baki,,bata san lokacin da murmushi ya subuce mata ba,,harda dan dariya mai sauti..ya kallo ta yana murmushi,.haka suke kallon juna da murmushi, har ta manta da komai,,tunda take,bata taba kallon Hafeez ba irin na yau,, Hadadden saurayi ne mai barazanar zama tunxuru,fari ne,ba chan ba,yana da saje, mai taken Razana mata,, kyawun shi na Fulani biyu,yana da kwarjini a fuska,,da dan gashi wajen gemun shi zuwa sage,anyi aski sai yai mishi dan dass.. Murmushin shi yafi komai tafiya da hankalin mata,dan baiyanar kyawawan farin hakwaran shi Tass dasu,,dogo ne,Amma ba chan ba,sannan yana da kaurin jiki,a dire yake,. Uhmmmm"Aminu ne yai murmushi,, da sauri ta saukar da kanta kasa cike da jin haushin kanta.,Hafeez ya harari Aminu,, shikwa murmushi yai tare da kada kai,. Da halamun hasashen shi ya kusa zama gaskiya. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/6, 1:01 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 27_Sai bayan magriba ta tashi,.har lokacin Shima yana nan.,tun fitar ta yai musu sallama,,sai dai da mamakin shi tana ta tada mota taki tashi, sai tsaki take kamar ta rufe motar da duka,,sai dai ba hali,,yai murmushi kan ya karasa wajen,,ta dago kai ta kalle shi kan ta cigaba da abinda take, yace"May I?ta dago,da har zatai gardama, kuma dai sai ta fito.. Shima yai yin Duniya taki fitowa,, ya fito tare da rufe motar,duk ta wani marai rai ce mata,har magana take mata kamar mai jinta,shi dariya ma take bashi,,yace"Muje na sauke ki, ta kallo shi,ta girgiza kai taga yana murmushi,sai ta kule.tace"No tnks,, kan ta kauda kanta gefe..ana haka Aminu ya fito za shi wani gu ya dawo,,turus ya tsaya kallon su,," Ya na ganku anan?Baku tafi bane?ya kallo Hafeez daya harde hannu kawai yake kallon ta,, tai dan tsaki"taki tashi ne,,ga dare nayi,.ya kalli Hafeez, "Toh ka sauke ta man,in yaso gobe na taho miki da ita in an gyara,,ya kallo ta," ko ya kika ce?sai ta dan sachi kallon Hafeez din,,"Nifa Aminu da dai..ya katse ta "ki saman a mota,, yai baya kan ya bude motar, ta kallo Aminu,, ya daga mata kafada halamun bata choice,. A mota duk ta takura kanta,,ta gyara gyale, ta murza zobe, da sun hada ido tai saurin dauke nata,,ganin yadda ya wani seta mirrorn yana facing nata,shi dai sai murmushi,ya dan kallo ta lokacin da yake kwanar wani gu,," zan karbi sako pls,, ta kalle shi tare da kada kai,, Ya karbo suka fito da mutumin,, wanda zai bashi kwangilar Zane na gini..ya kallo shi, "mutumin kace da amarya kake tafe?da sauri ta kallo shi, ya wani kashe mata ido.. Yace" Madam ina wuni,.da yake ta amsa,.tana nanata amarya a zuciyar ta,, bari ya shigo,,ta kauda kanta gefe,har ya shigo,.ya kalle ta yana daura belt,"Muje koh?tai mai banza,, yai murmushi,, ta kallo shi, "Nice amaryar? Ya kallo ta yai dariya,," no, ta kada kai "yauwa,.ya sake kallo ta" Uwar gida ce ai,,da sauri ta kallo shi,, ya daga gira,,"yes,.uwar gida ko kinfi son amaryar? Tuni ta hade rai,. "Malam kaja ni ko ka sauke ni,,uwar gidan wa??Shima ya hade fuska kamar gaske,,"uwar gida na man,baki ta sake,tama kasa furta komai,ga ya wani hakimce ya tsare gida,,kawai ta juyar da kanta,,.sun kusa zuwa wayan ta yai ringing,, ta duba number ne,sai da ta kusa tsinkewa kan ta daga,a gadaran ce ciki ciki take maganar,," wane Alin?.. Tai Jim,ta kallo Hafeez din, Shima ita yake kallo yana kallon titi, sai ta waske dan ta bashi haushi"Oh,na gane,ya akai toh?..wayar ya warce dai dai sunxo kwanar daza ta kaisu gida,,ya kai kunnen shi a kai kai ce,,"Tana tare da mijin auren ta ne,, kai hakuri ka Adana Tarihin sunan ka,,ya kashe wayar tare da ajiye wayar bai ko kalle ta ba yai parking,. Lalle man din nan akwai karfin hali!..baki sake kawai take kallon shi,,wannan irin tusa kai haka,.jin bata fita ba yasa ya kalle ta, shi take kallo,yace"na sauya miki ne hala??ta maka mishi harara kan tai waje,.da sauri yace"wayan ki,.ta warta, zata fita ya dago glass din.."wannan fa?Shima ta warce,kan tace "ba'a Sani ba,.sai kuma ta manta jakar ta,. Ya kunshe dariya,, tuni ta kara kuluwa,.zata shiga gida ya fito yace" Sa'ada,.da sauri ta juyo da zummar masifa,,jakar ya mika mata yana murmushi,. Sai kuma dafe kai"Ya salam,.sai kunya ta kamata,,toh saurin mey take haka??ta tako zata karba tare da juyar da kai ganin yana murmushi,. Maimakon ya bata,sai yai baya da ita,ta juyo ta kalle shi, suna hada ido ta dauke kai,."ban man,.yai shiru,,ta sake kallo jakar ba tare da ta kalle shi ba,yai murmushi, "Toh yaushe zan dawo?ta sake kallon shi a kai kai ce,." Kamar ya??da abinda ya rage kuma?ya kada kai, "kwarai,da abunda suka rage da yawa,. Ta kallo shi da rashin fahimta ,,ya daga mata girar shi,." Ai in kinga abubuwa sun kare,toh tabbata uwar gida ta tare,.gaba daya kamar an kulle mata baki taji,. Ta sake mika hannu ya kautar, "in kina son na baki ki fadan yaushe zan dawo??da kaguwa tace" Gobe,.sai kuma tai shiru,.ta rasa meye dalilin kasa kallon idon Hafeez da tai,.murmushi yai,kan ya mika mata jaka,.tana karba da sauri ta arche gida. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary  Posted by Feenat Jaafar on 05:28 AM, 02-Oct-16       RECENT POSTS K'ADDARA CE 1BARIKI IYAWA 7BARIKI IYAWA 6 « PREVIOUS POSTNEXT POST » COMMENTS No comments yet. Why not make the first one! NEW COMMENT NEW COMMENTS DISABLED FOR THIS POST. NAVIGATION HomeAbout MeGuestbookFeedbackFollow This BlogBlogrollFeed: RSS / AtomComment Feed: RSS / AtomGet a Free Mobile BlogBack to top © 2016 FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG. POWERED BY MYWAPBLOG.COM REPORT ABUSE [10/27, 12:08 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG  HOMEABOUT MERSSNAVIGATION BARIKI IYAWA 4 [10/2, 6:16 AM] Feenat Ja'afar: [1/7, 10:02 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 28_Harta shiga yana Binta da kallo,ya sauke ajiyar zuciya,.Lalle ba makawa a kamu da ciwo,wanda yake tunanin koh shine So din,.ya sake ajiyar zuciya kan ya tada motar shi yana ji da nishadi. A bangaren ta itama haka,kwance take sai juyi take a gadon ta,ta rasa dalilin da yasa yanzu ta daina jin zafin shi kamar kullum,ga wani dan karan kwarjini da ya fara mata yanzun da da bata gani,, ta furzar da iska kan ta kara juya wa dayan gefen, buguwar zuciyar ta ya tsanan ta, lokacin da ta tuno yadda yake mata wani kallo wanda ta kasa fassara shi,, kai ta girgiza, tana mai rarrashin kwakwalwar ta da ta daina tunano mata Hafeez,. Tai adu'a tare da gyara kwanciya. Shima hakan ce ta faru,.sai juyi yake a katifa, sai yayi kamar ya kira ta,sai kuma yai murmushi, a yau kam,ya rasa nutsuwar shi, ga wani fara'a da yake tamkar gonar audiga,ya duba agogo,8 da wani abu,ai dare bai ba,. Waya ya dauka ya danna kiran Aminu,.yana dauka ya fara mishi tsiya,"Tsiyar gauro kenan,bai gane dare yayi,,yai dan karamin tsaki,"Gargadi zan ma Malam, wallahi BARIKI ya fita a bakin ka,ka kirata da Sa'adatun ta sak.. Dariyar keta ya fara mishi, har sai da yaga ya fara kuluwa ya dan sarara, "I knew it,. Dama nasan Biri yai kama da mutum,,kuma ance in kaga Kare na shinshina Takalmi,toh dauka zai,Lalle Abokina ka afka da yawa,.ya cigaba da dillika dariya,Hafeez yace" kai fa dan iskan gari ne,mey na afkawa dayawa? Yace"Son Sa'a kuwa,da sauri yace"So?yace"kwarai kuwa,tun farkon ganin Sa'a nasan ka afka son ta,amma ka tsaya a haushin ta ne,. Shidai Hafeez mamaki yake,tunda ya kashe waya yake murmushi, Ashe sone hakan?Toh amma ya akai bai San So ba shi?abu daya ya Sani yana da muradin auren Sa'a,. Tuni ya dau waya ya fara tsantsara mata Text,a lokacin da itama bacci ya gagari idon ta, kwakwalwa ta kasa daina turo mata hoton Hafeez.,Ji shigowar Text yasa Ta bude ido,takai dube kan wayan,ta mirgina ta dauko,tuni taji bugun zuciyar ta ya karu, duk da murmushi take yayin karan tawa, "Hafeez.. A hankali ta furta,,kan tai tsam tana tuna wani abu,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/7, 1:07 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 29_Washegari kowa ya tashi cikin farin ciki,musamman Hafeez, duk da bata mishi ko reply ba,amma yasan ta ga sakon shi, har Hajiya sai da ta kula da hakan,binshi da kallo kawai take,, ya zauna a kujera.,lokaci lokaci yana dan duba waya ko zaiji shigo war amsa.."Ni Hafeez, yau ko mafarkin Aljanna kai ne haka?Yai murmushi, "ko daya Hajiya,.ta kada kai,. Ana haka su Zahra suka fito ita da Tasleem,suka gaida shi,ya kallo Zahra,yana tunanin mey yasa bai jin komai game da Zahra irin na Sa'a??..ya lumshe ido, Sa'a kam ta daban ce..da sauri ya bude ido jin Tasleem tana ga abincin shi,.Zahra sai satar kallon shi take,Hajiya na kula dasu,ba tasan mey aibin Zahra ba a gun Hafeez, duk irin zaman da zatai a gidan bazai taba kallon ta a Wai wacce zai aura ba sai dai qanwa,kai shi manta wa ma yake da wani batun auren ta,, koda kuwa zai aure ta, toh gini ma na mata 2 yai,daya a sama da turakar shi,daya a kasa da dakin yara,kai da kaga gidan kaga na zaman mata 2,. Hajiyan ta kalli Zuhra tai mata halama da hannu suje daki,.ta yafico Zahra sukai chan,kan ta kallo Hafeez,." Wai ina zancen mu ya tsaya ne Hafeez??.. Ya kallo ta da rashin fahimta,. Ganin haka yasa tamai ta gwari gwari,"zancen ka kai da Zahra man,ko har yanzun baka fahimta ba??tuni yaji gaban shi ya fadi,sarai yasan Hajiyan su akwai zafi,musamman akan lamarin family, yasan bai isa cewa bazai auri Zahra ba yanxu,dan yana son Sa'adatu,, sai dai yana tsoron hada Zahra da Sa'a a matsayin Matan shi,.. "Hafeez,. Tunanin mey kake haka ina magana??..Ya Sosa keya," Am Hajiya,yana nan, sai dai dama ina da magana..da sauri ta daga mishi hannu,,"idan har maganar auren nan ne,toh anyi an gama Hafeez,. Ba zaka maida mu ya'yan ka ba fa,.Yace"Bashi bane Hajiya,.Amm dama wata ce naga, kuma,.kuma..ya kasa karasa wa, ganin yadda Hajiyan take kwada mai harara,,."kuma mey?eyeee, nace Kuma mey?kana nufin ka fasa auren Zahra dan kaga wata bare chan??ko mey kake nufi??.Da sauri ya girgiza kai, "aa ba haka nake nufi ba,,.. Dama,sai yai shiru ganin Abban su ya sakko,ya sunne kai yana gaishe shi, da fara'a yake kallon shi,."Mey kuma ya faru Kaida Umman taka nake jiyo fadan ta tun a sama haka??Tai kicin kicin da fuska,,"Ka zo dai ka jiye wa kunnen ka,dama duk kai ne mai daure mishi ai,,toh wallahi karan nan bai isa kauce wa auren Zahra ba,,yai murmushi, kan ya kallo Hafeez," Ya akai Hafeez?? Ya kallo Hajiyan da sai harara take binshi dashi,.ya fada mishi yadda sukai da Hajiyan, "kuma fa Abba ni duka zan aure su fa,,..A zabure Hajiyan ta tashi," kana nufin mata 2 zakai??!ya sunkuyar da kanshi,,ta kalli Alhajin, "ka dai ji da kunnen ka koh?ta nuno Hafeez," Toh baka isa ba,babu wacce zaka hada da Zahra,,Abban yai mishi halamar yai shiru,,ta kallo Alhajin,"kafa sa baki, dan karan nan zamu bata da Hafeez kwarai..tai sama tana bam bami,. Zahra da tazo jikin kofa tana zatan zancen auren su zatai mishi Hajiyan ta soma kuka,, Tasleem ta taso,"lfy Aunty Zahra?Ta zaunar ta akan gado,,"Tasleem mey na rasa da Ya Hafeez bai sona ne Wai??duk zaman nan dan shi nake yi,amma banda amsa gaisuwa ba abinda ke shiga tsakanin mu,,shine yanzu zai ce zai hada ni da wata ya aura dan tsabar rashin so??.,,,, ta barke da kuka abin tausayi,Tasleem tace"Kut,,wata kuma?ta daga mata kai,. Tasleem ta sake matsowa "Kwantar da hankalin ki,ni nasan Hajiya bama zata soma yadda ba,,Wai mata 2,,kuma kar ki ji kom,ya Hafeez na son ki,kawai dai miskili ne na karshe,, ni nasan indai da Hajiya,toh ke kadai ce Matar shi,. Ta share mata hawaye,.sai lokacin ta dan sararawa kanta.. Shikwa Bayan Abban yace zai ma Hajiyan magana,yai ta murna,abincin da bai ciba yai daki,,wata zuciyar tace" Toh kai da kake ta murna, tukun Sa'an ma ka same son ta ne??sai kuma yai Jim,Toh fa,tanan gizo ke sakar, shifa bai ma San ya ake cewa a wajen budurwa ba bare in yaje ya tsara ta taso shi,,yai kamar ya kira Aminu,abokin shi ne ya fado mishi,wani dan Delhi da sukai school a Hyderabad, ya tuno yadda yake tsara yan mata,duk mai ji da kanta a school din tasan da zaman Kunal,.tuni ya kira ya kora mai bayani,,yai dariya Shima son ran shi, dan jin Wai Hafeez ya fada tarkon so,,Yace mishi ai ba'a koya zance,sai dai ya dan bashi wasu formula,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/7, 2:40 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 30_Dakyar Abba yasha kan Hajiyan,ita sai fadi take batace haramun bane,,kawai Zahra take so ita daya..sai da ya burkice mata kan suka dai dai ta,,Zahra ai zabin ta ce,.Da Zahra taji tuni kuka ya karu,,shikenan kuma. Da Yamma Zahra ta tartara inata ina ta zatai gida,,ta kudiri kuma ba ita ba kara zama gidan su Hafeez Wai dan shi,,lokacin da suka fito baya nan, kuma sarai tasan dan su ya bar gidan dan kar ya kaita,,ga Drivern Abba sun fita,kawai suka je a tsayar da Taxi,,itama da kyar suka samu da mace a ciki.,,Yace zai kaita kan ya kaisu,,a rashin babu suka shiga,,har akaje unguwar da za'a ajiye wacce suka tarar a Taxin,sun zo zasu wuce wata a tsaye da wani da yai musu kama da Hafeez a tsaye sai murmushi yake,,ta motar ta daga wa ta tsayen yatsu tana kiran "BARIKI Ba..Zahra ta kalli Tasleem," Ba ya Hafeez bane wannan kuwa??..da sauri suka kara juyawa,akai Sa'a dai dai itama Sa'a ta daga wa ta motar yatsu,ya dan juyo ganin Taxin da ta wuce,sai dai baiga na ciki ba,,Tasleem tace"La,wallahi shine Aunty Zahra,, tuni ta cika ta batse dan gane da wa yake tsaye,wato itace wacce zai gama su tare??mai Taxi na yin kwana ya sauke dayar suma suka sauka,Zahra zatai kwanar Da sauri Tasleem ta ruko ta,,"mey zakiyi Aunty Zahra?? Ki bari man muji wacece tukun mu karasa tunda wannan ta San ta,.sai a sannan ta dawo hankalin ta, mai Taxi Yace in bazasu tafi ba su bashi kudin shi, da sauri suka sallame shi suka bi bayan Kaltum da zata shiga gida,,. "Baiwar Allah,, ta juyo da fara'ar ta" Aa,Baku tafi ba?sukai yake, "eh, tambaya muke pls?ta gyara tsayuwa," toh muje daga ciki,Zahra ta kada kai, "Aa,muyi anan,." Dan Allah wace wacce muka wuce yanzu da wani a tsaye kika daga mata hannu?tai murmushi, "au Wai BARIKI?? Yar Duniya ake fada miki,badai saurayin ki bane ba koh?Tasleem ta kalli Zahra da ke mai maita sunan BARIKI.. Dake uwar surutu ce tuni ta hau fadi ba'a tambaye ki ba,." Ai in saurayin ki ne toh wallahi ki hakura dashi,dan ba mai Iya ja da BARIKI a fagen nan,,indai har ya shiga hannun BARIKI toh sunan saurayin ki "Sorry ",nan ta hau basu labarin irin kasa wasu da tai da samarin su,Ku harda Matan aure bata bari ba,,campaign na siyasa tai kadai aka mallaka mata dankareriyar mota da katon gida,tuni suka waro ido,,.ta cigaba" wallahi ina baki shawara ki ma bar mata,duk da batta gwani ita..haka tai ta basu karya da gaskiya,tuni Zahra ta tsure,Tasleen kira take "Shikenan yaya ya hadu da karuwa,.ji yadda yake wage mata baki,.bata Ankara ba sai gani tai Zahra na hawaye..tai Dede kwanar tana leken su,, a dai lokacin da Sa'an ta miko wa Hafeez waya,sai wani yauki take irin na yan Duniya.. Yayin da gogan baki tamkar gonar audiga,,dan ko bata furta ba a formular da Kunal ya bashi ya gano da son shi a tattare da ita,,dan yau ba hade rai, mai makon haka ma sai murmushi take mai dan cike da kunya,. Ina,Zahra in ta cigaba da tsayuwa a tana kallon su zata Iya hawan ruwa,tuni ta juya Tasleem ta daura bayan ta tana waiwayen wannan BARIKIN, kai ko ita ta tafi da imanin ta wallahi,, duk ba Wai kyau tafi Zahran ba amma da gani ta fita sanin kan ta Duniya..sai dai ba yadda za ai Yayan su ya kaso musu yar BARIKI.. Tab, bari suje gidan. Gidan su zahran da ba'a je ba kenan sukai gida,in banda hawaye ba abinda Zahra take, Tasleem tayi tayi ta kasa dai nawa,. A parlour suka tarar da Hajiya,itama ta tsunduma tunanin Wai Hafeez da mata 2,,kukan Zahra ne ya dawo da ita,,tuni ta hau tambaya,, kan Tasleem tace komai Zahran ta amshe,tana kuka tana tsarawa Hajiyan. " Kuma Wai yar BARIKI fa Hajiya?da sauri ta waro ido waje,,tace "wallahi Hajiya Wai ma sunan ta" BARIKI,Tasleem tace"Hajiya kinga yadda yake mata dariya, tamkar wacce ta mishi ishara da Aljanna.."Ni ya ishe ni haka,,ni dama nasan yaron nan ba haka kawai yake ba,,Ashe yana chan an dauke hankalin shi, kuma Wai Karuwa yar BARIKI?? Ta kallo Zahra,"yi shirun ki,bari baban naku yazo,,bazata sabu ba Sam,,da hankali na bazaa auro min sirika yar BARIKI ba wallahi.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:31 AM] Feenat Ja'afar: [1/9, 1:03 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 31_Hafeez na dira gida Hajiya ta fara sauke mishi,,da tsananin mamaki ya sauke kai kasa,yasan bai isa wanke kanshi da Sa'a ba yau a wajen Hajiya,.."Saboda ta dauke maka hankali har ka gagara ban bance tsakanin Aya da Tsakuwa,,Yace"Hajiya Wallahi ba haka Sa'a take ba,,wannan sunan daban,kuma.."Rufe min baki shashasha kawai,, in baka Sani ba toh ka Sani yanzun,Zahra kawai na Sani,ba ruwana da da wata BARIKI,Macen kwarai ce za'a kirata da sunan BARIKI ta amsa??. Mita take har Abba ya ritsa ta bayan ya dawo,,yana hawa ta bi bayan shi. Hafeez ya juyo yana hararar Zahra da Tasleem,,"Yaushe na zama abin wasan Ku da har zaku Bini a baya?? Sukai tsurutsuru,ya nuno Zahra da yatsa, "Bari ma kiji,wannan abun bazai hanani auren Sa'a ba,sannan Gobe kisan nayi ki tattara ki koma gidan Ku,,.Ya tashi yai daki,,ta bishi da ido,Tuni ta fara hawaye,abun harda gori?Ita kwa mita tsinana a zaman gidan banda takaici?Bari taje gida,har gidan Aunty salma zata,karya ne a gama ta zaman aure da wata,,. Shikwa yana shiga daki ya jawo waya,ita kanta Sa'ar haushi take bashi,,dan dazun suna tsaye Ali yazo,, saboda tsabar rashin so Wai tace mishi " Excuse me"?,..Tai wajen Ali,duk da bai ji mey suke cewa ba,amma ya gano wanda suke waya dazu ne,tuni koh ta kanta bai bi ba ya shiga mota..shine kuma yana zuwa Hajiya ma ta sauke mishi,.Yai dan tsaki, Lalle sai ya dage,,Ashe da gaske take Wai Bai karbi soyayyar taba? Toh ya take so yayi??Ya fidda zuciyar shi kan Yace"Sa'adatu I luv u,komai??ya sake tsaki,,a hankali ya furta "Sa'a matsala,.. Ita kuwa tunda taga Hafeez ya zuciya ta rasa sukuni,gashi ta kasa kiran shi, a nata tunanin ajin ta zai zube,. Tai kwafa,amma Alin nan sai ta sa kafar wando daya dashi zai ki yayi zuwa wajen ta, in takamar sa gidan na uban shi ne,toh itama tana da gidan daya taka wannan na bulo ma..ta kara tsaki,,ta juya ta dau waya kan ta tashi zaune..tai dailing numbern Hafeez din,da sauri ta katse,," Oh God,,ta rike kai,"Wai Sa'a mey ke damun ki ne akan Hafeez??Tun farkon haduwar su da Hafeez shine kadai Namijin da ta taba mafarki,,shine kadai wanda ta taba chachar baki dashi dan Dabarar ta takare, shine kadai ke sawa ta bata lokacin ta wajen tunanin shi, Shine kadai a yanzun in suna tare take jin wani nishadi kadan kadan na shigar ta..Sannan yanxun yayi fushi ta damu,ji yadda take gwara kan maza,manya da kana nan su,,yau 1 wanda taki jini ya hana ta sukuni.." Ya Ilahiii", "Mey kenan hakan yake nufi?? Ta kalli agogo 9,kwanciya tai kamin ta hau Mishi text da bata San ma ta fara ba..Da sauri ta goge na ban hakuri ta rubuta. " Shine ka tafi ba koh sallama??Tasa halamar shagwaba.. Tai murmushi, kan ta kishingida. Text yaji ya shigo wayan ya kara tsaki kan ya kwanta,chan ya jawo wayan,dan yana zata koh Alert ne na contact na Zane da aka bashi,,da mamakin shi yaga Sa'ada,.yai murmushi, take yaji kuncin shi ya yaye,tuni yai reply.. Taji text itama,tai murmushi dan tasan shine,."Munyi fada ai,, tai murmushi da har hakwaran ta suka fito, tai rufda ciki kan ta mishi Reply.. "Ai bama fada..Triple sorry" ..Shima yai rubda cikin yana karanta wa,,yai murmushi,,"No banyi ba..ban Aron minti 5 naji muryan ki sai nai sorryn..ya tura..chan itama ta bude,,tai murmushi tana duba sling,, kan ta kada kai tai reply"An baka. Ringing 5 tai kan ta katse ta dauka da sallama,,yai Jim,,tace"koh ba'a yafe ni ba??ya sauke wata ajiyar zuciya,, kan Yace"u know what?? Kina da dadin muryar sosai,,Tai murmushin jin dadi,. Kan tace "kaima haka?..sai kuma ta datse harshen ta da hakorin ta,bata ma San ta furta ba,,yai murmushi,." No,ke ai ta daban ce,,Tace"Koh,? Yai shiru,"Sa'ada waye Ali nan ne??tai dan murmushi,, "Dan mai gidan Baba ne,,Yace" ehm,sai mey kuma??ta kada kai "shikenan, Yace" Ba So??tai Jim, kan tace"akwai,.tuni ya mike zaune,,sai ta kara da"Shi yake kayan shi amma,,ya sauke wata ajiyar zuciya da taji ta,, Yace"Toh Ni fa Sa'a?? Tai shiru tana,tace"Hafeez ne kai,Yace"ehm?Toh ana son Hafeez din?? Tai Jim,gaban shi ya fara faduwa,,ita kwa murmushi take a hankali,. Sai da ya kara magana,"Ko har yanzu ban karbi Son ba Sa'adatu?? Wallahi believe me,I am madly, deeply in love with you ...Sa'a I really Love you, en u know?? Tun farkon haduwar mu na kamu da son ki,sai dai a wancen lokacin ban San so bane Sa'ada, nasan dai ina tsananin kishi na ganki da gyale shara shara,,sai naji zuciya ta na tafasa,,in na tabo ki mukai ne kawai nake samun relief.. Tunowa take da lokacin, tabbas tun ganin Hafeez na farko ta ji sauyi a tare da ita. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/9, 1:43 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 32_Ya cigaba, "Kin tuna ranar da na watsa miki lemon strawberries a jiki??? Tuni ta rintse ido dan tuna wa da wannan rana,ba zata manta ba har kuka tai,,.ya katse ta" nasan ke a zatan ki dan tsokana nai,,Ya girgiza kai, "Ganin mai shagon nan fa nai yana ta kallon ki sai ga kin dame Riga,ga nan gyale a kafada,,shine yasa na tashi na harare shi yana sosa kai,kan na baki baya na watsa miki,nasan Ummi ta gani,en dole ki nemi agaji,sai kwa gashi ta baki kin suturce jikin ki da abayar ta,,.Jin shi kawai take..ta katse shi da" Mey zakace da Marin da kamin kuma??Ya sauke ajiyar zuciya,, "Sa'adatu.. Taji kiran har kwakwalwar ta,.," Naga shigo war ki kina ta wani yauki,,ga kayan sun dame ki,ga wani Wai shi gyale da kika dakko kin maka shi a kafada,baki sa maraba da wacce ta fito haka,,ga duk kusan ke ake kallo,,amma ke na fuskan ci baya ma damun ki,haka kika kutso taron nan kika shigo fa,,da zaki kula,da zaki gano tsabar haushin da nake ji, hararar ki nake tayi ko zan samu saukin zugin raina,,ina fa jin wani a yan uwan su Ummin yana cewa wani "Woow,,she's Beautiful!! Kamar na cire babbar Rigar Aminu na rufa miki naji,.sai dai nasan ba laifin shi bane,,naki ne,. Dan na rage zugin dake raina na koma baya,,juyo war da zanyi naji ki kusa dani,kuma kamar ki shige min jiki,,bazan boye miki ba,a lokacin nan ji nan kamar ma na rufe ki da duka,,dan na tsani mace mai chudanya da maza,.ban Ankara ba naji saukar sanyi a jiki na,,...Yai shiru tare da rintse ido,,." Sa'ada ban so tuno Marin nan da na miki,, duk da har gobe kowa yana kallon kece kika mare ni in kika cire Ummi da Aminu,tanan kawai na gode Allah. Tai ajiyar zuciya,, Lalle sai yanxu ta kula da kishin da Hafeez ke nuna wa,,ya katse ta,, "Da fatan kin gamsu zaki yafen,..yaji shiru,, Ashe kudin ya kare.. Shi yana ta zuba ko warning din bai jiba,,ya dau wayan Glo ya kira..dai dai zata kira.. Yace" kiban dama gobe nazo gida da safe,yanxun dare yayi,. Ta kada mishi kai,,"Ok.. Yace"Mey toh zan samu??tai Jim,dan bata gane nufin shi ba,,sai tace*Sai dai kazo gobe,,Yace"Promise?,, ta kada kai "Promise.. Haka suka sallamar kowa ya kwanta da tunanin Dan uwan shi..barin Sa'a yau da taji duk wwani haushi ta daina ji na Hafeez,, a ganin ta ko a haka ya barta ta gamsu da Lalle So ne ya Jawo Haka. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 6:38 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 33_Tun safe Zahra tai niyar gida,.ko jiran Tasleem batai ba,, tana zuwa ta zube a tsakar dakin Mamyn nasu,, Aunty Sadiya ta kallo ta,"Lfyr ki kuwa??Kinzo kin wani zube min ba koh sallama??Tuni ta marai rai cewa Mamyn tasu tana hawaye,, "Mamy,,Na shiga 3 wallahi,,.sai ta barke mata da kuka,,Da jin haka ta waro ido waje,, Ta tashi ta kamo yar ta ta,tasan dai tatsuniyar gizo bata wuce ta koki, Amma sai ta tambaye ta" Meye kin shiga 3?? Nifa ban son wautar nan taki ta yan fari?? Ta lafe jikin shi tana kuka,,"Mamy Wai Fa Hafeez mu 2 zai aura,, kuma ya rasa da wacce zai hadani sai yar BARIKI mamy,, Mamyn tai Jim,ita dai dama wannan hadin na Zahra da Hafeez kwata kwata bai mata ba,,duk da Hafeez da yake a gurin ta,amma tasan ba abunda yar tata zata tsinta a gidan shi sai ciwan rai, toh amma ita batta da wani power a gidan,tunda itace auta a cikin gidan su kakanin Hafeez din,, haka itama aka mata wannan auren hadin,, gashi za'a sake da yarta tilo mace,dan duk sauran kannen Zahra maza ne,,. Rarrashi ta fara,,"Toh meye ne abun kuka anan Zahra?Ta sake magana cikin kuka"Mamy Abban su fa Wai ya yarda,,Hajiya ce kawai tace bata yarda ba,, Dan Allah mamy ki Taimaken ki samu Fodio da maganar,tunda Abban yana jin maganar shi,,.. Ta sake fashe wa da kuka"wlh mamy ban son zama da kishiya.. Da sauri ta kwade mata baki,,ta rike bakin tana cigaba da hawaye "Wato kaddarar ki a hannun ki take koh Zahra?Ta hade fuska mamyn,,"Da hankalin ki kike furta irin kalaman da wanda basuyi makaranta ba kadai ke fadan shi??tai kwafa,"Sannu autar mata,,Toh ki sata a ranki,,sannan ki daura damarar zama da ita tun yau,.Da sauri ta kalli Mamyn nasu,, "Anya mamy kuwa tana son ta??,,Bari Abban yazo,shi zata tsara mishi komai ya shige mata gaba,,.kamar tasan tunanin yar tata,,sai ta dawo mata Nasiha,,kan tana saukaka kishi,dan duk yadda ka dauki Kishiya toh fa a haka take zuwa maka,," Ki duba ni da auntyn Ku,da yawa mutane basa gane kishiya tace,dan tsabar muna zaman mutunci da girma ma juna..ki cire wanna akidar taki tun wuri Zahra,,Dan kin fini sanin halin Hafeez, bare akan abinda yake so,,sannan duk Family nan suna matukar yaba dashi,hakan yasa suka zaba mishi ke suna ga da hankalin Ku zai zama daya..kar ki fara bata rawar ki da tsalle tun yanzun,, tai ta mata,amma ina,ita gani take Mamyn bazata gane ba,. Karfe 9 da rabi yana gidan su Sa'a,, ita duk daukan ta wasa yake,yai katari kuwa Baban su yana waje,,Har kasa ya gaida shi cikin girma mawa,. Da fara'a Baban ya amsa,,Take yaji Hafeez ya kwanta mishi,dan ba kasafai yaran yanzun suka Iya girma ma manya ba haka..Ya kalle shi da fara'a, "Hala ka wani kake nema??Ya sunkuyar da kai kasa cikin girma mawa,, Da halamar kunya Yace"Baba dama wajen ka nazo,,Yace" Toh mu shiga daga ciki,Ya Sosa kai,Daga zaure ya cire musu farar kujera,suka zauna,sai leken cikin gidan yake ko zai hango sahibar shi,,Baban ya dan kula da hakan,"Allah dai yasa lfy?Ya sunne kai kasa cikin kunya,"Amm Baba sunan Hafeez, muna chan kasa daku kadan, dama,Amm,Sa'adatu na gani Baba,shine nake Neman izinin fara Neman auren ta a gun ka..Baban yai murmushi, a ranshi yana ambaton "Allahu Akbar,,Lalle zabin shi Dana Sa'an shi Yazo,,Dan duk wanda zai cika sharudan mulunci na Neman aure Hafeez ya fara,.Bai manta zancen shi da Sa'a ba akan Tara samari ba na aura,,bai manta amsar da ta bashi a lokacin ba,," Baba duk saurayin da ya fara zuwa Neman aure na wajen ka toh ya cika sharuddan aure na,,ka shaida hakan Baba,,nasan zaka fini sanin dawa na dace Baba..Da irin kalaman nan Sa'an take kara shiga ranshi,, ga daga gani daga gidan mutunci Hafeez din ya fito,,Ya kada kai, "Tabbas kayi abinda ya dace Hafeez, hakan ya nunan daga gidan da ka fito,,Allah yasa alkairi a ciki,,.Tuni ya fadada fara'ar shi yana sunne kai,, Baban ya tambaye shi iyayen shi,ya dai gamsu da duk bayanan shi,sai kuma bincike ya rage.. By Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 34_Baban ya shiga dashi ciki,yai wa mama magana,,ta fito da kamalar ta,Ya dan duka ya gaida ta, itama da fara'ar ta ta amsa,,kan tai dakin Sa'an da ta koma bacci,,. Ido waje take kallon shi, tunda mama tace tana da bako ta sa hijab,ta zata Ali ne,dan tama manta da Yace safe,,ido 1 ya kanne mata,, dai dai Baba ya fito zai tafi,yai mai sallama,, Ya dawo da kallon shi kanta,,Ta zauna tana mai mamakin jin sallamar shi da Baba kamar sun San juna,," Ina kwana,, yai mata wani kallo, ta kauda kai tana murmushi,,A hankali tace"Allah sa ma kai break irin wannan sammako,,ta dan harare shi,, yai murmushi,Tare da kama ciki, halamar yunwa..Ta make kafada,,ya marai rai ce fuska,,"Wajen Baba nazo,kuma na dace,,harma ya ban auren ki,harda dan duko kai a hankali kamar mai rada,,Ta kara dukar da kanta,,kan ta tashi ta debo mishi abinci,,ta zauna,,kunun gyada ne mai cous cous, yasha madara da lemon tsami,sai Doya da kwai,,Ya kalle ta yana nuna dakin mama,,yana yin halamar kar ta fito,,Tai dariya,,Ya dau cup din kunun yakai baki yana kara kallon dakin mama,ita dai sai dariya take mishi,,ya rintse ido,dan jin dadin kunun,ita kwa da sauri ta waro ido, ya bude ido a kanta,fuskar shi ba yabo ba fallasa,zatan ko bai mishi dadi bane,Yace"Hope ke kika dama,,ta [10/27, 12:11 PM] 💍🛍🍬Salma🍬🛍💍: FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG  BARIKI IYAWA 5  [10/2, 6:51 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 38_Ta daga mishi kai tana sunne kai,, "Tunda Baba ya sanar dani zuwan ka da abunda kazo nema wajen shi na amince maka,,." Hafeez, buri na ka cika a gun Abba,,Ta kallo shi," I'm inluv with you than I ever was...I love you too Hafeez,, Da sauri ta rintse idon ta da murmushin kunya, dan jin wata kunya da bata San tana da ita ba ta rufe ta,, Kallon ta yake yana murmushi,, kai shikam baiga abunda Sa'a ta rage shi ga mace da yake son aure ba.. " Kunya " "Addini: "Class" Kyauu " Da Iya kwarkwasa.. Shikam ya gode Allah, Sa'a ta mishi komai da ta so shi.. "Tnks much My Unique,,Yaushe zan turo a mini Tambaya?? Baki ta fara kunshe wa tana dariya kadan kadan,Tuni ta so zautar dashi,.. Yau sun buga luv,tamkar kar su rabu, Dakyar ta samu ta gudu gida dan magriba tayi,,Ashe haka "So" din yake??..Ashe Haka masoya suke ji amma a baya take ganin wautar su??..ita kam indai haka ne,toh itama sai ta sarrafa zuciyar ta, dan gujewa so mai zafi,,Ji take kamar dama ta girma ne da son Hafeez,,. Mama ma sai da ta gano yau Sa'a na cikin farin ciki matuka,,Dan komai ta ke sai kaga tana murmushi ita kadai,,. Shikam daga nan wajen Zahra yaje dan cika hukuncin Hajiyan shi,Da Tasleem ta sanar mata murna fal ranta,Wai yau Hafeez ne yazo gidan domin ta??.. Suna zaune bayan ga gaisuwa ta kasa ce mishi komai,dan jinsu take wani iri.,Shikam kallon ta yake yaga ta ina ta Gaza,, sannan mey Sa'a ta fita?..Ya kada kai,, "Amm Zahra magana nazo muyi ta fahimta,. Ta kallo shi fuska sake,,.Yace"Nasan kinji maganar ba ke kadai zan aura ba,,ina fatan tun yanxun ki rike ta yar uwar ki tun kan azo ga batun zama,,dan Sa'adatu she's simple, baki da matsalar zama da ita.. Tuni Annurin fuskar ta ya kau,,tai tsagal ta mike," Ya Hafeez kar muyi haka da kai,,Ban San wata Sa'adatu ba kai na Sani,,sannan ni kishiya,wallahi kishiya na dauke ta, ba Wai yar uwa ba..akan mey an gama magana tashin farko ka watgazan tsari..Kallon ta kawai yake yana murmushi,, Sa'an shi kawai yake tuno wa,mace mai Iya lafazi da kawai ci,,Akallah a haihuwar kaji zai haifi Zahra,amma dan fitsara shi ta tasamma aka tana mishi haka..Kyale ta yai sai da tai mai Isar ta harda hawaye,kamin ya taka mata birki. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/14, 6:30 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 39_Tuni ya hade rai,, Yace"Bafa shawarar ki nazo nema ba da zakimin fitsara,aure na da Sa'a kuwa zan Iya cewa shi yafi zame min dole,,so tun wuri kisan inda kika dosa,dan gaba bazata mana kyau ba,,.Nan ya barta tana ta kuka,A ganin ta magana ya fada mata, wato ita auren ta dashi bai zama dole ba??,,.Mamyn tata ta shigo dakin ganin Ta fito daga parlour tana kuka,.Lalle yar ta tana da aiki a gaban ta ja,don tana son tusa kanta a inda bata kwarjini, tasan tabbas kukan ta bazai rasa nasaba da Hafeez ba,, Gashi ta nace da sauran dangi sai anyi auren nan,amma tana tausaya wa rayuwar auren yar tata data ki jinin kishiya... Soyayya ake yi tsaftacacciya a tsakanin Hafeez da Sa'a, a yanxun kam ya maida gidan su Sa'a kamar gidan su, tun yana jin nauyin zuwa har ya ware,,sai dai abu 1 dake kawo musu cikas Ali,,Ali ya nace sai Sa'a,, tashin farko yazo da Baban shi Wai a bashi Sa'a,, kai ranar tai dariya har taji ba dadi,,sai a ranar ta kara tabbatar da Lalle Ali ba tsaran ta bane,, duk da Abban yaso tun wuri hakan ta faru,bai rufa wa mai gidan nashi ba ya sanar shi Sa'a Nada Miji,,sai dai a bawa Ali hakuri,,dake shi Dattijo ne mai dattako ya amince da Allah baiyi Matar shi bace,amma shifa Ali fir yaki daina zuwa,,duk da ko yazo ba kula shi take ba,da yaga baci ya dawo gori,inda alkawari ai Baba bazai ki bashi auren ta ba,kodan muhallin da Abban shi ya basu,,Take Sa'an tace"Indai wannan gidan kake wa toh ka kwantar da hankalin ka,amma aure ne ka kara lalata shi,dan ka nunan kai ba na kwarai bane,kuma dole mubar muku gidan Ku... gori har yaje kunnen Baba,.Tuni ta bawa mutanen da suke mata haya Notice, ta hau gyaran gida,,shi Baban bai zata ta dau zafi haka ba,,sai ranar Laraba bayan anyi da wata tazo Wai gobe zasu tashi,,da fari Baban dariya yake mata,sai dai ganin ta fara parking yasa ya tsayar ta,,"Sa'adatu ba fa Ali ya bani gidan nan ba,kinga bai kamata muyi wa Alhaji haka ba,, tace"Baba ai ko ba gori yaci karan nan ka yarda mu shiga gidan nan, Ina da gidan zama,amma fur kunki zama ciki,sai dai nasa haya,Baba chan gashi na zamani,nan na kasa,ya kamata inn ka samu dama Baba kai amfane ta,,kawai ce mishi zakai tashi zakai,daga baya ni nasan abin yi...Duk da haka Abban bai yarda ba,sai dai kamar yadda ta fada Washegari ta dakko mai katuwar Daf, Baban baya nan aka fara kwasar kaya,sai gidan Sa'a,, gida ne mai daki Uku,,biyu kana na,daya katon parlour, duk da baida wani girma,amma na bulo ne,kuma na zamani,daya dakin mai bandaki a ciki nan ta jera wa su mama kayan su da gadon ta,tasa aka sa carpet a pparlourn da manyan tuntu,,sai fridge da Katuwar TV,,Ita kuma ta hular da katifa da sauran tariki cen ta..Lalle gaya wa mai zuciya,bamai Dukiya ba,,,sai da kudin account dinta yai kat.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/14, 11:41 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 40_Baki sake su Baba suke kallon Sa'an,basu isa musu ba,dan har kuka ta sau musu,,Mama ta lallabi Baban,,ta kira Fadeela ita tazo,Gidan ya musu dai dai,Dan tsakar gida ne mai dan fadi kadan,anyi mishi siminti,suna da ruwan su,komai dai dai sauki akwai shi,Fadeela ma tai farin ciki sosai,,. Da yamma Baba ya sanar da Alhaji cewa sun tashi,yai hakuri abinne yazo musu a bazata,,yai mishi Allah sanya alkairi, ai gida kam nashi ne duka,zai yi duk yadda yaso,sai yazo ganin gida,,.yaji dadin yadda ya fahimce shi kwarai,yai mishi kwatancen inda suka koma,.kan ya dawo yana fada ma su mama yadda sukai,Sa'a tace Baban ya bata mukullin tsohon gidan toh,za ai mishi aiki,zuciya 1 ya bata,yana mai shi musu albarka. Tai ma Hafeez text, cewa sun tashi da address, dan tasan zai Iya zuwa bai same su ba,,5da rabi kuwa yazo, yana ta yiwa mama murna,,da Allah sanya alkairi,, Nan take sanar shi ai Sa'a ce ta tada ballin sai sun tashi,ba shiri,,yai murmushi, Yace "Toh ya kikai da yan hayar cikin??Da mamaki take kallon shi, Ya akai yasan nata ne?,Sai da suka je parlour yana yaba tsarin gidan,komai a saukake, amma da kyau,,yadda suka zauna a Chinese carpet din ma ya kayatar shi,ya jin Gina a tun tun,kamar wani basarake,,nan ta sanar mishi abinda Ali Yace, " Shine na basu Notice, bawai kora na musu ba,tana murmushi, ya kada kai, "Good,kin min dai dai,nan din tunda ba na uban nashi bane naga kafar mutum,,Tuni ta hau kunshe baki tana dariya,,Fadeela ta shigo suka gaisa,yana mata itama Allah sanya alkairi,.. Alhaji yazo daukan Fadeela yaga gida,,yana ta son barka,,nan yai wa Sa'a zata ga gudun mawar shi,,. Ko minti 3 ba ai da tafiyar Fadeela ba,Ali yazo,Baban shi ne Wai Yace yazo yaga gida kan suzo,,Allah yasa baban baya nan,Sa'a tace ya jira ta a waje toh,,Da dariya suka fito,da ka gansu kasan suna cikin nishadi,in ran Ali yai dubu ya baci,,a zuciyar shi yana,,"shifa kota ya ya sai ya samu Sa'a, atoh, yama ji da kyau,,..Ba ko magana ta mika mishi key, Ya karba yana kallon ta,,. Hafeez Yace" Ganan keys na gidan naku,,an bar muku shi sarkin yan gori,,en ya zamo last da zan kara ganin kafar ka a gidan nan,, dan bazata mana kyau ba,,Suka juya Sa'a na daga mishi hannu da shakiyanci,,ya kulu Iya kuluwa,,. Direct Baban shi ya kaima key in,,. Washegari sai gashi yazo da kanshi ba'asi,, Baban ya kira Sa'a,ba ko dar ta korowa Alhaji bayani,kan danshi ne ya Goran ta musu,Alhaji ya girgiza kai, "Sa'a in banda abinki, ai ni nai kyautar nan ba Ali ba,,Ya ajiye musu kan ya basu hakuri,tare da sanar shi zai ga Alin. Sa'a sun gama schl,sai Attachment,Zancen aure sai karfi yake,yayin da Zahra sai baudewa take,Da son abun Sa'a take attachments din,daga dan wannan sukai sha'awar daukar ta bayan ta gama.. Ansa bikin su zuwa Hafeez din ya gama ginin shi,,Duk bangaren kowa na shirye shiryen biki. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 7:13 AM] Feenat Ja'afar: [1/19, 1:13 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 41_Matsala 1 da ta fara fuskan ta shine kana nan maganganu da dangin Hafeez suke a kanta,,dan sau daya da ya taba kaita ta gano basa yi da ita,,tun daga ranar ta kudiri wani abu a ranta,burin ta kawai Allah kai Damo ga harawa. Makarantar zama da Miji mai mata ta bazama nema,,duk wani wa'azi mai kyau da ma'ana, mai taken mallakar Miji Sa'a Nada shi a waya,,duk wasu littattafai da tasan tabbas zata kara Sani akan su ta neme su,, Matakin farko data fara shine Bincika yanayin kayan Dakin da Hafeez yake da muradi,cikin wasa sukai abinsu,nan kwa bai son satar amsa tai ba,,a haka in fira tai dadi a wasa da wasa sai da tasan mai Hafeez yafi so na daga abinci, sutura,color, best perfumes da sauran su,,kan ma ta shiga ta gama karantar daga A har Z.. Tanan tai wa Zahra zarra tun kan su shiga,ita kullum batta dabara sai ta yaya zatai Hafeez ya zama nata ita kadai?? Duk abinda aka sa mishi lokaci toh tabbas zaizo da sannu,babu wanda yakai Hafeez da Sa'a farin ciki, duk da Zahra tana farin ciki, amma Sa'a ce ta tsokane mata ido,,ganin har yanxun yadda yake rawar kafa a kanta,duk da tayi nasarar sanya dangi yadda da cewa Lalle Hafeez zai auro musu karuwa,,kuma tabbas sun yarda,,. Hakan yasa dai dai da lefen ta a dangin Hafeez din sai yan tsirirai ne suka kai,,yai kaya na azo a gani,duk dunsu ba banbanci,,,Ware kunya Sa'a tai ta hau gyaran kanta da kanta,,.Tsohon gidan su sukutum ta maida gidan gyaran ta,Tun kamin sati da biki ta kammala duk wasu jeka ka dawo na hidimar ta,,ta hada nutsuwar ta waje guda,,dan kwarai tunda taji wa'azin Malama zuwaira ta dau darasi,,don tabbas itama ta fahimci yawancin amare basa cikin nutsuwar su ake kaisu gidan Miji,,kenan duk wani gyara da za'a miki kadan ne zai tasiri a gare ki,dan komai yana bukatar nutsuwa.. Kaflas din fenti babba tasa aka nemo mata madarar shanu,dan tasan takamar da za'a gwada mata kenan su Zahra, dangin Fulani,tasha tai wanka ..,sai da tai ta wankan amare na Lalle kullum a daura Dana madarar shanu da turaren Durot,,,Wata kwararriya ta samu,tazo har gidan tana biyan ta,,su fresh Nonon Rakumi, Su ganyen Tumfafiya,tai,duk wani sirri ta nemo su ta hada anyi mata,kan satin biki yazo in ka kalli Sa'a tamkar wata yar black Indian nan masu kyau,sai shining jikin nan yake,ga wani dan karan kamshi da laushi da fatar ta take,,kai kace daga Maiduguri ta fito,,Dan tun kan biki tasa wata Qawar ta yi mata hanyar wani mai hada turarurrukan mata masu kyau da kamshi,,Dan ita akwai son kamshi,musamman na turaren wuta.. Yau Juma'a, ta kama gobe za'a dauro auren su Hafeez da Matan shi,sun shirya kyatattiyar Dinner,, Kowa ya halatta Sa'a kawai ake jira,,in kaga ango sai wage baki da ido yake yaga ta ina zata ratso,,Zahra an hakimce a kusa da Hafeez, an Gaji da kyau itama,,gashin nan an zubo shi baya,duk da taiwa Hafeez din kyau amma shi burin shi yaga Sa'an shi,,duk sunyi waya tace suna wani room ne a hotel din 5 mint's,,. Hargowa da fadin MashaAllah shi ya juyar da hankalin Hafeez da Zahra,,tafi ake mata,ganin gasu Tj yan kanan Bodyguards dinta na unguwa sunyi wankan bakaken suite, kowa yasha bakin glass,yaran sunyi kyau matuka,sun shassha kunu su a dole masu tsaran Aunty Sa'a, sai abin ya kayatar,Ga nan Qawayen ta yan karya da wanda sukai Turkish suma sunsha kyau,,sanye take cikin wata doguwar Riga ta net Golden da ratsin Orange,, sai ta temaka wajen kara haskaka mata fatar tai wani yellown kyau,,ga wani arnan Hill Orange da Pose ,,sai dan mayani data rufa a gefe,,Fuskar nan ta Gaji da kyau,Ko Zahra sai da ta firgita ba Hafeez, dan tunda biki ya karato ta fara gyara da dogon hijab da Nikaf take fitowa su gaisa..tayi kyau ainun,,ga wani tsadadden murmushi da take sakar wa,sabanin Zahra da ta nemi fara'ar ta ta rasa,,Hafeez ya tafi duka,,A ranshi fadi yake"Tsarki ya Tabbata ga Allah,, Ya ma manta da jama'ar hall din kamar an tsikare shi ya tashi,ba ko kunya yai wajen ta,,tana ganin haka tai saurin dukar da kai tana murmushi,Tuni aka hau flashes ta ko'ina,, in ran Zahra yai dubu toh ya baci.., haka suka jera har mazaunin su. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/19, 2:25 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 42_Ta dan kalli Zahra a takaice,sanye take da Baki da Arsh na net itama,tai mata kyau,kamanin ta na fulanin usul ya fito,kai inba kallon tsoro ta mata ba sai tace suna yanayin kama da Hafeez, Ta sau mata murmushi cikin kissar ta,,A Yatsine ta jutar da kai,dan bazata juri ganin Sa'an ba,,.Kai ita sai yanxu ma take da na sanin zuwan ta Dinner... A Bangaren Sa'a, tun daga kallon da Zahra tai mata tasan zasu dama.. Wannan shine karo na farko da taga Zahra,,dan koda sukaje gidan su kin fitowa tai su gaisa,,. Har aka tashi Dinner Zahra bata cikin walwala,har Aunty maryam yayar Hafeez ta fara mata nuni da hannu kan ta saki fuska,sai dai ina,ji take kamar ta sau ihu,dan tadin su suke tamkar rada rada,,ga wani munafikin murmushi da suke sakar wa juna,,koya juyo kan tasa baki sai dai ta tabe baki,, Tuni ta kara jin haushin Sa'an a ranta.. Yai yin Duniya dakyar ta shiga mota Wai shi zai kaisu da Sa'a, ganin Sa'an ta hakimce a gaba,yasa ta ja Tasleem suka shiga baya tana turo baki,,Zahra ya fara sauke wa,wanda dama Allah Allah take ya sauke ta,,Sa'a ta dago mata hannu halamar bye bye,,"Sister good nyt,,Tai mata banza tare da doko kofar,,Duk yana kula dasu,,Sai dai ganin Sa'an ta cigaba da fara'ar ta yasa bai ce komai ba,, Tasleem ta kallo su,,"Kai Matar yaya kin ganki kuwa??Ta kallo Hafeez ya kashe mata ido 1,,da sauri ta dauke ta dawo da kallon ta Tasleem,,Tace "Na kai Yayan ki kuwa??..Tai dariya,," Kai Aunty na kin fishi,,Wallahi u look so Gorgeous..Kunyi keda aunty Zahra...kai Bros kai samuwa,..Suka kyalkyale mata da dariya,,.Sai santin Sa'a suke ita da Yayan nata,har abun ya fara bawa Sa'an mamaki,ganin basuyi wa Zahra haka ba,kuma Bilhakki tai kyau itama.,Kai badan Tasleem ba,yau da sai 12 zai tafi,dan bai Gaji da kallon sahibar ba.. Suna tafiya ta makawa Aminu kira,yana dauka ya hau mata tsiyan nashi,,chan tace" Abu daya zaka min Aminu, yace "ina jin ki amaryar mu,,tai murmushi, kan tace,,"so nake kai duk yadda zakai na rigata zuwa gidan Hafeez.. In kamin wannan kamin komai a rayuwa.. Yai murmushi.,Dan tuna wa da Hafeez da yai,Shima dazun ya gama mai mitar su fara dakko Sa'an shi, dan ita yake so ta zama uwar gida..Da karfe ya furta "Done.., Kaga uwar gida sarautar mata..ta kada idanu tace" Dadina da kai Aminu akwai saurin gane karatu..suka kyalkyala dariya..Ummi ta karba. Washegari da misalin 10am aka daura auren Zahra da Hafeez,kan suka rankayo Gidan su Sa'a,, Murna a cikin Hafeez sai an tona,,Wai yau shine mallakin mata 2?musamman Sa'an shi??,,.Wayyo dadi,banda godiya wa Allah babu abunda ya ke. Da yamma kwa Aminu ya cika alkawari, sai da suka jera motocin daukar amarya kan suka cewa su aunty Maryam Wai suzo su kai su za'a karbo amanar Sa'a, duk da Hajiyan taso ranfo su,dan a dole ita fa Zahra za'a fara kaiwa,yadda aka fara daura auren ta. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/19, 3:39 AM] BARIKI...IYAWA 43_Kwarai su Aunty Maryam sunji dadin karramawar da dangin Sa'a suka musu,,kayan gara nasu turum haka aka yi musu tsaraba,zo kaga kukan tausayi wajen zahra da mama da Baba,kai ko tafiyar Fadeela basuyi haka ba,,musamman Baba,,haka ya kankame Sa'an shi suna kuka yana mata fadan ta zauna da abokiyar zaman ta da mijin ta lafiya,,Aunty Maryam sai murmushi take musu,Gaskiya familyn Sa'a ita kam sun mata,dan ta fuskan ta akwai Tarbiya...Da kyar Aunty Maryam din ta banbare Sa'a ita da Fadeela,, suka kai amarya Gidan ta,, Dan gin su Zahra basu kara barke wa da lamarin ba Saida suka ga Wai anyi sama da amarya,,wato sama ya bata ya ajiye tasu a kasa,,Dan su basu zo Jere ba,dangin Baban su ne,suma maza kawai,,Aunty Maryam ce kadai bata tabe baki cikin su,kowa da abinda yake tofa wa,,basu gama mamaki ba sai da suka dira bangaren Sa'an,, a haka suna musu kallon talakawa zo kaga uwar dukiyar da aka narka mata,,dan mai gidan Baba ne ya dau nauyin Gado,wani dan uban su Chinese bed milky brown,,komai na bedroom din milk n brown,tsarin ra'ayin Hafeez kenan,,yana son daki haka ko Blue.. Parlourn ta kwa an zuba wasu uban su kujeru ledar, green ne da ratsin dan milky kadan,sai grass carpet Shima green da milk,center table da wani dan tray an sa mishi Apple na roba masu kyau greens,sai Set na kayan kallon ta na plasma screen TV katuwa,flowers ne masu design din Royal tree,,sun kawata parloun sosai,,ya sanar ta bai son tarkace a parlour,shi yasa ta sanar da yan Jere fridge a kai mata kitchen,, show glass asa ta a daki,,.. Su Kansu dangin Zahra baki suka saka dan ganin komai yaji cikin tsari da wayewa.. Sai dare aka kawo Zahra,,abinda ya kara burge Sa'a ta kuma kara tabbatar da Lalle ita ne uwar gida shine, ana zuwa Saida aka hauro da Zahra saman ta,aka musu fada su zauna lafiya,tunda itace Babba,,Tuni Zahra ta kulaci su Aunty Maryam,,ya zasu ce Wai itace Babba, bayan ita aka fara daura aure da ita?? Kowa ya watse sai tsiraran Qawayen amare da Tasleem data makale a dakin Sa'a, dan tun Ran sakun Lalle take hararar ta, Wai dan taje Sa'a tasa an mata Lalle..Fanfo kawai Qawayen Zahra suke mata,Wai sai ta tashi tsaye,dan kishiyar nan tata Lalle da gani kam yar BARIKIN Asali ce. Ango yazo bayan yan rakiya sun rako shi,suka wuce da Qawayen Amarya,Ya kira Zahra sama,Da kamar baza ta zo ba,sai dai ganin yana jiran ta,, Komai na Kayanta Ja take da muradi,,Sunyi kyau sosai,dan auren Gata aka mata,musamman da take yar fari,,Sai dai duk da ken nata tana zuwa saman na Sa'a ta sau baki,,amma Lalle an mata ba zata,,Saima taga kamar sunfi nata haskuwa,,Ya kalle ta,, "ki zauna bari na kira Sa'adan,,ta tabe baki kan ta zauna.,yai ciki yana ta zumudin arbawa da sahibar shi,, Akan sallaya ya tarar ta, ta daga hannu sama tana mai kwararo mishi godiya daya nuna mata itama ranar ta,tana mai fatan Allah kawo na yan baya. Murmushi yake yana mai kara yaba halin Sa'a, tabbas yasan yai dace,Sa'an shi da ya kira da "Unique,,Ta juyo tana mai murmushin kunya tare da dukar da kai,,ya kare wa dakin kallo,komai yayi kamar an tambaye shi,,takowa yai tare da tsuguna waa gaba ta..Hannun ta ya kamo ganin taki tashi,Karo na farko da ya fara gigin taba hannun ta,,Wani irin abu yaji yana tsirga mishi,,yayin da ita ma taji makaman cin haka...ya sauke ajiyar zuciya,a hankali ya tada ta tsaye "Muje parlour ina son magana daku,,Ta kada kai. Bayan ya bude taro da adu'a ya fara musu bayanin abinda yasa ya Tara su,sannan da fadan kowa ta zauna da kowa cikin Aminci.. Ya kallo Zahra.." Sa'a uwar gidan ki ce,so duk wani girma natane a gidan nan,,kiyi respecting nata..ya juyo gun Sa'a,, "Amm Unique, ta kallo shi da murmushi, Shima ya maida mata,," Ganan Zahra,duk da nasan kin dauke ta a matsayin yar uwa,pls ki kara akan Nada..Ta daga mishi kai,,Ya kallo Zahra,"Da mai magana??.. KAMAR jira take kuwa tai zaraf.."Nifa ban gane ba da naji ana kiran ta uwar gida na?? Ina ce ni aka fara aura kamin ita?Ya kallo Sa'an, ita kuma tana kallon zone tare da kokarin cire wa..ya dawo kan Zahra.. "A ka'ida,wacce aka fara kawo wa ita ce uwar gida, bawai wacce aka fara aure ba,,Am I clear?Ta kara tabe baki tare da hararar Sa'a ta gefe,,ya cigaba," So tunda kin fahimta,My Unique, ta dago kai,"Kwana nawa kike ganin za ana yi?Ta kalli Zahra, "Sis, nawa nawa yake tambaya?Da sauri Yace" Ok, sorry,,Nawa kuke ganin za ai??Sa'a tace 2 sai Zahra ta rigata da sauri.."Uku yayi,,Ya kallo Sa'a, "Unique 2 naji kince ba,,ta kada kai tana wani yauki,,yai murmushi kan ya kallo Zahra data kule,"biyu it's Ok,dan zai fi min nima,,ya kamo hannun Sa'a," Yayi ba?Ta jijjiga kai, ya dawo kan Zahra, Tuni ta mike,tace"Yadda kuka ce,Yanxu sai ka taso a fara ta kaina.,Da sauri suka dube ta,har Sa'a na Neman dariya,,yai murmushi A ranshi yana"Lalle hasashen Fodio gaske ne,da Yace duk dangi ba mai fitsarar Zahra. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 7:20 AM] Feenat Ja'afar: [1/21, 5:19 PM] Feenat Ja'afar BARIKI..IYAWA 44_Ya sake kallon Sa'a, ta mike itama tana wani rausaya "Baby ka raka ta,Kila tsoron sauka take,,yai murmushi ya kallo Zahra,da zumudi ya mike," Atoh muje na rakaki ki kwanta,,na ma manta ne,,Baki sake kawai take kallon Sa'a, wacce tai hanyar daki tana tafiya tamkar hawainiya,,Da sauri ta juya tai kasa tana hawaye,, Hafeez yana kiran ta ko oho,,ya tabe baki,, In ta shine dama bai son motsawa yau ko kadan a wajen Sa'an shi,, da azama ya dau abinda ya taho dashi nata ya shiga da sallama,, kai duke tana sake mamakin karfin hali irin na Zahra,,Wai kuma a haka gaba da bayan ta bafulatana,, wannan Ai bada kai ne ma wallahi, sai ta Rena mata wayo ma,,. Duk kan wani ala'ada sun gabatar cikin wayewa,,a yau,yasha mamakin Sa'an shi akan ilimin addini,,Dukkan wata Amsa gamshasheya ya same ta game da Sa'a, murmushi kawai yake kara mata,,jin yadda take fidda harrufa kowanne da hakkin shi,,babu ta bangaren da Sa'a ta Gaza mishi,.. Kyau Ilimin addini Ilimin Boko Wayewa Ga Iya zama da mutum, a yau kadai yasan zatai adalci,. Hmm Bariki ce Hafeez. A gaskiya shi bai taba jin salon kamshin Sa'a ba a Duniya,,duk inda ta gifta kamshi ke tashi, ga wani shining da ta kara yi,ansha wankan lalle da madarar shanu,,ita kam tana girma ma abubuwa Natural,, Yabon kyaun ta yake,har Saida ta fara jin ko ta zama wata Queen ne,,laushi da santsin fatar ta ya kara hura wutar da ke ruruwa a sassan jikin shi,, ko da da yai zaman waje yasan ya tsallake dokokin Allah, burin shi yai aure kamin ya mallakawa Matar shi ta Sunnah dukkan kaunar shi da gaskiya,,komai karo da karo,,sabbin shiga,duk sai ta gigita shi,, dan tabbas tasha gyara Iya gyara,,Wannan dare a gare su sun ware mishi shafi daban a rayuwar su,,Duk da tai juriya,amma Hafeez din ta sai Da yasa ta data sanin gyaran datai mai yawa..Waras ta samu yabo da kirari wanda har yanzun da take kan sallaya murmushi take in ta tuno su,,Bazata gushe ba,tana mai alfahari da kai Budurcin ta gidan Miji,,a ganin ta, duk wani ji da kai,ko isa a gun Y'a mace,Toh Indai ta tsallake wannan siradin,toh she's lucky,, In ta tuno da Daren jiya.,sai taji tana fatan Ina ma ita kadai keda Hafeez? Ina ma ita kadai ya zama mallakin ta.,Bata zata ba taji hawaye ya taho zirrr,,Kan ta goge taji hannun mutum,,A tsorace zatai baya ya ruko ta,, Ta tsinne kai a jikin shi tana sauke ajiyar zuciya,, dan shaff ya shammace ta bata ji ya shigo ba,,ya cikata yana murmushi, murmushin da tun jiya yaki ya kau a fuskar shi,, lalle bai ji kom ba da ya kira Sa'an shi da "UNIQUE"... Zame wa yai ya kwanto a cinyar ta, Tuni ta kara sunne fuska cikin kunya,," Ina kwana??...murmushin shi ya karu,ba tare da ya amsa ba,shafo fuskar ta yai,,Yace"Ya kike??Ta kada kai itama da murmushi, tamkar sirikan juna haka suke ta murmushi, sai dai shi daga Ya shafo fuska, sai sumbaci hannun ta, lalle ya tsaru a fatar ta,,Sa'an shi Zuma ce,,ta kuma harba mishi Sonta,,ga ta da wata Ni'imar dumin jiki da Allah ya hore mata,,shi yasa yanxu kawai burin shi yaji shi jikin Sa'an shi,, ko hannun ta ya taba Dumi ne,,yaja doguwar ajiyar zuciya,, ji yake tamkar ya maida ta ciki dan So,,kokari yake ya kalli fuskar ta su hada ido,amma fir ta ki,,Yana matukar mutunta mace mai kunya,,shi kyau ma take mishi yaga mace tana kunya..Indai jiya ke bata kunya toh,dan ko shi yasan ya kasa Sarrafa kanshi,,amma yasan akan Sa'a ne,,don abu ne ya kuma hadu Da Tsantsar so...Hannun ta yakai hanci yana shakar kamshin su,,tai murmushi,,har kunnen ta ya Gaji da yana kamshin nan. Ita kwa Zahra tana sauka daki tai tai ta rubzar kukan ta son rai,,Lalle Hafeez, tun yanxu ya fara rawar jiki akan wata karuwar Banza,,Da sauri ta tashi ta goge hawayen ta,Zubur ta mike,Kamar wacce aka tsikara da allura,ta zuge jakar ta,. "Dani kike zance,,guntun titi kawai,,Ta fara kade kaden magun guna tana sha,,duk tasan an mata gyara a gida,,"indai ta nan ne,Ai Sa'adatu Sorry,,dan wallahi sai na maida ki Mowa,,Hmm Lalle Zahra,Sa'a Ai ta Riga da ta kafa Govnatin ta. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/21, 5:21 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 45_Bacci suka koma,cikin daddadan sanyin safiyar,, Sai 10 suka tashi,Shima ji tai ba mutum a kusa da ita,,sanye yake cikin Farar shadda, an mata aiki da brown din zare,,ya daura hulal shi yar zanna brown da milky ajiki,,sai kamshi yake tashi a jikin shi,, ta lumshe ido a hankali ta kara budewa,,yai mata kyau ainun,,Ta mika mishi hannu da Shagwaba,, bai wata wata ba ya kamo,,Tun jiya yake shan shagwaba, gashi Aminu sai waya suke mishi zasu gaisuwar sirikai,,ya sumbaci hannun ta,, "Ga abinci Hajiya ta aiko,,En Aminu suna ta kira..Ta rausayar da ido,," Ai da ka tashe ni,,yai murmushi,, cikin 10 mints tai dan wanka,ta shirya cikin Brown less, da ratsin milk,,Batai wata kwalliya ba,dan sauri suke,,Ya sauka ya tarar da Zahra har ta gama cin nata,,ta hakimce a kan kujera tana kallo,,doguwar Riga tasa ta Attamfa, tai kyau itama,,sai dai a hakika ba kallon ne a ranta ba,dan tun da ya kwankwasa mata kofa tai sallah ta kasa koma wa bacci,,hatta hawan shi sama ta gani bayan ya bude an kawo abinci,,. Rike suke da hannun juna suna murmushi, sai wani langwabe kai take a kafadar shi cikin salon ta,,Tuni Zahra ta fara cika tana batsewa,,taja dan karamin tsaki ta cigaba da kallon ta,, Hafeez ya kalle ta,,"A Zahra,,kin tashi ne??Tai mai banza,, Yace"Magana nake fa??kan ta daga kai,.Ko gaisuwa babu,, Wai ita a dole sun bata haushi jiya,,Sa'a tai murmushi, Lalle yarinyar nan batta da wayo,,dan tsabar ta kara bata haushi tace"Sister in kwanan mu?Zahran ta kallo ta fuska a tamke, Lalle Za'a gwada mata BARIKI,, sai ta dauke kai ba tare da ta amsa ba,, Hafeez ranshi ya baci,cikin fada Yace"Ke baki Iya gaida mutane ba sai mu zamu gaida ki??Ta kallo shi, ganin ya fara kumfar baki ta gaida shi yai mata banza yaja Sa'a kan dining,,Tashi tai ta tafi daki,tana"kar ka amsa,a ranta.. Sun ciyar da juna cikin kulawa da kware wa a so,,yana fita ta rufe sauran tai sama tare da tsantsara hadaddiyar kwalliya,taja dauri,,. Da akwai wuta ta sanya turaren wuta tare da kullo glass din saman dan kar ya fice,,ta shiga ta hau gyara har ta gama ta kira mama da tsabar kewar su..tana in Fadeela tazo a bata sakon. Tana sama taji hayaniyar baki,,Ta fito tare da daga labilen jikin glass din kadan,,su Aunty Maryam ne da wasu dangin su Hafeez din baki da sauran cousins din su,suna gaisawa da Zahra da tai zirif ta fito parlour kar a bata mata daki,,Tana ganin dangin su ne ta fara yake baki suna fillanci,,Dan autan Aunty Maryam Habeeb mai koyan tafiya,yaron mai kiriniya ne sosai,,Yana sauka yai wajen TV stand din ta,,ba kunya ta debe remote din ta tana nifa kar kamin ta'asa,,Sa'a duk tana kallon ta,, duk da batajin abinda take fada,ta kalli yanayin Aunty Maryam,Duk da yake take amma in ka kula zakaga ta sauya,,ita kam Tasleem dama binta kawai take da ido,,sai ta kashe kallon ma duka,,tana cigaba da musu tadi,,ita mai yan uwa harda fada musu abunda ya faru bayan tafiyar su,,kowa kallon mamaki yake Binta dashi,,mamaki suke Zahra tamkar ba yar gidan Aunty Sadiya ba,,wannan Ai abun kunya jiya ta tafka,,Sa'a taga tana dai ta kumfar baki,sai ta sauke labulen ta ta fesa Air weak,,ta hakimce a parlour,, komai take kallo cikin tsari an jera mata,,Tai murmushi da ta tuna da Hafeez din ta,,Yace "Komai Unique kamar kin tambaye ni tsari na...kwankwasa glass din ne ya dawo da ita,ta kara kallon kanta jikin glass din kan ta bude,,Da fara'ar ta ta tare su,," A Aunty,,Sannun Ku da zuwa,,Qanwata,,Tasleem ta wage baki,,Habeeb yana ganin ta ya bangale baki,,ta mika hannu tare da karban shi tana"Oyoyo Habeebe nah,, Missed you,, Tuni kwa Aunty Maryam din suma suka hau murmushi,, da fuska duk ba fara'a,, tun zuwan ta take son yaron lokacin da taje gaida ta,,. "Bissmillah., Ku zauna,, harda yan tsofi 2,da jiya basu zo kawo amare ba yan uwan Baban su Baffa Modibo,,saboda haka Tuni tai kasa su kuma suka zauna a kujera suna yaba tarbar data musu,,da girma mawa ta gaida su,, Saboda haka fuska sake suka amsa,,barin ma Aunty Maryam,, ganan Habib sai tsayuwa yake a kanta yana tabo daurin dankwalin ta,,chakulkuli ta fara mishi a wasa,sai ta dau hankalin sauran yaran,,data tashi sai suka biyo ta,, Lalle,Shimfidar fuska,tafi ta Taburma,,Ta kwala kiran Tasleem a hankali,. Takwara cire gyale ta ajiye a kujera ta bita kitchen,, Aunty Maryam ta kalli yan uwan nasu da cousins din ta,," Allah yarinyar nan yar mutunci ce,,ga Waccan uwar fitsararrun tarbar da ta muku,,ko ruwa babu sai shegen mita ya Taga courtu,,.. tai shiru ganin su Tasleem,,Tasleem dauke da Cups na glass, Yayin da yaran ta basu flates guda 4 cike da hadadden Doughnuts da cake,ta bawa Habib exotic babba daya ya rike,ta debo wasu Drinks din da ruwa a flats,,"Aunty kuyi hakuri mun barku,, Tana murmushi tana tsiyaya musu,,kamin ta mika musu,,Tashi tai ta kunna kallo,,Ta kallo su Inna Balki,," Inna Wanne kuke so,,Inna tai murmushin jin dadi,,tace"Muda zamu tafi,Ta kallo Maryam, "Mairamu kishiya ta na son mu jima hala,,tai murmushi, Kan ta kallo Sa'a," sa musu na Dan ibro,dan she really enjoy his Movie show,,Sa'a ta kada kai da murmushi, itama tana son Film din ibro,shi yasa ma ta siyo wani film da ya jima amma tana son shi,,NA MAMAJO...Ta kallo Habbeb daya kin kumo kwali ya kawo mata,,Wai ta bude mishi,,ta dau cup din Tasleem ta zuba mishi,,Tasleem tace,"Ganan su innan mu,jiya basu samu zuwa ba,,Da fara'a ta kalle su,,"Aiya,,Sannun Ku inna,,ya taro??suka ce Alhamdulillah, chan aka fara show na ibro Abin dariya,,Ta yafico Tasleem, tana tashi Habeeb ma ya tashi,sai glass cup din hannun yaron ya subuce,Tuni ya fashe,,Ta juyo da sauri tana"Subhanallah,Habeebe,,hope bakaji ciwo ba??Shima yaron duk yai kamar zai kuka,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/21, 5:23 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 46_Hanun yaron take duba wa,,Wai koya yanke,,Aunty Maryam ta taso,"Dama ban so ki bashi glass cup ba,,gashi ya fasa,Habib da kiriniya,,ta kallo ta,"Kai Aunty,ni tsoro na ma kar ya yanke,,ta Kar kade mishi jiki,"Aunty rike min shi na kwashe,ya make kafada,,Tace"Sorry yanxu zan dawo,,ta shafi kumatun shi lufulufu,,"That's my Boy,,Aunty tai ma Tasleem da ka kan ta karbo tsintsiyar,fir ta hana ta,ta share tai moping wajen,,Sai mamakin kirkin Sa'a suke,. 12 nayi ta bar su sukai kitchen ita da Tasleem, guntun kajin jiya tasa Tasleem ta sauka kasa ta dakko miyar cikin flasks din da aka kawo da safe,ta gyara ta ta juye kajin,,Tuni kamshi ya gauraye saman,,tai cous cous mai sauki,,ta taho da sobo ta daura a wuta ganin tana da kankara da cucumber data zo da ita,kan 1 da wani abu ta gama komai,,Ta dawo parlour sun gama kallo suna ta tadin su da fulanci, duk na yabon ta,,duk da bata ji,amma 4 sure tasan yabon ta suke,ganin yadda suke kus kus suna dariya,,Tace"Aunty su Inna kwa sun shiga ciki??Ta kallo ta da murmushi,"No,mai daki na kitchen Ai basa shiga ba,,ta waro ido,, "La,Ai ba komai,Inna Ku shiga Ku ga,,ta Jere musu abinci a flasks,sai ga su Fadeela da Ummi,,ana fara kiran sallah ta ta shimfida musu Darduma,,wasu suka shiga bandakin parlour, Tace wasu su shiga ciki,Ba kyama haka ta dinga tafiyar da su,,nan wajen ta suka kai sallah suka ci abinci hade da jin dadi,basu bar gidan ba sai da ta tabbatar da kowa ya tafi da kirkin ta a bakin shi,,. Ita kam Zahra qawaye na zuwa suka kule daki,,Inna ta leko,"toh mu zamu wuce,Fatuu ba dan karar kuzo kuga dakina ma koh?Tace" Au,Ku shiga,kudai tsofin nan sai ganin gulma,,Ita kam Aunty Maryam tai gaba da danta da sauran yara,tai ma Hafeez waya cewa sun fito ya dakko su inna,yaran sai murna suke ta basu chocolate,..A mota sai yabon Sa'a su Inna suke,"Kai Hafeezu kai dacen mace mai son Jama'a, sai son barka,Sa'a tai kaza,Sa'a tai kaza,,shikam Murmushi kawai yake,Tuni yaji Sa'a ta kara samun martaba a idon shi,Tuni ya kara share mata waje a cikin Birnin zuciyar shi,, tuki yake yana murmushi,, Sa'a, Sa'a, a ranshi fadi yake"She's d Best,,.Duk da sun ma manta da iskancin da Zahra ta musu. Suna dira,suka fara bawa Hajiya labari,,a ranta tana mamaki,da Wai suka kasa gano wace ce YAR BARIKI?.. Sai dai ta bisu da murmushi, amma ita kam Zahra ce ta ta,duk tsiya,,. In banda waya,ba abinda suke,ta kira,ya kira,Su Ummi sun tasa ta gaba suna ganin fi'ili iri iri a wajen Sa'a,,. A yanxu ma waya take,su da suke kusa da itama dakyar suke jin zancen,magana take tana wani kashe ido,kai kace Hafeez din yana gaban ta,, Ta ajiye ta kalle su,,"Ya akai ne Guys,irin wannan kallo??ta tashi daga kishingi den da take,,Ummi tai Murmushi, "Wallahi Ade tausayin Kishiyar nan taki nake,,Wai kishi da Ade BARIKI?? Woo, amma fa a dan mata sassauci pls,,suka tuntsire da dariya harda shewa, " Ke,in taso zan zame mata tamkar yar uwa,buh ta sake tace zata ja Sa'ada,, woo woo,sunan ta sorry,,dan Wallahi yadda nake jin Hafeez yanxu a kokan raina...Hmm kedai abar tone tone,but he's d best, ta lumshe ido,, Fadeela tace"Ai itama da ganin ta yar yi ce,kiga fa yadda take amsa mana gaisuwa tana wani yatsina fuska,nidai dan Allah kisa da hakuri kar ki biye mata.. Ta dallah mata harara,,"An fada miki kowa ma irin ki ne,,hakuri?? Ai ban ganshi ba,indai akan kishi ce,tana Dana min,wallahi zan Dana mata nawa,in ta rissina sai mu sai saita,,but bafa fada ba,No,BARIKI kawai,ya ishe ta,, Ummi tace "Toh Allah ka bawa Zahra hakuri,dan zamuyi kuli da ita,,tai wani murmushi," Ummi kenan,,ni Ai bana fatan haduwa da kishiya Lumbu lumbu,hmm wutar k'ai k'ai ce,,Bana son ajiye makaman yaki na da wuri,gwara wacce zamu dama a fagen yakin Ni ko Ke??..Kuma Allah ya bani,don Haka nake so,,ban son munafukar kishiya,Wai Ita mai hakuri,,. Ta kallo Fadeela,"Toh ke ya batun sanjan gida??Tai murmushi, "Kai Sa'a,Wallahi u r too much,, duk da kin sa Matar nan ta rissina,kinsan da bakin ta ta fada mishi Wai sai ya sauya mana gida,indai zaman lafiya yake nema,ba ko musu ya yarda," Tun kuwa da ta kalla taga cikin nan ta kara haukacewa,Ai sauri a sauya gidan nan,,,Tai kasa da kai,"Wallahi har tausayi ta fara bani,,Sa'a tai tsaki,,"Ai sai kiyi ta jin tausayin nata,,ke ta Tausa ki Ai,,Taje itama Allah ya bata rabon ta Albarka cin ki,Ai adalci ma na mata,dan kazantar da baka gani ba tsafta ce,kina ga in ta cigaba da ganin rawar kan da Alhaji yake akan cikin nan bazata hadayi zuciya ba??,,.Suka tafa "Baki kyau,,tace" Ko nai wanka,,Yanzu Ai ban fara komai ba Wallahi, zan daga mata kafa na fake da kunya ta sati guda,daga nan zan fara bude koli na a gidan nan, Suka tuntsire da dariya,tace "Kudai Ku rike dangin Miji,dan tamkar shi kuka rike,dan duk abinda kika musu zasu fada yaji,en tanan, wani sirrin rike wuyan Miji ne tamau in fada muku,,. Sai da suka Taya ta ta gyare gidan ta tsaf, sukai magriba kamin Suka tafi,direct wanka ta shiga,banda kamshin turaren wanka,babu abinda ke tashi,,Ta fito daure da Towel,ta cire hular wankan,Zara zaran kitson nan sun zubo mata kafada,ta gyara na gaban kan tahau kyali,tamkar wacce zata Dinner,,Ta dame cikin Riga da skirt din wata Holland blue da ratsin purple ajiki,,Tai kyau ainun,sai kamshi ke tashi na Amarya,,ta kullo Kofar glass din dan taji har yanxu Qawayen Zahra na nan,,tasau turaren wuta, Tuni yahau kamshin dadi,,ta feshe Air weak,tare da yarfa turaren Carpet da kujera,Tuni wani irin gamsashen kamshi ya kewaye saman,har yana dan ratso kasa,,. Kai Zahra sai fa kin dage,ji wannan hadadden kamshi,Tai murmushi," Lokacin ta ne,daga yau Ai sai ni,nayi imani in ya dani kunamar nan,sai wata ba ita ba,,Jumai tace"Toh tashi kiban kudi na,dan nasha wahala kan nasamu kayan nan,,.nan Ita tafi karfi,gani take tunda ba ita keda Hafeez din ba,Ai ba sai ta gyara ba,ita dai ta gyara chan.. Da zumudi ya shigo gidan,dan tun fitar shi yake mar Marin zuwa gidan,duk Sa'a ta gama kar kato da hankalin shi gare ta da daddan muryar ta a waya..Sai dai mey,yana shiga gidan Zahra na fitowa ta bata mishi budget,,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S [10/2, 7:25 AM] Feenat Ja'afar: [1/22, 2:23 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 47_Wai sai ya kai Qawayen ta gida,,A ranshi yana toh mey suke har yanzu da basu tafi ba??8 fa saura,,. Amma haka ya Nada,tana ta murna Wai ita ta fara danawa Sa'a Bom,dan tasan in har zai kai kowa gidan ta zai bata lokaci,,wannan plan din jummai ne,,Har dan tsalle ta buga tai daki,Sa'a ta kada kai, tare da sauke labule,dan tunda taji horn din motar shi ta leko,duk tana ganin abinda Zahra tai,,ta kada kai tare da murmushin mugun ta,,. 8:30 ya shigo,da mamakin Zahra sai ganin shi tai,,Ko ta kanta bai bi ba yai sama,,yaja glass din,,yana tunanin ya zai tarar da Sa'a, dan tunda zai shigo ya fada mata,,amma da mamakin shi da fara'ar yaga ta taho,,ta dan lafe a jikin shi, Tuni ya sau ajiyar zuciya, ta zaunar shi kamar mai rada tana mishi sannu da isowa,ta zame takalmin shi,ta cire socks din,Murmushi kawai yake mata,,taje ta kai kayan kitchen ta dawo,, hau,Kusa dashi ta zauna tana hura mishi iskar bakin ta, "Sannu,.hannun ta ya kamo," Kinyi kyau,tai murmushi, "Muje kai wanka,zaka ware,Allah sa ka ci abinci baka bar min kan ka da yunwa ba,ta wani marai rai ce, Jawo ta yai,da halamar jin dadin kulawar da take nuna mishi tun fitar shi zuwa yanzun,,. Bayan yai wanka,Ta zuba mishi abincin da Fadeela ta taho musu dashi,,bashi ya sakko ba sai Kusan 11,da mamakin shi Zahra na parlour, Yai turus,," A,ke bakiyi bacci bane har yanzun?? A kai kaice ta kalle shi, Ta watsar,"Bana bacci da wuri ni,,Ya kada kai, kan ya kulo kofa,ya mata sai da safe,,Da sauri ta sha gaban shi,,"Nifa yunwa nake ji,,Ya kalle ta da mamaki,,"Yunwa kuma??..Ta daga kai,,"Ince Sa'a ta aiko miki abinci da yamman nan??Ta daga kai, "Ba na ci ne,dan bansan mey aka bar bada min ba wallahi, yai murmushi, A ledar da na baki babu abin ci??..Ta fara marai rai ta,ita a dole so take ta bawa Sa'a haushi in ta rike shi,,"Kayan zakin zanci na kwanta?..Tab..A hasale yace" Toh ki kwana da yunwa..Ya haura sama ya barta nan,,Tai kwafa,"Ba dan kai nai ba,,. Washegari sukuku Suka tashi,barin shi da yake ga yau ba Sa'a gare shi ba,dan kwana 2 nan,sun musu wuyar fassara, babi guda Suka ware musu a Rayuwar su,,. Zahra ba zama,dan jummai tace kar tai sanya,,sai dai gaba daya lamari haka ya tafi sukuku,dan barta da kyallin chan, bangaren tarairaya an baro ta a baya,. Da yazo ma Sa'a sallama harda kukan ta,, Dakyar yai ta lallashi,, dan ji tai wani mugun kishi ya tokare ta a makoshi,sai da tai ta Inalillahi tukun ta samu sa'ida,Ashe haka kishi yake??Ashe mugun ciwo ne??..Lalle dole in ka kasa control da shi yai maka illah,Ranar bacci sai barawo ga Sa'a,,. Ita kam yana shigo wa dakin yasha freshener,sai dai sirrin kamshin Sa'an shi daban ne,,Shi ko hade ran da Zahra take bai kula ba,,fatan shi Allah bashi ikon adalci... Gashi dai Yayi Iya yinshi ganin yayi Adalci, amma abin yaci tura,,Sa'a kadai ya mallakawa kanshi da zuciyar shi,, duk itama Zahra ya yaba da yadda ya riske ta,sai dai d"ai da'i da sallah ta gagara tashi,, Har ya dawo tana yadda ya barta,bata da niya ma bare ya taimaka mata,,Yai murmushi, ya tuno da Sa'a, Zai latti a masallaci tace yaje zata Iya,sannan ya dawo ya tarar ta a kan sallaya,,baya yai kawai ya koma parlour,, Bangaren Sa'a kawai ya sawa ido,,Yana murmushi, yaje tashin ta yaji tana karatun Qur'ani, Tuni yaji tausayin ta, Allah dai yasa tai bacci yau,,.Sai da yaji zubar ruwa a bayan gida ya koma dakin,zanin gadon ya yaye ya sanya wani,,kan ya dan kishin g'ida,,Bacci ya sure shi,,Farka wa yai ya ganta a kwance itama,,kare mata kallo yake,Tana da kyau na nuna wa Sa'a, a dabi'a tana da ita mai kyau,ya rasa meye dalilin da yasa karfi da yaji Zahra ta chanja hali??..Yanzu yar gatse gatse ce,,Tashi yai ya shiga bandaki ya watsa ruwa,ya fito ya shirya,9:20.,yasan yau kam bamai kawo musu abinci, dan jiya ma Hajiya bata kawo ba,duk da yai wa kowa cefanen ta da yamma. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/22, 7:02 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 48_Parlour yai,kamshi yaji ya karade gida,ga nan kofar glass din parlourn Sa'an a bude,,ya lumshe ido yana shakar kamshin,,gudu gudu,Sauri sauri ya karasa saman nata,,bata parlour, sai yai daki,Halamun kashe shawer yaji,Ko'ina sai kamshi ke tashi,a gadon ya kishin gida tare da jawo rigar baccin data cire kan ta shiga wanka yana shaka,,Ta bude kofa,daure da Towel babba,, har ga Allah ta tsorata, dan bata ji bude kofar shi ba,A razane take kokarin komawa bandakin kan ya kira ta,, Towal har yana kokarin kunce wa,,Gaban ta ya fara dukan uku uku,,Da sauri ta rintse ido, kawai haushi ma ya bata,,Sai fa tayi da gaske wannan kishin Hafeez din kar yai mata cikas,Jawo ta yai,bama ruwan shi da lemar dake jikin ta, harda sakar ajiyar zuciya, Da sauri ta nemo hankalin ta ta fara kiciniyar zame wa,sai dai ina,ya kara kan kame ta,"Ka rufan asiri Fa Baby,,. Wallahi ba ruwa na,,ya dan sassauto ta,"Gaisa wa fa nazo muyi,ko ya Haram ta,da sauri ta daga mishi kai,,.."La'ila Ha'illalahu,,..Da sauri Suka juya jin muryar Zahra,,kallon Hafeez take da tuhuma,dan ita a zaton ta daga badaki suke,dan duk jikin shi ya jijike da ruwan jikin Sa'an,, Ta maka wa Sa'a harara,,"Haka zamuyi da dake??,..Ni zaki gwadawa BARIKAN ci ranar kwana na,,. "ke dan Allah ya isa,mey ta miki na BARIKI??,.. Ba tasan lokacin da Shima ta maka mai harara ba tana hawaye," Nidai aka shiga hakkina Wallahi ban yafe ba,,tai kasa tare da mako musu kofa..Sa'a ta dau hijab tana kokarin sawa ya rike,,Da sauri taci mur,,"Ina kwana,,,kaje pls yanzu zan sakko,.ka kuma rarrashe ta,dan baka kyauta ba,,Yai dan karamin tsaki,,"Mey nai ne Wai tukun??Ta karbe hijab din ta,"kaje zan fada maka inna sakko,abinci na dining,,Ta fara janshi a hankali, yana kaiwa tsakiyar parlourn ta juya da gudu ta rufe kofa,,.Toh mey suke nufi dashi??Suna nufin sun fishi sanin addini da adalci kome??..Yai kwafa,tare da sakkowa kasa,,. Dakin Zahran ya nufa,ta hada kai da gwiwa sai nadar kuka take,ya zauna a bakin gado abin na bashi mamaki,Toh mey yai na kuka har haka??..Dan ya taba Matar shi shine ya shiga hakin nata komai??..Yadai daure yace"Yanzu Zahra dan abun nan danayi ne har na chan chanci kimin fitsara?,,Tuni ta kara kuluwa,,"Au,dan abu ma ka dauke shi??,,wato dan kaga ina bacci shine zaka silale harda zuwa ka mata wanka??..Da sauri ya dago,."Wanka kuma?ke bana son shirmen nan naki fa,,.Gani kikai mun fito a bandakin komai??ta kada kai..yace"Toh ban son zargi,,Gaisuwa kawai naje muyi,,.A ranta tace"Oho,dan tsabar BARIKI ne yasa ta rungume shi kenan?.. Badan na shigo ba Allah ne yasan abun da zata mai,,Ta goge hawayen ta,,duk da haka bata gamsu ba sai da tace"Amma ran kwanan ta ni Ai sai 10 ko 11 nake ganin ka,,Ya girgiza kai,, Ashe haka mata biyun suke??..Tab,shikam bamai sa mishi Tension,,. "Zan gyara Toh, ki shirya kizo Dining muyi break,,yai waje bai jira mey zata ce ba,Da azama tai bandaki tai brush ta dan watsa ruwa, powder kawai ta mitsika,,. Dakyar ta tattara nutsuwar ta ta Shafa mai da dan light make up,, sai dai tai kyau,,ta feshe turare masu kamshi kan ta zabo wata shadda milk mai dan laushin jiki,tasha aiki da zare brown da stones, Riga da skirt ne,ta danyi dauri a saukake single, ta sake fesa turare,,,ta kalli mirror kayan ya kamata,tai murmushi kan ta fito parlour,, Dai dai shi kuma ya fito a dakin Zahra,,Ya Ilahee,, Rokon Allah take ya saukaka mata kishi.,, Kallon ta yake yadda take wani rausaya kamar bata son taka benen, murmushi ta sau mishi da taga ya dan harare ta,, wato fishi shi adole yayi??Ta ja mishi kujera,ba musu ya zauna,.kan itama taja ta zauna,,ta daura hannun ta a kunne halamun " Sorry?Yadda ta langwabe kai bai San sanda ya sau fuska ba,,Ya kai hannu zai kama hannun ta,da sauri ta zame,Tana dan dariya kadan tace mishi"Kai Baby mu akwai Neman fada,,ya dan harare ta kadan,,Tai murmushi, "Allah ni na yafe gaisuwar nan taka nan gaba,,zan na sakkowa mu gaisa,,Ya kara hararar ta,,. Tai murmushi,, yace" Toh ni ban yafe ba, Ba wacce nake tsoro,,Tace "Toh,it's Ok,,Bazamu kuma ba,amma kaima ka kiyaye mu,,Ya dungure mata kai,,Dai dai Zahra ta fito,,.Turus ta tsaya,,ita kam mey zatai wa Matar nan ne ta fita har kar ta??..Tai kwafa kan ta karaso,,Kujera ta ja ta kusa dashi ta zauna,ta dallah wa Sa'a harara,.ita kwa sai tai mata murmushin Da yafi komai ci mata rai, wannan munafukin murmushin Sa'an ba karamin tsanar shi tai ba,," Sis ina kwanan mu??Ba kunya ta amshe,,ta juyo kan Hafeez da wata murya tace"Baby An tashi lafiya??Ya yage baki,, "Lafiya Unique,, Da sauri Zahra tace" Au,Ina kwana Yaya?,,Sa'a ta kunshe dariyar ta,kai Lalle wannan Baho ce amma??Ya kallo ta da mamaki,,Ashe fa ko gaida shi batai ba koh??Ya kada kai, "Lafiya lau,,Ya kuka tashi??Zahra tadan harare shi cikin wasa,"sai yanzun zaka San ya na tashi Fisabilillahi Dear??Suka zuba mata ido shida Sa'a,, ta cigaba cikin gwalli," Dakyar fa nakai kaina bandaki,, Ta kallo Sa'a, ganin yadda take kallon ta yasa ta cigaba da fi'ilin ta,ita adole zata bawa kishiya haushi,,bata San bada kanta take ba,..Banza Yai da ita yana zuba Tea,,Tuni zuciyar Sa'a ta fara tafarfasa,,amma ko a fuska bata sake ta gane ba, sai ma murmushin kara tusa bakin ciki da take mata,, Amma dan ta kashe zancen yasa tace "Toh kiyi serving namu gashi Baby na jin yunwa,.ta harare ta kadan kan ta fara zuba wa Hafeez din,,da in ranshi yai dubu ya baci..Ganin bata zuba mata ba yasa ta jawo ta zuba,ta hada tea Baki kawai,,Ya kallo ta, murmushi ta sau masa,Tuni kwa ta yaye mishi kunci,,duk loma 1 sai ya kallo ta,, Sai kwa ta sau mishi murmushi, shaf sun manta da Zahra,,. Tsaki tai,ta tashi tai kitchen,indai dan ta mata break ne toh ita zatai launch din ta,yar BARIKI kawai,.Ai kamar jira yake ta kauce ta fara bashi a baki,,,Gogan ya ware harda zuba musu pic,,Tace suje kitchen su Taya sis aiki,ba musu ya bita,sai ganin su tai suna dariya, Sa'a tace" Sis,dame zamu tayaki??tai mata kallon banza,,"Na yafe,,tai murmushi kan tace"Ok,ta juyo ga Hafeez, "Baby,bari na wanke kwanika,.ya kada kai," Toh muje na Taya ki kwashe wa,,Ta kallo Zahra,"No tnks, ka Taya 6s,.tai waje,. Tana hawa sama tai kitchen ta kulle,kuka ta fara,tai ta wanke fuska,ta dauraye kwanikan ta,,kan tai daki,,ta kwanta bacci,kiran sallah ne ya tada ta,,ta tsaya gaban madubi,Allah ya sota fuskar ta washe,,kai Kishi bala'i ne,Ya Allah ka saukaka mana. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/22, 10:39 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 49_Yau sati guda,kai karar Zahra 3 wajen Hajiya,yau kam ta kudiri musu zuwan ba zata,shi yasa ko Zahran bata sanar wa ba..Da yamma ne,Lokacin kowacce na dakin ta,, sallama tai,kan Zahra taji,,Da gudun ta ta fito,ta kan kame ta,,Tace"Toh bari mu zauna tukun,Ta cika ta, Suka zauna tana kallon ko'ina, a share amma ba kamshi,ba wari,,Ta kallo ta lokacin da ta dakko Lemo,ta ajiye.,"kai Hajiya naji dadin zuwan nan Allah,. Ta zauna,chan tace "Au,.taje ta dakko cup,Sannan ta zauna zaman gaisuwa,.Bata tashi ba sai da ta zube mata korafe korafe sun fi a kirga, ita kanta sai da ta Gaji,,. Ta kallo ta," Rakani dakin yar uwar taki toh Zahra, ta bata rai,"Hajiya a kira ta ta sauko man,.Tai murmushi, "Aa,bari itama naje dai,.Sukai saman,,Ba ko kwankwasa wa Zahra ta ja glass din,,Turus sukai,Lokacin da suka tarar tana rera kira'ar ta mai zakin sauraro,cikin Suratul Yusuof,,earpiece ne a kunnen ta, ya zame mata dabi'a karatun Qur'ani da safe da yamma.,inkwa bata cikin tsarki,toh tana tare da Earpiece a kunne ko ta kunna Mpn ta tana bi cikin nutsuwa, A jikin ta taji kamar mutum a kanta,a firgice ta mike,,.Zahra ce tana wani yatsina,sai Hajiya a gefen ta, Cikin fara'a ta cire Earpiece din cikin nutsuwa,da tsabar girmamawa tace" Sannu Da zuwa,.ta mike tare da nuna mata waje"Bissmillah, Zahra sai harara take aika mata,,Hajiyan ta zauna,Zahra ma ta zauna a kujera kusa da Hajiyan, ita a dole mai uwa a gindin murhu,. "Ina wuni Hajiya?Fuska sake ta amsa mata,Ina su Tasleem?.."Tana Gaida ku,da tare zamu zo,,Ta dukar da kai cikin kunya tana murmushi...Woo Sa'adatu BARIKI.. Tashi tai ta nufi kitchen, sai gata dauke da flate da cups da ruwa da lemo,,Tana zuwa ta durkushe gaban ta, da murmushi fal fuskar ta, ta tsiyaya mata ruwa,ta tsiyaya lemo,Ta dau lemon da girmamawa ta mika mata,. Cike da fara'a ta karba," Sannu,,tai murmushi. Ta tsiyaya Tace"Sister ga ruwa,,Ta tabe baki kan ta karba tana yatsina, duk Hajiyan tana kula da su,,tasan kurba zata ajiye Sa'an ta karba da sauri ta ajiye,,.shiru har yanxu Zahra ba taji an fara bam bami ba,sai ma fadan da Hajiya ta musu dukan su,kan ta tashi,,Sa'a Tace"Toh mun gode,a gaida su Tasleem,Tai murmushi, "Zataji,. Suka fito ita kuma ta koma da sauri,.Har sunje bakin mota ta karasa da dan saurin ta,..Tadan rissina kadan," Hajiya,ta juyo,mika mata ledar, karba tai tana kallon Sa'an, Tace"Ku gaida gida,Tace"Da wahala haka??Toh an gode,Sa'an tai kasa da kai,,Hajiyan tai murmushi,"Allah ya muku albarka,. Suna tafiya ta juya,Zahra ta dauro bayan ta.. "Chusa kai ba kwarjini,,.Chak ta tsaya, kan ta juyo da murmushi a leben ta, Hannu ta mika leben ta kan tai kissing hannun ta nuna Sa'a dashi" Muahh,,Kan ta juya,Tuni ta kara kuluwa,,"Karuwar kawai,,Ta daga mata kafada,,kan ta haye saman ta tana kara bata haushi ta baya,,. Ta bita da harara,ba abunda yafi kona mata rai sama da yadda kota takale ta bata kulata,sai dai ma ta bita da wannan murmushin da ta kira da munafuki,,. Yau watan su guda,duk yadda Zahra taso taga sabani tsakanin su ta kasa,Sa'a ta tsare gaba ta tsare baya,,.A ko yaushe Hafeez rawar kafa yake akan ta,da girkin ta da ba nata ba,,.Sai dai yau da Jummai tazo ta bata dabara,,girkin Sa'a ne, amma taci uwar kwalliya da dogayen brown din nyty,,Yau tasan duk tsiya sai Sa'a ta kwana kukan takaici,. By Feenat Ja'afar ®ONLINE HAUSA WRITER'S.  Posted by Feenat FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG BARIKI IYAWA 6 [10/2, 7:32 AM] Feenat Ja'afar: [1/23, 12:51 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 50_Tana jin horn din Motar Hafeez ta dan budo kofa,,ta fada gado ta rike ciki,,yana shigo wa ta kwala ihu,,"Zan mutu wayyo Mamy,,Dai dai Sa'a ta fito zata sakko tarar shi kamar yadda ta saba,,da gudu yai dakin Zahra,, tam ta tamke ido tare da rike ciki,, Ita Wai mutuwa zatai ya kai ta gida,,Turus Sa'a tai,.Kai da gani kasan karya ne,,amma shi ina,ya rude da jin tana ambatar mutuwa,,Da sauri Sa'an ta karasa,tare da kamo Zahran"Sannu sis,Cikin ne??..Hafeez ya kallo Sa'an, "Unique dan rike ta na kira Dr Seuss, Da sauri ta rukunkumo shi,," Nidai kar ka tafi,.zan mutu,,....Kut...Humm humm,.Lalle,Turnuku kenan,Wai Fadan Ibilisai,,Yaro bai ga ba,bare ya raba,Sa'a ta kan kance ido ta ciki,Lalle Zahra bata San wace ni ba??..Amma yau,zan fara ware mata True colour na Wallahi, Daure wa tai bata nuna musu ba,sai ma sannu da take ta kwararo mata ba adadi,,Sune har 9,amma dai dai da second,zahra bata daina kururuwa ba..shifa har ga Allah bai gano karya Zahra take ba,dan tana da ciwan ciki,musamman lokacin period. "Unique!.. Ta kallo shi, " Na'am Baby,,.Kije ki kwanta,in ya ware zan taho,,ta kada mishi kai., "No Baby,,Kawai ka kwana da ita,,Kaga ciwan nata,,Ya kalle ta zai magana tai murmushi," It's Ok,,sis Allah baki lafiya,,Ta juya tana daga mishi hannu,, Tafiya take da wani irin yana yi, sai yanzun ya kula da kayan jikin ta,, Riga da wando ne yan kanti,wandon Brown robber ne,ya dan bude ta kasa,sai rigar mai net 2,Orange,ta baya tai zalolo,ta dame mata kugu,ta gaba ta dage,,tai parking din gashin ta a tsakiya tare da daura siririn gyale Orange,,Da kallo ya bita har ta rufe kofa,,Ya lumshe ido,, Zahra ta na kallon shi,a ranta tana "Yau kam sai gani daga nesa,.Ko minti 5 Sa'a batai da fita ba ta ware,,tare da daura kan ta a kafar shi,,. Sa'a na shiga daki tai wani murmushin mugun ta,, Tuni ta hau changing kayan jikin ta.,''Zahra kinyi na kudin ki,,en my time start now!!.. Ko'ina tabi ta kara fesa daddadan turaren ta,,ta dawo daki ma haka,,Ta duba agogo 10 saura. Dube ta fara,ta hango gwangwanin Air weak a mirror,,.. Tadi take mishi,,tamkar ba ita ta gama ihun yanzu zata mutu ba,nufin ta ta janye hankalin shi,sai dai ina, gaba daya shi hankalin shi yana ga Unique Ladyn shi,dan tunda suke yau ya taba ganin ta da English wears,, Murmushi yake yana kallon kofar waje,ji yake kamar ana janshi sama wajen Sa'an shi.. Duk Zahra na kula dashi,Tuni ta mike a cinyar tashi ta fara huci,," Wato har yanzun kwakwalwar shi naga Sa'a?? Gangar jikin shi ce kawai a nan??Tai kwafa tana kokarin cire doguwar Rigar saman Suka ji an kwala ihu,,.A zabure ya mike,kamar Sa'an shi yake ji fa??Zai waje Zahra ta tare hanya,,"ina zaka kuma??Ya kallo ta yana kallon kofa,,"Bakiji Kamar ihu bane a gidan??Ta maka mai harara,,"Ni banji ba,,Yayi dai dai da lokacin da Sa'a ta kara sakar wani ihun. By Feenat Ja'afar ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/23, 2:02 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 51_"Ahhhhhhhhhhhh....wayyo Allah... Inalillahi... Da gudu ya fito, har yana tun tube,,itama Zahra ta biyo shi da kira..a tsaye ya same ta a kan gado..daga ita sai wata guntuwar rigar bacci pink,mai hannu siriri da breast cup,da wandon ta iyakar shi cinyar ta, Shima kuma duk net ne,,da gwangwanin air weak a hannun ta halamar zata daki wani abu...da sauri ya karasa Shima ya Dane gadon,,tana ganin haka ta kan kame shi,, " wayyo Baby,bera..bera ne..tana nuna mishi bayan kofa..tamkar Zahra zata hadiyi zuciya taji,,ita kam ta gamu da muguwar yar BARIKI,, ji tsinannun kayan jikin ta??yanxu shikenan Kila ta wargaza mata plan.. Da ihu ta kwalla mishi kira,,suka saki juna suna kallon ta,, Da sauri yace"Zahra ki shigo mu kwana a nan.,dan kinsan wlh nima tsoron Bera nake,,.tuni ta fara hawayen bakin ciki,ta juya zata tafi ya kira ta,.a zaton ta ko cewa zai jirani,sai yace"Dan turo mana kofar please,,.ya wani marai rai ce, Sa'a ta sau mata gwalo,tare da kashe mata ido daya,Ta rungumo Hafeez din da wani salo,,Tuni gogan ya sau ajiyar zuciya...kafa ta sa da masifa ta bige kofar, "Bazan rufe ba,macuci kawai..Ina,shi bai ma san tana yi ba,,Daki tai da gudu,sai kwa kofa ta tafi luuu ta rufe kanta..Ya kara kan kamo ta,,." My Unique,. Love you,, Nan ta biye mishi,sai da ta mantar bayanin bera kan ta zame tace"After Dinner,.. Yau kam ta nuna mishi ainahin wace Sa'adatu BARIKI, Duk wani abu da tasan zatai ta faran ta mishi a daran nan tayi,,Sai da ta tabbatar babu wani gibi da yarage na nauyin shi akan ta,,Hmm Sa'a Sa'a, Lalle she's Unique a wajen shi,,. Fir Zahra taki fitowa Break,shikwa kamar jira yake Suka kara yin sama bayan sun gama cika tankin su,,dan yunwar cikin ta ta fito 12,ganan abinci a cikin flaks din ta,ba kayan Sa'a ko 1,sai dai kofar glass din a bude tana Iya jiyo dariyar da suke kyalkyala wa,,Tai kwafa,tana gama cin abincin ta makawa Jummai kira,,"Banza kawai,wannan dabarar taki banda ciwan zuciya ba abinda ta sa ni,,Jiya kwanan kuka nayi,sai da nai Dana sanin aikata hakan wallahi,, Daga chan Jummai tace "Ki jirani anjima kadan,,. Sai bayan la'asar suka sakko kasa domin cin abinci,tana kallo a parlour,da sauri ta dauke kanta,dan wannan fitsarar bazata juri ganin ta ba,zuciyar ta zata Iya bugawa,a kujera ya zauna,1 setter,hannun su rike da juna,Sa'an ta zauna a hannun kujerar,, Ta kalle ta,," Sis,ya kwanan jikin??Ta maka mata harara tare da sauya tasha ta manna mata,,ta kallo Hafeez, "Baby,koh dai jikin ne ya dawo??Yai murmushi," Zahra bakya ji ne??Muna miki ya jiki..Ta kallo shi,, "Au jiki?kasan da jikin ka barni ni kadai?,na mutu ko nai rai baka da asara,, Yai kicin kicin"Ke Maintain fa,,Ina ce ware wa kikai kina ta dirka firar ki,sai da na tabbatar kin warke kan na tafi,.Baki sake take kallon shi, Dan haushi kasa masa magana tai,,Sa'a tace, "Baby yunwa,,ta ruko hannun shi tana marai rai ce fuska.." Oh sorry,.Muje,.Sun zauna ya kallo Zahra, "Kizo muci man,ko ta dazu zaki mana??..Da kamar kar ta tashi,sai dai kuma ta taso,,Sa'a tai serving nasu,ta tura wa Zahra nata,su kuma ta zuba musu flate d'aya,, A baki take bashi,shikwa Tuni ya kara narke wa kamar yaro,,Zahra in banda chaka cokali ba abinda take tana hararar su,,in ta bashi loma d'aya, sai ta kai loma d'aya itama,tare da aika mishi murmushi,,. A haka har Suka gama,abincin da Zahra bata ci ba kenan,,Kitchen din Zahran Suka shiga,Suka kuskure bakin su,,yai ma Zahran sallama kan zai fita shi kam,,sai da suka zo dai dai kofa,ta dai dai ci Zahra na kallon su kan ta rungumo shi,," Ka kula min da kan ka,tai mishi kiss a gefe gefen kumatun shi,kamar irin larabawan nan,,shikwa sai yage baki yake,, Zahra bata barke da lamarin ba,sai da ta ga Sa'an na wani shagwabe fuska,,"Please Baby,,Come back soon,,U know am gonna missed you.. Shikwa harda dan bubbuga bayan ta halamar lallashi,, Yana "InshaAllah my Unique, Love you,,Yama manta da zahra na wajen,,Ta cika shi tare da dan bashi light kiss a lips, tare da goge bakin dan Jan baki ya taba" Love you too Baby,,.Dakyar Suka ban bare yai waje,ina Zahra huci kawai take,.Ta dawo daga rakiyar .. Tarar ta a tsaye tana huci,,.Dariya ta fara harda rike ciki,,.Tuni Zahran ta kara kuluwa..Ta rasa mey zata ce,sai cewa tai, "Karuwar Kawai,,ai ba sai Kin nunan kin Iya BARIKI ba,dama nasan da abar ki kika zo,,.ta harare ta tare da kama kugu.. Tako wa tai tazo gaban ta,tare da dafa kafadar ta,,da sauri ta zame hannun tana harar ta..Murmushi tai kan ta kada kai. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [1/23, 3:54 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 52_"Kwarai,fadi da ihu ki kara da wayyo Allah,,Rausaya take da kanta,,tamkar wata K'adangaruwa "Sa'adatu nake,,,tai murmushi da ya baiyana kyawawan hakwaran ta,, ta rausayar da kai gefe,, kan tace"BARIKI IYWA Ba,," ehe."BARIKI ikon Allah ba,ta nuno kanta da hannun ta"Ni din nan da kike gani na wlh naci dubu sai ceto,, of course,Karuwa nake,amma A wajen Hafeez,,,. Kara dafata tayi,kan tace"Ya kamata kisan fa Qawata "BA'A FAFE GORA RANAR TAFIYA,,sama taka kar kija da BARIKI wallahi,.Dan ke da kanki kince da Bariki na na shigo,,kinga kenan babu wani guntun salon BARIKIN ki da zakiyi ya firgita ni..Ta sauke hannun ta kasa kan ta dan ja baya,,Ki sararawa kanki,gudun kar ki shiga gona ta,.dan duk tsiya ta bazan shiga taki ba,.Jiya kin min d'aya,kar ki kara mai maici..Ta dafa kafadar ta ta matso dai dai kunnen ta,kamar mai rada,tace"Be a good girl.. Ta dana mata hannu,kan tai gaba tana jujjuya mata wani gu.. Daskare wa tai,tama rasa na cewa,.Tasan dai a doke, karya take ta daki Sa'a, dan a dire take, ta fita kauri,sannan komai yinshi take Cikin cire shakku,.Daki tai,.Tana daura wa da kunce wa,,tana haka Jummai tazo ita da wata Qawar ta,,Anan Suka lalace suna kunce wa suna Daura wa, Wai nan duk mafita da zasu ja da Sa'a suke nema.. Parlour Suka dawo,lokacin Sa'a ta sakko jera abinci,,tun daga habaicin da suke ta gano su,saboda haka inda suke ma bata kalla ba,,tana jera abincin ta tana wakar "Charaman Dudu,.Ta juya tana kada musu bayan ta,, Suka tafa,Jummai tace. "Fago guda kenan,Tana jin Su,,aiki ta hau,tana kamalawa ana magriba,tai sallah,tukun ta hau make up,,ta dakko wasu shegun kaya,,Jeans ne skirt din,iyakar shi gwiwa, ya dame ta tam,.ta juya tana kallon bayan nata,,tai murmushi," Ga Fago fa ya fito,,tai murmushin keta,kai Lalle Jummai, tama bata dariya,.Tasa rigar Green mai garen hannu,sai Top din na jeans,sanin Hafeez yafi son ganin gashi a tsefe yasa ta dau damarar gyara shi,.tai parking din a tsakiya,ta tattare yai doughnut cif a tsakar kan,ta dau dan kunne barima green tasa,.tasa flat shoes din ta green,ta kunnan burner ta tsaya a kai,kayan ta suka dau kamshin turaren,ta kashe ta sake feshe turare a Dakin da parlourn, ta dau katon hijab da wayan ta,ta cilla chewing gum a baki,tana kas kas ta tako, Suka bita da ido,,Har ta sakko suna Binta da ido,,tai murmushi"Hi Guys,. Da sauri Suka dauke kai,Zahra taja tsaki,,Tai murmushi kan taja daya daga kujerun dining ta zauna,,K'afa d'aya kan d'aya ta daura tana Taunar chingum,,Waya ta dakko,ta fara game,, Zahra ta zungure su Suka ci gaba da tadin su,,. Shigo war kira ne ya katse ta, ta dubi wayan tana murmushi,cikin wata mayaudariyar murya tai sallamar,,duk Suka juyo kallon ta"Assalam Alaikum,.. Tai murmushi mai sauti dan jin abinda yace,,tace" Allah ja min Ran Namiji d'aya tilo ga mata biyu,.Tuni ta hau mishi kirarin nata dake kara fasa mishi kai har ya jima yana waya da ita ba tare da ya Sani ba,,Murmushi take cikin salon da ita kadai ke Iya sarrafa lamarin shi,,."Ya akai Toh your Royal Highness,, Da Girman kujerar ka,,yai murmushi, bakin nan yaki rufuwa, Sa'a, ta daban ce,shi yasa dan ya kira ta da "Unique, bai jin kom... By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [10/2, 7:35 AM] Feenat Ja'afar: [1/24, 1:42 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 53_Yace"On my way,,mey kika tana nadar min?,,Tai fari da idon ta, wanda ya kara kular da Zahra,,"Farin ciki, So,Kauna,,Tare da ni Sa'ada,, r all yours Janeeman,,.Ya sauke Ajiyar zuciya, yayin da yake kwana da mota,,yai horn,mai gadi ya bude,,Duk da taji shi,hakan bai sa ta sauke wayan ba,ta ci gaba da bashi Hot kalam din ta,,Ta zira hijab,,Rike da waya ya shigo,bakin nan tamkar gonar audiga,,hmm,Namiji tamkar wawa ne,mudin ya dace da mace Yar siyasa,,Bata ko kula da su Zahra ba taje ta Dane abinta,, cikin hijab din yake kokarin shiga kan tai saurin ja da baya yaga su Zahra,,huci take tamkar kububuwa,,.Wannan iskancin har ina?..Ita ran girkin ta bata isa yai mata hakan ba,,. "Sannun Ku, baki mukai??Ta ruku hannun shi suna kallon su, Jummai ce tai karfin halin gaishe shi, ya amsa kan ya juyo kan Sa'a, ta sau mishi murmushi sukai sama.. Suna hawa ya rukun kumo ta tare da cire hijab din suna kyal kyala dariya,,Ganin ta a kayan,yasa kawai ya tsaya jujjuya ta yana kallo,," Wow...U look so Beautiful in Green tonight..Tai kada ido,tare da sakalo wuyan shi, Tnks Dear,. Yace shi a kawo mai abinci nan,dan baima son sauka,.Zahra na ganin ta hau sama da abincin ta kallo su Jummai, "Ku jirani,,ta tashi tai saman. Tazo bakin kofar,ba ko sallama,, "Dear, su Jummai zasu tafi,,Ya tsaya yana kallon Sa'a, ta ajiye cokalin abincin da take bashi,kan ta tashi," Yi zaman ka,Bari a sallame su Dana Taxi,.yai murmushi, "yauwa Thanks,.Rigan shi ta dauka,ta Ciro 500,tai yo bakin glass din,.Ta yaye labule,," Sis,gashi a basu na Taxi,,en kice su gaida gida.. Harara ta maka mata,taja dogon tsaki,,kan ta juya,dan tasan Tunda ta fada a gaban Hafeez tofa bazai ba kota ce ya kai,ta juya.a hankali Sa'a tace "Umma ta gaida Aisha,,..Ta juyo tana murmushi,shi har ya cigaba da cin abincin shi,dan baida jumurin yunwa. Ranar Juma'a Yace su shirya zasu gidan su Hajiya,..Zahra keda Girki,.Amma ita a dole dauki ko Girki batai ba,. Tun alhamis ta soya kajin ta,tana tashi ta hau pape chicken,,Ta zuba katon flaks,,ta shirya cikin wani purple da ratsin pink din Swiss less,. Taci make up kamar mai shirin zuwa zaben Miss Universe,,Sun fito,fir Zahra tace bazai hau saman ba,Ya mata waya ta sakko,,.Takun ta ya fara ji,Tuni ya zubawa stairs din ido,,harda mike wa, Rabon shi da ganin ta tun jiya da dare,,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. BARIKI...IYAWA 54_Wannan k'ayataccen Murmushi ta sau mishi,,taku take sannu a hankali, tamkar Tausayin Carpet din, Zahra ta dalla mata harara tare da kau da kai daga kallon ta,Zuwa yai ya karbi kwandon hannun nata,ba musu ta bashi,ta gyara gyalen ta tana kallon Zahra,mudin bata gaida ta ba toh sai dai su zauna haka,tai Murmushi, "Ina kwana sis?Ba tare da ta kalle ta ba tace" Lafiya, ta kallo mutumin nata,da kawai Murmushi yake, sosai yana yabawa Sa'a ta ko'ina,bata da girman kai,bata la'akari da itace uwar gida,tsawan zaman su bai taba ga Zahra ta gaida ta ba,sai dai ita ta gaishe ta,ba gajiya wa... shi yasa take kara shiga ranshi,,.Zahra tai gaba,,yana ganin haka yai saurin zuwa gare ta,, Taja baya tana murmushi,, "Ina kwana daga nesa,,Ya harare ta," Bana amsawa,,Dama dazu ma ina kule dake,kinsan zan zo kika kulle kofar ki ta ciki koh??Tai Murmushi, "So sorry,,yanzu dai muje kaga sis ta fita,,Ya kara hararar ta kan yai waje,,Suna zuwa ya danna Remote motan ya bude,,Da sauri Zahra tai gaba tare da bude gaba,Sa'a tai Murmushi,, Hafeez Yace" Uwar gida ke zama a gaba Zahra,,Ta kalle shi ta watsar,,"Kai ka Santa,,nidai ba mai fitar ni nan,,Zai magana Sa'a ta Riga shi,, "No,Nama fi son Baya Habeebi,,Sis ce ai,,No worry,,Sai ta zaga kofar gefen da zai na ganin ta ta mirror, ita ai baya zai fiye Mata gaba,yadda zata kara bata haushi,.Da sauri ya bude mata,,ta shiga,ya rufe,yasa kwandon a boot,kan ya shiga,aka bude mishi gate ya fice,,Sai da ya tsaya,ya kwa saita mirrorn saitin ta,,Suna hada ido ta kashe mishi ido d'aya,, yai murmushi,,. Tafe suke cikin nishadi,Zahra sai kokarin tusa magana take,ganin yana murmushi yasa ta dage,chan dai ta kula,Ashe fa sai ya kalli mirror yake murmushin,,ta juyo baya a fusace,,Dai dai Sa'an tana mishi fari da ido kai a langwabe., suna hada ido da Zahra ta yage mata baki,,Ta harare ta sauke kan Hafeez dake kallon hanya kamar bai ba,,. Da sallama Suka shiga,Da gudu Tasleem ta fito,ta kama hannun su, Zahra ta zame," Ni kauce min,ina Hajiya?,Sai kwa tai kan Sa'a ta kan kamo ta,, Sai ga nan Hajiyan sun fito da Zahra daga kitchen da fara'ar ta, Sa'a na ganin ta ta maida gyalen ta saman kai tana murmushi,,Ta zauna,Zahra ma ta zauna,yayin da Sa'an tai kasa cikin girma mawa tana gaida ta,, da fara'a ta amsa,Hafeez ma yadan zamo yana gaida ta,. Suna haka Abba ya sakko,.Shima fara'a fal fuskar shi,, Tuni Sa'a ta kara dukar da kanta kasa,,Suka gaida shi,,.Suka dan taba fira dasu,Yace Hafeez yazo zai bashi sako Suka fita,,.Hajiyan ta tashi ta koma kitchen, Sa'a tace Tasleem ta dakko kwandon suje kitchen din,ta cire gyale ta ninke tare da daura wa a kan jakar ta..Zahra ta tabe baki tare da gyara zama tana sauya tasha,,. Hajiyan ta dago,Tasleem tace"Gashi inji Aunty Sa'a,ta ajiye kwandon, Hajiya ta kallo Sa'a, "Bakya gajiya kekam,,Tai murmushi tare da zuwa ta karbi muciyar," A haba daga zuwa Baku ko huta ba??basshi Yan nan,na ma kusa,"A ba komai,zamu karasa da Tasleem, Ta kada kai, " Toh,Allah dai ya muku albarka, Tace"Amin,,ta fita a kitchen,Tasleem ta kan kamo ta "Kinji yadda kullum kika kawo abinci yadda Hajiyan Mu ke yabon ki kuwa?.kai Aunty u r amazing,. Suka sa dariya,,Tace" Miyar mey za ai??Tace"Miyar kubewa,,Ta kada kai, ta taimaka mata da bude Leda,,Ita kuma tana kan kare kubewa,,Ta kunna dayan Gas din,.Ta daura ruwa,ta yanka albasa ta zuba maggi,,Tasleem duk tana kallon ta,, ta sa Curry a tafasshen ruwan,Tana gama gurza kubewar ta zuba aciki,,kubewar tai kyau da ita,,Ta kallo ta "Fadi kar ta shake ki,tai Murmushi," No naga Taki miyar special, kawai albasa da maggi kika sa,"zaki ce min baki taba gani ba,.tai Murmushi "yanxu dai na rike,.amma haka za'a ci??Ta girgiza mata kai,tare da nuna mata flasks din" Da wannan za'a ci,.kan 12 da wani abu sun kusa gama wa,,lekowar Hajiyan biyu,,. Suna daki ita da Zahra, kara take kaiwa,akan yau Wai girkin tane Amma Sa'a ta dafo abincin fi'ili,,.Ta kalle ta Hajiyan kan tai Murmushi,, "Ni Zahra na rasa yaushe kika sauya?.Yanzu kiga fa,ina aiki daga zuwan Ku ta karba,,amma ke kinyi zaman ki,Kar ki bari ta fiki kirki fa. Ji tai an ruko kugun ta ta baya,ta juyo,ko Tasleem ce,sai ganin Tasleem din tai ta fice sai Ogan ta,,Ta dan harare shi, "Sannu,nazo Taya ki ne,Tai Murmushi," Ai ma mun gama,,Ni dai sakan ni ko ka manta inda muke?.Ya kara kan kamo ta,,tace"Allah fa zan sa ma ihu,,Ya fara mata chakulkuli,,Tuni ta hau dariya,.Shi ya Taya ta har tai wanke wanke Suka fito,.Tasleem ce kawai a parlourn, nan Suka zauna su Zahra Suka fito,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [10/2, 7:43 AM] Feenat Ja'afar: [1/25, 1:20 PM] Feenat Ja'afarBARIKI...IYAWA 55_Bayan sun gama firar Su gidan su Zahra Suka sauka,,Dakin auntyn su Suka fara sauka,kan sukai wajen mamy,, Ta tarbe su da fara'ar su,,Sa'a kawai kallon ta take,Mace ce mai waye wa,tasha boko,sannan daga ganin ta "Allura batai halin ruwa ba,dan ba nuna Zahra ta'ta ce,,a yadda Mamyn ta kula itama Sa'an zatai saukin kai,duk da yar tata na complain akan zaman su,wanda dama tasan a Rina,,Sa'a ta fito da Chocolate na coconut parket d'aya ta bawa yaran k'annen Zahra,,Mamy tai murmushi,a dan zaman da sukai ta gano Sa'a tafi Zahra sanin siyasar Duniya,, Domin har wajen da yara Suka bata da ledar chocolate din Sa'an ta share,,Lalle yarta keda gyara a gaban ta,,.Lokacin da zata shiga bandaki alwala, akwai dan gidan Auntyn su Zahran a foo, Yace Mamyn shi ya gama,,Sa'a ta kallo shi,," Tashi toh na wanke ma,,haka ta wanke mishi ta shiga da foo in bandaki,,kwarai mamy da kishiyar ta sun ji dadi,.sai murmushi suke,.Sa'a kam yar siyasa ce,,. Gidan Aunty Maryam Suka sauka,,da sallama Suka shiga,,Habeeb yana mota a parlourn, yana ganin su ya taho da gudu gun Sa'a,, Hafeez har mamakin sabon shi da Sa'an yake,Da sauri ta ware mishi hannu," Oyoyo Habebee nah,,Aunty Maryam ta fito tana musu dariya,,Sabanin Zahra da ba yabo ba fallasa,,Suka zazzauna,Hafeez yana"Sister kodai zaki bamu Habib ne??Tai murmushi tana kallon Sa'a,, Mai D'a wawa ne,indai zaka so nashi,toh zai so ka,, "Wa zai Iya da kiriniyar Habib Bros?? Sa'a tace " Mukam a bamu,zamu Iya,ko Habeebe??Ya daga mata kai,, Nan Suka gaisa,,yaran ta suka zo,kai Familyn Hafeez sun mata,kowa ka gani da fara'ar shi, a zaton ta bazata samu tarbar nan a wajen su ba,ganin yadda akai kan tazo gidan,amma da mamakin ta kowa yana maraba da ita yanzu,,.Yadda take son Hafeez, dole taso Familyn shi,shi yasa a siyasan ce take siye su,.Da zasu tafi Tace su biya zatai ma su Fodio siyayya,Yaji dadi kwarai,dan bai kawo wata siyayya a ranshi ba,,Tasan tsofi akwai son Turaruka,.Nan ta jidar musu,Drinks ne,da sauran kayan tsaraba,. Zahra har abin ya daina bata haushi,mamaki ya dawo bata,,wato tana nufin ta ma fisu son dangin nasu ko mai?? Biyar Suka yada zango a Family House din su,su Fodio yai murna da ganin iyalin Hafeez din, Kowa ba nuna waraki ya tarbe su,,Nan Suka yada zango,ta zage tare da sakin jikin ta dasu,,Kakar su Hafeez kadai ta rage,Itama duk ta tafi,,.kwarai sunji dadin tsarabar,duk da dama Hafeez din yana kyautata musu ta bangaren sutura,da dan abun masarufi,,Yara suna ta murnar chocolate,. Sai bayan Isha'i Suka nufo gida,Fir zahra taki zaman Gaba,har dariya abin ya bawa Hafeez,. Da mamakin Sa'a taga sun baude, Layin su ya dauka,Dan murna harda rukun kume shi,. By Feenat Ja'afar 56_Da murnar ta ta Dane Maman,lokacin Baba ya dawo,,Ta dawo kan Baba,Sai dariya suke mata da Hafeez, Tuni shagwaba ta dawo,,kan ta tashi ta dakko ma su Zahra ruwa bayan sun gaisa,,. Basu Suka je gida ba sai 10,,a jabe Zahra ta zube a parlourn,, Sa'a tai musu sai da safe,ta haye sama,,banta yai da kallo,kan ya shiga dakin Zahran, itama binshi tai,yai wanka,dan lokacin zafi ne duk ya takura,yana fitowa itama ta shiga,, yai murmushi, Sa'a, Sa'an shi, da itace toh da tare zasu shiga,,Saman yai,lokacin tana parlourn, daga ita sai towel halamar daga wanka ta fito,chargy take jona wa ganin NEPA,,yai murmushi, tana ganin shi Ta sau mishi murmushi,, kamar jira yake ya karasa,.ajiyar zuciya ya saukar,idon shi lumshe,, Sa'a itace nutsuwar ruhin sa,,idan tana kusa yakan manta komai,sai yai da gaske ko ta nusar shi yake Iya kaman ta adalci,, yanzun ma ji tai kidan na Neman sauya wa,,da sauri ta mai chakulkuli ya sau ta,, Ta Matsa baya,,"Good Night,. Kai ya kada mata, sai ya bata tausayi,,Ta matso tare da riko hannun shi, har wajen glass din ta rako shi,.Tamkar wani marayu haka Suka rabu,.Ko kadan bata son shiga hakkin Zahra. "Amma ya Hafeez kana sane da rashin adalcin da kake mun ina hakuri koh??Ya kallo," Da nai mey kuma??sarauniyar yan complain? Naga randa girkin ki zai tsaya,ba tare da kin kawo Suka ba,Tuni ta kara kuluwa harda hawaye,,"Ni in girkin ta ne a sharp sharp kai min sai da safe ka fice,amma in nawa ne,toh fa in ka hau sama sai na ganka,,.Ya girgiza kai., kan ya gyara pillow,, kwanciyar shi yai,ta kara kuluwa kuwa,''Dama nasan ni Matar tushe ce,kullum ni ke laifi,yar goal din taka bata yi,,Ya juyo,,"Yanzu toh mey kike so ayi??Tai mishi banza tana ci gaba da kukan ta,,. "Na Sani,Allah ne ya dauran son ka,amma at least ka nunan ko kan kani kana yi dani ma da dadi,,yai shiru, ," Zahra problem, yaga ranar da zai zo dakin ta bata bashi sukar Sa'a ba,,dole Sa'a tana birge shi,dan fin wata kenan,amma bata taba kawo mishi sukar Zahra ko kara ba,asali ma sai dai ta tunasar shi adalci a tsakani,,sannan yasan indai so ne!toh Sa'a tafi Zahra son shi, don tana komai dan faran ta mishi,matukar bai saba wa shari'a ba.. Ya sauke ajiyar zuciya, jawo ta yai,,"Toh shikenan, yanzu ki bar kukan,.Nima ina son mata na duka Sweet Zahra,. Tuni ta fara murmushi,, a hankali da dan guntun salon ta ta tafiyar dashi,Sai dai shi abinda ke daure mishi kai, duk tsiwar nan ta Zahra a fagen nan kunya take,komai a kunya ce,ita ba'a sabo da ita,duk da bata da makusa,,amma Sa'a ta daban ce,,.Yau kam tashin farin ciki akai,tun asuba ta gaida shi,ita a dole ta samo kan Hafeez,, tai break, tare da taimakon shi,.Bayan sun gama yai sama kiran Sa'a, nan fa ta fara cika tana batse wa,,ita kam mey zatai wa Hafeez ya dau lokaci ba tare da ya tuna hawa saman Sa'a ba??,koda Suka sakko tare da Sa'an yai mamakin sauya war Zahran, dan ana wasa ya barta ya hau saman,ya girgiza kai, Zahra? Sai a barta,,. Kamar kullum, yauma Sa'a ta gaida ta, a dakile ta amsa,Kan ta hau hada ma Hafeez tea,,Yau da matukar farin ciki ya tashi,,dan yau kam,yasan sai kwanan saman Sa'a, tana kula dashi,,kujerar shi na facing ta Sa'an, yayin da Zahran ta zauna gefen shi,,Cokali take juya wa a tea in data hada,lokaci lokaci takan dan kalle shi,, kamar mai jin kunyar shi kuma sai ta dukar da kai tana Murmushi, Sa'a mai dubun salo,yau kuma da salon kunya ta motsa da rashin son magana,,.Ta kai Cup bakin ta taji yana mata tafiyar tsutsa a K'afa,,ta kalle shi tai Murmushi tare da dukar da kai,,Kafar shi ya matsar gefe,da zummar in ta kawo tata ta rasa,dan yasan zata rama,,Ai kwa kamar ya Sani,,Kurbar tea Zahra take,,taji wani salo ana mata a kafar data mike ta,Tuni ta kware lokacin da ta gane mai mata,Dan taga lokacin da ta kanne mishi ido,,a zabure ta mike cike da masifa,"Nifa ban son karuwan ci!ehee,in banda jaraba ki bari yau Ai zai dawo gare ki,sai ki cinye shi danye ma.Da sauri Sa'a ta gintse dariyar ta, "Kai sis.,ban fa kula ba,,ta wani marai rai ce mata harda langwabe kai gefe,,",mtsww.. Taja dogon tsaki" kyaji dashi dai,,.Ta ture kujerar ta basu waje..Tana shiga daki Suka fasa dariya...Da sauri ya taso ya dawo kan plate din ta,,Sai da sukai mai Isar su tukun Tace "Amma fa baka kyauta ba,,Yanzu da ta rufe ni da duka fa???Ya kara tuntsura dariya," Allah bansan ta kawo kafar ta ba...Ta dan harare shi, "wataran ina ga sai kasa Zahra tamin lilis a gidan nan,I swear na tsorata,.kuma kai kaja, da akan ka zan rama.. Yai Murmushi tare da ruko hannun ta,," Ada!.Ta zuba mishi ido..ido cikin ido suke kallon juna,sai dai takan dan lumshe nata,sun kai a kala 5mints,kan daga bisani ta kalle shi, kamar hadin baki su furta wa juna "I Love you,,..Suka sake kallon juna,Sai kuma abin ya basu dariya.,Ta kan kamo shi," Love you too sweetheart... Ya sauke ajiyar zuciya,,. Zahra da ta fito ta sake komawa, gado ta fada,ta fara rera kuka,,"Mai Sa'a ta fita ne a rayuwa??.. Kyau??Tasan bazata gwada mata shi ba,,..diri fa?? Sai dai ta fita kauri da cikar muzauna,,Gashi tana da dai dai gwargwado,, tana kitso duk bayan sati,sabanin Sa'a, da sai dai tai wash and set,,.tana kokari sosai ganin itama tana kwalliya,,.Ance mata yan BARIKI akwai su da gyara kodan su kwace maka Miji,Toh tasan a bayan auran su kadai kudin data kashe dan ta gyara kanta ba kadan bane,kuma ko yau Jummai tazo da sabon da zata kawo mata,,Amma Sa'a fa,tun zuwan su in banda Ummi da tai zuwa 2,toh bata taba ganin wata Qawa tazo mata ba,,..Toh meye sirrin da Sa'a take da wanda ita batta dashi???Tai tunanin har ta kare bata Gano da mey ta Gaza ba..Zahra kenan...Duba da kyau dai,am sure akwai su... Bude kofa taji,ta juya,Hafeez ne tsaye,tashi tai tare da goge idon ta,, amma a ranta tana wallahi Sa'a zata biya bashin nan na yau.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/25, 7:08 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 57_Zama yai rarrashi, murmushi kawai take mai,wanda na mugun ta ne,,abin yi zuciya ta raya mata,,Kallon ta yake shikam da mamaki,dan yasan da a da ne,da Tuni Zahra ta fara complain, amma yau Murmushi take mai,,Shima sai yai murmushi, "Zan tafi office, 9 tayi,Ta kada mishi kai,," A dawo lafiya,,.Shima ya kada kai, Ya tashi,.ganin batta niyar tashi yasa ya girgiza kai,, Allah sarki Sa'an shi, da yanzu itace tana manne dashi da yar shagwabar na Kar ya jima,,sannan ya kula mata da kanshi kamar tana gani,,..Yai Murmushi har hakwaran shi Suka fito,kan yai waje.. Yana mai daukin dare yayi yakai ga Unique din shi.. Washegari Bayan ta sallame shi ta koma sama dan ramakon baccin ta..Zahra najin shiru,ta shiga kitchen ta hada miyar Tankwar ta,attarugu zallah,tana yi tana dariyar mugun ta,tana gamawa ta zauna a parlour tare da daura K'afa d'aya kan d'aya, jira take Sa'a kawai ta sakko da abinci,,ita kuma ta sau mata Bom din ta ciki,.Da mamakin ta har 12 bata ji motsin Sa'an ba,.Tashi tai ta hau saman da zummar tada ta.. Mafarki take Wai Hafeez na sabe da ita a baya suna kewaye parlour suna dariya,. Murmushin take dirka wa a baiyyane,taji ana buga mata glass,,. A firgice ta tashi tare da kallon agogo,, "Subhanallah,,past 12??..Da sauri tai kofar,,Zahra ce,da mamakin ta tana Murmushi,," Sis,naji shiru ne,shine nace ko bacci ya dauke ki hala,,tai Murmushi,. "Wallahi kuwa,nagode kwarai sis..Ta juya kasa tana murmushi,, Sa'an ta bita da kallo,,kawai sai taji bata yadda da murmushin nan na Zahra ba,dan tsawan zaman su sai dai tai wa mijin ta, ita kwa sai dai ta bita da harara,,ta dai kada kai,ta shiga kitchen a gurguje, Allah ya sota ta dafa markade,. Tasan Gogan ta bai fiya son k'yali a abinci ba,shidai basshi a shinkafa, saboda haka cikin gaggawa ta daura,ta hau soya miya,duk ta manta da wayan ta dake a kashe da zata kwanta,.Yi take tana kallon agogo,,1pm yake dawo wa gida,ga indai ya kwaso yunwa,toh fa tanan ake fada dashi,dan shi Sam baya jimirin yunwa da yaji a abinci,yanzu za'a ji kanku dashi,dake ita tasan abinta Shi yasa take karewa,, a kalla in tai latti bata gama abincin rana ba takai 1,Shima kan Ya koma bakin aiki ne,. 1 da 20 ta sakko ta ajiye flasks dinta,har Zahra na mata sannu,,. Komawa tai ta fara yanka cabbage da zata hada cous low,da mamakin ta shiru Hafeez bai zo ba,har 2 na Neman yi,,kan ta gurza karas tai wajen wayan ta, kai ta dafe,kan tai saurin kunna wayan,.Tamkar wanda ake jira sai ga kira ya shigo,tai kitchen tana receiving,,. "Am sorry,aiki ya kachamen,kasan kana raina,,.Yai ajiyar zuciya," na aza kin manta ni ne?? Tai murmushi, "Da kuwa na manta kaina ma Baby,,.u know u r special.. Yai Murmushi n jin dadi,,kan ya fara sanar ta Ya kai sako ne,sai Fodio ya kira shi,amma Gashi nan,dan duk yunwa ta rarake mishi ciki.. Bayan sunyi sallama da gaggawa ta tattare komai,tabar cous lown takai daga baya,,Wanka ta shiga,dan sai zufa take tai komai cikin sauri. Zahra na ganin hawar ta tai saurin shiga kitchen,, leke take,tamkar wata muna fuka, ta juye kusan Rabin Miyar Tankwar a miyar Sa'a, ta juya,Tuni ta hade kamar ba'a zuba ba,da gudu ta koma kitchen har tana tun tube,, Ta dawo Taji kamshin miyar data bude ta cika parlourn, da sauri ta dakko freshener ta hau fesa wa,.Kallon Dining din take tana wata shu'umar dariya,,ta kalli agogo,2:09,tasan duk inda Hafeez yake iyanzun yunwa ta ciwo shi,. Ta tuna randa ya fara fita office datai lattin abinci ya yai mata,tamkar ya rufe ta da duka,dan Hajiya tasha fada mata Hafeez baya jimirin yunwa,,akwai lokacin da yaji ya zarce mata a miya,da bai ci abincin nan ba,kwana 2 yai basu dai dai ta ba...Tai murmushin mugun ta..." Sa'adatu Yau sai Buzun ki a gidan nan,,. Zan ga karyar BARIKIN yau.,Kai Kila ma ya kifa mata mari yadda yai lattin nan,tadan doka tsallen murna,,Daki ta koma,tai alwala Ta hau make up..sai kuma jiran zuwan Hafeez. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. [10/2, 7:50 AM] Feenat Ja'afar: [1/26, 7:36 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 58_Da Sallama ya shigo,duk din su suna parlour, Kallo suke,sai dai duk hankalin su ba'a Kallon yake ba,kowacce da abun da ke ranta,,duk da kowacce murmushi ke kwance a fuskar ta,,. Ba karamin dadin ganin su yai a haka ba,,da dan gudu gudu Sa'a ta taro shi,,.Zahra ma ta tashi,.da yar dariyar da take kunshe wa,"Sannu da zuwa,,Ya daga mata kai,"yauwa, ya gida,.tai daki,dariya take dillikawa,nan da yan mintina zata ji kan su,,. Ba'ai 10mints ba Suka sakko,,Manne take a kafadar shi, tana jin su ta fito,sabanin D'a da sai a an kira ta tana yanga,,. Kujerar Sa'a ta ja mishi,ganin yau suna dasawa da Zahran yasa ta barshi yaci da kanshi,,Tai serving kowa ta tura ma Zahra,,ta bashi nashi tana Murmushi, ja yai,zai fara aka kira wayan shi,Zahra ta danne cokali,, da jin haushin wanda yai kiran,,. Sa'an ta zuba mishi ido,, a fada fada yake wayan,ta kuma San yunwa ne,, sai da taga ya ajiye wayan Kan ta dau cokali d'aya bakin ta... Da sauri ta rintse ido, dan jin wani azababben yaji da ya ziyar ci kwakwalwar ta..da sauri ta bude ido, dan tunawa da yanxu Hafeez zai kai tashi lomar shi,ta kuma San halin shi akan "Y'aji," baya son Y'aji a abin,,,.Sai dai ina ta makaro,dan har Ya kaita,Furzar da abincin yai,yama rasa ina zai sa bakin shi yaji dadi,.. batai wata wata ba tai wajen shi tare da saurin tallafar kanshi ta hau kan dining table din ta zauna,,shishitu ya fara,idon nan Tuni har sun kada dan azabar attarugu,,in banda kunshe dariya babu abinda Zahra take,,yau daya,tasan sai buzun Sa'a,, dan tasan sarai bai son Y'aji,sannan gwani ne wajen Iya masifa akan yunwa inta ciwo shi,sai dai da mamakin ta, sai ganin Sa'a tai itama tana shshitu cikin marai rai ce fuska,,fadi take"Am so sorry Baby tana hura mishi bakin halamar yajin ya huce,,.Zumbur Zahra ta mike,sakamakon ganin Sa'a ta hada bakin Hafeez da nata,,Saida ta tabbatar ta kauda duk wani yaji kan ta dago,shikwa gogan abin nema ya samu,tuni ya manta da wani yaji yahau mata murmushi,, abincin ta jawo,sai ta dan matsar da miyar,ta kara cous lown,da plantain din ta cigaba da bashi,,duk loma daya saita manna mishi kiss,,Ina,Zahra har ta fara zufa dan ganin Ajab,, bashi take yana murmushi,, ita kwa sai aikin ta take,,cokalin hannun ta ta buga akan flate din nata,,da gudu tai daki tana kunshe kuka,,duk Sa'a na kula da ita,,. Sassayan ajiyar zuciya ta sauke,ganin ta tsallake rijiya da baya da kyar..Sauka tai zata tafi ya ruko hannun ta yana langwabe kai gefe,sai kace irin qananan yaran nan"Ban koshi ba?,,Tai ajiyar zuciya kan ta kakalo murmushi,,shikwa yadda take mishi ne bai son ta daina,,.Saida ta tabbatar ya koshi,kan ta sauka ta je fridge tana mai gode wa Allah,, tabbas tasan wannan aikin Zahra ne,,amma tasan ko giyar wake tasha gaba bazata kara mata haka ba..Ta dakko mishi fresh milk,Allah ya sota akwai,Ta tsiyaya mishi dan shashe baki,,.a ranta tunani take,wani irin attarugu Zahra ta afka mata a miya haka??..Oho,wato wannan ne dalilin Murmushin ta na tun dazun? Ta girgiza kai, "wannan Ai dabarar yan Da ce in banda Zahra,,tai Murmushi kan ta koma tana tsiyaya mishi,,.. Kuka take,tana da ma bata aikata hakan ba, dan Gashi a karshe ita ce da kuka,ranar dan bakin ciki bata fito ba sai taran dare,. By Feenat Ja'afar 59_Washegari ta fito zata kitchen ta tarar da Sa'a ta daura K'afa d'aya kan d'aya a kan kujerar ta,, murmushi take,wanda yasa Zahran saurin kawar da kai,,ta tako a hankali tana rausaya, "Sis ina kwana?. Da sauri ta dago kai,dan batai tunanin haka zata barta ba,. Murmushin dole ta kwakulo,,tare da amsawa,,.tace" Tun jiya shiru,hope dai lafiya naga baki fito ba??. Ta dan harare ta, "Lafiya,,.ta kada kai" Ok,.Ga nan abincin ki,,.ta juya tai sama tana mata sai ta sakko anjima.. Da kallo ta bita,da mamakin maganar da bata mata ba ta jiya,,. "Baby,ya juyo yana kallon ta,,. Ta tashi tare da kwanto wa cinyar shi,,.ta dan shafo fuskar shi,," Ya roko na please, gobe date line da suka bani please,,. Tuni ya sanja fuska,,tare da matsar da system din gaban shi,,. "Na zata na gama da nan wannan shafin Unique??.. Bana sha'awar mata ta da aiki,bare na gidan TV,,. Da marai rai ta ta dukar da kai da dan murmushin Neman kuka,,. Allah yaga Babban burin ta ne ta ganta tana News,amma Gashi mutumin nan yana son kwafsa mata,,. Bata San guntun hawaye ya zubo a,,sai ji tai ya bar sababin ya janyo ta,,." Am sorry,,.Ta dukar da kai kasa,,."Zan kare komai Dear,,wallahi buri na ne hakan,please,. Ya furzar da iska,,a times Sa'a tana sashi abinda bai niya ba,,.Yai ajiyar zuciya, "Da sharadi, Cikin zumudi ta mike dan jin sharadin,,. Yace " Na farko,babu zuwa da gyale,,na biyu,Babu magana da kowanne abokin aiki sai dole,,. Na karshe,aikin ki bazai shafi kula dani ba,,. Ta rukun kumo shi,"Duk na yarda Allah,, wannan Ai masu sauki ne,,. Washegari girkin Zahra, Yau da zumudi Sa'an ta tashi,,ta Riga kowa,kan kwa 7:30 ta shirya,. Jira take su gaisa da ogan kawai ta wuce,..Zahra ta kallo ta da mamaki,"Wai da gaske aiki zaki fara?. Ta daga mata kai"ya fice Wai,.Ta kada kai, "Yayi,.Tai kitchen,,. Lalle Hafeez bai ya adalci a lamarin shi,. Toh wallahi ko sama da kasa zasu hade sai ya nemo mata itama aiki.. A wajen aiki ana ta nuna mata tsarin wajen,,Murna fal ranta, yau gata a office,,. Bilkisu ta zo wajen ta,. " Suna na Bilkisu, kefa??. Sa'a tai Murmushi, "Sa'adatu,,. Da fara'ar ta tai mata barka da zuwa office din su,,. Tana tashi gida ta wuce,dan yau chan zata wuni,. Tana tuki ta dau waya," Ranka ya dade,,Yanzun kake raina sai ga kiran ka,,. Yai Murmushi, "Ya aikin toh? Naga first NeWS naki,very interesting, sai dai fa da matsala.. Tai karamin dariya," Nasan matsalar, sai an daure,,.Suna ta tadi har ta isa gida,. Yau auren su wata (6) kenan, Matsalar da ta fara fuskan ta bai wuce samun cikin Zahra ba, Gar da gar zata na Goran ta mata haihuwa.. Ko in sun zauna ta tsiri ko dai Sa'a tana planning ne??.. Tun abin baya tasiri a wajen Hafeez ya fara,sai ya fara zargin ko dan aiki Sa'a take planning,,. Duk randa Zahra tace haka takan yi Murmushi,. Dan tasan da gaiyya take fada mata haka a gaban Hafeez kullum,. Yau suna kwance ya riko hannun ta,,. "Unique,, ta kallo shi tare da shafo fuskar shi,,." Please in da gaske kina planing ki taimake ni ki daina,,ina matukar son yara,musamman su fito ta tsatson ki,,Aiki baya hana haihuwa please,.. Da mamaki take kallon shi,dan ko kadan batai tunanin maganar Zahra zatai tasiri a ranshi ba,,.Kallon shi take ta ma kasa cewa komai, shi kuma sai ya zata bata yarda bane,,. Dan haushi ma ta kasa mai maganar,. Tashi yai yana mai gaskata zancen shi, lalle Sa'a planning take tunda bata Musa ba,indai kuwa hakane dole ya sa mata ido,. Tun ranar Sa'a ta kasa sukuni,yau ta kudiri niyar ganin likita in ta tashi a aiki,,.File yasa ta bude tare da bata appointment ran Friday,,. Allah Allah take Friday tai ta gano meye matsalar ta. Dr ya kalle ta bayan an kawo result din ta,sannan ya fidda result na scan,."Madam (you are absolutely fine,,. The uterus is normal in size,,.But abinda ban gane ba shine,cervix naki naga halamun rufe wa,Sannan akwai kince dan ruwa na linking kadan,,so bazan tantance yanzu ba since kin ce this month kinyi period, right??. Ta daga mishi kai,,. Ya kada kai,"OK, yanzu let see,PMC nakin yazo ending, if ba wani Sign then sai muyi tackling next month,,. Don't worry,everything will be fine,,.Kin ma yi dabara da kika zo da wuri,. Tai Murmushi,. Ya bata result da magun guna ko da da infection ya baje,,. A gajiye taje gida,dan ma Ta sanar shi zata biya anguwa,,Yana zaune a parlour shida Zahra,,cikin ta har ya tasa,fi'ili ake mishi kala kala,.Sa'a tai murmushi,, "Sannun Ku da hutawa,.Yai Murmushi,," Yauwa Unique,, kin dawo??. Ta daga kai tana Murmushi,,. Kallon Zahra take yadda tai d'ai d'ai a cinyar shi da duk Rabin jikin ta,,. Wani malolon kishi ya tokare mata makoshi,,. Ciki tai tana musu bari ta huta,.. Ta fara fuskan tar chanji a Hafeez kwarai tana kula,da a da ne da yanzu ya biyo bayan ta,. Ta cire kayan ta tare da Ciro maganin ta sa a side bed,.Ta fito a wanka sai Gashi,,. Kallon ta yake,Fatar nan a mur mure,, sai shining take,,ta dan kara kiba kadan,,.Ya riko cikin ta tabaya,,. Kallon su yake a mudubi tare da ajiyar zuciya,,. Shi indai bai dangana da jikin Unique din shi ba bai samun nutsuwa, Gashi Zahra ta dakko mishi wani sanabe,Wai kamshin jikin shi take so,,Haka zai na bata lokaci agun ta,yasan kwarai Unique din shi mai hakuri ce,,dan bata taba complain ba a kan hakan,,duk da Gashi yau girkin ta ne,. "Missed you Janeeman,. Tai Murmushi tare da juyo wa,,.Ta shafo fuskar shi" Missed you too Pyaree,,.Yai Murmushi tare da riko kugun ta,, Na matso naga kin fara min rakin masu ciki kema,,kokarin kunce mata towel yake,amma sai ta rike Kam,,Ta fara gazawa da mitar Hafeez,, Ai ba sai ita zata Haifa mishi yara ba,ganan Zahra ta wadatar,,Kallon ta yake ganin yadda ta sauya,, ya fuskanci a yan kwanakin nan in yai mata irin maganar nan sai ta sauya fuska,,it means bata son zancen haihuwa ko mey??.Cika ta yai ya zauna kan gado,ba tare da ta tanka shi ba ta fara Shafa mai,, shedan ya fara hura mata zuciya,,sanar ta yake Hafeez fa gori yake miki a fakaice,,. Tuni ta kara cika da masifa,.kiris take jira ya kara tofa wa,,ganin tana Neman fita hanyar da ba ta ta yasa ta fara karanto adu'ar Neman tsari daga shedan,,. Ta rintse ido, a hankali taji nutsuwar ta na dawo wa,.Da yanzu ta tafka kuskure babba, wato masifa wa Miji..,Drawern ta ta bude tana son daukar kaya taji ya kara rukun kumo ta,,. "Fushi kikai Ada??.Da sauri ta kada mishi kai da murmushi, Ya juyo da ita,Kallon shi take cikin ido,Shima haka,,." Ina son yara ne musamman daga gare ki, ba laifi bane dan na fada,,Tai murmushi, tare da sadda kai kasa,ta Sani bai fita son yara ba a yanzun,kodan ta tsallake gurin Zahra, sannan ta wanke kanta daga zargin tana planning,,. Dago habarta yai,tare da manna mata salon shi dake mantar ta bacin rai,,.Tuni suka Lula Duniyar su tasu kadai. Yau ta tashi da murnar haihuwar Fadeela, Direct chan ta nufa,,an sake mata gida kamar yadda Hajiya Rabi ta nema,duk tayi laushi tunda taga yadda Alhaji ke rawar kai da Fadeela,,. Ita kwa har a labour sai da ta Roka mata Allah ya bata itama.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/27, 10:57 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 60_Takarda yake dube,Gashi Sa'an ta na gidan Fadeela,ya kira wayan ta ya shiga bata kusa,,. Turus ya tsaya tare da kwaso su ya zube a kan gado,,Plygyl ya gani da sauran tarikicen mugun gunan da likita ya rubuto ma Sa'a,, Gasu nan har ta kusa shan rabi,,budewa yai ya fara karanta wa,,Duk da bai fahimci komai ba, amma ya ga an rubuta mai ciki Kar ta sha in yana first trimiser,.Tuni wata zuciyar ta fara fada mishi na hana daukar ciki ne,,deba yai Ya sakko kasa,sai huci yake,Tana gado tana waya da Jummai ya shigo,da sauri ta katse ta,. Dake tayi science, sannan bangaren ta karan ta a Deploma a pharmacy,, Ya zube mata magungunan,. "Na meye wannan Zahra?Ki waren wanda yake hana shigar ciki,.Tuni ta harbo jirgin shi,.Tai murmushin mugun ta,, kan ta daga flygyl,,. "Wannan flygyl ne,400g,Yana Iya zubar da ciki koda na kwana d'aya ne,.Ta daga dayan,sarai tasan na dan infection ake rubuta shi tace pills ne,,dayan kuma na infection,,. Huci yake kamar wanda zaici babu,,ya kwashe su har yana warta,,.Da gwalo ta bishi,," Jeka dai,,kai ba mai yar goal ba,ba'a taba jin kan Ku ba,yau maji ma gani Ai.. Missed call taga nashi,da azama ta hau kira,. Dafe yake da kai a hannu,"mey yasa Sa'a zata mishi haka??.wato dan ya barta aiki shine ta samu damar raina mishi hankali.., Wayan ta katse shi, yasan ita ce,dan ringing tune nata daban ne,,yai tsaki,da kamar bazai dauka ba,,. "Am sorry Habeebe,muna chan hidimar aiki,Ya kake... "Ki dawo ina son ganin ki yanzu,A tsorace ta waro ido,dan jin yadda yake magana fada fada,,sannan ba ita gare shi ba,,.Da marai rai ta tace" Ok,. Ta kalli Ummi da. Fadeela, "Zan je na dawo,,suka daga mata kai,dan duk sunga sauya war ta,kuma sun San da wa take waya,. Ta dau mukullin motar ta ta fice. A saman ta same shi a daki,yai kicin kicin,Zahra najin sallamar ta ta labe a gefe dan jin mey zai wakana,,.Yadda ta tarar shi ya bata tsoro, ganan mugun gunan ta a watse kan gado,. A rabe ta zauna a bakin gado,," Baby hope dai lafiya kake?,,. Cikin daga murya ya fara fada,ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba,,.Kai tai kasa,dan tsabar al'ajabi,Bai taba mata haka ba sai yau,,Tuni hawaye ya fara zirya a fuskar ta,. "Mey zakice game da wannan??. Ya nuno mata magani,,sai ta zata dan taje asibiti bata fada mishi bane yasa hakan,,." Kai hakuri,naso fada maka,Sai..."Kimin shiru,tambayar ki nake na meye??.Baki sake take kallon shi,,. Sai dai yai nisa,,ta girgiza kai "Na infection ne,.Yai Murmushin cin rai ganin ta ma raina mishi hankali,. Kai ya kada," Daga yau na soke aikin ki a gidan nan toh..Da sauri ta tashi tana waro ido,. "Hafeez mey nai haka da zafi ne??." Au tambaya ta ma kike??. Ta girgiza kai tan hawaye,"Kai hakuri,wallahi ban San zuwa asibiti na zai bata ma ba,.Yai Murmushin takaici,."na dai sanar ki na soke aiki,kinga sai ki zauna zaman Tara yaran yanzu,.Amma Sa'a ban San lokacin da kika daina so na ba,,ta dago da sauri,.Waje yayi dan ganin kukan nata na k'aruwa,.zahra dake labe a kasa da sauri ta zauna a kujera..waje yayi ta bishi da dariyar keta.. A gado ta zube tana mai kuka mai tsuma rai,.Wato maganin ne ma na planing??. Ta kuma sanar shi na meye yaki yarda,,. Tai mai Isar ta har magriba kan ta tashi ta goge ta shiga wanka,,.Tana fito wa ta tsantsara uwar kwalliya kamar mai zuwa party,,kai in ka ganta baka ce ita tasha kuka ba,. Riga da skirt ta dakko,skirt din ya wuce cinya mai yalwa Green da ratsin baki baki,,.Sai top din shi Mai yankekken hannu,.Ta tufke gashin ta sai kamshi take tai kasa,.Lokacin Zahra na kitchen, sai fitowa tai taga mace ta daura d'aya kan d'aya tana waya,."Eh sai dai goben,,InshaAllah da wuri zan zo,.. Suna hada ido ta sau mata Murmushi,. Zahran itama tai yake,.kitchen ta koma tana cije lebe,. Wace irin jarababbiya Allah ya hadata da ita??. Ji kamar ba da ita akai dazu ba??. Tai kwafa,ta gani Ai.. 8:pm ya shigo,.Kallon Sa'an yake,ta bala'in mishi kyau,,.Ta kallo shi,. Da sauri ya dauke kai,. Zahra ta kulu Iya wuya,.sannu da zuwa ta mishi fuskar ta sake,.ya amsa yana kallon ta,,. Da yaga zata kallo shi sai ya dauke kai,.. Suna cin abinci sai dan tsakura take,,yana kula da ita,,.sai dai bai son mata magana ta ga ko ya sakko,.Amma duk tausayin ta yake,. Yasa Unique din shi kuka,. Suna gama cin abinci tai musu sai da safe.. Da kallo ya bita har ta kule,,.Ya sauke ajiyar zuciya,,Zahra ta buga plate kan wani tana tattara wa,."Anya Sa'a haka ta bar Hafeez kuwa??.Anya baza tabi shawarar Jummai ba na iyaka tsakanin shi da sa'a ba??.. Tai kwafa,.. Washegari sunan Fadeela, da wuri ta tafi,.Yaro yaci sunan Baban shi,,harda Hajiya Rabi a wajen hidima,in ka ganta gwanin tausayi duk tai laushi,,tunda taga ba sarki sai Allah ta fauwala wa Allah komai,.Dan Fadeelan bata da bace,. Anyi suna an tashi lafiya,.Ta dawo gida da jin haushin Zahra, dan sai da tai Dama bata je mata ba,. A gaban su Aunty Maryam take mata feleken ita bata son kaza da kaza,an kawo abinci ma bata son warin curry..Hmm sai ita halin ta. Ita ke gare shi, duk tayi kicin kicin,kiris take jira ya kula ta tasau mishi kuka,dan kwarai ya bata mamaki jiya,. Shima dake Namijin Duniya ne haka ya daure yaki lallashi, sai dai da aka zo kwanciya kamar kullum ta lafe jikin shi, anan komai ya sai tu.. Dan baya Iya hakurin Iya jure rashin ta kusa.. Washegari warai aka koma kamar ba Ai ba,.sai ma wani nan nan da yake da ita,.Batun aiki ta share shi,.Wai aka ce fadan masoya ba fada bane,. Sabe ya sakko da ita tana bayan shi,. Dariya suke yi tamkar basu bane jiya da shekaran jiya,. Da azama Zahra ta koma daki,.Tabbas zargin ta ya zama gaskiya,.Dan ita sun sha fada daga baya sai an kai ruwa rana ashirya., Dan ita in tai fada da Miji toh fa kowa sai ya Sani,.Dan zata hau fishi ne har a shimfida,. Yayin da shi kuma sai ya basar ta.. Amma sa'a Duniya,cikin ruwan sanyi ta mantar shi komai. Yana Office tace mishi zata unguwa,. Yace sai ta dawo,.So take ta kai ga likita,dan sanar mishi changing da take ji kamar yadda yace,.Ta koyi nawa kwana biyu,ba ita ta bar gidan ba sai dab da yana dawo wa,. Dai dai zata bi junction Shima ya taho,.yana ta mata horn ina,bata kula ba,.sai ya samu kanshi da bin ta ganin tayi hanyar asibiti.. Tai parking.,Shima yai a dan nesa da ita,.Binta yake ba tare da ta kula ba,,.gaban shi sai faduwa yake,.a tunanin shi Sa'a ta hakura tunda ya barta aiki,.Ashe ta daura daga inda ta tsaya,. Toh zai ga likitan mai planing din,zaiji uban mey yasa zaiwa Matar shi planning ba tare da yardar shi ba... Anti Nital tabi, yaga a sama an rubuta /Family Planing,. Kwanar yaga tayi,.da azama ya bita dan ganin inda ta dosa. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary ®ONLINE HAUSA WRITER'S. FEENAT JAAFAR'S MOBILE BLOG JUST ANOTHER BLOG BARIKI IYAWA 7 [10/2, 8:08 AM] Feenat Ja'afar: [1/28, 10:28 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 61_Ita Hakima ce,bata bin layi,,dan da shigar ta ma sai ka dauka Matar wani Babban mutum din ce,Direct ta shige data tabbatar ba kowa,,Shima da fara'a ya kallo ta, dan gwanin Kallon News ne,kuma yasan Sa'a,.Ta fara mishi bayani kenan sukaji an banko kofa,.Da azama ta mike lokacin da tai arba da Hafeez,,. Shi kam bai wata wata ba ya chakumo Dr,. "Da sa hannun wa kake wa mata ta planing??. Dr ya zaro ido,," Hala baka hankali??..kaga an rubuta planing a office dina??..Ya rike hannun shi tare da kokarin ban bare wa,,.Amma ina,Hafeez ya rike shi tamau,. Sa'a ta fara Hawayen takaici,,. "Hafeez yaushe ka fara min Titsiye a rayuwa??..Ya juyo yana hararar ta.." Ki bari,zan zo kanki kema Ai,.Zanji dalilin zuwan ki nan?.Allah ya bawa Dr Sa'a ya ban bare da kyar..,"Ya kamata kana bincike kan ka hau zargi,,.Ya daga mishi hannu,"A kaga malam,kayi na kudin ka,dan duk randa zan kara ganin ka da mata ta court ce zata raba mu..Dr Dariya ma ya fara,Ganin sai wani dage wa yake,,.Tabbas yana son mutum mai kishin Matar shi,. Yace"Toh madam din ka tana dauke Da ciki yanzu haka..,Ya maka mishi harara,"Kar ka layan ce min malam,ba shi zai hana na yarda da kai ba,.Yai murmushi tare da dafa kafadar shi,."Abokina ka nutsu,,.Kaga kasa Matar ka kuka,.Mu fidda zancen wasa,.Tabbas likitan Mata ne ni,bari in ma gwari gwari,kuma ina planing, amma ba ga Matar ka ba,,.Ita nata planing din Samun ciki muke,Kuma da dukkan Alamu mun dace,,.Ya kallo Sa'a, "Madam,inda muje ki kwanta,,.Ya dafa Hafeez," Calm down,. Ka zauna please,. Ya zauna da niyar Ganin gudun ruwan shi,,.cewa yai Sa'a ta dan daga rigar ta ta mike sosai,.Hafeez ta kallo da shi kuma yake Kallon Dr,,yai Murmushi, "Scanning zan yi,so ka rintse ido, Tashi yai ya tsaya a kan machine din,.Likita ya girgiza kai yana masa Dariya,.Da kamar minti 5 ya dago kai,,." You see,,Ganan Babies din ku a cikin madam,,.Matsowa ya karayi baki sake,,Likita ya sake daura abin a kan marar Sa'a., Tuni hawaye ya silalo mata,.Da sauri Hafeez yakai hannu zai goge mata ta gantsara mishi cizo da harara,ba shiri ya sau kara,.Likita sai Dariya yake sha,,.Nuna mishi har Heartbeats na Babies din ya fara harbawa,,. Hannun ta ya ruko,"Am Sorry my chocolate,,. Tuni ta sau dariya ita da likita,.Ta kan kame hannun shi suna Kallon yaran yan yiri yiri a alon Machine din,.Dr ya juyo bayan sun gama.."Toh yanzu zamu shiga court da dalili,,.Yai Murmushi, "afuwan,Yanzu Unique ma Courtn kanta ce.,Toh amma Dr.,pills din Dana gani kwanaki ka bata fa kuma na planing? Ya kallo Sa'a,." Madam,wane pills kuma??.Ta kada kai, kan ta mishi bayani,.Yace "Abokina Ai wannan Antibiotics ne na bata,koda in akwai infection, ba mai flygyl ba??Ya kada kai,,." Kuma ance Shima yana zubda ciki..Yai dariya"kai madam sai kin dage,, Mutumin ki Ba dama ne,,.Yanzu dai wancan sun wuce,,Ganan wannan,,.Yanzu zata fara sha dan inganta lafiyar yaran,.cikin zumudi tace"Dr Watan su nawa??..Ya kallo Hafeez, "Madam fa ta fika dauki,kaji wata nawa take tambaya,. Yai Murmushi,tare da kallo Sa'an," nidai nasan basufi 2 month ba,,.Ya gyada kai, "Suna cikin week6 ne,,. Sukai Murmushi, sai kuma ta dukar da kai,ita kunya. Suna fita a asibiti ya bita a baya har suka je gida,.Tana fitowa ya dauke ta chilak,.Da dariya suka shigo,Zahra ta sau baki tana kallon su,.Ganan ciki ya mata ham a gaba,,dan ya doshi 7month,,.Kiciniyar sauka take amma yaki sauke ta,Ganin Girkin Zahran ne,,.Har sama ya kaita a haka,Wai baison ta wahala hawa stairs.. Tai murmushi, itama kenan ta shiga sahun su Ummi..Sakalo wuyan shi tai..tana yai alkawarin babu mai jin cikin ta ko twins take dauke dasu,in sunzo a bazata yafi.. Yai Jim" anya zan Iya??.ko Aminu sai Y'aji,,Tai Murmushi, "BBC kenan??..kace Duniya taji kawai..Yai Dariya, za su sha mamaki,ba mai ji toh Mom twins,.. Tasa hannu ta rufe fuska, Wai ita kunyar karya..Ya dungure mata kai yai waje.. Dan yasan Zahra an hau 90.. "Kiyi da jikin ki mana Zahra,tun kan su dawo,.ta daga K'afa da kyar,,Duk da gaban ta sai faduwa yake amma bazai hana ta zuwa inda zata samo yancin ta ba,,EDDn ta cikin satin nan zai tsaya,.Amma tunda Ta kyalla taga yadda abin Hafeez yake gaba akan Sa'a tace Ba taga ta zama ba,,.Dan tun kan ta haifi D'a, ya daina daukin shi sosai,.a Ganin ta Sa'a farraku tai mata da Hafeez da cikin tun kan yazo Duniya,,.Zuwan ta na biyu kenan wajen malamai,da taimakon Jummai. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary 62_Sanye yake da Babbar malun malun,Yaci uban rawani,,.Ganan wasu manyan charbi da maka makan littafai, kai ka dauka Qur'ani., Da Ganin fuskar shi yafi kama da irin yan Duniyar nan,amma in baka kula ba sai ka mishi Kallon Malami,,.Ya washe baki yana kallon Jummai,. Dama yana ganin Zahra ya karanci matsalar ta,,. Yace"Kishiya koh?.Da sauri ta kalli Jummai tana hadiyar yawu,,. Kai ta kada mishi,,. Ya gyara zama a wayan ce yana kare wa Zahran kallo,.Wai,chakwala dadi,. Yana son harka da Matan aure,bare kuma mai juna biyu,. Yasan akan kishiya,mata sukan yarda da wannan Halin nashi,.Bare Zahra,da gani ta k'agu.. Sai dai yau,yana da Mai debe mishi,.Bayan ta gama kwararo mishi bayani ya kallo Zahran,. "Kuna sake da taimako alhalin kuna da kishiyoyi,,.Ki duba ki.,duk ta miki dabaibayi da mijin Ku,zakiga baya rawar kai akan ki,Toh da baki zo da wuri ba,D'an ma da zaki Haifa bashi ba uban sa,.Tuni ta yarda har ta fara zufa,.Fadi take,." Yanzu malam ya za ai?,,. Ya hadiye yawu lokacin da ya kalli bakin Zahran,. Sai wani marai rai ce wa take mishi,.Ya kallo Jummai,. Yace Zahran ta jira su a waje,.Dakyar ta tashi,tai waje,.Ya kallo Jummai,. "Ina kika samo wannan yar dakwala dakwalan?,. Tai murmushi,." Nidai na sanka da cika aiki malam,.A taimaki Qawata,.Ya shashe baki,.tare da Shafa gemu,."Kin tabbata bata da gardama??.Ta kada kai, "indai akan kishiya ne toh batta gardama,,.Tana kashe ko nawa ne,.Yai murmushi.." Kizo min gobe da ita.,Zakiga aiki da cikawa.. Tana fita ta kora mata bayani,."Gaskiya Jummai zan so yau ayi ta ta kare,dan Kinga yadda nake,Gashi dakyar gobe ya kuma bari na fita,kuma weekend yana gida,.Tace"wannan mai sauki ne,.kedai Allah ya kaimu.,ta kada kai badan taso ba,.Gidan su ta wuce,.Kamar kullum su Mamy suna zaune da Auntyn su suna Fira,.Agajiye ta zauna tana haki,. Mamy ta kallo ta. "Yanzu Zahra baza ki sallama wa yawo ba haka??..ko tausayin kanki bakya ji??..Ta kallo ta,. Ruwa Auntyn nasu ta bata,haka ta daga ta kwankwade,.. Sai da ta samu nutsuwa tukun ta Iya gaida su,.Mamy ita dai sai fada take akan ta hakura da fita haka, indai ba Wai haihuwar Titi take nema ba,. Bayan sun shiga daki take sanar da mamy Wai Sa'a tai mata farraku tsakanin ta da Hafeez, kuma wallahi itama bazata barta ba..Hannu tasa a haba Mamyn tana kallon yar tata,." Zahra ina fata Baki bi hanyar bata ba koh??..Ta kallo ta da rashin fahimta,. Ta cigaba "A kullum ina fada miki ki kara hakuri,.Ki fawwala wa Allah lamarin ki,.sannan kisa a ranki babu mai miki abu sai da ikon Allah.. Kishiyar ki mai saukin kai ce,a gani na inkin bita zakiji dadin zama da ita,.Ki fidda zargi cikin lamarin ki,, Sannan ina rabaki da Qawayen banza Zahra, wallahi su suke kai mutum su baro,..Nasiha take mata mai ratsa jiki,kan ta guji bin malaman Tsibbun nan,Ta kuma kuji sharrin Qawaye Marasa kan gado,.Duk nasihar ta ratsata,amma banda ta Sa'a, dan ita ganau ce ba jiyau ba..Tabbas Sa'a ba haka tabar Hafeez ba,.A haka a ta jogana ta shiga gidan Meenat Qawar ta,. Duk da ta zubar ta da.,tunda ta samu Jummai,. Basa shiri da meenat, dan takan tsage mata gaskiya duk daccin ta, sai dai ba taje gidan ta ba,.takan gaya mata Sa'a Yar siyasar Duniya ce,zama da ita sai Ka koyi hakuri da Iya kaima siyasa,sannan a yadda ta kula da ta yi a hankali zasuyi zaman lafiya da Sa'an, toh fa anan sukai Baran Baran,. Ita Wai data hada kai da kishiya.toh gwara ta sallama mata mijin.. Da fara'ar ta meenat din ta karbe ta, duk da karshen rabuwar su da fada suka rabu,.Amma tasan Zahra tasan Value nata,.Dole gaba zata neme ta,. " Ya kamata ki ajiye fita Zahra haka,.kinga kafar ki kuwa??,.Tai dan tsaki,."Ke barni.,fitar ta dole ce,. Nan ta koro mata bayani duk da tasan ba yarda zatai ba,. Murmushi tai tare da girgiza kai,. "Zahra,a kullum bazan Gaji da baki shawara ta Gaskiya ba,koda kuwa zamu b'abe…Sa'a ta fiki Tattalin Hafeez,.a kan ido na ina gani,kefa?Gani kike Wai duk abinda take Wai a Ganin ki karuwa ce,.Dole kiga Tasku Zahra, dan Namiji na tarai rayar mai Taryar shine Zahra,.In yayi rawar kai a kanta,itama tana yi akan shi,.Ki duba abinda idon Basira,. Wallahi ki gujewa muguwar Qawa,zata kai ki kawai ta baro ne,.Shiru tai,a duk zance tana dauka,amma mudin an sako Sa'a, toh fa sai taji tana mai jin haushin maganar ma.. Karshe sai shiru meenat ta mata.. Duk ta mata gargadi akan Kar ta koma wajen Bokan nan,dan duk malamin da zai fada maka haka wallahi Boka ne..Toh taji wannan. Sai dare Hafeez ya dauke ta sukai gida,.A daran yake fada mata gobe zai tafiya kwana d'aya.. Washegari gida ita kadai,Sa'a taje barkar Ummi data haihu da asuba,.Tana zaune,tun jiya take jin dan milmil,amma taki nuna wa kowa,.Duk Sa'an har daki ta mata sallamar ta fita.. Tariyo zaman su da Sa'a take,. Bata taba takallar sunyi fada ba,.Bata taba rama sharri da sharri ba,.sai dai tai abinda zataji haushi,.matsalar ta d'aya??.. Data mallake Hafeez ita kadai... Sallamar Jummai ce ta katse mata tunani,. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary 63_Ta kallo ta, "Tunanin mey kike haka ina ta kwankwasa kofa da sallama?? Tai ajiyar zuciya," Kin Sani Ai Jumee.,Ta tabe baki., "Keda kike da maganin tunani,sai kinje kin kashe kanki a banza ita kwa tana Shana war ta,.Yanzu ki tashi.,dan ina da wajen zuwa,.Ta kalli Jummai.. Ba wata kyakyawa bace,fuskar nan taci bleaching, kan nan Dan kare da attachment din gashin kanti,.kai da ka ganta Kaga yar Duniya,,kuma ita Zahra ta zaba a matsayin Qawa,. Farkon haduwar su a saloon ne tun ana saura 3 month bikin su,a time din taje Shampoo na sallah., Baje kaya tai tana wa Matan wajen Talla da bayani,Wannan duk iskancin kishiya kikai amfani dashi sunan ta sorry,,ita tasan makamar kishiya,tai ta zurma su..anan Zahra ta zurmu,bata aure,auren ta 3 duk ya mutu,dan da zancen hakane,toh yaci ta zauna gidan Miji.. Taja gauran numfashi, tare da kada kai,"Jummai anya zani kuwa?.Dan yau banjin dadi kadan, sannan wallahi gani nake ma kamar mutumin nan fa Boka ne,.Jummai tai tsaki.,a zuciyar ta tana tunanin Kar Zahra ta kwafsa mata,dan har sun shafci kudin da za'a fadawa Zahran,na kan ya zama nata.. Da sauri ta dawo wajen ta, " Waya fada miki Boka ne??.Malama inma zaki ware ki ware,ita ina take??..kika San ita wajen wane bokan taje??..Nan tai ta zugo ta tare da zugar shedan,suka hadu suka sha tunanin ta har ta amince,. Tana cije ciwo har suka je kwalta suka tsaida keke Napep sai wajen Boka.. "Yauwa,Jummai kice ta shigo,.ta kallo Zahra," ki kula,kiyi yarda Yace,dan wannan ce kadai damar mu da abinda ke jikin ta..Yanzu ki kawo sarkar naje bakin asibiti na sayar, dan dole mu cika mishi kudin shi,,.Tai Jim,dan sarkar auren su ce.,Abban su Hafeez ya sai musu,amma tanaji tana gani ta cire,sai zugata take.Ai Wai biyan bukata yafi dogon buri,,. Ta shiga ciki,da sauri ta fito,dan Ganin dakin baki kirin dashi,.sai da ya kara mata magana tukun ta shiga da sallama,. Ya amsa.,a rabe ta zauna tana karanto ayatul kursiyu,, Ta zauna,,.Ya taso yazo kusa da ita,.Zaki tashi ki cire gyalen ki,sai ki kwanta akan gadon Nan, ya nuna mata wani gu tare da haska mata da waya,,gaban ta ya fara dukan uku uku,"Gyale malam??.Yace "eh.,saboda komai ya ratsa Ku keda yaron,,.Ta kada kai tana Dari Dari,.tun kan ta zauna ya matso,.Da sauri ta tashi,." Malam mey za ai ne??."Kinga, ba'a magana a dakin nan,yana kokarin kamo ta ta Matsa da sauri tana,"Amma Allah ya isa,.Ashe wajen dan iska ta kawo ni??..Da sauri ya biyo ta,ina Ai ko nauyin cikin ta bataji da gudu tai waje,.ba gyale bare takalmi,jakar ma ta manto ta dakin,.Allah yasa doguwar Riga baka ce a jikin ta, ta kunce dan kwalin,.Tafiya take bata ma San ina zata ba.,Ga wani azababben ciwo da yafi na tun jiya yana ratso ta,.Wani mai Taxi ne ya shigo layin da fasinja,.Dakyar take daga kafar ta, ta zauna a baya tare da sanar shi inda zai kaita,..Tun tana cije wa har ta bara gantsare wa tana yarfe yatsu,.Mai Taxi ya kula da ita,.Da sauri ya tsaida mota yana masifa,."Dama nakuda kike kika shigo min mota salon ki haihu mun aciki??..Toh wallahi fito,Fito maza.,Dakyar take motsa baki,."Dan Allah ka karasa ni gida,.Yace"aa..fito.na yafe kudin ma,.Gashi dai tsakanin su da gidan baifi kwana 2 ba, ga unguwa sabuwar unguwa ba kowa,.Haka tana ji tana gani ya dire ta nan,. Ta sawo kan motar ta kenan ta hangi wata a chan nesa rike da kugu a durkushe,,. Daga gani Matar na jin jiki,,Sauri take ta koma dan 5 har ta kusa,.Gashi ta bar Zahra a gida da tsohon ciki,.Ummi tayi tayi ta kai dare taki,duk da ko ta zo kusa da ita banda habaici bata abin mata,amma Hakki ne a kanta zama da ita tsakani da Allah da tausaya wa. Birki taja,kan ta fitotaiy wajen Matar da kanta ke durkushe,. "Ya salam,Baiwar Allah Daga ina haka??..Da sauri ta dago kanta dan jin muryar mai magana,. Ido ta waro dan Ganin mai murkususun...ido fal hawaye sai cije lebe take. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 8:12 AM] Feenat Ja'afar: [1/29, 1:04 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 64_"Sis Zahra mey ya kawo ki nan??..Inalillahi,.Ciccibar ta ta fara,."Kiyi hakuri.,yanzu ma saurin da nake na dawo gida na barki ke kadai,.Ita dai Cije lebe kawai take,.Dakyar take fadin"Sa'a ki taimaken zan mutu,.Da sauri ta bude baya tana fadin"ba zaki mutu ba,kiyi hakuri muje asibiti,. "Ga waya na ba chargy,na mota yaki min,ban San wa zan kira ba,,Ya salam,sannu,,.Reverse tai a hankali, tana hawa kwalta ta fara gudu,.Ganin yadda take zufa yasa ta kure mata A.C,duk da bata son kamshin dake fita aciki,.Ajima kadan ta juyo,kan ta kalli titi..Ta mata sannu yafi a kirga,.Ta kara dabarar sa chargy fir wayan taki karba,. Suna zuwa ta kira Nurse da attaindance suka ciccibe ta,.Nurses Yi suke amma ina,fir cervix yaki budewa,,Ga tazo har 8Cm..Sa'a ta sai kai kawo take,har 6 shiru,sai lokacin ta tuna da Drn dake duba ta,,Tana zuwa yana kokarin tashi,.Dake yana da kirki sai ya biyo ta..Har ciki suka shiga,,Yai yan dube duben shi,,.Sai lokacin ta tuna da ta kira Hafeez ko a wayan wani ne,.Dr ya ara mata waya,,.Zatai waje Kam ta rike Sa'a Wai Kar ta tafi ta barta,.Ta zauna a gefen gadon,." Zahra kiyi hakuri,zan kira Hafeez,yasan halin da muke ciki,InshaAllah zaki sauka lafiya,.Dakyar ta cika ta,,sai dai tana fita ta cije cije ta fara mai yawa,.Matsalar protein,Sa'a ta shigo,.Likita yace ta samu,ta girgiza kai.. "Wallahi matsalar network,yace" Gashi Preeclampcia ya fara,dan akwai protein a urine din ta,.sannan ga major problem din,Bpn ta,.Tana ma zuwa awu kuwa??.Ta daga kai,.."Eclampcia, Dr ya za ai toh??Subhanallah,. Babu numbern wanda ta rike a Familyn Hafeez, duk suna waya tana mota,"Baba,.Baban ta ne ya fado mata,.da sauri ta karbi Wayan,"Dr bari na sanar da Baban mu sai yazo,.Ya kada mata kai,."Zai fi,.dan a yanzu (there is no cure for Pre-eclampcia beside delivering of the baby,.),.And wannan yaki samu wa,cox cervix nata yaki buduwa,.Ina tunanin. Cs,.shine best solution indai muna gudun Kamuwar mai duka,.Yanzu zan fita,in kin kira abinda kuka yanke zan nemi sauran Doctors sai mu shiga emergency... Ta daga mishi kai,.Juyo wa tai Ta kallo Zahra da hawaye,.Itama mai d'aya kenan, toh ina ita ma biyu,.Har ranta ta tausaya mata,.Zama tai a kan gadon tare da ruko hannun ta., Tunda taji Cs ta tsaida kukan ta,. "Sa'a, Amini dan Allah,. Ta kallo ta,," Toh Zahra,yanzu ba numbern da zamu kira sai ta Baba kawai,,.Ga wayan ki kema yana gida,.Tana jin ta ambaci waya ta tuna inda ta baro jakar tata duka.,Baba ne ya dauka take sanar shi abinda ke faruwa, Yace "ina shi Hafeez din,. Tana kuka tace" Baba baya gari,Gashi layin shi yaki tafiya,.Baba Gashi Ba wanda ya Sani ko a gidan su Zahran,.Zan sa hannu kawai gudun Kar abinda ake gudu ya faru,..Yace"Gashi nan zuwa,.. Tunda ta fara wayar zahra take kallon ta tana hawaye,.Sa'a wace iri ce??..Mai saka alkairi akan sharri??.. Tun samun cikin nan kullum sai ta mata gori akan shi,.Ta wa Sa'a abu dayawa a zaman su,.Duk da zata rama,. Ga niyar ta ta zuwa wajen malam.,amma Sai gashi yanzu ita ke dawainiya da ita harda hawaye,..Wani irin kuka ta saka mai cin rai,. Kila ma Allah ne ya kamata da hakin Sa'a, ga fitar da tai ba tare da izinin Hafeez ba,Gashi ta kuma tsallake iyakar Allah,. Duk da ta gude Allah da ta gudo da Kila achan ma zata mutu a gadon Boka.. Kuka take Sa'an na aikin lallashi,ita a zaton ta Zafin ciwo ne,.it a ranta tama manta da Zahra kishiyar ta ce,gani take tamkar Fadeela ce a gaban ta a haka,ga ciki yai sama ba halamun zai sakko kasa...Hawaye take tana lallashin ta,."Zahra kiyi hakuri kiyi shiru,InshaAllah yanzu za'a shiga dake,.Ina tsoron sa hannu ne alhalin babu wani Babba a kusa.. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [1/29, 2:11 PM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 65_Amma bari na fado wa Dr sai su fara shiri.,kai ta kada mata, ta bita da kallo har ta fita,.Ba'a jima ba sai gata ta dawo,tace "Ga nan Baba a waje,.ki daure ki samin numbern ko mutum d'aya ne a gida,Ta mika mata wayan,.Iyanzu tama daina jin ciwo,sai Sai abinda ba za'a rasa ba,.Numbern Mamy ta bata,.Ta tashi,Kamin tai dailing ta ruko hannun ta,." Sa'adatu, juyo wa tai kan ta amsa,,.ta kallo Nurses din,"Dan Allah sisters Ku dan bamu waje,.Suka kada kai sukai waje,.Zama tai tana kallon ta,. Hawaye take,."SA'ADATU dan Allah ki yafe min duk abinda na miki,.Ashe da gaske yar uwa kika dauke ni,.Nasan hakin ki Dana Hafeez ne yake tambaya ta yanzun,.Nasha binki da sharri kina tsallake wa,.Gashi yau har ta kaini da aikata Babban aiki,.Wanda nasan yau inna mutu wallahi wuta zani Sa'adatu... Kuka ta kara fashe wa dashi,Da sauri Sa'an ta ruko ta,. "Zahra ni baki min komai ba,. Inma kinyi wallahi na yafe miki,.Amma ki Sani.,Ba'a yanke rabo da Rahmar Allah, Kar ki kara ambatawa kan ki wuta Zahra,.. Murmushi tai wanda yafi kuka ciwo,." Sa'a meye hukuncin wanda yaje wajen Boka a wajen Allah??.Ta kallo ta,. "Boka Zahra,.Allah yai mana tsari dasu,. Tace" Amin,.Sa'a jiya da yau naje gun Boka, tare da taimakon shaidan da Muguwar Qawa,.Sa'a nayi shirka wa Allah Alhalin nasan hukunci,. Sa'a Bani da sallah ta kwanaki Arba'in,. Ga tsinuwar mala'ikun Allah dake bina har na dawo dan ban tambayi Hafeez ba,.Taya in na mutu yau,zan ce ina Aljanna??,.Taya ya Sa'a.. Nan ta hau bata labarin yadda sukai da Shi.,da tafiyar Jummai da gudowar ta har zuwa Ganin da ta mata,."Allah kadai ya cece ni a yau,da Tuni na tafka kuskuren da har na mutu bazan Iya goge wa ba.,.Kuka take kamar ba ita ke labor ba,.Da tsananin tausayi Sa'a ke kallon ta,. "Ki gode Allah Tunda baki yarda dashi ba,.Sannan ki gode Allah Tunda kin tuba kin kyautata niya,.Allahu Gafurur Raheem ne Zahra,. Tabbas kin Tafka kuskure, Amma baki idda ba... Shigo war Dr ne ya katse su,." Ga nan Baban ya sa hannu,.sannan ya kira Baban Mai gidan,.Kar Ku damu,Lafiya za a fito da ita.., Yace Sa'a ta fita zasu kimtsa Zahran dan wuce wa Operation Room,. Da kuka Suka rabu da Zahra,ita fa gani take in ta shiga bazata fito ba,.Burin ta tace wa Hafeez ya yafe mata.. Tana fita Abba Yace"yanzu na kira shi Alhajn su Hafeez din, Sai Ku kimtsa,Ganan na basu advance kan a fito da ita,dan 10k kawai gare ni a gida.., Ta kada kai "Baba mun gode,.Bari naje gida,dan dakko kayan ta da abin bukata.. Ya kada kai,.. A hanya Suka hadu da Mama,ta fada mata inda Baban yake., Tana bude gida waya ta fara sawa a chargy Allah ya so ta da wuta, Dakin Zahran a bude,ta shiga,kaya ta debo set uku,karaf kaf ba zani sai skirt sai doguwar Riga,. In ba shadda ba,duk dinki ita kan batta a skirt, ganan ranar zani tazo,..Tana bude Dayan Side din ganan kayan baby duk na mata sai unisex,. Sa'a tai murmushi,. wato itama mace take so kamar ta?..Allah basu Nagari shine fata...Allah dai yasa Zahra ba tai tarun Banza ba..,Ta fito ta haura sama,.Kayan ta masu Riga da zani ta dakko guda 2,ta dau pillow da sauran abin nema,.Abincin da tai kan ta fita ta juyo duka,,.Ta Bude ma'ajiyar kudin ta ta dakko kudi,Na Adashen da suke a office ne,jiyan nan ta dauka,tana burin rabawa 2.,ta kaiwa su Baba,d'aya tai wa Zahra siyayya,.30k ta dauka,ta maida sauran,.Ta kulle gidan ta fito Chargern mota ta sauya,ta kunna wayan,.Kamar mai jira aka kira,.Hafeez ne,duk hankalin shi a tashe,. " Unique yau ina kuka shiga ne haka??.. Na kira Zahra wani yana dauka Wai a gidan shi ta bari!.Bata gidan ne??.Damm taji gaban ta ya fadi,. Wato dan iskan bokan ne ya dauka??,.wace karya zata mishi dan wanke Zahra ita kuwa a yanzu???..katse ta yayi,."Hello,.Da inda inda ta amsa,."Amm..Dama,.Am,Tun dazu nake kiran Ka yaki shiga,.Zahran ce dama..Da sauri ya katse ta cikin fada.."Wajen wani katon ta bar wayar tayi??..Kenan bata gidan??.."Aa,,Dear Ka saurare ni,.ina ai ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,."Dan taga bana gari ta sirki wani iskanci koh.. "Hafeez tana Theater Room..Sit yai dan jin ta ambaci sunan shi da kuma Theater Room..Sai kuma ya dawo ya rikice..," Mey ya same ta??..Haihuwar ce??."Eh.Amma yanzu za'a fito ma InshaAllah,. Ka mata adu'a.., Ce mata yai ta kashe ga Abba yana kiran shi...Katse wa tayi,,Tai ajiyar zuciya,. Hafeez akwai kishi,Tuni idon sa zai rufe..,Tana tsoron yasan abin nan,Allah yasa Bokan nan Kar ya tona wa Zahra asiri,Tunda ga Jaka,Takalmi,Gyalen ta duk suna gidan shi. By Feenat Ja'afar & Hauwa Damary [10/2, 8:16 AM] Feenat Ja'afar: [1/30, 1:52 AM] Feenat Ja'afar BARIKI...IYAWA 66_Baba mai gadi ta sanar wa abinda ake ciki,.Tana kokarin fita da mota sai ga nan Jummai, rike da Jaka 2 a hannun ta,. Fitowa tai a motar Ganin kanta tsaye tai cikin gida,Binta tai taga Iya gudun ruwan ta,. Kofa take ta ja taki bude wa.."Hala da gadon Ubale a gidan nan ne Jummai??. Ta juyo baki sake tana kallon ta,. Harde take da hannu a girji, ta hade girar sama da kasa., Sai tai mata bala'in k'warjini,. Dan Tunda suke zuwa gidan Sa'a basu ishe kallo ba bare tai musayar yawu dasu,. Kai ta girgiza mata,. "Wajen Zahra nazo.. Rai hade tace"Uhmm, daga nan fa??.Duk rashin mutuncin Jummai sai ta zama kamar wata doluwa a gaban Sa'a,. " Jakar ta na kawo mata,. Baba mai gadi ta kwalawa kira,cewar ya kulle mata gate ya zo kuma, Tace ta bata jakar,.Ba musu ta miko mata,. Maimakon ta karbi ta Zahran, sai ta warce ta Jumman,. Yayi dai-dai da zuwan Mai gadi,. Matsowa tai da zummar kwace jakar ta taja baya.. Hannu ta nuno mata,.tare da kada mata su,. "A'a.,ta kada mata hannu halamar gargadi," (Don't even think about it),.Tai mata wani kallo.." Dan Kinsan Allah? kika yarda kika matso sai kin yaba wa A'ya zakin ta a gidan nan,.. Chak ta tsaya,baki sake ta kasa magana,. Ta kallo Baba maigadi,wanda ya dakko katuwar gorar shi,. Jira yake Tace "Ass,ya sau aiki.. " Baba in tai k'wak'waran motsi Ka bigen yar iska,.Ya kada kai "An gama Hajiya,. Tuni ya Matsa gaban Jummai yai (ready)da sandar shi,. Zazzage jakar tayi,kudi Suka zubo da tarikicen magun gunan ta,.Ta zuge munafukin zip din cikin, sai ga sarkar Zahra ta fito,. Wanda akallah zatai 250,haka Abban su Hafeez ya sa musu,.Ta makawa Jummai harara,."Macuciyar Allah ta'ala kawai,.. Jummai ta hadiyi yawu,.. Tace" Da kika boye sarkar,ce mata zakiyi dan wannan chanjin ne kudin sarkar??.Ta girgiza mata kai.., Sa'a tai kwafa,."Allah ya so ki baki siyar ba,da wallahi na Lahira sai ya fiki kwanciyar Hankali,."Ashawo kawai,.Ta warce jakar Zahran tana kara hararar ta,. Gyalen Zahran ne aciki da wayar ta, ta dago tana zare mata ido..,"Ina kudin da ke jakar ta'ta kan kije Saida sarkar??..Da tsananin mamaki Jummai take kallon ta, a zuciyar ta tana "Wai ina Sa'a tasan duk wannan abun?.."Tambayar ki nake?..A yatsine tace. " wane kudi??.."Au tambaya ta ma kike?.."Eyee??.. Ni zaki gwada wa BARIKI??.. Tai kwafa,. Kudin jakar jumman ta tattara ta mikawa mai gadi,."Baba kirga min su da sauri..,Da sauri ya lissafa,."Dubu Asirin ne da Bakwai da Dari uku,.Ta kada kai,. "(Good),.Baba ware min Ashirin da biyar aciki,.Ya kada kai, tuni Jummai ta zaburo,,."Wallahi baki isa ba,Dubu ashirin ne nata,.Toh Wai ma ina ruwan ki da harkar mu??..Sa'a tai wani murmushin mugun ta,. Tace" Karamar Yar iska kawai,.Ba kince babu ba??..Nasan Na Zahra dubu Ashirin ne,.Biyar din cikon na Taxi ne,.Sannan,daga rana irin ta yau, Baba idan Ka kara Ganin kafar ta a gidan nan na baka izinin Ka karya shegiya,. Yace"An gama Hajiya.,Jummai tai mata kallon Banza,. "Ai ba wajen ki nake zuwa ba Malama,. Wajen k'awata nake zuwa,.Kai ta girgiza mata, tana murmushi, Da key din motar ta ta nuno ta " Idan Jummai ta fito a cikin Uwale da halaliya,toh ki kara sako kafar ki a layin nan ma kadai inda kiga??.. Ta dawo kan Baba,"Ka ajiye min wannan jakar,Ka bata sauran chanjin Ta,. Sannan kan na kirga(10),Ta bace min da gani anan,.Tace"D'aya,.. Ya duk'ar da kai "An gama Hajiya,.. Kan Jummai yai.," Maza tattara kan wa'adin ki ya cika,. Sa'a tace"Biyu,.Kallon banza ta tsaya yi mata,."Uku,.Ba tsammani taji Baba ya rafka mata Gora a gadon baya,Ai ba shiri ta hau tattare kaya tana Kunkuni,.Sa'a Tace "Hudu,.. Baba ya sake sakar mata wata,.Ba shiri tai magana" Toh Ka dakata man na hada,.Da mugun ta Sa'a tace"Biyar,. Ai kwa ya kara dagawa zai muka mata,datai wani uban tsalle sai tai gefe,."Allah ya isa wallahi,. Sa'a tace"Shida,.Sai kwa Baban yai kanta da gora,.Haba wa.,Jummai K'afa mai naci ban baki ba,.Sai ta runtuma Gate a guje tana kiciniyar bude wa,. Sa'a tana dariyar mugunta Ta kwala da karfi,."Takwas,.Ai baba ya samu moriya, tuni ya kara sau mata aka,.Ihu ta kwala, "Wayyo,Toh Ka bude na fita man,.Harda yar kwallar ta,.Baban yace " Ba kin tsaya taurin kai ba??..Ni dan Tauri ne,.Sa'a ta kara kwalo wa"Tara..,Dai dai baba ya bude mata,amma da yake Shima chali-chalin kansa ne sai da ya muka mata,.Sa'a mey zatai inba dariya ba,. Har kasa..Fadi take "Ki tsaya man,Yar Kot'ar nan..Sai abi wani sarki kuma,.. Da Allah ya isa ta shiga Taxin da ya kawo ta,dama tace ya tsaya,..Har ta bar unguwar tana Allah ya isa,. Sa'a ta zo gun Baban, Shima sai Dariyar keta yake bayan fitar jumman,. Kudin ya bata,." Kaji Min Y'a da taurin kai Hajiya..,Sa'a tai dariya,"Ai nasan bazata dawo ba,. Dubu (2)ta ware,"Ungo Baba, kaima Allah ya sha dakai,.Bani kayan ma kawai nakai ciki,. Ya duka baki har kunne,."Wai Wai Wai,.Hajjaju Harda mu??..Tai murmushi,. "Toh Allah ja da kwana,.Allah ya sauki Yar uwar ki lafiya.. Tace" Amin,.Sai Lokacin ta tuna da asibiti, da sauri ta sa kayan aciki,ta boye sarkar ta kullo tai asibiti.. By Feenat Ja'afar 67_Tana zuwa duk yan uwan Zahran sun zo,.Su Aunty Maryam,. Suka tare ta suna mata sannu,.Tasleem da Auntyn su Zahran Suka Taya ta debo kaya..Tambaya suke an shiga??.Suka ce"Wai sai(9),.(In charge)din ne sai yanzu yazo,. Ta duba agogo,(8:43)..Tai ajiyar zuciya,. "Toh Allah yasa Ai a Sa'a,. Suka ce " Amin,. (8:55)Suka garo ta daga labour Room,. Tayi lamau,kamar mai bacci,.Cewa tai a tsaya tukun,.Duk Suka iyo kanta,."Sannu Zahra,.Ta daga musu kai,.Sa'a take kallo,.Kan ta ce ta duko kanta kadan,kamar mai rada tace"Sis ya Tambaye ni koh??..Ta girgiza mata kai,. Hawaye ta fara,"Nidai kira min shi dan Allah,Nace ya yafe ni. Sa'a ta dago,."Kiyi hakuri sis,.kinga Doctors na jira a theater room,. Amma nayi alkawarin zan nema miki(Right now)..Ta goge hawayen ta, "Nagode,. Allah ya kaddara haduwar mu,..Sai ta karyar mata zuciya ta fara itama kuka,. Kowa Kallon su yake, musamman Aunty Maryam da tasan Sa'an Basa shiri da Zahra,. Ta rike Sa'an aka gara Zahran,. Sai fatan a fito lafiya. Hafeez din ta kira,.duk da wayan shi biyu tun zuwan ta,. Ta Isar da sakon Zahran,. Suna nan zaune har kusan (11)Kamin aka garo ta,.Ba inda ke motsi a jikin ta,. Suka basu Babyn girl din data samu,. Zahra taje wajen Nurses din,." Ya naga bata motsi toh??.. Sukai murmushi,. "Ai an mata (Anesthesia),. Za ta Iya tashi " (any moment) …Kar ki damu,.Ta sauke ajiyar zuciya..Tace wa su Aunty Maryam zata zauna taga tashin ta,. Su kace taje gida.,Ga masu kwana da yawa,. Sannan gidan su ba kowa.. Aunty Ladi aka bari ta kwana da ita,.Dakyar da taimakon wayar Hafeez ta Iya bacci,. Dan ma ta taho da Tasleem,. Washegari sassafe ta gama komai,.Su Bahon wankan baby,ruwan zafi,.Abinci, Tun asubar fari data tashi bata koma ba,.Bacci ne tun yana diban ta har ta daina ji,.Akai Assalatu ta tashi Tasleem, da mamakin ta taga sai kiciniyar soye-soye take,.Tace Ai da ta tashe ta,. (7)Suna asibiti,.Ta tashi Alhamdulillah,Sai dai Rashin karfin jiki,. Sukai mata sannu,,ta dau baby,mashaAllah, Babyn Mai kyau da ita jinin su Hafeez, kamar su guda,. Tace"Umm,su Zahra, An samu abin nema,.Ganan Zankadediyar Budurwa mun samu,.Tai Murmushi tare da kokarin a gyara ta,. Aunty Ladi tace zata gida Tunda Sun zo,dan bata shirya ba,.Tasleem ta tafi karbo wani result,. Ta kallo Sa'a,. "Sis kema Allah ya baki Baby,.Tai Murmushi,. "Sis sai dai fatan sauka lafiya,.Ido ta waro,." Kai haba??..Ta kada kai tana murmushi,. Sai yanzu ta kula da farin Sa'an, tai wani fresh da ita,. Ga cikin duk yabi jikin ta, musamman kasa.. Tai murna kwarai har ranta,.Tai mata fatan Rabuwa lafiya,. Kan (11),yan uwa sun zo da daman su,.Kowa yana tai wa Sa'a son barka,dan kwarai ta burge su,.Ga nan mai kula zai ga cikin ya dan tasa,.Aunty Maryam data kula da cikin Sa'an taji dadi kwarai,.Tana son Sa'a, don mai son naka Ai Ka so shi. Hafeez ya kira su ta bawa Zahran Suka basu waje,.Amma sai ta rike Sa'a,. By Feenat Ja'afar 68_Azahar Hafeez ya danno Asibiti, ko gida bai je ba,.Sa'a ta mika mishi baby tare da manne mishi suna Kallon ta tare,.Zahra tuni ta fara adu'a,.Dan jin chanji a ranta,.kai gaskiya kishi jaraba ne,.Ita Sa'a bata dauki abun wani abu bama,. Kwanan su 3 aka sallame su Suka tarkata gida,.Dan fa Zahra tsaf take manne kayar ta ba ko kara,. In za'ai wanka,ta dinga"Ai hankali da idon ta,. Koda Hafeez ya nemi ba'asin waya,Sa'a ce tace"Ai ita ta bari a despensry,.Ya chake mata kudin ta na asibiti,.Fir tace Gudun mawar tane,.Baba ya kira yai mishi godiya.. Sa'an shi ta daban ce. Zahra ko ta Jummai bata yi,burin ta ta tsallake fadan Hafeez, tasan yanzu K'afa ya daga mata. Batun suna da ya tambayi Zahra ta bashi mamaki da tace Sa'a,. Kuma yaji dadi sosai. Amma tace ya rufe Kar ya fada mata sai ran suna. Dake garau take,suna ba fashi sati nayi,. Da safe taci Ado na kece raini da Wani less Din su da Sa'a ta din Ka musu na fitar suna,. Kiran wayar ta Sa'an tayi kan ta same ta a stairs,. Ta kalli mudubi, komai yaji,.Taso sarkar ta na nan yau ta Kar kwalliya,."Fashion"tasa ta fesa turare,.Mai zama mata tace"Kayan nan sun amshe ki Zahra,. Tai murmushi tare da fadin ta gode,. Saman ta haura, dan amsa kiran Sa'a,. Tana zuwa ta tarar ta taci Ado itama da Less din nasu,.Color ne kawai ya banban ta..Ganan sarkar ta irin ta ta a dambare a wuyan ta,.Ga zobuna manya guda biyu,.Bangles na Awarwaro manya kamar Gold,. Tasha Adon Gold, sai shining take,.Sai ta gane kyaun les din a jikin Sa'an.. Tai murmushi, "Sis kinyi kyau fa,. Itama tai murmushin,. Kan ta zaunar ta kan kujera,. Ta kamo hannun Zahran,,. "(Guess what)?.Ta bude ido da Neman Sani,."(what)??..Tai murmushi,. "Kawo hannun ki,amma ki rufe ido,.Ta kada kai da murmushi,.. Sarkar Sa'an ta zaro a inda ta boye,,.Ta daura mata a hannu tare da fadin,"Tan taran.., Ido Zahran ta bude,.Aikwa Tana Ganin sarkar ta ta rukunkume Sa'an da murna..Hafeez da Tunda ya shigo yai tsaye yana kallon su a bakin kofar,.Murmushi yake,.Komai Sa'a tai burge shi take,.Yaji dadin ganin su kwarai a haka.. Karaso wa yai yana. " Kun dai manta dani a rayuwa Matan nan koh,.Suka cika juna suna dariya,. Ko Break ba wacce ta kula nayi."Ai angon karni baya yunwa,.bari (1)minutes,. Zahra rike ta tai,."No yi zaman ki Maman twins na zubo mishi..Ta kada kai tana kallon hafeez,. Yana Ganin ta fita ya ruko hannun ta,."Ya Zahra tasan ke Maman twins ce?.Tai Murmushi, kawai (Guessing )ne..kai ya kada "Kai kunyi kyau fa Allah,.. Tai murmushi tare da Ruko kumatun shi kamar Wani yaro" Mun gode,.Sunan wa aka sa ne ni?? Yace"sistern naki naki bata baki Bayani ba??..girgiza kai,. Dai dai shigo war Zahra da faranti a hannun ta shake da papee chicken,.Zahra ta taro ta tare da karbar Abincin,. "Wannan fa ya miki nauyi.. Tai Murmushi,. Hafeez yace"Baki sanar ta mai sunan Babyn ba?..Tace "Da zumudin Dana zo kenan,so nake na fada a gaban ka,Da fatan baka rigani ba?. Sa'a sai Kallon su take.,amma su sai ja mata rai suke., Tace"Hajiya aka sa Ai na Sani Tunda baza Ku fadan ba,. Sukai Murmushi,. Zahra tace" Baki chan Ka ba,.Ta rike hannun ta,. "Sunan Babyn mu, SA'ADATU Hafeez Takwarar Momyn ta..Sa'a ta waro ido,."Ni Sa'an?. Ta nuno kanta,.Kai ta kada mata,.Basui aune ba takwa kwala kara,tare da Doka tsalle,." Wayyo dadi Barni da raina,. Da sauri Hafeez ya nuno ta,. "A'a,kinyi na kudin ki Unique,.Kar ki mini illah.. Tace" Sorry.. Sorry,.Murna fal ranta ta rukun kumo shi,. Ta hado Zahran ma duka tana kwarara musu Godiya.. By Feenat Ja'afar [10/2, 8:19 AM] Feenat Ja'afar: BARIKI...IYAWA 69_Dariya suke tayi,farin ciki fal ran su,.Cika su tai ta ban kada cushion din ta dakko kudi ta mika wa Zahra,."Ga nan ajiyar ki,.Ta karba,tana kallon ta da rashin fahimta,. Ganin Hafeez a wajen yasa tai mata gwari gwari,."Cikon Sarkar Jummai,. Zakui waya dai,.Ta Ciro 5k,"wannan kuma Tukwici ne,kan Babban yazo,.Zahra tama rasa mey zata ce mata,.Ganan sarka ta amso mata,.Ashe harda Kudin Boka sai da ta lale su wajen Jummai? Har ga Allah ta fidda rai da samun su,dan tun daga ranar Jummai har yanzu bata kira ta ba,.Tai murmushi, Lalle maganin shege,akace sai Dan Iska,.Jummai ta gamu da gamon ta,. Kawai sai ta Rungumo ta tana zuba godiya ba adadi,.A ranta tana rokon Allah Kar ya kara kawo ranar da zata sabawa Sa'a, dan ta mata Hallaccin da zata Iya kiran ta da YAR UWA CE kadai mai mata ba kishiya ba,. Haka Suka tafiyar da sunan su gwanin sha'awa, komai Sister, komai Sa'a,. Har aka watse lafiya.., Tabbas Zahra tasan Sa'a ta daban ce,ba yadda za ai ta hada kai da ita,.Don Bazata Iya ba,Hakan yasa ta dau damarar janyo hakurin ta na Da,ta yarfa wa ranta,..Takan gujewa duk wani cikas na zaman su da Sa'an, Duk da ta fara mata karar abubuwa da dama,.Sai dai babu ta inda ta rage wa Hafeez.. Tabbas kowanne bawa da irin baiwar da Allah yake haifar sa,.Musamman mata,kowa da irin tata salon Iya kissar,. Tanan kam,ko ita ta sarawa Sa'a,. A hankali ta siye su da yan uwan su Cikin hikima da Dabara,.Sai dai Abu d'aya ta Kudirta a ranta,,shine duk yaran da zata Haifa mata,toh fa zata damkawa Sa'a su,dan ta karantar su Darasi,Musamman na gidan Miji,. LAIFIN DADI???.. Naufal,da Nailah ne ke ta kai kawo Cikin Sittern su a parlourn,. Twins din Sa'a kenan,. Yaran gwanin sha'awa,bulo bul dasu,.Watan su(6).Amma in ka gansu ka dauka yan wata (8)ne,.Danna Button din sittern Naufal ke yi yana wakar "Twinkle Twinkle Little star,.Yayin da Nailah ke ta bangala mishi baki tana dariya tana bubbuga tata,. Da sallama ya shigo,.Daga chan kitchen aka amsa mishi,.Tuni ya karaso da sararrafa wajen yaran,wanda tun sallamar shi Suka fara murna,." Ina Matan gidan aka bar mun 2 little Angels na su kadai??..Ya cire Nailah "My little Princess,. Papa's home,.Sama ya hulla ta ya chafe,.sai dariya take bangala wa..Ya sauke ta ya dau Naufal,Shima ya masa,.Fitowa sukai a kitchen din zahra inda suke hada kwanikan lunch,. Da fara'ar su Suka fito,.Zahra dauke da karamin Cikin ta data kara Nad'a,. Jikin shi Sa'an tai kamar yadda ta saba,. Da sauri Zahra ta kau da kai,.Gudun zigin shedan,.Irin haka yasa take mar Marin yin nesa dasu,dan tasan zuciya batta kashi,kuma zo mu zauna,Tabbas wataran zo mu saba ne,gwara kazantar da bata ga ba a wajen ta tsafta ce,. Sai dai tana tunanin rayuwar gidan da bata tare da su Naufal,Ga Naina ta saba dasu,. Tai murmushi, dan tuna wa da Naina da aka kai yaye..Da tasan ta na nan da Tuni tana makale dasu Naihan.. Ta kallo Sa'a, Yadda ta maida hankali kan Mijin ta,. In Hafeez na gaban ta, toh hatta yaran ta gefe suke.,bare ita,.Tai murmushi,. Bazata kara da Sa'a ba,dan ko ta bangaren kula da Miji ta daga mata tuta,Burin su Allah ya kara hade Kansu. Alhamdulillah... Nan muka kawo karshen BARIKI IYAWA...Muna rokon Allah kuskuren da mukai ya yafe mana.. SADAUKAR WA. An sadaukar da labarin BARIKI IYAWA ga daukacin Masu karatun shi,.Da fatan an tsinci abinda ke Cikin shi. Nafisa Bashir Tanko(Feenat Ke muku fatan Alkairi. Luv All

Contact Form

Name

Email *

Message *

Translate

LATEST POST