GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 1
Posted by ANaM Dorayi on 02:56 PM, 30-Apr-15
Under: Gangarjikinsa ta Aura
Hatta iya abu data tsani hanna yau hanna ta
batatausayi matuka sai ta rushe da kuka ta dinga
rikehanna tana lallashinta. Da kyar matan nan
suka iyabanbare hanna daga kan shimfidar
mahaifintasuka shiga da ita cikin gida. Hanna
tana rusa kukakamar rabta zai fita amma ta nemi
hawaye ta rasa. Sai tayi shiru ta shiga dakinta ta
kwanta ita damahaliccinta ne kadai tasan me
takeji a ranta waniabune ya tokare mata zuciya
kamar dutse abun yafikarfin kuka. Hanna ta kalli
gabas da yamma kududa arewa taga babu wani
mai fitar da ita dagatsananin bakin ciki nan da
take ciki sai allah . Ta tuno nasihohin da haisam
yayi mata aranarkarshen da ya rakasu tasha sai
tasa hannu ajakarta ta lalubo carbi ta fara ja.
Addu'oi iri iri hannako magana ta daina yi, yan
gaisuwa a jere a jeresuna shigowa dakinta suna yi
mata gaisuwa sai daikawai ta bisu da kallo har
sha.awa take idan taga masu kuka da hawaye.
Don ita kukan ma takenema ido rufe tayi ko taji
sanyi a ranta ta kasa sallace kawai take fito da
hanna tsakar gida sai kumaasuba take shiga
bandaki tayi wanka.Banda wannan babu abinda
hanna take yi sailazumi. Babu ci ba sha sai da
aka ga kwana da kwanaki hanna taki cin abinci
sannan su iya salmaisuke dama dan farau farau
suka tsaya tsayin dakaakanta suka ce sai tasha
kurba kawai take badondadi ba ji take kamar
madaci suka dura mata donrashin jin dadin
bakinta da take ji anyi sadakarbakwai kowa ya
watse gida ya zama daga hannah sai iya abu .
Yayanta ma suk sunyi aure kowacce takomagidan
mijinta sai mutuwa ta dawowa hannasabuwa fil
sai a yanzu ne ta fara samun zubar dahawaye .
Kullum hanna kuka take rusa ita kadai adaki
babu mai lallashinta kaico hanna. Sati daya
satibayu iya abu ta gaji da ciyar da hanna, ayau
da sassafe shida da rabi iya abu tazo ta fara
bugawahanna kofa kamar zata karya kyauren
hanna nakishingide akan abun salla tun asuba
bayan tayisalla ta zauna jan carbi gyangyadi ya
dauketakamar a mafarki take jin bugun kofar tayi
firgigit tabude ido taga ba mafarki take yiba ta
zabura da sauri taje ta bude kofar. Iya abu ta
gani a tsaye takama tsantsan tayi kalar rashin
mutunci. Hanna tajigabanta ya yanke ya fadi
tasan rashin mutuncin yamotsa yau kuma sai
yadda allah yayi da ita.tace'' hanna a to an gaba
hada hadar mutuwa nayina allah nayi na annabi
na ciyar dake a aljihuna har sati bayu. Ga rogo
can n aika a siyomin zan dafa infara zuwa kasuwa
ina siyarwa don nima dan kudincefanen hannuna
ya kare ubanki bakar dawakadai ya bar mana a
rumbu don haka ke kincikashinki saura ta zama
kashin 'ya'yana zan ringasiyar da rogo ina samun
na cefane ina tuka dawata, daga yau ki fara ziyar
da kanki kafin a raba gadogama sunce sai na fita
takaba kar kice daman bangaya miki ba dan kar
in ajiye tuwan dumame nekizo ki gutsira mun
tuwo in kuwa kika sake kikagutsirar mun sai na
shakeki sai kin amayo shi.Hanna ta sunkuyar da
kai kasa hawaye ya zubo shar tace'' to naji'' iya
abu ta tafi ta barta anan atsaye kamar an kafata
ta rasa mafita kuma. Hanna ta kasance tana
kwana da yunwa sai ruwada take dirka wai ko iya
abu taji tausayinta ta dingabata dan tuwo amma
taga makatau, sai ta shirya tanufi gidan malam
uba kanin mahaifinta ta shaidanasa cewar yanzu
bata da abunda zata ci ko zaiajiye mata kwano a
gidansa ta dinga zuwa tana daukar abinci ko da
sau daya ne a rana ? Yanabudar bakinsa sai yace
mata daman ta girma ta rikawai ita yar boko ga
irinta nan abincin da zata ci yagagareta shi dai
shawara daya da yaga ta dacetunda duk samarin
garin suna tsoron zuwawajenta suce suna sonta
ganin ita 'yar boko ce to ta yarda yayi wa alhaji
bilya mai kudin garin nanmagana yazo ya aureta,
zata fi karfin abinci don hartuwan shinkafa
dafawa akeyi a gidansa dadaddare. Wani daci ya
disu a zucitar hanna da tajibayanin kanin
mahaifinta. Alhaji bilya da yakemagana wani
shirgegen tsohon mutum ne matan sa uku yaya
kuwa sun doshi talatin da yawaiyayensu basa
gidan kuma jikokinsa ma sa'annintane,
manomine ba laifi yana samu a dai garin shi
maikudi ne amma ai tana zuwa gidan ada
wajenkawayenta tasan yadda yanayin gidan .
Watakatuwar tukunya ake dorawa a gidan kamar
ta yan makaranta girki ma kadai ya ishi matan
baya gadukan mata da yake yi yana da ciwon
kuturtakuma harma ta fara fitowa hannunsa da
bakinsazaka kalla kasan kuturu ne yatsun ne
kawai basugama guntulewa ba amma sun fara
diwa. Hanna tatabbatar lallai baba uba ba sonta
yake yiba tunda zai hadata da alh bilya aure. Tayi
shiru a durkushe agaban malam uba tana jin
bayanan da yake matayace'' kin amince inje in
sanar masa ko kuma kinada magana kiyi.Hanna
ta nisa ta sunkuyar da kai kasa tace'' bababana
kin jin maganarka bane ko naki yarda alh bilya fa
kasan halinda yake ciki yana da lalurarkuturta.
Baba yanzu zaka yarda in aureshi a haka?Malam
uba ya fusata ya zabura hanna da fada'' kekinfi
sauran matan zane ne, asirinsu a rufe ko goyashi
zaki yi kina yawo dashi? Kuma shi da kansa
yasameni yace yana sonki zai aureki. Nake jira
daman a gama zaman makokin nan in shaida
miki. Tundakinki sai ki tafi ki nemo abinda zaki
dinga ciigardiya dake kinki aure babu mai ciyar
dake, tashiki tafi bani waje mutuniyar banza.
Hanna ta tashisumi sumi ta fice tana sharba
hawaye. Tana fita tanufi makarantar boko, ta
kuwa ci sa'a ta sami alhaji wani ma'aikacin da
yake zuwa daga local gov'nt tarubuta takardar
neman aiki[application]tun tuni zainemar mata
aikin koyarwa a primary garin.Hanna cike da
fara'a da murna tazo ta duekusahar kasa ta
gaishe da alhaji ya amsa. Tun ma kafintace masa
komai yace''hanna na kai takardarneman aikinki
wajen manyana alhamdulillahkansilan garin nan
ya gani ta sa hannu an kaiofishin sacretary''
murna ta rufe hanna yaci gaba da cewa'' to
amma abunda sakatare yace shine bazasu iya
daukarki aiki ba saboda akwai
wadatattunmalamai a wannan makaranta akwai
daimakarantun da aka rurrubuta za'a kara
ma'aikataamma daman banda garin nan don
haka sai daikiyi hakuri. Hanna taji ba dadi
hankalinta ya tashi tace'' yanzu malam alhaji ko
share share baza adauke ni ba ko a can local
govnt din? Ya ce shareshare ai kinfi karfin yin
shara hanna kije dai kicigaba da addu'a , na
manta ma ban fada miki ba natambaya ance
result dinku na jarabawa yafito amma an rike na
f.g.g.c kazaure saboda kunyi matukar ci sosai wai
har da masu nine distinctionkinga dole aki sakin
sakamakon sai anyikyakykyawan bincike anga ko
an baku amsa ne.Hanna tace'' binciken zai dadae
ne? Ya ce''gaskiyairn wannan yana daukar kusan
shekara ma ba'asaki ba. Amma daman da da
result dinki a hannu da tuni na samar miki aiki ko
ba'a garin nan ba.Hanna ta dade a tsugunne a
gaban alhaji tayi shiruta rasa yadda zata yi can ta
yunkura zata mikedakyar saboda jikinta yayi sanyi
sai alhaji ya mikomata yan kudi yace'' gashi kya
dan kashe'' dadi yalullubeta ta sami na cin abinci
don yunwa take ji. Tayi masa godiya ta nufi gidan
iya salmai . Ta isketaa zaure ta kasa zogale tana
zaune tana jiran masusaya hanna tayi sallama ta
shiga, bayan sun gaisaiya salmai ta ce'' hanna
lafiyar ki kalau kuwa kinburkice gaba daya kamar
ba keba? Hanna tayimurmushin karfin hali ta
ce''iya yunwa nake ji ko da sauran dumame''
tace''wada na ajiyewa ya tafokwallo, rabonki ne
zuba kici, da sauri hanna tamike ta nufi kicin don
ta zubo tuwan. Iya salmai tabita da kallo, cike da
tausayinta. Sharkab tana kukahanna ta fito ya
sami iya salmai tana cewa allahsarki habu ka
mutu kanar yarinya marainiya a duniya kaine
daman gatanta'' hanna ta zauna asanyaye tana
cin tuwan su duka hawaye suke yi.Iya salmai na
tausayinta itama hanna na tausayinkanta. Bayan
taci ta koshi tasha ruwa taje ta ajiyekwanon a
cikin gida ta wanke hannunta sannantazo ta
zauna ta shaidawa iya salmai halin da take ciki ta
ce kuma tana neman alfarma idan da hali
iyasalmai ta ajiye mata kwanan tuwo a gidanta
tanaaika mata iya salmai taji dadi kwarai da
hanna batayi kauron baki ba tazo ta sanar mata
da wuri taceinsha . Allahu kome taci da kashin
hanna to ammaitama ba kullum suke dora
tukunya sau uku a rana ba.Itama ba da ko ta
agareta ba bishiyoyin zogalene burjik a shuke a
gidanta. Ta tsinka ta dafa tasayar ko azo a tsinka
a danye a biyata. Daga ita saiwada wani dan
kanwarta data rasu ta barshi tunranar da aka
haifeshi ta dauke shi. Shima yanakokari ya samo
kudi, to da haka suke cin abincin, ranar da ba'a
samu ba su sayi na siyarwa ko suhakura idan
babu kudin sayan na sayarwa. Iyasalmai tace'' ai
idan naga 'ya'yan Habu raina dadiyake yi, ba don
habu yana dan uwana bamasoyayyar da nake yi
masa ce Hanna har yau ina jindandanonta a
raina'' hanna tayi shiru tana tunani a ranta tana
kuma tausayawa kanta cewar'' in har iyaSalmai
bata daina jin dandanin soyayyar da takeyiwa
mahaifinta ba har yanzu shekararsu tafiashirin da
biyar da rabuwa gashi kuma ma har yamutu rana
zancen sonsa ashe har abada iya Salmaibaza ta
daina jin dandanon son nanba. To itama tana
kyautata zaton haka zata kasance da donHaisam
tunda gashi dai yanzu bata ganinsa yayiaurensa
ma amma sai kara jin tana kara sonsa takeashe
itama haka zata dauwama kenan har
karshenrayuwarta. Soyayya gaskiya ce'' Hanna ta
fadaabaiyane. Iya salmai tace'' soyayya gaskiya ce
Hanna. Haka dai suka yini suna hira hanna ce
tadafa musu abincin dare suka ci sannan suka
yisallama Hanna ta tafi gida. Sun rabu akan iya
Salmaizata ringa turo wada yana kawo mata
abinci duksanda suka sami damar dafawa. Haka
hanna ta kasance duk sanda iya salmai tadafa
abinci ta aiko mata taci ranar da itama batadafa
ba haka hanna take zama da yunwa. Ta
ramekurkut da ita sai ido da dogon hanci tayi
duhukuma saboda tsaban wahala da tsananin
tunani .Ranar da iya abu ta fita takaba sai
maigari ya hado malaman garin da masu fada aji
na garin da yanuwan malam Habu don raba
gadonsa ga iyalansa.A zauren gidan aka zazzauna
ga iya abu gayayanta kakaf mata da maza ga
hanna a gefe.Itama da iya salmai. Maigari yace''
a karantawamamacin kulhuwallahu kafa uku uku,
da inna a'adaina kalkausar uku uku aka shafa
Allah yakaikabarinsa. Sai maigari ya fara da
cewa'' malamHabu ya rasu yabar mace daya da
yaya takwas.Dukiyarsa kuwa wannan gidan ne da
kumakatuwar gona. Amma tun ranar daya mutu
akabiya masa basussuka da ake binsa da dan
kudin daya bari. Ga manyan malamai nan zasu
raba gado.Ga sunayen 'yayan nan a wajensu zasu
shiga cikingidan su tsatstsaga su bawa kowa nasa
bangaren.Iya abu ta nisa tace ina da magana
nidai nicematarsa uwar yayansa kuma bare daya
ce Hannedon haka a tabbata an bata bangarenta
daban kar a saka min ita cikin kason 'yayana azo
ana rigima.Maigari yace'' ai abu rabon gado ba'a
cewa bareAllah ne ya raba da kansa don haka
duk yadda takama haka za'ayi. Malamai sun yi
iya kokarinsu sunkacaccala dan mitsitsin gidan
nan d gona. Allahcikin ikonsa hanna bata tashi da
komai ba sai rumbun ajiyar abinci,wani dam
mitsitsine kasace turmus a kasan da gidan
tururuwa sai dan wanibangare karami a tsakar
gida shine kashin hanna agona kuwa bata ciki.
Murna ta lullube iya abu gonada gaba daya
dakunan gidan nata ne da yayanta sai tace''
wannan rabo yayi daidai to yanzu ta tashidaga
dakin nan'' mai gari yace haba abu har
yanzutsangwamar da kike yiwa hanne baki bari
ba harmahaifinta ya mutu bakya rangwama mata
ba''iyaabu tace a'a babu wani rangwame yan
haya zansaa sauran dakunan ina karbar kudi
wannan abu ne fa na gado. Nan fa duk suka
hadu suna ta bawa iyaAbu hakuri ta barHanna
taci gaba da zama a dakinda take har Allah ya
yanke mata wannan zamatunda komai dadewa
aure zata yi. Iya Abu takekashe idanuwanta ta ce
in anga ta yadda Hannayauta sake kwana cikin
dakin nan nata to ta bata kudin haya ne a
matsayin tana haya.A cikin mutanen dake wajen
harda Alh bilya ya ceto tunda Abu tace haka shi
yayi alkawari zai dingabiyawa Hanne kudin haya
daga yau ya tambayiAbu ko nawa ne kudin hayar
dakin da hanne keciki ta kai kaice ta zambada
kudi ya zaro ya biya ba tare da ya nemi ragi ba,
ya biya na shekara ya saniya abu kora da hali
take yiwa Hanne ta zambadakudi dan ace yayi
tsada a kama mata a wani gidacikin ikon Allah sai
taga ya biya.Mai gari da sauran mutanen dake
wajen suka dingashiwa Alh bilya albarka, Hanne
ita da baba Uba ne kadai suka san manufar Alh
Bilya shi a nufinsaauren hanna zaiyi shi yasa ya
fara mata hidima,wani gululun bakin ciki ne ya
dira a zuciyar Hannamusamman da ya biya mata
kudin haya ta san lallaida gaske yake auren nata
yake so yayi ita ko garaa kasheta da a daura
mata aure da wannan mutumin kamar tace bata
son kudin hayar baza tazauna a gidan ba karya
biya sai tayi tunanin in bagidan uban nata ba a
ina zata zauna saita hakurakawai tayi shiru idan
tace zata koma gidan iyaSalmai to ai daki daya ne
kacal a gidan dan karamiita da wada suke kwana
a dakin ba zaiyu ita ta hadu da Wada a daki daya
ba saboda yanzu Wadashekararsa goma sha
takwas yama girme ta dashekara daya don haka
ya haramta su cusu a dakidaya bayan nan babu
gidan wanda zata iya zuwata zauna duk
danginta.Da daddare bayan kowa ya shige bacci
ya kwanta hanna na juyi a yar katifar ta kasa
bacci tsananinbakin ciki ne ya dameta a ranta
bau abinda takenanatawa a ranta sai zancen
hayar na. Ita da gidanubanta yau ta zama 'yar
haya sai ta rushe da kukahar ta gaji. Tace''Allah
kana ji, kuma kana ganina,kana kuma sane da
irin abubuwan bakin cikin da nake gani tun ranar
da mahaifiyata ta sakoni aduniya Allah ka fitar
dani. Kaine gatana ya sarkinsarakuna. A haka
Hanna ta kasance har shekaraguda da rasuwar
mahaifinta. Yau taci abinci gobe tarasa wannan
bai dameta ba sosai irin zurga zurgarda Alh Bilya
yake yi a danginta yana cewa shifa yana so ya
aureta. Dan har yaje ya sanarwa damaigari.
Maigari yasa aka kira Hanna fada ya shaidamata
abunda Alh Bilya yake nema a wajenta shin
taamince zata aureshi, ta yarda tana so a
dauraauren ? Hanna ta fito gar da gar ta fadi
gaskiyatace'' ranka ya dade banki jin shawarar da
ka bani ba amma dan Allah ina so a barni haka
bana so inauri kowa. Gaba daya aka dau salati
aka fara yiwaHanna ''cari to ba'a garin nan ba.
Duk garin nanwacece ta taba kaiwa shekara goma
sha takwas baa yi mata auren fari ba? Hanna
tace'' ba zan iyaauren Alh Bilya ba a matsayinsa
na mahaifina dan ni tamkar mahaifi yake a
wajena. To haka akayi daHanna a fada. Alh bilya
yaji haushin Hanna data kiyarda amma yasan
tuggun da zai tafka mata yarama.Bayan anyi
haka da hanna a fadar maigari dakwana uku. Alh
bilya yazo har cikin gidan su hanna da rana tsaka
. Hanna na daki a kwance tanajin yunwa tana
jiran a kawo mata abinci daga gidaniya salmai
tana fargabar ko suma basu yi abincin bane yau
sai ta jiyo muryar alh bilya yana rafsasallama iya
abu ta fito iya abu tace''yau alhaji dakanka a
gidan namu. Yace'' eh wallahi zuwa nayi mu
gaisa inji ko yaushe kudin hayar dana biyayake
karewa? Iya abu tayi dariya ta sosakwarkwata a
kai tace'' ai sauran wata uku ne inajin''ya ce''to
ki raba kudin hayar gida hudu ki daukikashi uku
naki ki bani kashi daya ragowarwatannin uku ki
kori hanne daga dakin da take haya in bata biya
ki ba ba ruwana'' iya abu ta batarai tace. To ni
yanzu na kashe kudi yaya kake sonayi a ina zan
samo kudinka da zan dawo makadashi ? Hanne
fakara'u ko sisi bata dashi ina zayasamo wani
kudin haya ta biyani? Gaskiya alh bilyakai ya dace
kaci gaba da biyan kudin haya don haka kace a
gaban maigari''yace''kash ni bakifahimceniba abu
ba don in takura miki ba nace kibani sauran kudi
ji rike sauran kudin ina nufinyanzun ki koro
hanne daga dakin da take donnibada yawuna
take zaune a dakin ba kuma ba'akudina ba. Iya
abu tayi dariya tace''oh na gane wato yanzu dai
in rike ragowar kudin watanniukun da suka rage
kenan sannan in koro hannewaje idan bata biyani
kudin haya ba ko. Ko bahaka kake nufi ba? Alh
bilya yayi dariya yace''hakanake nufi mana.iya
abu tace an gama ai a gabankazan koro shegiyar.
Gaban hanna ya yanke ya fadi tayi zumbur ta
tashi zaune ta dafe kirji tana tainnalillahi wa'inna
ilaihirraju'un. Iya abu ta wangalelabulen dakin ta
shiga budik ta sami hanna a kankatifa a zaune ta
mikawa hanna hannu tace''banikudi. Hanna
tace''bani da kudi. Iya abu ta wawurijakar hanna
zata wurgar waje hanna ta rike tana mata magita
tayi hakuri dan Allah ta rufa mata asiri,amma
kamar zuga iya Abu take.Hanna ta fito da gudu
daga dakin ta zo ta durkusaa gaban Alh Bilya
tana rokonsa dan Allah yayihakuri ya bar mata
kudin hayar wata uku kafin nanzatasan yadda
zatayi ta sake biya. Amma yayikunne uwar shegu
da ita yana cewa''yauwa Abu ki tattaro kakaf
kayanta ki watso''ana cikin wannanhali sai ga
Wada nan dauke da kwanan abinci yakawowa
Hanna abincin rana ya sami Hanna kacekace tana
kuka a durkushe a gaban Alh Bilya tanarokonsa
iya Abu kuwa tana ta faman watsi dakayanta.
Cikin kuka Hanna tace'' wada kaga halin da nake
ciki jeka ka kira iya Salmai tazo ta rokarsu.Nan
da nan wada ya garzaya dan ya shaidawa
iyaSalmai halinda yazo ya tarar da Hanna.
Bayantafiyar wada ba dadewa sai ga iya salmai
da maigarida tawagarsa sun shigo gidan suka iske
hanna acikin wannan hali. Maigari ya ce''
subhanallai Alh Bilya da girmanka meye haka?
Alh Bilya yace''ranka ya dade babu yadda za'ayi
taci gaba da zamaa cikin kudina bayan bata sona
shi yasa nazo na ceto in Abu taga zata bar Hanna
taci gaba da zama akyauta to. Amma ba dai nine
ke biyan kudin nandole Hanne ta fita don bazan
barta taci gaba da zama a kudina ba tunda bata
sona. Nan dai akahau bawa Alh Bilya da iya Abu
baki ana musuwa'azi da nasihohi akan rayuwa ce
kuma sumasuna da yaya zasu iya mutuwa su bar
yayansusuma ayi musu haka. Hanna tasa gefen
zaninta tagoge hawaye ta mike daga durkusan da
take yi ta juya ta kalli su maigari tace'' ku kyalesu
ni nahakura da zama a dakin zan koma rumbun
inzauna hanna ta fara dibar jakunkunan ta
tanashigarwa cikin rumbun nan mai gidan
tururuwa dacinnaka ga bunhunhunan dawa da
kaikayi.....ANA CIKIN WANNAN hali ne Musa
danmakwabtansu ne ya shigo yace'' wasu maza
gudabiyu gasu nan a waje wasu farare ne
kamarlarabawa sunce suna neman Hanne 'yar
gidanMalam Habu. Mai gari yace'' larabawa daga
ina ?Musa yace sunce daga Niger suke maigari
yace'' to muma ai tafiya zamu yi mu tafi kawai,
har Hannasuka yiyo waje wasu samari farare sol
sol ne gudabiyu a tsaye a kofar gidan daya daga
gani kotambaya babu jinin hanna ne don kamar
su dayakamar an tsaga kara maigari yace ''kune
bakindaga Niger ? Suka amsa 'eh' sannan suka
duka suka gaishe dasu maigari. Hanna ta tsaya a
gefetana kallon wadan baki nata bata san suba
ammadaya daga cikin samarin kamarsu daya
futik dagagani babu tambaya daga tsatso daya
suka fito.Maigari yace'' to ga Hanna . Yaya kaman
baku sanjuna ba. Mai kama da Hanna yace'' ni
sunana Ahmad wannan abokina ne sunansa Bello
Madu. Nikanin mahaifiyar hanna ne uwa daya
uba daya.Hanne bata taba ganina ba ban taba
ganinta bashine nazo na nemota don muga juna''
Hanna najinhaka sai ta daka tsalle ta rungume
Ahmad sai itadashi suka rushe da kuka. sai suka
rushe da kuka. Maigari da sauran mutane sai
suka hau girgiza kaisuna masu tausayinsu.
Maigari yace'' Alhamdulillahgara da Allah ya kawo
ku sai mu koma daga cikin atattauna. Bayan kowa
ya sami waje ya zauna,Hanna ta tashi ta dauki
kwano ta kwalfo musuruwan sha a randa ta kawo
musu, bayan sun sha. Maigari ya fara bayani ya
shaida musu duk halindaHanna take ciki yanzu
ma ga jakunkunanta nan awatse a waje dakin da
zata zauna ma yanzu yazama garari. Ahmad ya
matse hawaye yace'' hakikatuntuni munji irin
halin da mahaifiyarki ta shiga harta rasu mun san
kuma halin da yarta Hanne zata shiga amma da
yake ni ina yaro bani da ikon inzoin dauketa shi
yasa na hakura akwanakin nankuma na dinga
mafarki iri iri na 'yar uwatamarigayiya uwar
Hanne. Kullum na kwanta baccisai inga yayata
Habi tazo tana cewa Ahmad danuwana yanzu
baza kaje ka nemo 'yata ba Hanne kaga halin da
take ciki ba a duniya ba, ko darenjiya ma nayi
mafarkinta abu daya kuma takemaimaitawa don
haka yanzu daman nazo da niyyarmu tafi da ita
ko da mahaifinta yana nan zanrokeshi ya bani ita
idan batayi aure ba in tafi da ita.Balle kuma
yanzu da ya rasu dole in tafi da ita. Iya abu ta
tabe baki tace malam tunda ransa ya hanaakai
hanna wannan garin'' maigari da jama'arsa suka
yiwa abu caa suka rufetadafada suna cewa'' ba
yanzu kika gama mata watsida kaya ba? Bayan
bakar wahala da take sha tuntana karama ta
zamo tamkar baiwa a gidannan.Ahmad ya ce'' ba
saikun bata bakinku bama wajenbata amsa mu
dai zamu tafi da ita . Sai yanzu daya mutumin
yayi magana wato Bello Madu yace'' aianan kusa
muke a garin dashi muke. Dashi dababban
mutum ai border ce ta raba. Ni costom neina aiki
a border lokaci lokaci zan dinga kawomuku Hanne
kuna gaisawa. Ahmed ya katse shiyace ''duk
zancen ka lallashi matan nan bai taso ba kaga
kankat din gari wato maigari da jama'arsasun
bamu izinin mu tafi da ita to wacece kuma zatace
sai hanne ta zauna yunwa ta kashe ta. Iya
Abutaji wani dacin bakin ciki ya rufeta ganin
Hanna tasami wajen da zata je ta huta. Taso ace
da ta yiwaHanna watsi da kaya duk garin ta rasa
inda zata zauna. A haka dai aka rabu Ahmad da
abokinsaBello Madu suka yiwa mai gari da
jama'arsa sallamasuka daukarwa Hanna
jakunkunanta, Hanna tayafa gyalenta tarungume
iya salmai suna kukanrabuwa Hanna da kawunta
suka tafi.sun isa garin Dashi da daddare gidan
Ahmadsuka sauka. Ahmad yana da mata daya da
'ya'yabiyu , sunan matarsa Hajir itama irinsu ce
buzuwa.Hajir ta tari hanna cikin fara'a da murna
ta kaitadaki ta kawo mata ruwa ta sha sannan ta
zaunasuka gaggaisa sannan taje ta shirgowa
hanna tuwo. Hanna taci tuwo nan tamkar tunda
allah yahalicceta bata taba cin tuwo mai dadin
haka basaboda tsabar yunwa da take ji, taci tayi
nat sannantace a nuna mata bandaki zata yi
alwala Hajir tanuna mata. Hanna ta shiga ta
dauro alwala tazo tayisalloli tana idarwa taje ta
watsa ruwa tayi wanka ta kwanta. Hajir taji tana
son Hanna, tana sonta dakawa daga gani ma
sa'an nune, hajir ta zauna agefen shinfidar
Hanna na kwance suna ta hira kalakala,Hajir bata
bar dakin ba sai da taga Hanna tafara bacci
sannan ta hure mata fitila ta rufo kofa tafita ta
nufi dakin kwanciyarsu. Da asuba Hanna ta farka
taji ana kiran assalatu ta mike ta nufi ban
dakitayi alwalla tazo tayi salla ta zauna tana
Lazumi.Gyangyadi ne ya dinga daukar hanna ta
mike takoma kan katifa ta koma bacci tayi ta
barci har shadayan rana babu wanda ya tashi
Hanna sai da tayibarcinta ta gaji ta farka dan
kanta. Tana tashi tayi ido hudu da soye soyen
abinci kala kala Hajir tazota jera mata. Ba Hajir
kawai ba 'yar uwan uwarHanna fa yawa labari
yakai musu cewar hanna tazodon haka suka aiko
mata da abincin karin kumalloiri iri sunka ce
kafin suzo su ganta. Hanna ta fadawanka tayi
brush sannan ta saka kayanta tazo ta zauna a
gaban abincin burjik a jere a tsakar dakintaduk
nata ne sai taji wani farin ciki ya lullubeta
ba'asabanba, yau hanna ce da barcin safe ta
farka tagaabinci burjik an jere mata haka Allah
yake, duniyajuyi juyi. Tun kafin hanna ta gama
karin kumallo tajitsofaffi da mata suna sallama a
tsakar gida, yan uwan mahaifiyarta hanna ne
suka fara cinci rindonzuwa ganin hanna, sai koke
koke daga su harHanna taga dangin uwarta
cunkus amma suka cemata wadannan ma kadan
ta gani don tushenzuri'arsu Azbinawa ne [buzaye]
suna Agadas state .Sai dai wani abu guda da
hanna ta lura duk danginta talakawane sosai
suna cikin rashi wasuNono suke sayarwa rugage
suke wasu kumamanoma ne. kawu Ahmad ne
kawai dan Bokowayayye mai dan hali akan
sauran koyarwa yake amakarantar firamaren
garin har ya sami matsayinmataimakin
headmaster. Shima dai rufin asiri ne kawai ba
wani arziki gare shiba. Gidansa ginin kasane
dakuna uku ne, bandaki da zana aka zagayekicin
kuwa a tsakar gida aka dasa murhuna. Hakadai
Hanna taji ta shiga wata sabuwar rayuwa maidadi
fiye da rayuwarta da agidansu. A koda
yausheyana godewa Allah da yayi mata canji
daga ukuba da bakin ciki hantara ya kawo ta inda
aketarairayarta. Hanna da Hajir sun shaku sosai a
kodayaushe suna tare suna hira wasa da dariya.
Tunhanna na boyewa hajir wasu abubuwa
nadangane da rayuwarta har ta yaba da
hankalinta tafara gaya mata wasu abubuwa da
suka faru da ita ada na dangane da tsananin son
Haisam ranarrabuwarsu. Tace har yau kullum da
daddare sai tayikuka idan taje kwanciya barci
saboda tunaninsa.Hajir ta tausayawa hanna sosai
har hawaye tayimata ,daga karshe tayiwa hanna
nasihoho akantayi hakuri kaddara ce daga Allah
haka Allah ya rubuto musu.BAYAN zuwan hanna
da kamar wata guda kawuAhmad da sauran
manyan danginsu suka kiraHanna babban zauren
dake gidan. Bayan ta gaisheda kowannensu ta
koma gefe ta takure. BabaSha'aibu yace'' Hanna
kinsan dalilin da yasa mukakira ki nan? Hanna
cikin ladabi ta amsa musu a'a yace to a
matsayinmu na iyayenki da kakanninkimunyi
nazari mun kuma tsayar da shawara abindanake
nufi da munyi nazari shine bai kamata ba
muzuba miki idanu haka nan ba babu aure don
hakaya kamata kiyi aure a watannan kuma.
Gabanta yayanke ya fadi ras dajin kalmar aure
cikin rudani tace''....... Wazan aura ai ni bani da
kowa a garinmuanan garin ma babu wanda yace
yana sona.'' suduka suka kyalkyale da dariya.
Ahmad yace''hanna kwantar da hankalinki dole
mu aurar dakega mai sonki kece dai baki sani ba
amma zuwankigarinnan maza sun doshi goma
suka sameni suka ce suna sonki shawarar da
muka yanke ita cemuduba a cikin waye yafi
hankali. Addini. Sana'aasali wanda zai rikeki
tsakani da Allah mu aura mikishi tunda ke
bakuwa ce ba sanin halayensu kika yiba babu
kuma isasshen lokaci da za'a barki kinasoyayya
dasu har ki zabi miji mu baza mu zaba miki
wanda zai cucekiba . Hanna babu wanda ya
fadomata a rai sai Haisam, soyayyar da take yiwa
Haisamsai kara yabanya take a cikin ranta, Hanna
ta ciresha'awar auren wani a rayuwarta tunda ta
rasaHaisam shine ma hawaye yake zuba
dagaidanuwanta don tasan ta rasa wanda take so
duk duniyar nan ta rasa farin cikin kuma.
Wannanhawaye na hanna da yake zubowa
dagaidanuwanta yasa jikinsu ahmed yayi sani
kumamamaki ya rufe su yaya za'ayi hanna ta
fara kukatun kafin taji waye aka zabar mata ta
aura. Koakwai wanda ta kudira zata aura ne basu
sani ba ? Inna rabi tace'' Hanna kukan me kike
bafa cewamuka yi dole sai kin auri wannan da
muka zabarmiki ba idan kina da wanda kike so
fadi mu auramiki,daman ganin babu kowa ne shi
yasa muketunanin hadaki da wani. Hanna ta
share hawaye tagirgiza kai tace'' babu wanda
nake so zan aura dukwanda kuka zabar min zanyi
biyayya in aure shi kowaye kuma. Nasan baza ku
zabar min wanda zaicutar dani ba'' gaba daya
suka fara shiwa hanna albarka suna jinjina mata
bisa tsananin biyayya datake yi musu allah yayi
mata albarka. Kawu ahmadyayi gyaran murya ya
gyara zama yace'' hanna tunfarkon zuwanki
abokinna koma ince ya zama danuwana saboda
tun muna yara muke tare nasanhalinsa ciki da
bai fiye da uwar data haifeshi bata sanshi ba fiye
da yadda nasan yadda yake yana damutunci da
sanin ya kamata yace yana sonkitsakani da allah
zai aureki wannan aboki nawashine bello madu
abokina din nan da mukajenigeria garinku dashi
muka daukoki . Yana dasana'arsa kuma yana da
ilmi gaba daya boko da arabiya yanzu ma babba
ne ba laifi a aikinsa aikincostom yake sune suke
tsaye a bordar nigeriazuwa niger. Ni dai a ganina
bello masu ne kawai yacancanci ya aure ki ko ya
kika gani? Iya ma'idatace'' wanne irin yaya ta
gani bayan ta gamamagana tace ko waye muka
zabar mata tana so. Cancanta ma ai ba sai an
fada ba sun dace ai''hanna ta sukuyar dakai kasa
sai hawaye shar yasake keto mata. Bello madu
kam ya cancanci asoshi bashi da makusa kyau
kuwa kamar shi yayikansa dan buzaye asali
kamar balarabe, hankali datausayi kuwa ba'a
magana don da yaji labarin hanna hawaye ya
dinga yi don tausayinta bashi damakusa ko kadan
amma ita abun da ya kara satakuka shine tana
matukar ganin mutuncinsa donhaka bata so aka
ce shine zai aure taba don dukwanda ya aureta
sai yayi hakuri sabod bazai samisoyayyar taba
GANGAR HIKINTA zai aura zuciyarta na wajen
haisam har abada, hankalin hanna yasake tashi
sosao da taji sunan wanda zata aurakawu ahmad
yace'' ni wannan kukan naki ne yaketsoratani
hanna kiyi magana idan akwai wani abunda yake
damunki. Hanna tayi dan murmushi tagirgiza kai
ta ce'' babu kimai zabin da kuka yi min yayi. Inna
goshi ta dau buda kiwa ya hau cewa''allah ya
sanya alheri ya baku zaman lafiya. Hanna tamike
ta shiga cikin gida bata tsaya a ko!ina ba sai
adakinta ta rufe kofa ta fada kan katifa sai ta
budesabon shafin kuka mai tsanani taji a ranta
kamarwata sabuwar soyayyar haisam aka kara
zuba mata taji sonsa ya sake sartseta kamar zata
yihauka. Bayan anyi haka da kwana uku hanna
nazaune a tsakar gida tana tankaden gari da
yammatana taya hajir aiki, hajir kuma na wajen
murhutana kada miyar kuka, suna taba yar hira
hajir tace''hanna ina ganin kinfi sauran mata
sa'ar samun kintsatstsan miji a duk yan matan
garin nan sabodaduk yawanci yan matan garin
babu wacce batakaiwa bello madu hari ba farin
jini gareshi sosai.Kyawunsa ne ko kuwa illminsa ,
ko kuma jan ajinsane yake rudarsu oho? Amma
ke gashi kwatsam yadamu da sanki kinsan tun ba
yauba kawunki ahmad ya fadamin cewar bello
madu yana sonkiamma ya gargadeni da nayi
shiru kar in sanar mikihar sai ya sanarwa da
magabatansa shima. Hannata cije tayi dan
murmushi tace'' hajir kenan watonayi sa'a sosai
ashe dana sami bello madu ta sama.Ba tare dana
wahala ba? Amma ni a wajena sai dai ma ince
shine yayi sa'a sosai ma kuwa.Alhamdulillah
amma akwai matsala tabbas. Hajir tajuyo gaba
dayanta tana kallon hanna can tace'' bangane
akwai matsala ba. Wacce irin matsala
kumahanna ? Ko bakya sonsa ne? Hanna ta
girgiza kaitace ta ce a'a ni naki shi bayan shine
zabin iyayena ina sonsa mana. Muryar bello
madu ce tace.''assalamu alaikum''.Kai tsaye ya
shigo cikin gidan kamar yadda yasaba shigowa
daman. Kai tsaye wajen hanna yadosa. Hajir ta
amsa masa sallaman gami da yi masatsiya ta ce''
oh dan halak kaki ambato yanzuzancenka fa
muke yi ango kasha kamshi dagazuwanka ka
doshi wajen hanna da idan kazo wajen wa kake
dosa? Bello madu ya kyalkyale dadariya yace'' kai
hajir kin fiye tsokana kinsan da saiinyi sati biyu a
boda ban damu da zuwa garin nanba amma
yanzu kusan kullum sai nazo garin nanko banzo
gidan nan ba ina jin dadin garin sabodamatar da
nake so tana cikin garin. To yanzu an banu izini
inzo wajenta kina nufin sai in doshiwajenki duhu
bayan shigowata hasken fuskarhanna ne ya bugi
idanuwana. Kinsan ko a kabarihaske ake nema
ana neman tsari da duhu. Hajir tarike baki tace''
ah bello madu daina hadani daduhun kabari
allah ya baka hakuri'' wannan hira tasu ta bawa
hanna dariya bata san sanda tatuntsire da dariya
ba duk da wani kululun bakinciki daya dira a
ranta yanzun nan da bello madu yashigo haisam
kawai zuciyarta take haska matainama inama
aceda haisam za'ayi musu auren nanwata guda
ya rage ayi bikinta. Bello madu yace'' hajir yi
hakuri bada duhun kabari nake hada kibani na
isa? Ai nasan kokarin da kike min wajenturani
fadar zuciyar hanna tun dazu ina zaune atsaye
ina jin hirar da kuke yi. Kuyi hakuri ba labe
namuku ba ina doso kaina bello madu naji
anaambato shiya sa na dakata sai dana gama jin
komai'' hajir tayi dariya tace a'a baba bello ka
faralabe a gidan mutane dai kawai zaka ce min''
yakarasa wajen hanna ya jawo wata kujera a
gefentaya zauna a hankali yayin daya kafawa
hanna idoyana kallonta. Ji yake tamkar ya
hadiyeta sabodason da yake yi mata. Fargabarsa
daya yana tsoro kada hanna taki amincewa da
soyayyar da yake yimata haka nan bayan
abokinsa ahmad ya shaidamasa an bashi hanna
yayi farin ciki amma farincikin ragagge ne yana
gudun kada a takurawahanna ta aureshi yazo ya
rasa soyayyarta ammayau sai gashi da kunnensa
yaji hanna tace''ni na kishi bayan zabin iyayena
ina sonsa'' don haka yauyafi kowa farin ciki.
Hanna ta dago a kunya cetagaishe shi ya amsa
cike da fara'a ya mika hannu yakarbi rariyar dake
hannunra ya fara tankade. Hajirkuma tana yi
masa tsiya tana cewa'' wai bellowannan bamu
san wanne irin abu za'ayiwa hanna bayan anyi
aure tuwan ma kai zaka dinga tukamata. Bello
yace ke kin fadi kadan tauna abincikawai bazan
yiwa hanna ba saboda bazaiyu intauna mata ba
amma a baki zan dinga bata bayanna dafa mata
domin hanna tafi saraunoyar da takemulkin
duniyar nan idan ma akwai yadda nake jinta a
raina,Ga mamakinsa sai suka ga hawaye shar
yatsiyayo daga idanuwan hanna. Babu abinda ya
satakuka sai tausayin kanta dana bello madu
dominkowannensu son maso wani yake yi, inama
haisamne yake jinta a ransa haka kamar yadda
bello maduyake jinta a ransa. Shima ina ma
yadda yake sonta tana sonsa haka'' allah sarki
bello ka makara''hanna ta fada a ranta' sai bello
ya kurawa hannaido kawai yana kallo sai ya juya
ya kalli hajir wacceitama tayi kasake a tsaye tana
kallonsu. Ya miketsaye ya kade garin da yake
hannunsa yace dahanna ta taso suje zaure yana
son ganinta yana da magana da ita. Hanna ta
mike ta dauko ruwa tawanke hannayenta ta yafa
gyalenta tana biye dashisuka fita zaure.
Tambayoyom da bello madu yajerawa hanna sun
doshi goma dom son yaji meyeya sata kuka ko
aurensa ne bata so amma duk daa'a hanna take
amsa masa. Domin idan ta kuskura ta bayyana
abunda yake ranta ta sake shiga ukutasan bello
ba zai takura yace sai ya aure ta bahakura zaiyi
idan ya fasa aurenta wazata aurakuma tunda
bata da maganin ciwon da yakedamunta. Na san
na rasa haisam, na rasa shi kumahar abada na
rasa soyayyarsa na rasa farin cikin rayuwata,
meye ya rage mun a duniya kuma?Banda jiran
ranar mutuwa. Bello ya katsewa hannatunani
yace'' to tunda na tambayeki kince ba
komaiakwai wata magana guda da nake son muyi
dakehanna don allah kiyi hakuri ki sake yin hakuri
daduk yadda kika tsinci rayuwarki, abinda nake
nufi shine watakila hajir ta fada miki ina da gida
nawana kaina yanzi ma a ciki nake zaune nan
za'a kaikibayan anyi bikinmu, to kinsan halin
iyayemusamman ma mata mahaifiyata ta
kekashe kasatace lallai lallai sai dai a kaiki cikin
gidanmu ma'anagidan da take zaune da
kishiyarta wanda ba karamar takura bane dakine
kwaya daya jal ganata ga wanda za'a kaiki. Kiyi
hakuri ko bayanbikin zanci gaba da bata hakuri
akan ta yarda inmaida ke gidana'' hanna ta
sunkuyar dakai tacekawu wannan ba wani abu
bane da zaka damukanka. Kaabi maganar
mahaifiyarka domin abunda babba ya hango yaro
koya bishiyar rimi bazai ganoba, ita ta haifeka
tafika sanin dalilin dayasa tacemaka ka zauna da
matarka a kusa da ita . Allah yabamu zaman
lafiya gaba dayanmu ni da ita. Ni dakai kuma na
gode'' wannan kalamai na hanna yakwantarwa
da bello madu hankali don bai taba zaton hanna
ba zata damu ba idan taji yare dasurukai zata
zauna amma sai yaji ita take kokarin yimasa
nasiha, akan ya kwantar da hankalinsa
yabimaganar mahaifiyarsa. Kuma hanna ita ce
take yimasa godiya. Daga karshe ya yiwa hanna
sallamayace zai koma wajen aiki sai nan da
kwana hudu zai dawo an turashi tsakanin boda
dake tsakaninmaigatari da niger da zarar ya dawo
za'a kawo lefeinsha allah. Hanna tayi masa fatan
dawowa lafiya yatafi ita kuma ta shiga gida,Ta
iske hajir tana kwasar tuwo . Taje kusa daita ta
jawo kujera ta zauna. Hajir ta kalleta taceamarya
a gidan custom bello madu kinsha
kamshi,amaryar nan da wata guda. Wai ya naga
duk jiknkiyayi sanyi ne har koke koke kike yi?
Koda yakemuma fa duk munyi wannan don
gabanin bikina kurket na rame sai kuka ina zaton
auren waniabun tashin hankaline ashe babu
abinda ya kai shikwanciyar hankali, ke kuwa daga
ke sai masoyinkiku biyu a gida ku rakashe kowa
kokarin yafarantawa dan uwansa yake yi. Ke
gidanki nasiminti ne kewayayye ai bello madu ya
zuba sumunti a gidansa tal a lailaye da simunti
kamar abirnin. Mu da muke gidan kasa ma muke
jin dadinrayuwarmu balle ke'' hanna ta ce'' kai
hajir ai dagidan simintin dana kasar duk dayane
yanzu yakecemun mahaifiyarsa ta tubure lallai
lallai bata yardata kaini gidansa ba sai dai in
zauna a gidansu. Hajir ta zabura ta wurgar da
marar da take kwasar tuwota mike tsaye ta rike
haba da hannu tace'' hanname kika ce kina nufin
yanzu gidan su bello za'akaiki? Lallai mun shiga
uku mu masu kai amaryama balle ke da zaki
zauna da ita. Hanna ra jawohannun hajir ta
zaunar da ita tace'' hajir zauna mana muyi
magana daga zaune me yasa kika cemun shiga
uku wani abune ? Hajir tayi ajiyar zuciyata koma
ya ta zauna tace'' hanna bazan boye mikiba a
gaskiya innar bello bata da haki saboda dukgarin
nan babu wanda bai san bala'in inna hauleba
har tafi iya abu matar babanki da kike bani
labarinta don tun maigidanta yana nan bai rasu
batake azabtar da kishiyarta indo wahalar
duniyarnan yau idan kika je gidan indo da
yayanta tamkarbayi ne a gidan. Debo ruwa ma a
rafi ya ishekibayan zuwa gona da sassafe amma
shi bello meyasa zai yi mana haka bayan yasa
halin mahaifiyarsa ko da yake ba laifinsa bane
don idanta saka musu kara basun isa su tsallake
bamusamman bello yana yi mata ladabi sosai fiye
dasauran kannanshi shine babba a gidan. Ina jin
batsso yayi nisa da ita gani take komai ya samu
yanzuke zai dinga dankawa gaba daya'' kafin
hanna tace wani abu ahmed ne yayi sallama ya
shigo sukaamsa masa gami dayi masa sannu da
zuwa. Amurtuke ya amsa sannan ya juya ta kalli
hajir tadaka mata tsawa yace. Ke hajir ki iya
bakin kidanme kike kokarin rikita hanna akan
aurenta dabello madu akanta aka fara zama da
sirikai'' ya juya ya kalli hanna yace'' to saikin
toshe kunnuwankishi aure dan hakuri ne kiji kiki
ji ki gani kiki gani,ladabi da biyayya shi zai rabaki
da masifa datakurawar surukarki. Kada ki yarda
da 'yan zugamasu nuna miki kin hadu da masifar
suruka mutumko shaidan ne yasan mai kyautata
masa don haka idan kika bi inna haule sau da
kafa dole ta dagamiki kafa. Bawai nace hajir tayi
karya ba hakahalayyar inna haule take amma sai
kinyi hakurikindaure kin mata biyayya zaki ga
ashe duk abundaake fada maki ba haka take
bama'' hanna tasunkuyar dakai kasa tace'' to
kawu naji abunda ka fadamin zanyi amfani dashi
na gode madalla'' tamike ta shiga daki. Ahmed ya
juya ya kalli hajirwacce ta cika tayi fushi taf
kamar zata fashe'' yashafa kumatunta yace'' ke
kuma daga maganameye abun yin fushin'' hajir
tace'' haba ahmed mekake nufi da ka ce kada
hanna ta saurari yan zuga, kana nufin nice yar
zugar kenan zan hanata yinaure ko? Ya ce a'a
abunda naga laifinki shinemuddin kika sanar
mata halin innar bello madu aizata tsorata kuma
zata ji ta tsani surukarta daganan zaman lafiya
babu kuma ni bello ne yafi banitausayi har cewa
yayi ko zai fasa auren hanna ne saboda yasan
tabbas zata hadu da halinmahaifiyarsa shi kuma
a duniya abunda yaki jiniirin batawa hanna don
yana sonta kamar yaddayake son rayuwarsa.
Mun kada mun raya da innahauke ta hakura ta
bar bello ya tare da amaryarsa agidansa taki fur
wani uban ashar ta soka min ahe haushina take ji
wai na dauki yata na bashi, ashetana so ta
hadashi da wata shine yaki,Sum sum nayi na
ficedaga gidan. Kuma wani abun bakin ciki shine
belloyayi yayi ta yadda ya rushe bangarensa yayi
nasiminti ya zagaye da katanga tace bai isa ba
ana kasar zai saka amaryar tasa. Sai zana ya
suyo yadanzagaye dakin su kwaya daya jal kuma
abincinsu ahade dana yan gidan zasu dinga yi
allah dai yakyauta mana nan mun dukufa da
addu'a alah yadora shi akanta ta hakura ta
barshi ya zauna agidansa hajir tace''amin nima
zan taya hanna da addu'a amma caf wannan
suruka ta hanna. Ai kogidan bazan taba takawa
ba da sunan ziyara ni tunina yarinya tsoronta
na ke ko gidan bana shigaallah ya sani banasan
masifa. Duk hirar nan da sukeyi kakaf a kunnen
hanna wacce ke daki tana jiyosu. Tayi ajiyar
zuciya ta girgiza kai don tausayin kanta da kanta
tace a ranta. Haka allah yaso danihaka zan kare a
kunci, wahala da bakin ciki narabu da wahalar
iya abu na fada wahalat innahaule allah kana
sane dani, kasan halin da nakeciki kaine
majibincin lamarina la'ila ha illa antasubhanaka
inni kuntu minaz zalimin. Babana yayi gaskiya da
yace babu mijin da zan aura da zairikeni amana
in ba haisam ba. Baba baka sanyadda mukayi da
haisam ba ka mutu ka barni akaninje in cewa
haisam yazo ya aureni ka bashini, yayahaisam ya
auri wacce yake so yar barni, baba kabarni a
duniya baka san na rabu da haisam din bama. Ta
rushe da kuka mai tsanani. Ta koma takwanta a
tsakar dakin tana tunanin rayuwar dasuka yi da
haisam shine farin cikinta a makarantabaya so ko
kuda ta cijeta tattalinta wasa da dariyakullum har
ya zuwa ranar rabuwarsu. Hanna tayikuka har ta
gaji sannan ta mike don zuwa bandaki tayi alwala
magariba. Ashe ta dade dayi bata saniba. Kamar
yadda bello madu yace za'a kawo kefeda sauran
kudade na al'ada an kawowa hanna lefeakwati
uku kowacce a cike danma inna haule dukta
rarrage kayan amma duk da haka masha allahan
zuba mata kaya. A nan kauyen sai zancen kayan
ake yi 'yan uwan hanna sai murna ake
ammabanda ahmed domin ya tsorata da ganin
yawanlefen nan yasan dole za'a zuba ido aga me
kymaza'a kai dakin hanna.A matsayinsa na dan
karamin malaminmakaranta firamare mai daukar
dan karaninalbashi shi zai yiwa hanna gado, gara
da kumaabincin 'yan biki gashi kuma a kurarren
lokaci akasaka ranar bikin. Gashi duk danginsu
shine maidama dama duk a jikinsa damgi suke
nema. Yasan ko za'a taimaka masa da
gudummawa bai wuce ayimasa fantekar alkaki da
nakiya ba sai 'yankwanikan cin abinci wadanda
suka daddage nezasu bashi setin samira. Da cin
bashi da komaiahmed ya hada kudin gado mabi
lamba one damadubinsa. Dan kudin da hajir take
tarawa na dinkin hular da take ta bashi ya hada
da sauran yargudummawar da ya samu ya sayi
ledar daki dalabule shikenan sai kwanukan rabon
abinci dasamira seti hudu aka haka aka jerawa
hanna adaki. Bayan an sha biki an kai amarya
dakinta tsaftsaf daidai karfinsu sai dai wani
babban tashin hankali ahmed ta buga sama da
kasa ya rasa kudinsiyama hanna gara. Don haka
yace hajir da wasumatan suje su bawa inna haule
hakuri insha allahukafin ta haihu za'a kawo mata
gara don har ta farahabaici an kawo amarya
babu gara. Kwanan hannauku cur tana rusar
kuka bayan an kaita gidan miji . A ranar na
hudun ne bello madu ya shigo dakintada jakar
kayansa shi ma ya kauro gidan daga cangidansa.
Da misalin karfe goma na dare gari yayishiru
kowa yayi bacci abinka da rayuwar kauyeamma a
zaune a gefen gado ya tarar da hanna tayitagumi
tana tunani ido yayi mata jawur a kumbure , yayi
mata sallama ta shigo. Ta daga kai da sauri
tadube shi sannan ta amsa masa sallamar da
yayimata. Ya shigo ya ajiye jakarsa a gefen
akwatinantayazo kusa da ita ya zauna yana mai
yi matamurmushi da nuna farin cikinsa a fili, ya
dubikwayar idanuwanta yaga jawur don tsananin
kuka da tasha yi yace'' hanna kukan ne har ya
zamarmiki da idanuwanki haka ? Don allah ki
daina kuka,hanna ni mai kaunarki ne bazan cutar
dake ba'' tasake rushewa da kuka yasa hannu ya
jawotajikinsa sai yaga tayi sauri ta zabura ta mike
tsaye,Wannan zabura ta Hanna ta bawa
Bellomamaki kamar wanda ya dona mata wuta,
ya miketsaye yasa hannu zai rukota. Hanna tayi
sauri tajada baya tana kokarin ta fice waje. Bello
ya ce'' a.ahar waje zaki fice to na kyaleki zo ki
zauna bazansake taba ki ba'' sannan hanna ta
dawo tazo ta zauna a kasa kan ledar dake
shimfide a tsakardakin ta hada kai da gwiwa tana
kuka tamkarranta zai fita. Wannan kuka na hanna
ya tayarwada bello hankali ji yake tamkar tana
soka masawuka a zuciyarsa idan tana zubar da
hawayen nan.Ya nisa sannan yace Hanna kiyi
hakuri dan allah ki daina kuka meke damunki
ne ? Nifa yanxumijinkine ki daina guduna kuna
ina da hakkinakanki muddin kina guduna kuma
kina kuka kinatayar min da hankali.Nace kiyi
shiru kinki ki daina.Ko kina so inyi fushi dake
Allah yayi fushi dakeMala'ikun allah su dinga
la'antarki har sai gari ya waye? Hanna ta dago da
sauri ta kalleshi yace yayakike kallona? Gaskiya
nake fada miki ai duk macenda take gudun
mijinta Allah da mala'ikunsa zasudinga la'antarta
har sai gari ya waye ko kin yaddaki halaka ?
Hanna ta girgiza kai tace bana so nahalaka'' yace
''to in ba kyaso ki halaka zo nan kusa dani ki
zauna muyi yira. Cikin sheshshekan kukaHanna
tace"kawu na zalunci kaina, na kumazalunceka da
ban fada ma gaskiyar abunda yakedamuna ba.
Kawu na kasance ina cikin wani hali natsananin
damuwa wanda har nake tunanin bazaniya auren
kowa ba. To amma dole nasan za'a yi min aure
shi yasa na hakura na amince na aureka
atunanina zan iya daurewa in zauna amma
yanzubayan da akayi auren ciwon da yake
damuna yadawo min danye bana jin zan iya
zaman aure har insami aljannar da kowacce
mace take nema akarkashin tafin kafar mijinki ta
hanyar biyayyar aure. Kawu kayi hakuri ka
yafemin dan allah karufa min asiri. Ka
sauwakemin mu zauna haka batare da kowa ya
sani ba, saboda sai in halaka idanmuka zauna a
haka da igiyar auren ka. Bello yabude baki yana
kallon Hanna can ya taso yazogabanta ya durkusa
ya rike hannunta cikin yar siririyar murya mai
dauke da tsananin dimaucewayace'' Hanna.,
fadamin ni kawunkine mai shirintaimakonki ta
kowacce hanya kada kiji tsoronfadamin ko mene
ne '' ta janye hannunta a hankalita share
hawayenta tace '' idan bakamantaba a labarin
dana baku a garinmu nace nayimakarantar
sakandire da taimakon yaya Haisamson yaya
haisam ne ya zame min dafi a zuciyatawanda
dafin nan zai iya zamra min ajalina. Kawubello
inason haisam harni ma kaina ina mamakin
yadda kayi zuciyata ta kamu da sonshi haka
nayiaddu'ar don allah ya goge mun , nayi azumi
nayikukan kullum akan allah ya yaye min amma
kamarkaramin ake . Daga karshe sai nake
addu'ar allahya dauki raina da in dauwama a
haka amma kaganni har yanxu a haka na rasa
yadda zanyi'' ta rushe da kuka. Bello yayi shiru
yana kallonta shimacan ya nisa ya ce'l hanna me
yasa nazakiyi addu'arallah ya hadki da haisam ba
kuyi aure kike addu'arallah ya yaye miki sonsa ko
kua allah ya daukiranki? Hanna ta goge hawaye
tace:: haisam yayiaure a ranar da mahaifina ya
rasu'' bello madu ya gyara ya zauna a gaban
hanna ya lankwashe kafadon jin labarin wannan
rikirkitaccen al.amarin nahanna. Hanna bata boye
maiba ta bashi labarintadana haisam tun daga
ranar da babanta ya kaitamakaranta har ranar
gidansu ta iske shi zai tafidaurin aurensa, daga
karshe tace'' ashe yaya haisam ba sona yake ba
taimako kawai yayi min nikuma zuciyata ta kamu
da tsantsar kaunarsa donhaka ne a koda yaushe
nake addu,ar allah yayayemun sonsa bana
addu.ar haisam yazo yaaureni. Bello madu yayi
murmushi karfin hali yace''haisam yana sonki
yana kaunarki sosai fiye dani kaina da duk wni
mai sonki a duniya. Akwai watamatsalar da tasa
bai aurekiba hanna'' hanna cikeda mamaki ta
kurawa bello ido tace me yasa kacehaka me ka
gani daka fadi haka?'' bello yace''saboda ke
yarinya ce shi yasa baza ki fahimcihakan ba,
kuma nasan irin yadda kike hanna bawai haka ta
taba faruwa akaina ba a.a inakwatanta nima
rayuwata zata iya shiga irin wannanhalin da kika
shiga idan na rasaki saboda kecewacce na taba
jin ina so a duniya. Ni na yadda naamince zanci
gaba da zama dake a haka amatsayinki na
matata amma babu zancen saki a tsakanina dake
saidai mutuwa ta rabamu sabodasanda nake
miki, hanna da ace haisam yana jirankibayyi aure
ba da zan daukeki ina kaiki wajenshiinaura miki
shi don kiyi rayuwa cikin farin ciki, ni indawo gida
in zauna ciwon son da nake miki yakasheni na
yadda indai na ceto rayuwarki. Amma yanzu da
yake haisam yayi aure kiyi hakuri. A cikinkashi
dari bisa dari da kike yiwa haisam, ki daure
kibani kashi daya a cikin dari har
karshenrayuwarmu ta aure na gode. Hanna ki
daure kicigaba da zama dani a haka kada ki barni
ni dakeduka muyi biyu babu, kin rasa haisam ni
kuma in rasaki'' yasa hannu ya jawo jikinsa zai
rungumetatayi sauri ta mike tsaye ta juya masa
baya. Ya tashi asanyaye yaje ya rufe kofa ya
datse da makulli. Yayinda hanna taji wannan
rana tamkar ranar damahaifinta ya rasu ta kuma
rasa haisam yau gata adaki zata kwanta gado
daya da wani a matsayin mijinta ba haisam ba,
hawaye yaci gaba da tsiyayomata daga
idanuwanta. Bello yaxo ya rungumetata bayanta
yana mai sunbatar kunnuwanta dagefen
kumatunta cikin sanyayyiyar murya hannatace'' a
matsayinka na mijina akan babu yaddazanyi ka
sami GANGAR JIKINA amma ruhi, zuciyata na
wajen haisam.'' bai iya bata wannan amsan
bacimak ya dauketa ya dorata a tsakiyar gado.
Hannata shide tama fita hayyacinta saboda
tsananin bakinciki yau gani ga wani daban zai
fara saninta 'yamace kafin haisam wannan bakin
cikin ne yayimata yawa yasa ta fita hayyacinta
ma iya cewa suma tayi amma gogan naka baima
lura ba ji yakeyau tamkar an masa albishir da
gidan aljanna gashiya auri hanna harma ta
mallaka masa GANGAR JIKINTA.A ranar da hanna
ta cika sati guda ta fara saninhalin uwar mijinta
ashe da kara take yi mata. Dasassafe ko tashi
daga bacci basu yiba Inna Hauletayi dirar mikiya
a bakin kofan dakinsu tana bugunkofar da karfi
tana fadin a tashi haka baccin ya isaduk inda sati
yayi an gama cin amarci bakunta ta kare kin
zama 'yar gida fito ki dora dumame. Indozataje
rafi debo ruwa.Firgigit Hanna ta mike ta dirodaga
kan gado ta bude kofa ta fito. Ta durkusa
harkasa ta gaishe da Inna Haule. A yatsune ta
amsatace'' a tafi wajen murhu a dora dumame
ga dawada gero can idan kuka karya kumallo
keda indo ku surfa''. Bello yaji tamkar yayi ihu
saboda takaiciyasan Hanna kuma ta shiga uku ta
lalace kamanyadda amaryar Babansa Indo take
dandana wahalakullum kamar baiwa.Ya tashi
zaune ya rike kaitausayin Hanna zuciyarsa da
tunani ina zai samomafita kafin ta zama baiwa,
to amma babu wata mafita tunda har yau har
waye war gobe innaHaule taki amince masa ya
koma gidansa shidamatarsa. Da ya isheta ma da
maganar sai tace dukranar daya sake rokonta
akan wannan bukata tasaAllah ya isa kuma zata
tsine masa, don haka Belloyaja bakinsa yayi gum.
Haka hanna ta kasance tana yin iya kokarinta na
ganin ta farantama uwarmijinta tana binta sau da
kafa amma a banza innahaule bata gani. A koda
yaushe zagin hanna taketana cewa.A yaushe
zagin hanna take tana cewa aurendaba gara ma
ai bai cika aure ba. Wai hanna tamallake mata da
don da sai yayi sati biyu,uku baizogarin ba daga
wajen aikimsa amma yanxu bayasati guda,
zantuttuka barkatai marasa ma'ana daina nuna
tsana tsagoranta. To wannan al.amari yasa hanna
ta sake fitar da rai daga samun zaman lafiyaa
rayuwarta, inna haule halinta daya da iya
abukoma tafi iya abu ko uwarka ka yanka musu
kadafa ka basu bazsu gode maka ba. Sai dai
kawaiidan abun ya isheta ta shiga daki tayi kuka
ta gaji.Idan bello madu ya dawo ya ganta a
wannan hali sai ya shiga lallashinta yana bata
hakurin nan nasababu abinda yake karama
hanna banda takaici.Abu daya ya gano lagonta in
har yana so tayidariya a duk halin bacin ran da
take shine yacemata haisam. Haka yake sakata a
gaba yace dolesai ta bashi labarin haisam. A koda
yaushe hanna na kirga kwanikin yaushe bello zai
dawo dagawaje aiki saboda dashine kawai take
hira mai dadihar tayi dariya hirar ita ce hirar
haisam.. Hanna daindo ne suke surfe a yau, inna
haule ta fita unguwashine ma suka samu suna
yar hira. Duk da indo tagirmewa hanna amma
duk da haka bata fi shekaru ashirin da shida ba a
matsayin suruka take a wajenhanna tunda matar
baban mijinta ce. Amma doletasa suka zama
kawaye. Hanna na bakace dusar,indo tana tikar
dawa a turmi. Indo ta tsagaita dadakan tace''
hanna sai dai hakuri ni harna saba dawannan
bauta haka Allah ya rubuto mana rayuwarmu.
Hanna tayi ajiyar zuciya tace '' Allahyana barin
bawanshi a halin daya so ya ganshi.Amma duk
abubuwan da inna kemun bayadamuna irin duk
abunda muke yi mata bata ganidubi fa irin aikin
da mukeyi kamar zamu mutuyanzu idan tazo
cewa zatayi munyi ha'inci bata surfu ba. Ga zagin
da take yimin akan gara ni narasa yadda zanyi da
rayuwata. Indo ta ajiye tabaryatace'' ai waike
kina nufin duk abinda ake baki saniba a gidan
nan yau? Hanna ta ajiye faifan dakehannunta ta
tattara hankalinta gaba daya a wajenindo tana
jiran taji me yake faruwa. Indo tace '' ko da yake
kin tafi debo ruwa dazu da sassafe ni innahaule
tasa na shifa dakinki na miko mataakwatinan
aurenki guda biyu wadanda baki dinkakayan ciki
ba tasa almajiri ya daukar mata wai zatakai wani
gida ajiya tunda ba.ayi mii gara ba sumabaza ki
daura lefansu ba. Daman wata uku ta daukar
miki a kawo gara gashi yanzu kin shigawata hudu
da aure . Don haka da zarar bello yadawo zata sa
ya sakeki, lefen kuma ta kaiwa watayarinyar a
daura masa aure da wacce zata kawomata gara.
Kuma kinsan bello babu yadda zaiyiidan ta sashi
a gaba tace '' ya sake ki . Hawaye ne sur yake
zuba daga idanuwanta hanna ta mike dagudu ta
shiga daki ta tara wayan an kwasheakwatina sai
kwaya daya 'yar karamar kaya kalauku ne ta
dinka a lefen su suka rage sai saurantsofaffain
kayanta nada gasunan a kasa an watsarmata. Sai
ta kwanta a kan gado ta fara rusar kuka hanna ta
kware wajen iya kuka dan ko gasar masuiya kuka
akaje ta duniya ina ganin ita zata zo tadaya. Can
ba dadewwa inna haule ta dawo ta tarada indo
ce kadai take aikin abincin rana tace'' inahanna?
Indo tace'' ciwan ciki take tana daki. Taleka ta
tarar da hanna sharkaf cikin kuka sai tace.'' babu
wani ciwan ciki ba ciwan cikiba ko ciwannakuda
kike kin bar gidan nan bazan iya ba harkartalauci
anyi biki ko gara babu lefan dana dauke neshine
yasa bakin ciki ya kwantar dake. Haka hannata
yini cur a kwance babu ci babu sha sai kukaAllah
cikin ikonsa sai ya jeho mata Bello da yamma
kwanansa biyu ral da tafiya ba zato ba
tsammanihanna taji sallamansa ya shigo, furgigit
tayi ta tashizaune kallo daya yayi mata yasan
akwai abindaaka yi mata har tasha kuka. Yaje da
sauri ya zaunaa kusa da ita ya jawota jikinsa ya
tambayeta mekedamunta take kuka. Ta amsa
masa da ba komai . Ya ce yasan dole da wani
abu kar ta boye masa ta fadamasa gaskiya, sai
tace cikin tane ke ciwo, yayi shirushi dai ya jita ne
kawai amma bai gamsu ba. Sai canaka jima
hankalinsa yakai wajen akwatina yagabasa nan
yace hanna ina akwatinanki suke? Tayishiru can
tace inna ta kwashe takai ajiya wai tunda
ba'yimin gara ba wata zata kaiwa ta aura maka
itani ka sakeni. Sai ta rushe da kuka. Bello ya cije
bakidon tsananin bakin ciki yayi shiru ya kasa
maganasai yasa hannu yana goge mata hawaye
ya nisayace. Daina kuka kece baki sani ba na baw
ahmedkudin da zai saya mika gata kakaf yanzu
ma cikon kudin da zai karasa sayyar na kawo
masa. Damanyanzu zan koma wajen aiki tunda
ina da aikin dare.Daman inna bata ganni ba ance
tana makwabtabari inyi sauri in tafi baza ta san
nazo garin bamaballe tayi min maganar sai ince
Ahmed suyi kokarisu kawo garar gobe kinga an
kashe bakinta kafin in dawo. Ya rungumeta
hanna ya sambacikumatunta yace '' bazan sake
kiba hanna ina sonkida yawa ki kwantar da
hankalinki kinji ko, sannanya fice yana sauri ya
tafi. Hanna ta bishi da kalloyayin da zuciya kece
mata'' ba haisam kadai ba bello madu ma
maisonki ne hanna ki kaunace shi.'' haka kuwa
akayiwashe gari da misalin karfe uku na yamma
saihanna taji an doso cikin gidan kamar a
mafarkitaga kartan maza suna ta ajiye
buhunhuna a kofar dakin inna haule . Mata suna
ta shigowa dafantekun alkaki, nakiya dibulan da
sauransu.Wannan al.amari ya bawa inna haule
mamaki,nauyi da kunya saboda sunyi mata ba
zata duk tabigari tana fadin ba.ayiwa hanna gara
ba kuma bazasu iya yiba kwatsam sai ga gara
wacce ko 'yayan attajiran garin ba'a taba yi musu
gara mai yawanbuhunhunan haka ba. Nan dai
inna haule ta haufara.ar borin kunya tana cewa
ashe kuna tafe ku kaki sanar min nima in gayyato
yan uwana suxo sutayani karbar irin wannan abin
alhairi sannunku dazuwa ku shigo daki mana ya
zaku zauna a waje. Hanna dibo tabarminki dana
indo a shinfida baki.Ai da kun sanarmin zaku zo
da nasa anyi mukugirke girke da soye soye irin
wannan abin arzikihaka'' yan uwan hanna suka
ce'' babu komai ai bazama muka zo yi ba mun
kawo gara gata nan,zamu koma don yarmu ta
sami salama a zamanta na aure da mijinta''
suma suka yaba mata ba dadi.Washe gari inna
haule da sassafe taje ta debowahanna
akwatinanta ta kawo mata amma ankwashe wasu
kayan da yawa babu ta kumagargadi hanna kada
ta sake ta fadawa danginta komijinta tayi shiru da
bakinta. Da bello madu ya dawo faran faran inna
haule ta kira shi ta nunamasa gara har tana
cewa'' allah sarki ashe bakaramin shiri suke yiba
shi yasa basu kawo dawuri ba irin wannan yawan
gara sai kace yarsarkin noma ka auro '' bello yayi
dariya ya ce'' Allahya sanya alheri ya bamu
zaman lafiya'' ya nufi dakin hanna, bayan tayi
masa sannu da zuwa ta kawomasa abinci da
ruwa yasha sai ya jawo akwatinanya bude kamar
yadda ya zarga tabbas mahaifiyarsazata kwashe
wasu kayan haka kuwa ya gani takwashe kaya da
yawa. Ya waiga ya kalli hanna saita sunkuyar da
kanta kasa bata ce masa komai ba...
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 2
Posted by ANaM Dorayi on 03:14 PM, 30-Apr-15
Under: Gangarjikinsa ta Aura
Yace '' hanna an kwashe miki lefenki ko?
Kiyihakuri zan suyo miki wasu insha Allah idan
muka yialbashi wani watan'' hanna ta dago cikin
ladabi datattausar murya tace'' ni na yafe duniya
da lahira basai ka biyani ba wahalar zata yi maka
yawa. Kawubello babu abinda zance maka sai
godiya da wannan gara daka yimin Allah ya saka
da alheridomin ka kwatar min yancina tun daga
ranar daaka kawo inna bata sake yimin gori ba.
Yanzu zanyizaman farin ciki a gidan aurena: yayai
murmushiyace'' farin cikin ki shine nawa Hanna,
Allah ya karasanya ki a farin ciki fiye dana yanzu''
tace amin na gode. Karshen wata nayi da bello ya
dau albashi saida ya sisiyawa hanna kayayyakinta
damahaifiyarsa ta kwashe cikin dare ya
kawowahanna a boye yace ai hakkintane dole ya
biya ta.Hanna tayi godiya ta karba haka hanna
da bellosuka kasance yana kyautata mata a boye
komai ya gani na sakawa kona marmari sai ya
suyo mata dadaddare ya shigo mata dashi ya
bata a boye ba taredaya bari mahaifiyarsa ta gani
ba. Bello yana karason hanna saboda ladabinta
hankali da nutsuwada uwa uba tsananin
hakurinta da tawakkali itakuwa hanna har yau
har wayewar gobe ta kasa masanya gurbin
haisam ta mayar da bello zuciyarta.Idan bacci
take yi tana kwance da bello ammamafarkin
haisam take. Idan tunani take yi haisamkawai
take hangowa a zuciyarta. Tana kokarin tamayar
da soyayyar da take yiwa haisam kan bellosaboda
ita ma ta saka masa da soyayyar, sabida irin
kyautata mata da yake amma abu ya faskara
hakadai take dagewa tana nunawa bello tana
sonsawanda a zuciyarta ba haka bane. Wasu
lokuta dayawa idan suka tashi da safe. Bello
yakan ce matayaya haisam? Don jiya kina kiransa
a mafarki.Hakika hanna duk sanda ta kwanta
mafarkin haisam take yi ashe har ambatonsa
take a fili.Saboda tsananin son da bello yake yi
mata ya yardaya amince kuma zai zauna da ita a
haka. Bai tabanuna mata bacin ransa ba. Ita
kuma hanna sai tajitausayinsa ya kama ta nauyi
da kunyarsa talullubeta. Amma yaya zata yi
tunda GANGAR JIKINTA YA AURA ZUCIYARTA na
wajen haisam.Matsalar gara ta wuce tsakaninta
da surukarta saikuma matsalar da inna haule ta
dakko ta dorawahanna ita ce har yanzu hanna ko
batan wata batayiba balle ta samu ciki fada da
gori a wajen innahaule babu dare babu rana.
Bello yayi kokari ya wayar mata dakai akan cewa
ba laifin hanna baneciki Allah ke badawa amma
abu yaci tura inna hauletaki ta saurarawa hanna
cewa take ga sa'anninaurenta nan dukka ciki
garesu wata bakwaibakwai tunda yanzu watan
hanna bakwai da aure.Yau hanna tun karfe biyun
dare take kai kawo a tsakar gida bacci ya gagari
idanuwanta. Duk budeidon da bello zayyi sai yaga
hanna tana fita ko tanashigowa cikin dakin
kaman a mafarki yake ganinta. Can yaji ana
kiraye kirayen sallar asuba tayi. Yasahannu ta
laluba gefensa yaji hann bata nan. Yayifirgigit ya
tashi ya fito tsakar gida ya hango hanna a gaban
murhu tana hura wuta ya karasa inda takeyace.'
Hanna yau lafiyarkikalau kuwa tun dare kike
shige da fice kinki kikwanta yanxu da asubar nan
wutar me kikehurawa? Hanna ta danyi murmushi
tace'' kawu kamanta yau da duku duku oganka
yace zai aiko damota za kuje Agadas shine nake
dora maka ruwan wanka naji yau garin da sanyi
sanyi''Yayi murmushiya ce'' Ai jinsa nayi kawai
meye abun turo mota daduku duku sai kace
zamubar kasar'' Hanna tace''Agadas ai da nisa
shi yasa kuma wata kila bakwana zakuyiba ko ?
Yace' Gaskiya agadas da nisaba kuma cikin garin
zamu shiga ba local government zamu je ina
ganin wajen 450 Km nekuma bana jin zamu
kwana ziyarar aiki zai kaimucan mu kuma yan
rakiya'' Hanna tace '' Allah ya kaiku lafiya ya
dawo daku lafiya. Ina jin kiran assalatukafin
ruwan yayi zafi ga buta ka fara yin yin Sallah ?Ta
mika masa buta ta durkusa har kasa. Bello ya
tsaya yana kallonta kawai saboda wata
tsantsarsoyayyarta ce take kara sarke masa
zuciya.Musamman wannan kulawa da ladabi da
Hannatake masa, ya karbi butar ya shiga
bandaki, kafinya idar da sallar Hanna ta hada
masa ruwa wanka .Ya tashi ya shiga wanka. Kafin
ya fito ta debo wankakkaun kayansa data wanke
ta goge masa tadora akan gado ta goge masa
takalmin da zai sakamar yadda tasaba masa
kullum. Bayan yakammala yana goge gogensa da
yan shafe shafesai ya dauko kayan da Hanna ta
fitar masa ya saka.Tazo tana balle masa maballin
wuyan rigarsa. Yayi murmushi yace'' Hanna na
gode da irin wannahidima da kulawa da kike
nunamin wannan yasaina kara sonki dari bisa
dari, idan akwai soyyya datafi dari bisa dari ina
miki Hanna sai dai ni anyakuwa na sami kwaya
dayan nan kacal da nake so asanmin a cikin darin
da ake yiwa haisam ?Cikin kunya hanna tace''
Haba daya kacal ai kafiguda daya'' yace '' a.a
zancen gaskiya muke, nawaaka karamin ? Tayi
dariya tace'' kawu ka wucegoma ma zaka kai sha
biyar'' su duka suka tuntsireda dariya. Yace '' to
tunda a wata bakwai na samigoma sha biyar nan
da shekara bakwai zan iya tadda haisam'' suka
sake tuntsirewa da dariya.Muryar inna haule ce
ta katse musu dariyar da sukeyi tana bakin kofar
dakinsu tana cewa'' tun dazumagana nake muku
baku jini ba kun shige dakikuna tuntsira dariya
da duku dukun safiyar nan tomotar ofishinku ce
tazo suna ta kwankwasa gida . Daman Hanna
abinda kika sani kenan ki shiga dakida miji kina
dariya aikin kenan ciki fal kashi, babugurbin
kwanciyar Da sai gurbin tarin kashi'' Hannatayi
kasake yayi sanyi fara.ar da take yi ta koma
cikiranta ya baci damin da ana siyar da ciki da ta
suyohaka kuma da a wani waje ake nemoshi da
taje ta nemo duk wahala koda kuwa zata mutu
ne. Ko tahuta da zagin da gorin da ake yi mata.
Bello yayiajiyar zuciya yace'' inna gani nan zuwa
shiryawanake'' ta wuce ta tafi tana tsaki tana
cewa'' Kaje kadawo dai daga tafiyar kazo mu
zauna muyimaganar saboda bazai yuba, in zuba
muku ido haka kawai aure wata bakwai kenan
babu ciki baalamarsa kaina da kafafuwana
turawa yarinyaabinci nake sai dai taci tayi kashi
kawai. Ai ba dantazo ta cika mana shadda muka
aurota ba mumamuna so muga dan jariri a
gidanmu. Tunda tashanye ka ta asurce ka baka
ganin lefinta to ni bata asurceni ba dole ka karo
aure idan ma baza kasake taba, kai dole ma ka
sake ta ka auro maihaihuwa don daki daya
garemu a gidan nan'' Harinna haule tayi nisa ta
juyo ta dawo ta tsaya a kofardakinsu Hanna tace''
Hanna kiyi ki fito daga dakinnan yau duk ke zaki
yi aikin gidan nan shara wanke wanke surfe da
girki ki fara debo ruwatukunna idan kin cika
randunan gidan kakaf sai kifara aikin gida da
yamma kuma kije gona ki tsinkowake da gyada
dan sun nuna. Yau wacce kukeaikin tare indo
aikenta zanyi magarya wajenkawata. Tunda ba
ciki garekiba ba goyo ba ai wannan aikin bazai
gagarekiba, sai dai idan kinjikashi sai kiyi a gonar
tunda cikinki sai kashi babuhaihuwa. Kinga kuwa
kashin naki ya zamar mintaki a gonar kinga kin
taimaka kema'' Bello maduya fisata baisan sanda
yace'' Haba inna ki dainayiwa hanna gorin
haihuwa ba laifinta bane rashin haihuwa Allah ne
yake bayarwa inna dama haryanzu Hanna ce take
debo ruwa a rafi ina almajiriindana dauko aiki
nace zan dinga biyansa. Ita taji daaikin gidan su
kuna almajiran suje gonar. Hannatasa hannu ta
toshe masa baki tace '' yi shiru karkasa taji
haushina, mahaifiyarka ce babu komai duk zanyi
aikin. Inna Haule ta rike baki tace'' inyedannan
ka fara fada in fada dani akan matarkalallai abun
babba ne jeka ka dawo ka sameni donwallahi ina
ganin zamanka ya kare da wannanyarinyar mai
kama da tumatir ina ganin rabaka takesotayi da
kowa a duniya har dani dana haifeka . Ba'a
haiyacinka kake ba na sani bayinka bane. Tatafi
tana surutanta dai barkatai. Hawaye yana
zubashar daga idon Hanna. Bello yasa hannu ya
gogemata zuciyarsa cike da tsananin tausayinta
ammayafi jin tausayin kansa da kansa. Saboda
zaifi hannashiga wani hali,idanmahaifiyarsa tasa
ya saketa don shine yafi sontafiye da yadda take
sinsa idan ya rabu da hanna yarabu da farin cikin
rayuwarsa. Kalma daya ce yasanidan yafadawa
Hanna duk irin bacin ran da takezata yi dariya
idan ya ambaci sunan Haisam . Yayi dan
murmushi ya kalleta yace'' Hanna dama ace
ayanzu kina da ciki ki haifanmun da namiji in
sakamasa suna haisam. Hanna ta dago ta
dubeshiidanuwanta a cike da hawaye sunyi jawur
donkuka amma saida murmushi ya subuce mata
a taketaji zuciyarta ta fara dan hucewa daga
tsananin tafasar da take yi saboda kunar
maganganun dainna Haule ta fada mata. Hanna
taji wani dan sanyi aranta wani abu ya dasu a
zuciyarta da bello yace ''dama ace ana da ciki ta
haifi da namiji ya saka masasuna Haisam taji
dama ace hakan faru mana. Ammadata tuna
yanxu ma haka al'ada take don haka zancen ciki
ma babu shi sai ta sake rushewa dakuka. Bello
ya jawota ya rungumeta akirjinsa yanashafa
lallausan gashinta yace'' Hanna lallai yauranki ya
baci sosai har in kira miki Haisam ammakici gaba
da kuka kiyi hakuri ki yafewa innata mucigaba da
yi mata addu'a Allah yasa ta gane gaskiya Allah
ya cusa mata soyayyarki a ranta. Hannatayiajiyar
zuciya tace amin'' amma ka tayani addu'aAllah ya
bani ciki kafin karshen watan nan inaganin haka
zai saka soyayyata a zuciyar inna. Belloyace amin
ya Allah, zan dukufa da addu'a kema kiyiAllah ya
amsa mana. Ya goge matahawayen idanuwanta
ya sumbaci kumtunta yace'' Haisamsunan danmu
fa. Hanna ta kyalkyale da dariya tarufe ido sai taji
wani farin ciki ya lullubeta. Tatsugunna ta jawo
takalminsa ta fara saka masa akafa tana sake
goge masa da tsumma. Ta feshemasa jikinsa da
turare tace'' Kawu bello Allah ya kiyaye hanya
kuje lafiya ku dawo lafiya. Yace aminHanna Allah
yasa nazo na sameki lafiya cikin farinciki'' yana
tafiya yana waiwayan hanna, itama ta fitohar
bakin kofar dakin ta tsaya tana daga masahannu
har ya shiga dakin mahaifiyarsa sannanhanna ta
koma daki. A zaune a gefen gado Bello ya iske
mahaifiyarsa tana tunani tana gayda kai
yadurkusa ya gaisheta ta amsa a fusace ta fara
masfada tace'' to dannan abunda nake so dakai
shinekarka yadda kayimin musu akan duk
hukuncindana yanke akanka ina nemar maka
aure a gidandagacin garinnan yar sarauta ka dace
ka aura tubda ka makalewa Hanna baza ka iya
sakinta bato ta zauna anan gidan tare dani ita
kuma waccamidan anyi aure sai a kaita gidan ka.
Bello ya dagakai ya kalleta zuciyarsa cike da bakin
ciki.Gidan da yasha magiya ta yarda akai Hanna
takiyau gata da bakinta tana cewa yayi aure
yakaimatarsa can amma banda Hanna ba. To
ashe hannadin ta tsana kawai . Ya nisa yace inna
me zai hanamu tare mu duka da amarya da
hanna duk inhadasu acan din'' Ta girgiza kaia
tace '' nace maka karka yimin musu ko? Haka
naga dama, tashi kajeka dawo din mu karasa
maganar amma idan kamatsa akan sai ka mayar
da hanna gidanka zaka saince ka sake ta don
wallahi hanna baza ta tare awancan gidan va sai
dai idan bani na haifeka ba. Kobayan raina ka
kaita can Allah ya isa'' Bello ya rike kai don
takaici can yace'' Naji inna na gode, danAllah ki
yafemin duk abunda nayi miki, idan na batamiki
rai a rayuwata gaba daya''Tayi dariya tace ''Babu
abunda ka taba yimin wallahi ko musun madaka
tarka kake mun bayin kanka bane ta shanyeka ne
na yafe maka Allah yayi maka albarka Bello ya
mike ya fita hawaye ne shar yake fita
dagaidanuwansa . Yana fitowa hanna tana jika
gero tayisharkaf da hawaye daga gani ta gama jin
dukmaganganun da suke yi. Kallo daya yayi mata
yajihawaye ya sake kece masa. Yazo ya wuce
tagabanta yace'' Hanna kiyi hakuri, ki sake yin
hakuri, Allah yana tare da mai hakuri'' ta bishi
dakallo tana hawaye yana waiwayanta yana
hawayehar ya fice . Tayi shiru tana sauraren
karar motarsuhar suka yi nisa ta daina jin karar
motar, ta rushe dakuka tana cewa a ranta'' A
bakin ciki ashe zandauwama? Yanzu aure inna
zata sa kawu Bello zaiyi ya tareda amaryarsa
agidansa ni abarni anan, meyasa inna ta
tsaneni ? Me nayi mata tatsaneni? Meyasa
kowaya tsaneni a duniyarnan ? Ubangijinayana
sane dani, Allah kasan halin da nake ciki,Allahka
fitar dani, Allah kaine abin godiya. Bayanfitar
Bello madu da kamar awa guda. A lokacin hanna
tana surfa gero, inna haule tana tsakar gidatana
cin dumamen tuwo, indo kuwa daga wanka tafito
zata shirya ta tafi magarya inda inna Haule
zataaiketa. Suka ji ,Mota tururus ta tsaya a kofar
gidansu.Wani ma'aikacine mai sanye da kayan
'yan sanda,yayi sallama ya shigo ba tare daya
gaishe suba. Yace '' Nan ne gidan su custom
Bello madu ko @inna haule ta tsaya dacin
tuwonta tace '' Nan neamma baya na waye yake
nemansa? Yace inazuwa'' ya fice, gaban hanna ya
hau faduwa . Daf-daf daman tun jiya ta kasa
bacci saifaduwar gaba take. Jingine tabarya da
take surfe ta tsaya. Kawai ji suka yi ana cewa' ku
kamada karfiwajen kafadan zaku rike inna haule
ta zabura ta mike da gudu ta lekoHanna ma ta
biyota da sauri idanuwansu sukagane musu
wannan gagarimin tashin hankalin,Gawar bello
madu ce ake shigowa da ita. Allahyayi masa
rasuwa a sanadiyar hatsarin motar dayaritsa dasu
yanzu-yanzun nan suna hawa hanyarsuta tafiya
Agadas wata babbar mota ce tazo gwaramusu
suka kutsa ta tsakiyar motar cikin ikon Allahbello
ne kawai ya rasu, sauran sun sami munanan
raunika suna asibiti. Hanna ta fadi ta suma,yayin
da inna haule take neman tube kayan jikntadon
gigicewa sai da aka rirriketa. kafin kace
kwabogida ya cika yayi makil da 'yan uwa da
makwabtamaza da mata. Ani masa wanka, an
suturtashi ankaishi an binne kamar yadda sharia
musulunci ta tanada. bello ya tafi ya bar rikici
gidansa kuma shitasa ta kare a duniya domin
rikicin duniya da mairai akeyi duk wani rai saiya
dandana mutuwa Allahyasa mu cika da imani,
amin. hanna tayiwa belloaddu'ar har yawun
bakinta ya kame, idan ta ya gajida addu'ar ta
rushe da kuka tayi ta huta haka dai har akayi
sadakar bakwai 'yan zaman makoki sukawatse
aka bar 'yan gida. yayin da bacci yakegagarar
idanuwansu, kamar yadda inna haule takekuka
cikin dare haka hanna ma sai ta laluba kusada ita
taji ita kadai babu bello sai ta tashi tayi kukahar
ta godewa Allah. kaico hanneta rasa kowa a
duniya. hanna bata shiga. watamatsala
batabangaran ci ko sha ko aikin gida ba har ta
fitadaga takabarta.sai bayan ta fita daga takaba
an fara zancenrabon gado sannan inna haule ta
daka tsalle ta diretace babu abunda za'a bawa
hanna na gadondanta tunda hanna ba
haihuwatayiba da bello saidai ta hada 'yan
komatsanta ta bar musu gida.kawu Ahamed yaji
haushi sosai ya kuma lashi takobin ko sama da
kasa zata hadesai ya kwatarwa'yarsa hanna
hakkinta a tumuli takaba shari'ar shida inna
haule har kotin koli idn bata bari an rabagadon
nan da hanna ba. yace kuma babu indahanna
zataje a gidan zata zauna sbd bello yana dagado
a gidan ubansa, inna haule kuma tace ita kuwa
baza ta bayar da dukkiyar belloba sai dai suzuba.
makudan kudi kuwa aka kawo daga wajenaikin su
bello, gashi da filaye da wannan tafkekengidan
nan daya sha suminti da bulo. inna haulekuwa
tace duk natae banda hanna ko sisi baza tabata
ba tunda ko kwai bata saka a gidan ba. tashin
hankali ya tabbata a zuciyar hanna ta rasa
yaddazata yi da rayuwarta da kawunta zai hakura
ya bariinna haule ta rike dukiyar bello dukka ba
sai anraba da ita ba. duniyar nawa take wanda
yatara ma ya tafi yabarta kowa ma mutuwa zaiyi.
dukwani hango jin dadin. rayuwarduniya yagoge a
zuciyar hanna babu abunda take bege sai
mutuwatazo ta dauketa ta tafi ta hutaitama. daga
gidankawu ahamed dake aiko mata da abincin
dare darana. tafi tafiya suma wata rana basa
aiko mata donyau da gobe sai Allah. hanna ta
fara fitar dazannuwan daurawarta da
kwanukanta tana siyarwa snnn taci abinci. wata
rana da yamma daindo sunje rafi sun debo ruw
suna tafe suna hira saisuka ji hassan me yekuwa
yana sanarwa yanacewa "yekuwa. jama'a ga
wata sanarwa, mai girmadagacin garin nan yace a
sanar muku matawadanda mazansu suka rasu
suka barsu da suzo fadarsa yanzun nan.
ma'aikata daga nigeria sunzomusu da tallafin
taimako. gwamnatin jihar kano anigeria ta aiko
da taimakon kudi za'a raba musu jaridomin su
rike kansu da marayin 'ya'yansu. ammakada
wata ta kuskurataje idan ba mijinta bane yamutu,
sai wacce mijinta ya mutu idon ta zunguri hana
tace hanna muje wajen taron nan ko Allah zaisa
mu dace. hanna ta rike baki tace babu
ruwanmuyanzu idan mukaje ai mun shiga 3 a
wajen innnacewa zatayi munje. mun tona musu
asiri aci muka jemu tambaye tako zata yadda. a
hanya sukadingahaduwa damata wadanda
mazansu suka rasu suna ta tafiya gidan dakaci
don karbarwannan tallafi mai tsoka. kowacce
tagasu hannasai tace au, baza ku taho fada ku
karbiwannantallafi ba daga nig fa bakin suka zo,
indotace gaskiya hanna in baza ki ba ni zanje sbd
idanmukakuskuramukaje gida inna haule baza ta
barmu ba.amma idan mun riga munje mun
karbobabu yadda zata yi damu fada ne dai da
zagi yazama jiki. hanna tace to mu shigagidan.
adama muajiye ruwa muje din daman gudun
fadan inna nake,to kobabu abundamu kai ma
kullum zagin mu takemuje kawai, suka shiga
gidan adama suka ajiye ruwan da yake kansu
suka nufi fada wajen taron.mata ne makil akan
layi suma su hana sukajekarshen suka tsaya.
wata kyakkyawar mata ce azaune akan kujera da
tebur a gabanta an dorawasu fles akan teburin.
kallo daya zakayi wa matarkasan tana cikin daula
fatar jikintamulmul sumul. dukda matar ba fara
bace amma ba baka bacekalarta mai kyau kayan
jikinta kuwa ko ba'a gayamaka ba leshin zai doshi
dubu hamshin sarkargwal da dankunneta da
zubbunan gwal reras ahannunta guda hudu sai
sheki sukeyi.matar maifaraa'a gata bata kyamar
talakwa sai gaggaisawa dasu take suna yin hannu.
tace. kowacce tazogabanta ta rubuta sunanta don
asan yawansukuma nawa ya cancanta a basu.
kowacce ta hauzara ido sbd basu iya rubuta
sunanta. matar taceyanxu duk cikinku babu
wacce ta iya rubutu tazo ta taimka min mu
rubuta sunayenku?Hanna tayi shiru kamr tace ta
iya amma gudunsurutun 'yan garin nan kar ace
ta cika nuna iyawasai tayi shiru. Indo ta
zungureta ta hanna bakn iyarubutu baki rubuta
mana Hanna tace a'a indo baburuwana a samu
wani yazo yayi dan kar ace nazogarinku na zake.
Matar ta sake cewa To tunda babu wacce ta iya
rubutu ina ganin ba zaiyu mu aiwatarda aikin da
zamu aiwatar ba a yau sai mun nemowacce ta
iya rubutu sannan saboda da mata zallamukeso
mu kafa kungiyar dole mace ce zata zo tarubutu
mana sunayen indo da taga kiri-kiri zasurasa bata
san snda tace A'a ranki ya dade ga hanna ta iya
rubutu" sauran suka hau cewa hannataimaka
mana ke kuwa ashe daman kin iya
rubuturubutamana karmu rasa Matar tace
wacece hanna?Ta fito tazo nan Hanna taje gaban
teburin matar tatsaya tace gani ranki y dade.
Matr ta kalli hanna smada kasa wata burgujejyar
doguwar riga wacce aka dinkintada wani
wagambari mai kauri irin nddinnan itama kanwar
kkrta ce ta bata, gashintatufke a tsakiyar ki tai
gammo dashi da zasu deboruwa sai wani yalallen
gyale baki ta yana akanta datakalminta dan
madina akafarta. Matar tayimurmushi tace yaya
sunanki? Hanna tace sunana Hanna Abubakar
imam" matar tace HannaAbubakar kin iyarubutu?
Hanna tace na iya ranki yadade, matar tace ko
da yake ku anan french kukeyiba turanci ba ko
irin na 'yan nig? Hanna tace ni nafiiya turancin
nig, french din kadan-kadan na iyamijina yana
koy min mtar taace , ta jawo kujera kizo nan kusa
dani ki dinga rubuta sunayen su, ki fararubuta
sunan ki sannan ki rubuta sunayen sauran.Hanna
ta zauna tana rubutu sunayen matan nandaya
bayan daya suna tahowa a layi. Ta gamatubuta
sunayen sai magaruba tayi sai aka tsayar
dashawarar sai gobe da safe su kra taruwa dan a
raba musu tallafin sukanufi gidanjen su,
matarkuma gidan dakci aka kaita a can zata
kwana,namijin kuma da sukazo shima aka kaishi
wanigida aka suke shi tunda dare yayi dokin gobe
tayisu koma fada. Hann da indo kuwa sai suka
haufaduwar gab suna shirya kalmar da zasu furta
wajen kare kansu daga fadan inna haule.
Aikuwadaga shigarsu gida ta fara yi musu fada
donlabari ya kai mata cewar anga su hanna a
fadasunje karbar jari. Tana cewa dole Hanna ki
barmingidana sbd so kike ki koywaindo kinji da
fitinawanda da bata iyaba, ki tafi can gidan ku
acan ake yunwa ake neman jari mu nan Allah ya
rufa manaasiri,kema indo tunda wanda ya du
nuyinki ke da'ya'yankiya rasu bello ne damn
yace shi zai dingaciyar dku gashi ya mutu dole
kema asan yaddaxa'ayi idan bangaren gidanku
zaku siyarmin to,idan ma wani zaku siyarwa dai
duk daya ki karbi kudinki ki kada 'ya'ynki ku
koma can Tawa localgobernment grinku. Ba zaku
zo ban haife ku bakusamun hawon jini tunda kun
hallaka mazan nakuni dai ku kyale ni. Washe gari
da sassafe su hnnasuka tashi suka hu aiyukan
gidan,bayn sun gaamsuka leka ko ina basu ga
inna haule ba ta shiga makwabtasai suka debi
bokitansu suka cewamasa'ud dan gidan indo in
inna tazo yace mata suntfi deboruwa . A tamfar.
Maikyau hanna ta daurabasu tsaya a ko ina ba
sai a fada wajen taro, sunmadanmakara don ynzu
tar da rabi wjen taro, sunmadan mkra don ynxu
tara da rbi tayi suka ajiye bokitansu a lungu
sukaje wajen taron matr ta. KalliHanna tyi
murmushi tace hanna ke muke jira kifarakiran
sunaye in rarraba muku kudin . Hanna tagaisheta
faram faram da fara'a sannan ta krbitakardar ta.
Fara kirn suna tace Hanna abubakariman ce ta
farko, matar tace to ki kira sunayen daya bayan
daya suzo subi layi sai kwai in dingamimmika
musu kudin a layi Hanna ta fara kirnsunayen,
kowace tan zuwa tana shiga layi kamaaryadda
sunayen suke a jikin takrdar,byn hanna
takammala kiran sunayen sai matr t mike tace
tomadalla Assalamu Alaikum jam'a su duka
sukace wa'alaikussalm tce ni sunana Haj Hindatu
umardaga kano state nigeria. Nazo nan grin mai
sunaDashi karkashin karamar hukumar mgarya
a.Janhuriyar niger don in kawowa 'yan uwana
matatallafi da taimako yaddamatan da suke da
mazasuke samun taimako daga wajen mazajensu
to ku da baku damazasai kusamu san'ar da
zakutaimakawa kanku da marayin 'ya'yanku.
Sukasatafi raf'-raf suna cewa Allah ya saka da
alheri mungode hajiya hindatu. Ta cigaba da
cewa dagagwannatin jihar kno matar maigirma
gwamanjihaar kano ta bude wta kungiya wacce
za'a dinga taimakwa matan da mazansu suka
rasu sukabarsu. Shine taga ya dace mu shigo
makwabciyarkasarmu Niger suma mu hada kai da
gwiwamutaimaka musu saboda Abunda yayi
nigeria shiyayiniger duk uwa daya uba daya
muke, tafi sukahauyi suna murna suna cewa
Allah ya kiyaye Nigeriada gwannatin jihar kano
Hajiya Hindatuumar taci gaba da cewa yanxu
anan garin zamukirkiro wani suna mu saka wa
wannankungiyatamu. Don mucigaba da turo
muku tallafi tako ina daga kasarmu. Bani za bawa
kungiyar nansuna bku d knku ykmt ku saka mata
suna. Nan dai wannan tace a sa mata kaza wacce
tace asa mt kazadaga karshe di. Suka tsayr da
shawarra akan asawa kungyar sun hindatu umar,
tayi darya tace a'aba sunana za'a sa ba sbd wata
kila baz ku sakeganinaba saidai kuga an turo
muku wata sbdmuma acan 'yan kungiyar muna
da yawa idan aka turoni yaugobe wata za'a turo
muku. Amma yanzutunda ga wacce taiya rubutu
da karatu hanna itazata dinga wakiltarku idan ta
kama mahar cannigeriazata dinga zuwa tana
karbo muku tallafi inaganin idan kun amince
asawa kungiyar sunnhanna. Gaba daya suka hau
cewa mun amince asa sunan HANNA,Dagakarshe
matar ta jawowata jaka ta fara mikamusu damin
kudi kowcce kudin data samu idanaka kiyasta
dakudin nigeria zaiyi kimanin nairadubu sha
biyar-biyar. Bayan kowacceta karbataceba'a kare
ba.akwai atamfofi da wasu kudadenda za'a
sakebasu shima daga gwannatin nigeria saidai
basu zo dakudin yanzu ba amma idan zaiyusu
nada wata daga cikinsu da zataje ta wakilcesudan
taga waje tacigaba da zuwa su sai suka hadabaki
suna cewa mun wakilta hannaa
matsayinwakilyarmu. Hjy hindatu ta juya ta kalli
hanna tacekin amince hanna zaki bini nigeria
kidinga karbo musu taimakon? Hanna tayi
murmushi ta ce hjymezai hana sai in biki din
akan haka sukayi sallamacewar hanna zata bi hjy
hindatu kano don karbomusu wasu tallafin masu
yawa,kafin hanna tabimatar saida taje da sauri
gidan kawu ahmad tashaidamasa duk sha'awarda
sukayanke akanta ya amince ya kumayi mata
fatan Allah yasa su dauketaaiki ma acan tayi yace
idan da sarari tajemakarantarsu takarbo
sakamakon jarabawarta tanemi aiki ko Allah yasa
ta dace. Ta rabakudintagida 2 ta bashi rabi. Ta
sake rabanata gida 2tabawa matarsa hajir.
Kogidan inna haule bataje ba dauko kayanta
kawai ta fada motar su hjy hindatuumar sai tafiya
daman hjy hindatu tayi. Sallamadagaci dasauran
hakiman garin tabasu kudi masuyawa sumata
sanar musu zata tafi da hanna dontasake karbo
musu wasu kudaden taimako. Sunyimurnasosai
sun shi albarka sunyi musu fatan Allah yakiyaye
hanya. Mutumin da sukazo dashimai sunashehu
shine yake tuka motr hjy hindatu a baya tazauna
hanna ce ta zauna a gidan gaba, motar
kirarhumma jeef dindimemiyar motamai dauke
darundumemyar rikoda an saka sauti mai tashi a
hnklsai sanyayyiyarna'urar sanyi ce ke dukan jikin
hanna. Cikin motar ma abun kallo ne
lallausankujerun motar su suka sa hanna ta
nutsu komagana bata iyayi,tace a ranta Allah ya
baku duniya wannanmota ce kawai ba gida ba,
Allah mai azurta wandayaso sun hau titi dodar
suna zuba gudu a titi saihanyar kan karfe 3 ma a
ciki garin kano tayi musutafiya suke kamar bayi
sukeyi ba sbd babu watakura ko gjy irin ta
matafiya a tare dasu. Hanna sai kaallon kano
takeyi galala komai yaci gaba bakamar lkcn da ta
zo ba. Babu abinda ya fado mata arai sai ranar
data zo wajen haisam zuwanta kanona farko
kenan kuma bata taba ska ran sakedawowa ba
ashe zata dawo yanzu Allah ya kawodalili. Ta
dinga kallon haanyoyi ko zata gane gidan su
haisam amma ina ba tama gane hanyar ba
balleta gane gidan. Haism haism take kira a
zuciyartayayin da kwalla ta cika mata
idanuwanta. Tamadubi hjy hindatu take kallonta
tace hanna yayadai naga kamar kwalla ta cika
miki ido ko iskar ACce tyi miki yawa a ido a rage?
Hanna tace a'a babu komai suka cigab da tfy can
hjy hindatu tace hannaga garinmu fa, kano kenan
kin taba zuw kano netunda naga kamar a nigeria
kikayi karatu? Hannatace nan FGGC kazure nayi
na taba zuwa kano saudaya sheraka 2 da suka
wuce amma bazn iya tunaina ne unguwar dana
zo ba, sulemanu cresent sunan unguwar , hjy
hindatu tace oh sulemncresent sunan unguwar ai
bamu da nis sosai ynxumun ahmdu bello way
zamu bi ta wajejen dai ni asokoto rd farm center
nake zan nuna miki kwanarhanna tace to suka
cigaba da tafiya.Daidai get din wani tsantsereren
katafaren gdamotar su hanna ta tsaya yayin da
mai gadin ya tasoda sauri yazo ya bude musu.
Hjy hindatu ta kallihnna tce hanna nan gidana ne
ina so muyi sallamuci abinci mu huta wajen
gobesai in kaiki wajenkungiyar subki tallafi a kaiki
can garin naku ko? Hanna tace babu komi na
gode hanna taga duniyawannan gida shine ake
kira aljannar duniya sbdkana shiga farfagiyar gidn
wasu fulawoyi ne anzagaye wani dan tudu yana
ta bulbulo da tsuntsayemsu kyau aka watsa a
farfagiyar gidan sunt t yawocan gefe kuma wajen
wnke ne (swimmingpool) an kewye da wasu
kujerun hutawa cn gefe kumawjen wsannin ne
ma motsajiki (games) wajenbsket ball, tble tannis,
football da sauransu. Iskuma gawta tafkekiyar
kofa wacce zata kaika cikingidan. Daga can bay
kuma boyi quarters ce itamakamar wani katfaran
gidan. Arziki ma anan ai ba'a magn kai kce a
turai kake ba'a nigeria ba. Hjyhindatu ta yukura
zata fita dagcikin mota ta juya takalli hanna
wacce ke zune tayi turus tace hnna fitoman
hanna tj kofar zata bude ta kasa sai da
hjyhindatu ta fito daga kujerar baya tabude mata
tawaje snn hanna ta fito, gidan ya baw hnna
sha'awakwrai da gaske. Tace hjiya gidanki yayi
minkyau wlh, ta kalli hnn tayi murmushi tace
nagodehanna.Wani dogon saurayi ne kyakkyawa
a gefe azaune akan wata kujerar roba yayi
tahumu ya rikekai. Hjy hindatu taje ta sameshi
tana zulayarsa tacemijin me akayi maka yau?
Kana ganina ko ka dagokayimin magana ko
budurwarce ta baka maka rai?Daga nan hanna ta
tantance kanin mijinta ne wasan kanin miji take
yi masa, ya dago a sanyaye ba fara'ada kyar ya
kalleta yace antynah muje daga cikimuyi mgn. Hjy
hindatu t kyal kylle da dariya tace kaidalla rago
nasan fada ku kayi kai da ummi dukydda kayi.
Yace wannan me sauki ne muje ciki dai,ya juya
ya halli hanna yace anty wacece wannan? Tace
yar niger ce yace niger? Daman niger kike jeyau
kwana 7 bakya nan ? Tace eh ehmuje ciki
dai,hanna zo mu shigo ciki. Suka isa wani
tafkeken falowanda zan iya kiransa aljinnar
dunita anan hjyhindatu ta ajiye jakarta akan
kujera ta kshingidadon gjy. Tace da hanna zo ki
zauna bakuwa kema kin gaji hanna tayi
murmushi dukka snsan jikintaya dau sanyin
na'auraa, a fakaice kallon alatun dasuke jifge a
falon take take tana tambayar zuciyartaabunda
bata sani ba bata taba gani ba. Saurayinyaje wjen
wata (telephone) waya da take sakale ajikin
bango ya dauka yana latsa wasu lambobi can da
aka jima yace" hello hjy ga aunty ta dawo
ashewai niger taje. Hjy hindatu ta tshi zune tace
lhhajiyrku kake gayawaa ashe niger naje
damanhaka kake kai in an gaya maka magana sai
kafada? Yazo a sanyaye ya zauna akan kujera
yaceaunty dole fa hjy tsn kin dawo kuma in kika
je tunda neman ki ake yi tuntuni "hajiya hindatu
tacehjyr a asibiti take ko kuma a ofis? Yaya mai
jikin inata tambayarka baka bani amsa ba? Yace
yana canyaji sauki tace bari. Inje inyi sallah inje
in duboshi,hour yanzu basu sallameshi? Yana
premier hospitalko Aminu kani aaka mayr dashi?
Ya ce yana can dai. Tace wai meke damunka ne
duk da kyaar kkemagana na lura. Hanna tace
wani ne bashi da lfy?Allah ya sawake. Hjy
hindatu tace wlh mai gidanane bashi da lfy yana
asibiti. Hanna ta girgiza kai tacekai kai Allah ya
sawake masa, ciwon ya tsananta nehaka har da
kwanciya a asibiti me ya same shi? Tace ciwon a
zuciyarsa yake ciwo ne sosai yakefama wallahi
hanna. Hanna tace zuciya? Is tarableAllah ya
bashi lfy. Ramlah tace amin shigo gabandaki muyi
sallah ko azahar bamuyi ba gashi 3da rabi yanzu
la'asar ta kusa. Hanna na biye da itahar wani
katafaran daki mai dauke da wani kayataccen
gado a ciki dakin kuma da wanikyataccen
bandaki. Hjy hindtu tace hnna ta shigabandaki
tayi alwalla idan ta fito sai ta shiga . Hannata
shiga bandaki sai da tasha kallo ta gaji
sannantayi alwalla ta fito. Hjy hindatu mata shiga
ta dauroalwalla.Suna idar da sallar azahar sai
kwai suka yi l'asardon lokaci yayi hnna na tahiyar
karshe hjy hindatuta idar tana jan carbi suka juyo
na rafsa kukakamar na mutuwa a babban flo a
guje hjy hindatuta fita hanna kuma ta hau sauri
tana so ta idar tajeitama taga meke faruwa
hanna taji ihun ya kara karuwa da hjy hndatu ta
fita kuka wiwi sukeyi.Hanna ta fita da sauri ta
iske mata makil a falo anata kuka. Hanna tayi
kasake tana kallonsu bata sanme ya faru b balle
tasan me zata ce musu. Hjyhindatu ce ta taso
tazo ta kama hannun hamma takawo ta tsakiyar
matan nan wadanda suka doshi su ashirin.
Hanna ta durkusa akan kafet ta gaishesuwata
kamillliyr datijuwa mai kyau ta dago da luhu-
luhun idanuwanta ta dubi hanna ta juya ta kalli
hjyhindtu tace ramlah wacece wannan? Tce
wannanitace hannar haism. Su duka suka bude
ido da bakisuka ce hanna, hanna ce wannan ina
kike nemota? Ta rushe da kuka tace har niger
naje na nemota saigba daya ka rushe da kuka.
Hanna ta kasa ganeabunda ake nufi, knta ya
daure abunya batamamaki. Tce meke faruwa, a
ina nake anan? Hajhindatu ta goge hawaye tace
hanna nan kano ne.Ta nuna wannan dattijuwar
matar tace wannan itace mahaifiyr haisam!
Hisam! Haisam haj hindatuta ce haism. Ta nuna
wannan saurayin tce wannanizziddin kanin
haisam ne, ni kuma ba sunana hjhindatu ba,
sunana ramlah nice matar hasamhanna ta
zabura ta mike tsaye tace ramlah, mekefaruwa,
me nayi miki? Ramlh ta jawo hannun hanna ta
zaunar da ita tace zuna hnna zan bki lbrnhism
ynxun nan, hanna ta koma ta zauna asanyaye ta
tattara hankalinta baki daya a
sauraronramlah,Ramlah ta sharbehawayen da
suka cika mata ido tace hanna, hisan,yana sonki,
haisam ne mai sonki, babu wani maisonki a
duniya irin hisam. Haisam yafi kowakaunarki a
cikin duk masu sonki a duniya hannatace ramlah
meyasa kika ce haka? Ramlah tace abunda yasa
nace haka shine haisam bai taba yinsoyayya ba
sai akanki, bai taba ganin wata 'yamace ba a
duniya da yaji yana sonta kamarkihanna, hanna
ta dago ta kalli ramlah tace ammahaisam ke ya
faraa kafin ma mu hdu dashi houryayi miki
alkawarin zai aureki. Ramlah ta girgiza kai tace
hiasam ya sanni tuntuni amma ba sona yakeba.
Allah ya jarabeni da tsananin son haisam
tunmuna america idan sunje hutu gidnmu.
Nashasanarwa mahaifiyata sai tace kada ma in
fara bazaiyiwu ba, saboda mhaifiyar haisam
kaawarta cetasha gaya mata cewa haisam bashi
da ra'ayin soyayya yace shi bai taba jin yana son
wata bakuma yana ganin bazai taba ji ba, har
muka dawokasar nan. Amma naki hakuria naci
gba da cusasoyayyar haisam a zucyata, na dinga
kokarinnunawa haisam irin soyayyar da nakeyi
masaamma sai yake nuna min baisan abunda
nake nufi ba. Da nag haka sai na dinga bin ta
hanyr iyayenmudon na sami haisam, da farko
mahaifina na samunasa masa kuka cewar in ba'a
bani haisam b xankashe kaina. Mahaifin ya
lallashe ni ya ce duk maisauki ne zi sami
mahaifin haisam. Haka kuwa akayimhaifina yaje
ya sami abokinsa mahaifin haisam ya shaida
masa bukatata. Sbd da sanin raa'ayinhaisam
akan soyayya bai amsa masa ki tsaye basida yace
zai tuntubi haisam zai kuma yi shawarada
mahaifiyar haisam kusan shekara guda
bamujiwata cikekkiyar msa ba daga gidansu
haisam to sainasan haisam yaki amincewa ne
yasa babu wata cikekkiyar amsa da naji game da
bukatata akannifa har yanxu ina son haisam,
babu irn kalmar damhaifina bai furta min b
wajen wayar min da kaiakan in cire son haisam,
in so msu sona ga sunnbarktai suna zuwa, naki
nace lallai-lallai sai haisam,Nazo nyi yjin ikin cin
binci naki ci naki sha naakaura daki sai kuka.
Iyayena suna ta lallashina nkicanj ra'yina. Shi
kuwa hisam bai san ma abindanakeyi ba, yn can
jami'a yana karatunsa. Kawrkirauda kanwata
nake aike da wasika in shaidwhaisam halin da
nake ciki amma bai taba bani amsar wasikata ba.
Ko dda naje gidansu bayacemin komai koda zamu
yini tare ko uffan bazaicemin ba. Haka idan yazo
gidanmu wajen auwalyayna abokinsaa idan muka
gaisa babu binda zaisake cemin ko hira nake
musu bai cika sa baki ba.D mahaifina yaga na
dmu sosai da son haisam shine ya sake samun
mahaifin haisam suka zaunasukayi magana sosai
mahaaifina y nunaa bacinransa yace b yadda
za'ayi suce haisam yakiamincewa tunda bashi ya
hifesu ba, susukahaifeshi in har suna so zasu san
yadda zasu sshi yaamince dole. Gudun kada
abokantarsu ta baci mahaifin hisam y kira
haisam yace ko yaki. Koh yaso is ya aureni, da
farko mahaifiyarsa taki tacebayayiwa a yiwa
namiji auren dole abarshi tundayce bashi da
ra'ayin soyayya gashi yanzun kara2yake a lkcn
yana shekararsa ta karshe a jami'a.Mahifiyar
hisam tag dai abun zai koma tashin hnkl tsakanin
ta da mahaifana da kuma mijinta sai taamince
tace ayi auren, taci gaba da lallaba haisamakan
ya yarda ya iya bikin. Da aka zo sa ranarauren yy
habib sai aka had damu. Aka sa ranaraurenmu
shera daya dai daii lkcn da haisam zaigama
bautar kasa ni kuma na gama sakandire sai ayi
bikin. Har lkcn da ka sa mana rana haisam
baitaba zuwa gidanmu ba da sunan yazo zance.
Nicekullum nake yi masa waya musamman da
tsakrdare. Yan amsa mun wayar amma wani lkc
sai yyibarcinsa m ya barni a layin wayar ina
magana nikadi. Hak a cikin hirarrakin da muke
akwai wasu tambayoyi da nake yi msa bi tba
amsa mun ba sidiyyi shiru. Tambyoyin kuwa shine
hisam ynxunkuw kana jin sona a zuciyarka?
Meyas baka zuwgidanmu znce? Idan ban ganka b
ko naji muryarkabana iya barci kaifa? Baya
amsamin duk watatambay data jibanci soyayya, n
sni kuma n gane haisam b sona yake ba kiri kiri
amma idona ya rufetunda ni ina sonsa zan iya
zama dashi a haka.Haisan yana bautar kasa.
FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama sai
ranar daurin aure a bda dasadaki in zama
matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya
kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala
butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba
ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu
daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda
lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi
mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin
cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi
shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin
zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan
yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da
yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya
dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki
ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na
sami wani na aura don shi kuma sai nan
dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga
jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren
kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata
zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da
zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai
wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana
sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa
bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC
london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can
london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin
nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki
ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen
haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa.
Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya
daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata
kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka
zuba mana ido Sai addu'a.Haisan yana bautar
kasa. FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama
sai ranar daurin aure a bda dasadaki in zama
matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya
kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala
butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba
ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu
daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda
lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi
mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin
cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi
shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin
zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan
yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da
yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya
dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki
ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na
sami wani na aura don shi kuma sai nan
dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga
jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren
kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata
zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da
zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai
wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana
sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa
bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC
london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can
london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin
nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki
ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen
haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa.
Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya
daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata
kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka
zuba mana ido Sai addu'a.Na shiga jami'a a nan
kano BUK ina karantar.Bangaran lbrn 'yan jarida
(mass com) ina Karatunaina jiran haisam na sami
samari kalakala akwaikyawawan da suka fi.
Haisan kyau nesa ba kusaba, akwai masuarzikin
da suka fi haisam, masusona fiye da haisan
amma. Na kisu ni sai haisam don bazan mant ba
har mahifiyt tke cemun zakiauri haisam in n
takura masa mma bazaki samisoyayyar da kike
nema ba. Nce idan anyi auren zaisoni ai. Nasa
kanwata rauda ta binciko. Mun wanneirin buri ne
haisam ya kudira a FGGC kazaure yakeso y cika
kamr ydda kullum ake cewa, rauda tace ai wata
yarinyace year jinsu mai suna hanna
yacekanwarsa ce tana jin sbd it yaki barin mkrntr
nasrauda taci gaba da lura d binda yake
gudanatsakanin hasam da hanna kuna ji 4 (ss1)
rauda tzomun da cikekken bayani game da
binciken danasata tayimun. Tace abu ya tabbata
haisan son hanna yakeyi,duk mkrt an sani zance
ya fito fili. Tabani lbrn irin gwagwarmayar da
akayi tsakaninhaisam da malai masu takurawa
hnna da dalbaimasu takura miki yaya habib ma
ya fada manayadda sukayi da haisam har hisam
ya wawaroadda kamar dabawa masa, yaya habib
yace haisam sai addu'a sbd kamar ya zautu a son
wata yrny donhaka nema yaki dawowa.Raina ya
baci sosai da naji nce haisam yana sonwta, na
lashi takobin ko wacece wannan hanna saina ga
krshent ko a ina take, shine nabi direban muda
zai dauko rauda ranar hutu don inga
wacecewannan hanna? Kuma 'yar waye? Dame
ta fini dahaisam yafi sonta dani? In kuma ja mata
kunne akan ta rabu da mijina, don alkcn yadda
nakeji zaniya hallaka duk wanda yake kokarin ya
rabani dahaisam, naje mkrt na tarat bakya nan
ance suhaisam sun tafi dake sai muka biki
garinku mukatarar bakya nan sai mahaifinki. Na
fadimagangannu iri iri a cikin bacin rai sbd
mahaifinki ya rabaki da mkrtr don ki rabu da
haisam, haisanbai bar kazaure ba is da kika gama
mkrt da sati 2snn ya dwo gida da kaynsa,
mahaifinsa na ganinsacewa yayi haisan har ka
cika burin daka kudira kadawo? Haisam yayi
murmushi yace eh baba,mahaifiyarsa tace idan
baka gama cikawa ba ka koma ka gama ka dawo
ramlah na jirnaka ayi bikinku, haisan yace ya
gama saidai kuma yazo wajensuneman alfarma
guda daya donAllah su taimakamasa , suk bukaci
haism daya fadi abunda yake soya fada inshaa
Allahu idan bta fi karfinsu ba zasuyimasa sai ya
zauna ya basu lbrn ki tas tun daga ranar da aka
kawo ki mkrt har halinda kike ciki agidanku, ya
kuma bayyana musu tsananin son dayake miki
yace su taimake shi su bashi izini yahadamu mu
2 ya aura sbd kece rywrsa zai iya shigawani hali
idan suka ki amincewa masa, bai rufebakinsa ba
mahaifinsa ya daka masa tsawa yace bazai yuba
karma ya sake yi musu wata magiya.Mahaifiyarsa
ma tace in har ita ta dauki cikins wata9 ta hifeshi
yasha nononta har ya girma to bataamince masa
ya auri hanna ba.Kwana 2 haisam ya kara
ramewa kullum kagnshi yana tunani kallo 1 zakyi
masa kasan yanacikin wani hali na tsananin
damuwa, ya daina ci yadaina sha balle yayi hira
da mutane mahaifinsa dayaga haka sai ya kira
shi yce yaje ya sameni yayimin bayani akan ko
zan yadda ya auremu mu 2 idan na mince to
zaije ya sami. Matarsa mahaifiyahaisam ya
lallashet ta yarje masa, haisam ya samenia
lambun gidan mu da yamma. Yake cewa
intaimakeshi in ceto rayuwarsa ya auremu mu 2
ni dake, na kekashe kasa nace ban yarda ba,
hism yadurkusa gwiwoynsa 2 a kasa yana rokona
ina duba girman Allah da tsknin iyayensa da
iyayenatun suna yar in barshi ya aureki yayi min
alkawarizaiyi adalci a tsakanin mu kawai don ya
ciro hannadaga cikin wahala ta dwo wajensa ba
don yafisonta ba a kaina. Mahaifansa sunce in
har naamince suma sun yarda ya aure mu mu 2.
Nace har abada bazan taba amincewa ba.
Hawaye ne yakezubowa daga idanuwan haisam
yana rokonaamma naki fur.Ramlah ta sharbe
hawaye tacigba da cewa.Bayan anyi hak haisam
ya hkr akyi bikinmu ranardaurin aure ma haisam
kuma yake ko. Bidiyo kasetan nuna babu abinda
zaka gani a idanuwanhaisam sai hawaye, anyi biki
an kaini gidana kowaya watse aka barni da
haism. Babu binda haisam yake saidai y zauna a
falo yayi shiru yan tunani saiinyi mgn sau gom
haisam baya sanin binda nakecewa yana can
yana tunani. Hira wannan ba mayida haisam
balle zncen wata soyayya. Ina alkunyaina
sharewa a matsayin na sabuwar amrya
baikamata in dinga binsa shi namiji bai bini ba.
To. In hour znyi sati ban shiga bangarens ba
bazaizo indanake ba, gaisuwa ce kawai take
hadani da haisam,bayan mun gaisa sai kllo da
ido ko abinci na kaimasa baya ci sai dai ruwan
shayi kwai yake sh, tunyan lekawa ofis wajen
aikinsa kmfanin babansaanan yake aiki harm ya
daina zuwa kwata kwata. Yaynsa habib yayi fdn
har ya gaji ya kyale shiabokansa gaba 1 mgn suke
meke damun hsam yacanja gaba 1 bay zuwa
wajensu babu. Walwalabayason yin mgn ko sunje
wajensa. Nim har wnnabu na haisam ya fara
damuwa, inyi wanka inacaba ado amma haisam
baisan nayi ba, is muyini a zaune haisam bai
dago ki ya klli fuskata ba balle yaga jan baki da
hodar dana shafa balle yaga fari daidon da nake
yi masa da kallon soyayyar da nakeyimsa, in
tkace miki. Munyi wta 4 cur da haisam. Hkko
hnnu n bai taba rikewa ba blle ya shiga dakina.Is
da abun ya isheni nayi yaji n tafi gidansu naje na
sami mahaifiyrrsa na shaida mata halinda muke
cikida haisam, ina kuka kamar xan mutu. T
lallashenitace in daina kuk muka tafi gidan ni da
ita mukasami haisam a zaune a flonsa. Kan
kujerar dayasaba zama yayi tagumi. Yana tunani
kamar ydda yasaba. Hjyr sa tayi masa fad sosai
ta shada masa gara ya ski jikinsa ya dwo da
walwalarsa zmansa danidram kuma har abada
baza ta yarje masa yaje yaauro wata hanna ba.
Bayn nan ne haism ya yardaya shiga daki na da
daddare wani babban takaici.Ma muna kwance
tre yana kirana da sunan hanna.Nayi fadan nayi
fushin saidai ya bani hkr yace mantawa yayi
gobe. Ma haka. Jikina ya fara sanyina fara sarewa
na fara fitar da rai akan smunsoyayyar haisam
yayi nisa sosai a fagen son hanna.Kullum sai ske
dulmiya yke a tunanin hannah,baya cn abincin
kirki ba'a hira dashi sidai gashi nanne kawi yana
kano amma zuciyarsa tan babbanmutum garinku.
Wasu lokutan da ymma yakn shigalambu yan
busa wani dan karfe dogo kamr naazurfa da nayi
bincke aka ce bun busrki ne akwai wsu tsakiyoyi.
Akwatinsa suma wasu lokutn yandauko su ya baz
a gdo da wani hoto tun. Kuna jjs 1ke da rauda
kanwat da nusaiba haisam natsakiyarku shim ya
kura ido yana kallo in takicemiki soyayya ta fr
zautar da haisam ni kuma inagefe ina son maso
wani, ni da dutse duk dya nake a cikin gidan. A
haka muka shekara da hisam saimuyi wta 3 snn
nake samu ya shiga dakina, tokoda ya shigo ma
ba farnta min zaiyi ba dagakarshe sunan hanna
zai dinga kirana. Nyi fad, nyiyji har na gaji haisan
bay tnkamin balle ya bini bikoidan nayi yaji, da
kaina nake zuw in dawo. Ban sami kulawar
haisam ba, bbu soyayyarsa. Akwaiabinci , ga kudi
da duk wani bu najin dadin duniyakatafaren gida,
galla-gallan motoci duk waccenakeso it xn shiga.
Mahifiyar haisam ce take yiminsutura. Ba'a yin
wata gud is ta aiko min da dinkunahaka
mahaifinsa ya budemin account. Banki yana
turomin da kudi, yay hbib duk wata yake
siyominkyn abinci komai da komai. Mahaifana
knsu dakafarsu kudi suke bani suna kara rokona
inci gabada hkrn zma da mjina tunda ni nace nji
n gani inasonsa haka. Amma dukka gatn da
surukaina sukeyimin da iyayena duk a banza ne
ba dadin rywta nkeji b tund na rasa soyyyar
mijina. Kowa ya rsakan haisam an rasa yadd za'a
kamo bakin zrenbare a ware mana matsalar mu.
Wani lkcmahaifiyata t kirani take shwarta ta ko
zan hkr dawnn aure inzo in auri mai sona shima
yaje ya aurowacce yakeso nace I ni ko da xan
mutu gara inci gab da zama da haisam a haka
sbd tsananin son danake yi masa.Haka nci gba da
zam d hisam, kullum a cikintunani yake hour
zuciyarsa ta samu matsala yakwanta ciwo likitoci
suka ce lallai lallai haisam yancikin mtsananciyar
damuwa ta tunani da kunci dolea dinga kwantar
masa da hnkl don har zuciyrsa takamu da ciwo
sbd damuw, bamu Da maganin wannan matsalar
ta haisam sbd kece maganintsananin sonki shi
yke damunsa. Don haka ciwonhaism yaci gaba da
yaduwa kusan kullum a asibitihaisam yake daya
ya dawo gida sai ciwo ya tashi amayar dashi
asibiti haisam ya rame yayi duhu abintusayi.
Wani abin mamaki a karkashin filonsa na asibiti
abun busrki ne da tskiyoyinki yke ywo
dasu.Likitoci sunyi sunyi da haisam ya rage
damuwa sbdsamun lfyr zuciyrsa abu ya faskara.
Akwai lkcn dahisam yayi wta 2 a kwanace premier
clinic jikinbabu sauki saida aka mayar dashi
aminu kanoteaching hospital amma in yanzu kaga
haisam zaka dauka kafin ka fita bakin kofar dakin
zi mutu sbdtsananin jin jiki da yake. Numfaninsa
sama samadakyar abun tausayi,Hanna ta rushe
da kuka gaba 1 wajen sai akafara hawaye, ramlah
ma hawayen da take ya karakaruwa. Taci gaba
da cewa nafi kow sanintakamaimai maye ke
damun haisam ina ta zarginkaina nice silr
wannan ciwon na haisam tunda nicena raba shi
da abar kaunars. Da naga haka sai na yankewa
kaina shawarar kawai in shiga gari dukinda
hannah take inje in nemo wa haisam sbd
itacekadai soyayyar da xan nunawa haisam
amatsayina na mai tsananin sonsa banason in
rrasashi gaba 1, gara na nemo msa maganin
wannanciwo da yaki warkewa fiye da shekara 1
yana fama. Ban bari kowa ya sani ba, bn
shawarci kowa ba nashirya tsaf da kayana da
guzurina da direbana nashirya fita neman hanna,
na yiwa surukaina daiyayena sallam akan zanje
kd gidan wata kawatada mijinta ya rasu inyi mata
ta'aziya kwana 2 kawizanyi, mahaifiyata ta nemi
ta hanani tfy sbd ga jikin haisam yayi tsanani
yana kwance a asibiti yaya za'yiince xanyi
bulaguro duk da ma dai bani bace nakezaman
jinyarsa kaninsaa ne izziddin damahaifiyarsa ai is
suga ban damu dashi ba harkatama na tafi,
nasan hakan data fada gsky ne baikamata in tafin
ba amma nace ni dai zanje ba dadewa zanyi ba.
Tayimin fatan Allah ya kiyayehanya sai na dawo
na tafi.Kowa ya gyara zama dan yaji ci lbr cike da
mmkda tausayin ramlah kowa ya zuba mata ido
yanakllo musamman hanna. A zuciyata cewa tke
waishin ko mafarki nake ne bad gaske bane ni
ramlahta nemowa haisam, yi zanga haisam
kenan? IkonAllah, Allah mai girma, Allah na gode
maka, ko bazan auri haisam ba in ganshi ma
nagode waAllah. Ramlah taci gaba da cewa
"babban mutumgarinku na nufa na rasa gidan
naku ma sai damuka yi tambaya don bn manta
sunan mahaifinkiba mallam habu, nace yana da
ya hanna wata farakamar da farko basu gane ki
ba da hnne suka fi sanin ki ashe ko yar baba
nace kece sannan akakaimu gidn naku she
mahifinki ma ya rasu? Hannata gyada kai tace
yafi shekaru 2 ma da rasuwa.Ramlah tace Allah
ya jikansa. Mahaifiyar haisambabu abinda take
iya cewa sai kuka kawai takeyikamar ranta zai fita
mahaifiyar ramlah ce take rike da ita tana lallashi
itam kuka take. Ramlah tace saimatar babanki
muka iske take cemin suma basusan inda kike
ba, kanin mahaifiyar yazo ya duke kitun bayan
rasuwar mahaifinki kun tafi ksarsuniger. Na
tambaya wani nigertace Dashi sunangarin muka
kwana sannan muka nufi garin Dashi. Na dan sha
wuya kfin nagano inda kike. Munyikwana 2. Gidan
wni bawan Allah a grin muna yiwamatansa
kwatance sai can daya daga cikin matantace hnna
matr marigyi bello mdu custom. Nacemijinta ya
rasu ne? Sukace ya rasu harta fita dagatkaba, naji
dadi da sukace a ynxu baki da miji don zan iya
tahowa dake, to amma yaya zanyi gashibaki
sanni ba yan wanki da yanuwn mijinki ba
zasubari in taho da ke ba, na tambaye su
'ya'yankinawa yanxu? Suka ce baki taba haihuwa
b watankibakwai d aure mijinki ya rasu ya barki,
sai kawai natuno wata dabara nace to tunda
mijinki ya rasu bari ince daga gwamnatin jihar
kano matar gwamna taaikoni don in kafa wata
kungiya da za'a tallafawamatan da mazajensu
suka rasu suka barsu damarayin 'ya'ya. Haka
kuwa akayi nasa aka rakanifadar maigari Ni da
direbana muka hada bkimukace tare aka turo
mu. Dajin hak mi gri da jam'ar gari yasa akyi
shela aka tar mana matan da mzansusuka rasu
suka brsu. Kallo 1 nayimiki na gane. Ki,sbd na
sanki a hotuna a wajen raudah kanwata tunkun
aji 1 har aji 6. Tund nasan kin iya rubutusauran
basu iya ba, nace to wacece tazo ta rubutasunan
ta basu iya ba, nace to wacce ta iya tazo t ding
rubutawa suka nun ku kika zo kika rubuta.Na
babbaku taimakon da zn baku sannan nacetunda
kin iya rubutu to ke zki dinga wakiltar sukina
karbomusu taimako dga kano na nemi d kibiyoni
kano, naci sa' kuwa 'yanuwanki sukaamince kika
biyoni, don kawai in kawo ki wajen
haisam.Wannan karon hann murmushi ne y kece
matasbd tsananin farin ciki. Ta sake tattara
hankalintawajen rmlh tana suaronta. Ramlah ta
cigaba dahawaye tace hanna gaki a tsakiyar
faalon gidanhaisam don kece kadai mganin da
zaisa haisam yawarke daga wannan
matsannancin ciwon zuciyar da yake fama dashi
"ta sharbe hawaye tci gba dacewa Haisam ya sha
wuy hanna a sanadiyyartsananin sonki, haisam
ya rasa walwala a rywr sa asanadiyyr tsananin
sonki. Haisam mi kaunar ki nefiye da duk wani
mai sonki a duniya. Sai yu hnnataji amsar wnn
klmomi data dde tan nemn dalilin da ke cewa
haism yafi kowa sonta a duniya. Mahaifintane y
fara fada mata, Bello madu ya fada mata
haka,snn ramlh ta fad mata. Lallai na yarda
haisam yafikowa sona. Hanna take fada a
zuciyarta. Ramlah tasake rushewa da kuka mai
tsanani tace ban barshikuma ya auri wacce yke
so ba. Hanna ta matso na rungume ramlah tana
lallashinta tana bata hjr itamakukan tkeyi, ramlah
tace hanna dole nayi kukadole na dauwama a
cikin bakin ciki har karrshenryw ta sbd halin
wahala da bakin ciki dana jefahaism na cuceshi
na cuci kaina. Hanna tce antyramlah daina cewa
haka Allah ya rubuto sai anyi haka amma bake
kikasa haka ta faru ba, ramlah tadago kalli hanna
tace haisam ya sha wuya, kullumyan tunani
kamar ya zautu don wni lokaci sai kagayayi
murmushi yace hanna kenan tsananin tunaninki
da yakeyi. Ni dai ina tare da GANGAR
JIKINhaisam ne amma zuciyarsa na wajenki.
Ramlah ta sake rushewa da kuka tce GANGAR
JIKINSA NAAURA zuciyarsa na wajenki hanna. Ke
kadai cemaganin ciwon nan na haisam hanna
kece kawaizai gani ya warke.Hanna tasa hannu
tana gogewa ramlah hawayecan cikin zuciyarta
kuma cike take da farinciki datadade bataji irinsa
ba cikin sanyin murya tace yanzuina yaya haisam
din yake, ku kaini in ga jikin nasa.Gaba daya
falon suka dauki kuka mai tsummazuciya. Hanna
cike da mamakin meyasa suka sake rushewa da
kuka kuma. Hnna ta dubi Ramlah tacelfy kuka
sake rushewa da kuka? Ramlah ta dafakafadar
hanna tace hanna saidai kiyi hkr Allahyayiwa
haism rasuwa jiya yya habib yayo waya.Zasu taho
d gawar a yau da daddare zasu iso.Hanna ta
zabura ta mike tsaye yayin da zuciyarta ta far
dukan 3 3 kanta ya fara sarawa kamar zai
fasheta dora hannu aka yayin da jiri ya dauke ta
ta komata zauna, ramlah ta riketa. Izzidin kanin
haisam neya katse hanna daga tunanin da take
ciki yazogabanta ya durkusa yana mai tsananin
kuka dahawaye yace ni nake jinyarsa yace min
duk ranar dana ganki na baki wannan. Ya mikowa
hannatsakiyoyinta da abun busarta. Cikin snyin
jiki tasaahnnu ta karba tana jujjuyawa ta gansu gr
dasukamar yau ya karba daga wajenta. Sai ta
tuno ranarda aka kai ta makaranta tan zaune
akan akwati,haisam n kn benci yana mata
tambayoyi har ya krbi wadnnn tsakiyoyin, sai
hawye ya dinga digowadaga idanuwanta.izzidin
ya ce bayan tfyr ramlahjikin yaya haisam ya rikice
sosai har aman jiniyakeyi. Ashe yaya habib yana
ta cuku cuku zai fitadashi turai. Bayan tafiyar
ramlah da kwana 2 yayahabib ya tafi dashi
londonRanar da suka isa da daddare Allah yayi
ikonsayaya haisam ya rasu. Gingirim hanna ta
tsaya tanakallon izzidin tamkar wata gunki. Izzidin
yaci gabada cewa yaya habib yn kuka yayi waya
yace yau dadaddare gashi nan zai juyo da gawar
haisam shinewannan taron da kika gani ana jiran
isowar su muke. Kiyi hkr hanna haka Allah ya
rubuta miki.Haisam yasha wuya a sandiyar sonki.
Kowa yayishiru ba abinda kakeji a falon sai sautin
shesshekarkuka kowa keyi. Can hanna ta rushe
da kuka tanacewa Innalillahi da inna ilaihir raji'un
haka Allah yarubuta min haka Allah yaso ya ganni
nagode wa Allah. Yanxu babu babana, babu
mijina bello madu,babu haisam din da nake sa
ran xan ganshi dukdaran dadewa. Hanna ta rusa
kuka tana bada lbrnrywr ta tun ranar da
mahaifinta ya kaita mkrnt sukagamu da haisam
har izuwa aurenta da bello madu,har izuwa rana
irin ta yau da aka bata lbrn mutuwar haisam.
Tace ta dauka ita kadai kehaukarta Haisam yana
can da matarsa ya manta daita tunda yace ya
cika burin daya kudira akai nainyi karatu ya dawo
gida yanzun zai cika alkawarindaya dauka. Sai na
dauka haisam ya manta da watahanna ashe ina
nan like a ransa. Hanna kuka wiwi
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 3
Posted by ANaM Dorayi on 04:41 PM, 30-Apr-15
Under: Gangarjikinsa ta Aura
Jama'ar dake cike a falon iyayensa da
iyayenramlah danginsa da dangin ramlah da
makabtaduk sukaji tausayin hanna fiye da kansu
da kansu.Hanna ke akayi wa mutuwa.inji
mahaifiyar haisamyace min hjy ku barni na auri
hanna, hjy hanna ceryw ta amma naki fur ashe
kuwa da gaske yake gashi yanxun babu shi ina
ma yana da rai yazoyaga hanna, sai duk falon
aka dauki kuka gabadaya.Hanna ta kankame
tsakiyoyinta da abun busarta acikin gyalenta ta
mike ta dakyar tana hadahanya tana tafiya
dakyar ta nufi wani daki ashedakin haisam ne,
can lungu gado ta shige tayizauna yayin da
idanunwanta suka fada kan wanikaton hoton
haisam dake like a jikin bangon dakin yyi kyau
sosai yana dariya a hoton. Taji gabanta yayanke
ya fadi ta kurawa hoton ido kem yayin dataji wani
ruwa dga hancinta yana zurara ta cikinkanta
numfashin ta na kokarin dauke mata abundazata
iya tunawa kenan , ashe suma tayi,
Amratukanwar haisam aka turo dakin tazo taga
wanni hali hanna take ciki karta nemi ta halaka
kanta. Saikuwa tazo ta ganta ta jingine a lungun
gado azaune ido babu baki sai fari ta kafe.
Amratu takwalla ihu sai duk aka shigo aka tara
hanna cikinwannan hali. Ba'ayi wata wata ba aka
daukota anasalati aka yayyafa mata ruwa ta
farfado.Tana bude ido taga dandazon jama'a har
sunfina dazu mata da maza an idar da sallah
magaribaan sake taruwa ana jiran isowar gawar
haisam.Kofar gida cike yake taf da maza. Hanna
tayi salatita tashi ta zauna tana tunanin a ina
take ko daimafarkin ne, amma ta murtsike idon
ta goge ruwan dake fuskrta taga zahiri ne ba
mafarki bane haisamya rasu , ya rasu da gaske
ne. Hanna taji sai sannuakeyi mata yayin da taji
wasu na tambaya itacehanna? Wannan ce hanna?
Wadanda suka zoyanzu kenan. Hanna tace a
zuciyarta wato kowama ya sanni kenan kamar
yadda nima acan duk wanda ya sanni yasan
haisam,KARSHE Hanna ta matsa kusa da
mahaifiyar haisam ta zaunasai taji mahaifiyr
haisam tasa hnnu ta goge matahawaye, tace
mata hanna yi hkr Allah ya kaddarahaka fatana
ki din da yiwa Haisam addu'a kinji ko,Allah ya
jikansa ya gafrta masa. Allah ya hadaki damai
sonki fiye da gafrta masa. Allah ya hadki da mai
sonki fiye da yadda haisam yake sonki. Hanna
tagirgiza kai tace har abada ba'yi ba, baza ayi
bakuma hjy, na rasa mai sona nima na rasa
wandanakeso. Sai su duka suka rushe da kuka.
Kanhanna akn cinyar mahaifiyr haisam tana
kukakamar ta shiga cikinta don tsananin son da
taji tana yi mata tamkar haisam tunda ita ta haifi
haisam. Itamahaifiyar haisam ta dafa knta jin
hanna taketamkar haisan ita tunda haisam na
son hanna itamaharga Allah taji hanna ta shiga
ranta. Amma aikingamaa ya gama haisan din
daya hada ya tafi yabarsu, Can Hanna ta dago
tace zanje inyi sallar mgariba?Hjy haisam tace eh
jeki kiyi. Hanna ta mike dakyarga tsananin
faduwar gaba da ciwon kai, ita kantabazata iya
musulta yadda takeji a wannan rana ba.Ta shiga
dakin ta kalli wajen da hoton haisam yakemanne
taga an cire shi sai ta wuce ta shiga bandaki ta
dauro alwalla tazo ta fara sallah. Bayan ta idar
dasallar magariba ta tashi ta fara jero nafiloli sai
tajigaba daya an dau salati tun daga yan kofar
gidahar matan dake falo sai taji ana cewa sun
iso, an isoda gawar. Tana tsaye tan sallah sai taji
ta sulmuye tazauna kafarta ta kasa daukarta
gbanta ya yanke ya fadi. Taji duk tsikar jikinta
tana tashi, kukan da yakizuwa dazu ya kece mata
tamkar ranta zai fita. Cantaji salatin da akeyi ya
lafa sai ta rike bango ta tashitsaye dakyar don ta
fita falon taje taga gawr abunkaunarta don idan
taga fuskarsa yanzu ita ce kadaizata dinga
tunawa har karshen rayuwarta. Duk dama taji a
jikinta itama ba dadewa zata yi ba aduniya zata
bi haisam dinta. Tunda damuwa datunani ne ya
kashe haisam a shekara 2 ita yanzuyadda takeji
ya linka yadda haisam yakeji don hakazuciyarta ta
iya fashewa a wata 3 ta mutu ta huta.Tana tafiy
a hankali don karta fadi.har ta fita daga dakin,
tana fitowa taga gaba daya daruruwanmutanen
da suke zazzaune a falon sun juyo sunakallonta
gaba dayansu. Idonta ya dira akan watafuska
wacce take tunanin ba gaskiya take gani bagizo
ne. Kash!! Anan zan dakata mu hadu aGANGAR
JIKINSA TA AURALittafi na 3 Naku ANaM
Dorayi,Nagode da karfafamin gwiwan da kukeyi,
Allah yabani ikon kammala 3 kamar yanda na
kammala 1en 2...Bye!
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
0 Comments