ads:::

GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 1

GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 1 Posted by ANaM Dorayi on 02:56 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Hatta iya abu data tsani hanna yau hanna ta batatausayi matuka sai ta rushe da kuka ta dinga rikehanna tana lallashinta. Da kyar matan nan suka iyabanbare hanna daga kan shimfidar mahaifintasuka shiga da ita cikin gida. Hanna tana rusa kukakamar rabta zai fita amma ta nemi hawaye ta rasa. Sai tayi shiru ta shiga dakinta ta kwanta ita damahaliccinta ne kadai tasan me takeji a ranta waniabune ya tokare mata zuciya kamar dutse abun yafikarfin kuka. Hanna ta kalli gabas da yamma kududa arewa taga babu wani mai fitar da ita dagatsananin bakin ciki nan da take ciki sai allah . Ta tuno nasihohin da haisam yayi mata aranarkarshen da ya rakasu tasha sai tasa hannu ajakarta ta lalubo carbi ta fara ja. Addu'oi iri iri hannako magana ta daina yi, yan gaisuwa a jere a jeresuna shigowa dakinta suna yi mata gaisuwa sai daikawai ta bisu da kallo har sha.awa take idan taga masu kuka da hawaye. Don ita kukan ma takenema ido rufe tayi ko taji sanyi a ranta ta kasa sallace kawai take fito da hanna tsakar gida sai kumaasuba take shiga bandaki tayi wanka.Banda wannan babu abinda hanna take yi sailazumi. Babu ci ba sha sai da aka ga kwana da kwanaki hanna taki cin abinci sannan su iya salmaisuke dama dan farau farau suka tsaya tsayin dakaakanta suka ce sai tasha kurba kawai take badondadi ba ji take kamar madaci suka dura mata donrashin jin dadin bakinta da take ji anyi sadakarbakwai kowa ya watse gida ya zama daga hannah sai iya abu . Yayanta ma suk sunyi aure kowacce takomagidan mijinta sai mutuwa ta dawowa hannasabuwa fil sai a yanzu ne ta fara samun zubar dahawaye . Kullum hanna kuka take rusa ita kadai adaki babu mai lallashinta kaico hanna. Sati daya satibayu iya abu ta gaji da ciyar da hanna, ayau da sassafe shida da rabi iya abu tazo ta fara bugawahanna kofa kamar zata karya kyauren hanna nakishingide akan abun salla tun asuba bayan tayisalla ta zauna jan carbi gyangyadi ya dauketakamar a mafarki take jin bugun kofar tayi firgigit tabude ido taga ba mafarki take yiba ta zabura da sauri taje ta bude kofar. Iya abu ta gani a tsaye takama tsantsan tayi kalar rashin mutunci. Hanna tajigabanta ya yanke ya fadi tasan rashin mutuncin yamotsa yau kuma sai yadda allah yayi da ita.tace'' hanna a to an gaba hada hadar mutuwa nayina allah nayi na annabi na ciyar dake a aljihuna har sati bayu. Ga rogo can n aika a siyomin zan dafa infara zuwa kasuwa ina siyarwa don nima dan kudincefanen hannuna ya kare ubanki bakar dawakadai ya bar mana a rumbu don haka ke kincikashinki saura ta zama kashin 'ya'yana zan ringasiyar da rogo ina samun na cefane ina tuka dawata, daga yau ki fara ziyar da kanki kafin a raba gadogama sunce sai na fita takaba kar kice daman bangaya miki ba dan kar in ajiye tuwan dumame nekizo ki gutsira mun tuwo in kuwa kika sake kikagutsirar mun sai na shakeki sai kin amayo shi.Hanna ta sunkuyar da kai kasa hawaye ya zubo shar tace'' to naji'' iya abu ta tafi ta barta anan atsaye kamar an kafata ta rasa mafita kuma. Hanna ta kasance tana kwana da yunwa sai ruwada take dirka wai ko iya abu taji tausayinta ta dingabata dan tuwo amma taga makatau, sai ta shirya tanufi gidan malam uba kanin mahaifinta ta shaidanasa cewar yanzu bata da abunda zata ci ko zaiajiye mata kwano a gidansa ta dinga zuwa tana daukar abinci ko da sau daya ne a rana ? Yanabudar bakinsa sai yace mata daman ta girma ta rikawai ita yar boko ga irinta nan abincin da zata ci yagagareta shi dai shawara daya da yaga ta dacetunda duk samarin garin suna tsoron zuwawajenta suce suna sonta ganin ita 'yar boko ce to ta yarda yayi wa alhaji bilya mai kudin garin nanmagana yazo ya aureta, zata fi karfin abinci don hartuwan shinkafa dafawa akeyi a gidansa dadaddare. Wani daci ya disu a zucitar hanna da tajibayanin kanin mahaifinta. Alhaji bilya da yakemagana wani shirgegen tsohon mutum ne matan sa uku yaya kuwa sun doshi talatin da yawaiyayensu basa gidan kuma jikokinsa ma sa'annintane, manomine ba laifi yana samu a dai garin shi maikudi ne amma ai tana zuwa gidan ada wajenkawayenta tasan yadda yanayin gidan . Watakatuwar tukunya ake dorawa a gidan kamar ta yan makaranta girki ma kadai ya ishi matan baya gadukan mata da yake yi yana da ciwon kuturtakuma harma ta fara fitowa hannunsa da bakinsazaka kalla kasan kuturu ne yatsun ne kawai basugama guntulewa ba amma sun fara diwa. Hanna tatabbatar lallai baba uba ba sonta yake yiba tunda zai hadata da alh bilya aure. Tayi shiru a durkushe agaban malam uba tana jin bayanan da yake matayace'' kin amince inje in sanar masa ko kuma kinada magana kiyi.Hanna ta nisa ta sunkuyar da kai kasa tace'' bababana kin jin maganarka bane ko naki yarda alh bilya fa kasan halinda yake ciki yana da lalurarkuturta. Baba yanzu zaka yarda in aureshi a haka?Malam uba ya fusata ya zabura hanna da fada'' kekinfi sauran matan zane ne, asirinsu a rufe ko goyashi zaki yi kina yawo dashi? Kuma shi da kansa yasameni yace yana sonki zai aureki. Nake jira daman a gama zaman makokin nan in shaida miki. Tundakinki sai ki tafi ki nemo abinda zaki dinga ciigardiya dake kinki aure babu mai ciyar dake, tashiki tafi bani waje mutuniyar banza. Hanna ta tashisumi sumi ta fice tana sharba hawaye. Tana fita tanufi makarantar boko, ta kuwa ci sa'a ta sami alhaji wani ma'aikacin da yake zuwa daga local gov'nt tarubuta takardar neman aiki[application]tun tuni zainemar mata aikin koyarwa a primary garin.Hanna cike da fara'a da murna tazo ta duekusahar kasa ta gaishe da alhaji ya amsa. Tun ma kafintace masa komai yace''hanna na kai takardarneman aikinki wajen manyana alhamdulillahkansilan garin nan ya gani ta sa hannu an kaiofishin sacretary'' murna ta rufe hanna yaci gaba da cewa'' to amma abunda sakatare yace shine bazasu iya daukarki aiki ba saboda akwai wadatattunmalamai a wannan makaranta akwai daimakarantun da aka rurrubuta za'a kara ma'aikataamma daman banda garin nan don haka sai daikiyi hakuri. Hanna taji ba dadi hankalinta ya tashi tace'' yanzu malam alhaji ko share share baza adauke ni ba ko a can local govnt din? Ya ce shareshare ai kinfi karfin yin shara hanna kije dai kicigaba da addu'a , na manta ma ban fada miki ba natambaya ance result dinku na jarabawa yafito amma an rike na f.g.g.c kazaure saboda kunyi matukar ci sosai wai har da masu nine distinctionkinga dole aki sakin sakamakon sai anyikyakykyawan bincike anga ko an baku amsa ne.Hanna tace'' binciken zai dadae ne? Ya ce''gaskiyairn wannan yana daukar kusan shekara ma ba'asaki ba. Amma daman da da result dinki a hannu da tuni na samar miki aiki ko ba'a garin nan ba.Hanna ta dade a tsugunne a gaban alhaji tayi shiruta rasa yadda zata yi can ta yunkura zata mikedakyar saboda jikinta yayi sanyi sai alhaji ya mikomata yan kudi yace'' gashi kya dan kashe'' dadi yalullubeta ta sami na cin abinci don yunwa take ji. Tayi masa godiya ta nufi gidan iya salmai . Ta isketaa zaure ta kasa zogale tana zaune tana jiran masusaya hanna tayi sallama ta shiga, bayan sun gaisaiya salmai ta ce'' hanna lafiyar ki kalau kuwa kinburkice gaba daya kamar ba keba? Hanna tayimurmushin karfin hali ta ce''iya yunwa nake ji ko da sauran dumame'' tace''wada na ajiyewa ya tafokwallo, rabonki ne zuba kici, da sauri hanna tamike ta nufi kicin don ta zubo tuwan. Iya salmai tabita da kallo, cike da tausayinta. Sharkab tana kukahanna ta fito ya sami iya salmai tana cewa allahsarki habu ka mutu kanar yarinya marainiya a duniya kaine daman gatanta'' hanna ta zauna asanyaye tana cin tuwan su duka hawaye suke yi.Iya salmai na tausayinta itama hanna na tausayinkanta. Bayan taci ta koshi tasha ruwa taje ta ajiyekwanon a cikin gida ta wanke hannunta sannantazo ta zauna ta shaidawa iya salmai halin da take ciki ta ce kuma tana neman alfarma idan da hali iyasalmai ta ajiye mata kwanan tuwo a gidanta tanaaika mata iya salmai taji dadi kwarai da hanna batayi kauron baki ba tazo ta sanar mata da wuri taceinsha . Allahu kome taci da kashin hanna to ammaitama ba kullum suke dora tukunya sau uku a rana ba.Itama ba da ko ta agareta ba bishiyoyin zogalene burjik a shuke a gidanta. Ta tsinka ta dafa tasayar ko azo a tsinka a danye a biyata. Daga ita saiwada wani dan kanwarta data rasu ta barshi tunranar da aka haifeshi ta dauke shi. Shima yanakokari ya samo kudi, to da haka suke cin abincin, ranar da ba'a samu ba su sayi na siyarwa ko suhakura idan babu kudin sayan na sayarwa. Iyasalmai tace'' ai idan naga 'ya'yan Habu raina dadiyake yi, ba don habu yana dan uwana bamasoyayyar da nake yi masa ce Hanna har yau ina jindandanonta a raina'' hanna tayi shiru tana tunani a ranta tana kuma tausayawa kanta cewar'' in har iyaSalmai bata daina jin dandanin soyayyar da takeyiwa mahaifinta ba har yanzu shekararsu tafiashirin da biyar da rabuwa gashi kuma ma har yamutu rana zancen sonsa ashe har abada iya Salmaibaza ta daina jin dandanon son nanba. To itama tana kyautata zaton haka zata kasance da donHaisam tunda gashi dai yanzu bata ganinsa yayiaurensa ma amma sai kara jin tana kara sonsa takeashe itama haka zata dauwama kenan har karshenrayuwarta. Soyayya gaskiya ce'' Hanna ta fadaabaiyane. Iya salmai tace'' soyayya gaskiya ce Hanna. Haka dai suka yini suna hira hanna ce tadafa musu abincin dare suka ci sannan suka yisallama Hanna ta tafi gida. Sun rabu akan iya Salmaizata ringa turo wada yana kawo mata abinci duksanda suka sami damar dafawa. Haka hanna ta kasance duk sanda iya salmai tadafa abinci ta aiko mata taci ranar da itama batadafa ba haka hanna take zama da yunwa. Ta ramekurkut da ita sai ido da dogon hanci tayi duhukuma saboda tsaban wahala da tsananin tunani .Ranar da iya abu ta fita takaba sai maigari ya hado malaman garin da masu fada aji na garin da yanuwan malam Habu don raba gadonsa ga iyalansa.A zauren gidan aka zazzauna ga iya abu gayayanta kakaf mata da maza ga hanna a gefe.Itama da iya salmai. Maigari yace'' a karantawamamacin kulhuwallahu kafa uku uku, da inna a'adaina kalkausar uku uku aka shafa Allah yakaikabarinsa. Sai maigari ya fara da cewa'' malamHabu ya rasu yabar mace daya da yaya takwas.Dukiyarsa kuwa wannan gidan ne da kumakatuwar gona. Amma tun ranar daya mutu akabiya masa basussuka da ake binsa da dan kudin daya bari. Ga manyan malamai nan zasu raba gado.Ga sunayen 'yayan nan a wajensu zasu shiga cikingidan su tsatstsaga su bawa kowa nasa bangaren.Iya abu ta nisa tace ina da magana nidai nicematarsa uwar yayansa kuma bare daya ce Hannedon haka a tabbata an bata bangarenta daban kar a saka min ita cikin kason 'yayana azo ana rigima.Maigari yace'' ai abu rabon gado ba'a cewa bareAllah ne ya raba da kansa don haka duk yadda takama haka za'ayi. Malamai sun yi iya kokarinsu sunkacaccala dan mitsitsin gidan nan d gona. Allahcikin ikonsa hanna bata tashi da komai ba sai rumbun ajiyar abinci,wani dam mitsitsine kasace turmus a kasan da gidan tururuwa sai dan wanibangare karami a tsakar gida shine kashin hanna agona kuwa bata ciki. Murna ta lullube iya abu gonada gaba daya dakunan gidan nata ne da yayanta sai tace'' wannan rabo yayi daidai to yanzu ta tashidaga dakin nan'' mai gari yace haba abu har yanzutsangwamar da kike yiwa hanne baki bari ba harmahaifinta ya mutu bakya rangwama mata ba''iyaabu tace a'a babu wani rangwame yan haya zansaa sauran dakunan ina karbar kudi wannan abu ne fa na gado. Nan fa duk suka hadu suna ta bawa iyaAbu hakuri ta barHanna taci gaba da zama a dakinda take har Allah ya yanke mata wannan zamatunda komai dadewa aure zata yi. Iya Abu takekashe idanuwanta ta ce in anga ta yadda Hannayauta sake kwana cikin dakin nan nata to ta bata kudin haya ne a matsayin tana haya.A cikin mutanen dake wajen harda Alh bilya ya ceto tunda Abu tace haka shi yayi alkawari zai dingabiyawa Hanne kudin haya daga yau ya tambayiAbu ko nawa ne kudin hayar dakin da hanne keciki ta kai kaice ta zambada kudi ya zaro ya biya ba tare da ya nemi ragi ba, ya biya na shekara ya saniya abu kora da hali take yiwa Hanne ta zambadakudi dan ace yayi tsada a kama mata a wani gidacikin ikon Allah sai taga ya biya.Mai gari da sauran mutanen dake wajen suka dingashiwa Alh bilya albarka, Hanne ita da baba Uba ne kadai suka san manufar Alh Bilya shi a nufinsaauren hanna zaiyi shi yasa ya fara mata hidima,wani gululun bakin ciki ne ya dira a zuciyar Hannamusamman da ya biya mata kudin haya ta san lallaida gaske yake auren nata yake so yayi ita ko garaa kasheta da a daura mata aure da wannan mutumin kamar tace bata son kudin hayar baza tazauna a gidan ba karya biya sai tayi tunanin in bagidan uban nata ba a ina zata zauna saita hakurakawai tayi shiru idan tace zata koma gidan iyaSalmai to ai daki daya ne kacal a gidan dan karamiita da wada suke kwana a dakin ba zaiyu ita ta hadu da Wada a daki daya ba saboda yanzu Wadashekararsa goma sha takwas yama girme ta dashekara daya don haka ya haramta su cusu a dakidaya bayan nan babu gidan wanda zata iya zuwata zauna duk danginta.Da daddare bayan kowa ya shige bacci ya kwanta hanna na juyi a yar katifar ta kasa bacci tsananinbakin ciki ne ya dameta a ranta bau abinda takenanatawa a ranta sai zancen hayar na. Ita da gidanubanta yau ta zama 'yar haya sai ta rushe da kukahar ta gaji. Tace''Allah kana ji, kuma kana ganina,kana kuma sane da irin abubuwan bakin cikin da nake gani tun ranar da mahaifiyata ta sakoni aduniya Allah ka fitar dani. Kaine gatana ya sarkinsarakuna. A haka Hanna ta kasance har shekaraguda da rasuwar mahaifinta. Yau taci abinci gobe tarasa wannan bai dameta ba sosai irin zurga zurgarda Alh Bilya yake yi a danginta yana cewa shifa yana so ya aureta. Dan har yaje ya sanarwa damaigari. Maigari yasa aka kira Hanna fada ya shaidamata abunda Alh Bilya yake nema a wajenta shin taamince zata aureshi, ta yarda tana so a dauraauren ? Hanna ta fito gar da gar ta fadi gaskiyatace'' ranka ya dade banki jin shawarar da ka bani ba amma dan Allah ina so a barni haka bana so inauri kowa. Gaba daya aka dau salati aka fara yiwaHanna ''cari to ba'a garin nan ba. Duk garin nanwacece ta taba kaiwa shekara goma sha takwas baa yi mata auren fari ba? Hanna tace'' ba zan iyaauren Alh Bilya ba a matsayinsa na mahaifina dan ni tamkar mahaifi yake a wajena. To haka akayi daHanna a fada. Alh bilya yaji haushin Hanna data kiyarda amma yasan tuggun da zai tafka mata yarama.Bayan anyi haka da hanna a fadar maigari dakwana uku. Alh bilya yazo har cikin gidan su hanna da rana tsaka . Hanna na daki a kwance tanajin yunwa tana jiran a kawo mata abinci daga gidaniya salmai tana fargabar ko suma basu yi abincin bane yau sai ta jiyo muryar alh bilya yana rafsasallama iya abu ta fito iya abu tace''yau alhaji dakanka a gidan namu. Yace'' eh wallahi zuwa nayi mu gaisa inji ko yaushe kudin hayar dana biyayake karewa? Iya abu tayi dariya ta sosakwarkwata a kai tace'' ai sauran wata uku ne inajin''ya ce''to ki raba kudin hayar gida hudu ki daukikashi uku naki ki bani kashi daya ragowarwatannin uku ki kori hanne daga dakin da take haya in bata biya ki ba ba ruwana'' iya abu ta batarai tace. To ni yanzu na kashe kudi yaya kake sonayi a ina zan samo kudinka da zan dawo makadashi ? Hanne fakara'u ko sisi bata dashi ina zayasamo wani kudin haya ta biyani? Gaskiya alh bilyakai ya dace kaci gaba da biyan kudin haya don haka kace a gaban maigari''yace''kash ni bakifahimceniba abu ba don in takura miki ba nace kibani sauran kudi ji rike sauran kudin ina nufinyanzun ki koro hanne daga dakin da take donnibada yawuna take zaune a dakin ba kuma ba'akudina ba. Iya abu tayi dariya tace''oh na gane wato yanzu dai in rike ragowar kudin watanniukun da suka rage kenan sannan in koro hannewaje idan bata biyani kudin haya ba ko. Ko bahaka kake nufi ba? Alh bilya yayi dariya yace''hakanake nufi mana.iya abu tace an gama ai a gabankazan koro shegiyar. Gaban hanna ya yanke ya fadi tayi zumbur ta tashi zaune ta dafe kirji tana tainnalillahi wa'inna ilaihirraju'un. Iya abu ta wangalelabulen dakin ta shiga budik ta sami hanna a kankatifa a zaune ta mikawa hanna hannu tace''banikudi. Hanna tace''bani da kudi. Iya abu ta wawurijakar hanna zata wurgar waje hanna ta rike tana mata magita tayi hakuri dan Allah ta rufa mata asiri,amma kamar zuga iya Abu take.Hanna ta fito da gudu daga dakin ta zo ta durkusaa gaban Alh Bilya tana rokonsa dan Allah yayihakuri ya bar mata kudin hayar wata uku kafin nanzatasan yadda zatayi ta sake biya. Amma yayikunne uwar shegu da ita yana cewa''yauwa Abu ki tattaro kakaf kayanta ki watso''ana cikin wannanhali sai ga Wada nan dauke da kwanan abinci yakawowa Hanna abincin rana ya sami Hanna kacekace tana kuka a durkushe a gaban Alh Bilya tanarokonsa iya Abu kuwa tana ta faman watsi dakayanta. Cikin kuka Hanna tace'' wada kaga halin da nake ciki jeka ka kira iya Salmai tazo ta rokarsu.Nan da nan wada ya garzaya dan ya shaidawa iyaSalmai halinda yazo ya tarar da Hanna. Bayantafiyar wada ba dadewa sai ga iya salmai da maigarida tawagarsa sun shigo gidan suka iske hanna acikin wannan hali. Maigari ya ce'' subhanallai Alh Bilya da girmanka meye haka? Alh Bilya yace''ranka ya dade babu yadda za'ayi taci gaba da zamaa cikin kudina bayan bata sona shi yasa nazo na ceto in Abu taga zata bar Hanna taci gaba da zama akyauta to. Amma ba dai nine ke biyan kudin nandole Hanne ta fita don bazan barta taci gaba da zama a kudina ba tunda bata sona. Nan dai akahau bawa Alh Bilya da iya Abu baki ana musuwa'azi da nasihohi akan rayuwa ce kuma sumasuna da yaya zasu iya mutuwa su bar yayansusuma ayi musu haka. Hanna tasa gefen zaninta tagoge hawaye ta mike daga durkusan da take yi ta juya ta kalli su maigari tace'' ku kyalesu ni nahakura da zama a dakin zan koma rumbun inzauna hanna ta fara dibar jakunkunan ta tanashigarwa cikin rumbun nan mai gidan tururuwa dacinnaka ga bunhunhunan dawa da kaikayi.....ANA CIKIN WANNAN hali ne Musa danmakwabtansu ne ya shigo yace'' wasu maza gudabiyu gasu nan a waje wasu farare ne kamarlarabawa sunce suna neman Hanne 'yar gidanMalam Habu. Mai gari yace'' larabawa daga ina ?Musa yace sunce daga Niger suke maigari yace'' to muma ai tafiya zamu yi mu tafi kawai, har Hannasuka yiyo waje wasu samari farare sol sol ne gudabiyu a tsaye a kofar gidan daya daga gani kotambaya babu jinin hanna ne don kamar su dayakamar an tsaga kara maigari yace ''kune bakindaga Niger ? Suka amsa 'eh' sannan suka duka suka gaishe dasu maigari. Hanna ta tsaya a gefetana kallon wadan baki nata bata san suba ammadaya daga cikin samarin kamarsu daya futik dagagani babu tambaya daga tsatso daya suka fito.Maigari yace'' to ga Hanna . Yaya kaman baku sanjuna ba. Mai kama da Hanna yace'' ni sunana Ahmad wannan abokina ne sunansa Bello Madu. Nikanin mahaifiyar hanna ne uwa daya uba daya.Hanne bata taba ganina ba ban taba ganinta bashine nazo na nemota don muga juna'' Hanna najinhaka sai ta daka tsalle ta rungume Ahmad sai itadashi suka rushe da kuka. sai suka rushe da kuka. Maigari da sauran mutane sai suka hau girgiza kaisuna masu tausayinsu. Maigari yace'' Alhamdulillahgara da Allah ya kawo ku sai mu koma daga cikin atattauna. Bayan kowa ya sami waje ya zauna,Hanna ta tashi ta dauki kwano ta kwalfo musuruwan sha a randa ta kawo musu, bayan sun sha. Maigari ya fara bayani ya shaida musu duk halindaHanna take ciki yanzu ma ga jakunkunanta nan awatse a waje dakin da zata zauna ma yanzu yazama garari. Ahmad ya matse hawaye yace'' hakikatuntuni munji irin halin da mahaifiyarki ta shiga harta rasu mun san kuma halin da yarta Hanne zata shiga amma da yake ni ina yaro bani da ikon inzoin dauketa shi yasa na hakura akwanakin nankuma na dinga mafarki iri iri na 'yar uwatamarigayiya uwar Hanne. Kullum na kwanta baccisai inga yayata Habi tazo tana cewa Ahmad danuwana yanzu baza kaje ka nemo 'yata ba Hanne kaga halin da take ciki ba a duniya ba, ko darenjiya ma nayi mafarkinta abu daya kuma takemaimaitawa don haka yanzu daman nazo da niyyarmu tafi da ita ko da mahaifinta yana nan zanrokeshi ya bani ita idan batayi aure ba in tafi da ita.Balle kuma yanzu da ya rasu dole in tafi da ita. Iya abu ta tabe baki tace malam tunda ransa ya hanaakai hanna wannan garin'' maigari da jama'arsa suka yiwa abu caa suka rufetadafada suna cewa'' ba yanzu kika gama mata watsida kaya ba? Bayan bakar wahala da take sha tuntana karama ta zamo tamkar baiwa a gidannan.Ahmad ya ce'' ba saikun bata bakinku bama wajenbata amsa mu dai zamu tafi da ita . Sai yanzu daya mutumin yayi magana wato Bello Madu yace'' aianan kusa muke a garin dashi muke. Dashi dababban mutum ai border ce ta raba. Ni costom neina aiki a border lokaci lokaci zan dinga kawomuku Hanne kuna gaisawa. Ahmed ya katse shiyace ''duk zancen ka lallashi matan nan bai taso ba kaga kankat din gari wato maigari da jama'arsasun bamu izinin mu tafi da ita to wacece kuma zatace sai hanne ta zauna yunwa ta kashe ta. Iya Abutaji wani dacin bakin ciki ya rufeta ganin Hanna tasami wajen da zata je ta huta. Taso ace da ta yiwaHanna watsi da kaya duk garin ta rasa inda zata zauna. A haka dai aka rabu Ahmad da abokinsaBello Madu suka yiwa mai gari da jama'arsa sallamasuka daukarwa Hanna jakunkunanta, Hanna tayafa gyalenta tarungume iya salmai suna kukanrabuwa Hanna da kawunta suka tafi.sun isa garin Dashi da daddare gidan Ahmadsuka sauka. Ahmad yana da mata daya da 'ya'yabiyu , sunan matarsa Hajir itama irinsu ce buzuwa.Hajir ta tari hanna cikin fara'a da murna ta kaitadaki ta kawo mata ruwa ta sha sannan ta zaunasuka gaggaisa sannan taje ta shirgowa hanna tuwo. Hanna taci tuwo nan tamkar tunda allah yahalicceta bata taba cin tuwo mai dadin haka basaboda tsabar yunwa da take ji, taci tayi nat sannantace a nuna mata bandaki zata yi alwala Hajir tanuna mata. Hanna ta shiga ta dauro alwala tazo tayisalloli tana idarwa taje ta watsa ruwa tayi wanka ta kwanta. Hajir taji tana son Hanna, tana sonta dakawa daga gani ma sa'an nune, hajir ta zauna agefen shinfidar Hanna na kwance suna ta hira kalakala,Hajir bata bar dakin ba sai da taga Hanna tafara bacci sannan ta hure mata fitila ta rufo kofa tafita ta nufi dakin kwanciyarsu. Da asuba Hanna ta farka taji ana kiran assalatu ta mike ta nufi ban dakitayi alwalla tazo tayi salla ta zauna tana Lazumi.Gyangyadi ne ya dinga daukar hanna ta mike takoma kan katifa ta koma bacci tayi ta barci har shadayan rana babu wanda ya tashi Hanna sai da tayibarcinta ta gaji ta farka dan kanta. Tana tashi tayi ido hudu da soye soyen abinci kala kala Hajir tazota jera mata. Ba Hajir kawai ba 'yar uwan uwarHanna fa yawa labari yakai musu cewar hanna tazodon haka suka aiko mata da abincin karin kumalloiri iri sunka ce kafin suzo su ganta. Hanna ta fadawanka tayi brush sannan ta saka kayanta tazo ta zauna a gaban abincin burjik a jere a tsakar dakintaduk nata ne sai taji wani farin ciki ya lullubeta ba'asabanba, yau hanna ce da barcin safe ta farka tagaabinci burjik an jere mata haka Allah yake, duniyajuyi juyi. Tun kafin hanna ta gama karin kumallo tajitsofaffi da mata suna sallama a tsakar gida, yan uwan mahaifiyarta hanna ne suka fara cinci rindonzuwa ganin hanna, sai koke koke daga su harHanna taga dangin uwarta cunkus amma suka cemata wadannan ma kadan ta gani don tushenzuri'arsu Azbinawa ne [buzaye] suna Agadas state .Sai dai wani abu guda da hanna ta lura duk danginta talakawane sosai suna cikin rashi wasuNono suke sayarwa rugage suke wasu kumamanoma ne. kawu Ahmad ne kawai dan Bokowayayye mai dan hali akan sauran koyarwa yake amakarantar firamaren garin har ya sami matsayinmataimakin headmaster. Shima dai rufin asiri ne kawai ba wani arziki gare shiba. Gidansa ginin kasane dakuna uku ne, bandaki da zana aka zagayekicin kuwa a tsakar gida aka dasa murhuna. Hakadai Hanna taji ta shiga wata sabuwar rayuwa maidadi fiye da rayuwarta da agidansu. A koda yausheyana godewa Allah da yayi mata canji daga ukuba da bakin ciki hantara ya kawo ta inda aketarairayarta. Hanna da Hajir sun shaku sosai a kodayaushe suna tare suna hira wasa da dariya. Tunhanna na boyewa hajir wasu abubuwa nadangane da rayuwarta har ta yaba da hankalinta tafara gaya mata wasu abubuwa da suka faru da ita ada na dangane da tsananin son Haisam ranarrabuwarsu. Tace har yau kullum da daddare sai tayikuka idan taje kwanciya barci saboda tunaninsa.Hajir ta tausayawa hanna sosai har hawaye tayimata ,daga karshe tayiwa hanna nasihoho akantayi hakuri kaddara ce daga Allah haka Allah ya rubuto musu.BAYAN zuwan hanna da kamar wata guda kawuAhmad da sauran manyan danginsu suka kiraHanna babban zauren dake gidan. Bayan ta gaisheda kowannensu ta koma gefe ta takure. BabaSha'aibu yace'' Hanna kinsan dalilin da yasa mukakira ki nan? Hanna cikin ladabi ta amsa musu a'a yace to a matsayinmu na iyayenki da kakanninkimunyi nazari mun kuma tsayar da shawara abindanake nufi da munyi nazari shine bai kamata ba muzuba miki idanu haka nan ba babu aure don hakaya kamata kiyi aure a watannan kuma. Gabanta yayanke ya fadi ras dajin kalmar aure cikin rudani tace''....... Wazan aura ai ni bani da kowa a garinmuanan garin ma babu wanda yace yana sona.'' suduka suka kyalkyale da dariya. Ahmad yace''hanna kwantar da hankalinki dole mu aurar dakega mai sonki kece dai baki sani ba amma zuwankigarinnan maza sun doshi goma suka sameni suka ce suna sonki shawarar da muka yanke ita cemuduba a cikin waye yafi hankali. Addini. Sana'aasali wanda zai rikeki tsakani da Allah mu aura mikishi tunda ke bakuwa ce ba sanin halayensu kika yiba babu kuma isasshen lokaci da za'a barki kinasoyayya dasu har ki zabi miji mu baza mu zaba miki wanda zai cucekiba . Hanna babu wanda ya fadomata a rai sai Haisam, soyayyar da take yiwa Haisamsai kara yabanya take a cikin ranta, Hanna ta ciresha'awar auren wani a rayuwarta tunda ta rasaHaisam shine ma hawaye yake zuba dagaidanuwanta don tasan ta rasa wanda take so duk duniyar nan ta rasa farin cikin kuma. Wannanhawaye na hanna da yake zubowa dagaidanuwanta yasa jikinsu ahmed yayi sani kumamamaki ya rufe su yaya za'ayi hanna ta fara kukatun kafin taji waye aka zabar mata ta aura. Koakwai wanda ta kudira zata aura ne basu sani ba ? Inna rabi tace'' Hanna kukan me kike bafa cewamuka yi dole sai kin auri wannan da muka zabarmiki ba idan kina da wanda kike so fadi mu auramiki,daman ganin babu kowa ne shi yasa muketunanin hadaki da wani. Hanna ta share hawaye tagirgiza kai tace'' babu wanda nake so zan aura dukwanda kuka zabar min zanyi biyayya in aure shi kowaye kuma. Nasan baza ku zabar min wanda zaicutar dani ba'' gaba daya suka fara shiwa hanna albarka suna jinjina mata bisa tsananin biyayya datake yi musu allah yayi mata albarka. Kawu ahmadyayi gyaran murya ya gyara zama yace'' hanna tunfarkon zuwanki abokinna koma ince ya zama danuwana saboda tun muna yara muke tare nasanhalinsa ciki da bai fiye da uwar data haifeshi bata sanshi ba fiye da yadda nasan yadda yake yana damutunci da sanin ya kamata yace yana sonkitsakani da allah zai aureki wannan aboki nawashine bello madu abokina din nan da mukajenigeria garinku dashi muka daukoki . Yana dasana'arsa kuma yana da ilmi gaba daya boko da arabiya yanzu ma babba ne ba laifi a aikinsa aikincostom yake sune suke tsaye a bordar nigeriazuwa niger. Ni dai a ganina bello masu ne kawai yacancanci ya aure ki ko ya kika gani? Iya ma'idatace'' wanne irin yaya ta gani bayan ta gamamagana tace ko waye muka zabar mata tana so. Cancanta ma ai ba sai an fada ba sun dace ai''hanna ta sukuyar dakai kasa sai hawaye shar yasake keto mata. Bello madu kam ya cancanci asoshi bashi da makusa kyau kuwa kamar shi yayikansa dan buzaye asali kamar balarabe, hankali datausayi kuwa ba'a magana don da yaji labarin hanna hawaye ya dinga yi don tausayinta bashi damakusa ko kadan amma ita abun da ya kara satakuka shine tana matukar ganin mutuncinsa donhaka bata so aka ce shine zai aure taba don dukwanda ya aureta sai yayi hakuri sabod bazai samisoyayyar taba GANGAR HIKINTA zai aura zuciyarta na wajen haisam har abada, hankalin hanna yasake tashi sosao da taji sunan wanda zata aurakawu ahmad yace'' ni wannan kukan naki ne yaketsoratani hanna kiyi magana idan akwai wani abunda yake damunki. Hanna tayi dan murmushi tagirgiza kai ta ce'' babu kimai zabin da kuka yi min yayi. Inna goshi ta dau buda kiwa ya hau cewa''allah ya sanya alheri ya baku zaman lafiya. Hanna tamike ta shiga cikin gida bata tsaya a ko!ina ba sai adakinta ta rufe kofa ta fada kan katifa sai ta budesabon shafin kuka mai tsanani taji a ranta kamarwata sabuwar soyayyar haisam aka kara zuba mata taji sonsa ya sake sartseta kamar zata yihauka. Bayan anyi haka da kwana uku hanna nazaune a tsakar gida tana tankaden gari da yammatana taya hajir aiki, hajir kuma na wajen murhutana kada miyar kuka, suna taba yar hira hajir tace''hanna ina ganin kinfi sauran mata sa'ar samun kintsatstsan miji a duk yan matan garin nan sabodaduk yawanci yan matan garin babu wacce batakaiwa bello madu hari ba farin jini gareshi sosai.Kyawunsa ne ko kuwa illminsa , ko kuma jan ajinsane yake rudarsu oho? Amma ke gashi kwatsam yadamu da sanki kinsan tun ba yauba kawunki ahmad ya fadamin cewar bello madu yana sonkiamma ya gargadeni da nayi shiru kar in sanar mikihar sai ya sanarwa da magabatansa shima. Hannata cije tayi dan murmushi tace'' hajir kenan watonayi sa'a sosai ashe dana sami bello madu ta sama.Ba tare dana wahala ba? Amma ni a wajena sai dai ma ince shine yayi sa'a sosai ma kuwa.Alhamdulillah amma akwai matsala tabbas. Hajir tajuyo gaba dayanta tana kallon hanna can tace'' bangane akwai matsala ba. Wacce irin matsala kumahanna ? Ko bakya sonsa ne? Hanna ta girgiza kaitace ta ce a'a ni naki shi bayan shine zabin iyayena ina sonsa mana. Muryar bello madu ce tace.''assalamu alaikum''.Kai tsaye ya shigo cikin gidan kamar yadda yasaba shigowa daman. Kai tsaye wajen hanna yadosa. Hajir ta amsa masa sallaman gami da yi masatsiya ta ce'' oh dan halak kaki ambato yanzuzancenka fa muke yi ango kasha kamshi dagazuwanka ka doshi wajen hanna da idan kazo wajen wa kake dosa? Bello madu ya kyalkyale dadariya yace'' kai hajir kin fiye tsokana kinsan da saiinyi sati biyu a boda ban damu da zuwa garin nanba amma yanzu kusan kullum sai nazo garin nanko banzo gidan nan ba ina jin dadin garin sabodamatar da nake so tana cikin garin. To yanzu an banu izini inzo wajenta kina nufin sai in doshiwajenki duhu bayan shigowata hasken fuskarhanna ne ya bugi idanuwana. Kinsan ko a kabarihaske ake nema ana neman tsari da duhu. Hajir tarike baki tace'' ah bello madu daina hadani daduhun kabari allah ya baka hakuri'' wannan hira tasu ta bawa hanna dariya bata san sanda tatuntsire da dariya ba duk da wani kululun bakinciki daya dira a ranta yanzun nan da bello madu yashigo haisam kawai zuciyarta take haska matainama inama aceda haisam za'ayi musu auren nanwata guda ya rage ayi bikinta. Bello madu yace'' hajir yi hakuri bada duhun kabari nake hada kibani na isa? Ai nasan kokarin da kike min wajenturani fadar zuciyar hanna tun dazu ina zaune atsaye ina jin hirar da kuke yi. Kuyi hakuri ba labe namuku ba ina doso kaina bello madu naji anaambato shiya sa na dakata sai dana gama jin komai'' hajir tayi dariya tace a'a baba bello ka faralabe a gidan mutane dai kawai zaka ce min'' yakarasa wajen hanna ya jawo wata kujera a gefentaya zauna a hankali yayin daya kafawa hanna idoyana kallonta. Ji yake tamkar ya hadiyeta sabodason da yake yi mata. Fargabarsa daya yana tsoro kada hanna taki amincewa da soyayyar da yake yimata haka nan bayan abokinsa ahmad ya shaidamasa an bashi hanna yayi farin ciki amma farincikin ragagge ne yana gudun kada a takurawahanna ta aureshi yazo ya rasa soyayyarta ammayau sai gashi da kunnensa yaji hanna tace''ni na kishi bayan zabin iyayena ina sonsa'' don haka yauyafi kowa farin ciki. Hanna ta dago a kunya cetagaishe shi ya amsa cike da fara'a ya mika hannu yakarbi rariyar dake hannunra ya fara tankade. Hajirkuma tana yi masa tsiya tana cewa'' wai bellowannan bamu san wanne irin abu za'ayiwa hanna bayan anyi aure tuwan ma kai zaka dinga tukamata. Bello yace ke kin fadi kadan tauna abincikawai bazan yiwa hanna ba saboda bazaiyu intauna mata ba amma a baki zan dinga bata bayanna dafa mata domin hanna tafi saraunoyar da takemulkin duniyar nan idan ma akwai yadda nake jinta a raina,Ga mamakinsa sai suka ga hawaye shar yatsiyayo daga idanuwan hanna. Babu abinda ya satakuka sai tausayin kanta dana bello madu dominkowannensu son maso wani yake yi, inama haisamne yake jinta a ransa haka kamar yadda bello maduyake jinta a ransa. Shima ina ma yadda yake sonta tana sonsa haka'' allah sarki bello ka makara''hanna ta fada a ranta' sai bello ya kurawa hannaido kawai yana kallo sai ya juya ya kalli hajir wacceitama tayi kasake a tsaye tana kallonsu. Ya miketsaye ya kade garin da yake hannunsa yace dahanna ta taso suje zaure yana son ganinta yana da magana da ita. Hanna ta mike ta dauko ruwa tawanke hannayenta ta yafa gyalenta tana biye dashisuka fita zaure. Tambayoyom da bello madu yajerawa hanna sun doshi goma dom son yaji meyeya sata kuka ko aurensa ne bata so amma duk daa'a hanna take amsa masa. Domin idan ta kuskura ta bayyana abunda yake ranta ta sake shiga ukutasan bello ba zai takura yace sai ya aure ta bahakura zaiyi idan ya fasa aurenta wazata aurakuma tunda bata da maganin ciwon da yakedamunta. Na san na rasa haisam, na rasa shi kumahar abada na rasa soyayyarsa na rasa farin cikin rayuwata, meye ya rage mun a duniya kuma?Banda jiran ranar mutuwa. Bello ya katsewa hannatunani yace'' to tunda na tambayeki kince ba komaiakwai wata magana guda da nake son muyi dakehanna don allah kiyi hakuri ki sake yin hakuri daduk yadda kika tsinci rayuwarki, abinda nake nufi shine watakila hajir ta fada miki ina da gida nawana kaina yanzi ma a ciki nake zaune nan za'a kaikibayan anyi bikinmu, to kinsan halin iyayemusamman ma mata mahaifiyata ta kekashe kasatace lallai lallai sai dai a kaiki cikin gidanmu ma'anagidan da take zaune da kishiyarta wanda ba karamar takura bane dakine kwaya daya jal ganata ga wanda za'a kaiki. Kiyi hakuri ko bayanbikin zanci gaba da bata hakuri akan ta yarda inmaida ke gidana'' hanna ta sunkuyar dakai tacekawu wannan ba wani abu bane da zaka damukanka. Kaabi maganar mahaifiyarka domin abunda babba ya hango yaro koya bishiyar rimi bazai ganoba, ita ta haifeka tafika sanin dalilin dayasa tacemaka ka zauna da matarka a kusa da ita . Allah yabamu zaman lafiya gaba dayanmu ni da ita. Ni dakai kuma na gode'' wannan kalamai na hanna yakwantarwa da bello madu hankali don bai taba zaton hanna ba zata damu ba idan taji yare dasurukai zata zauna amma sai yaji ita take kokarin yimasa nasiha, akan ya kwantar da hankalinsa yabimaganar mahaifiyarsa. Kuma hanna ita ce take yimasa godiya. Daga karshe ya yiwa hanna sallamayace zai koma wajen aiki sai nan da kwana hudu zai dawo an turashi tsakanin boda dake tsakaninmaigatari da niger da zarar ya dawo za'a kawo lefeinsha allah. Hanna tayi masa fatan dawowa lafiya yatafi ita kuma ta shiga gida,Ta iske hajir tana kwasar tuwo . Taje kusa daita ta jawo kujera ta zauna. Hajir ta kalleta taceamarya a gidan custom bello madu kinsha kamshi,amaryar nan da wata guda. Wai ya naga duk jiknkiyayi sanyi ne har koke koke kike yi? Koda yakemuma fa duk munyi wannan don gabanin bikina kurket na rame sai kuka ina zaton auren waniabun tashin hankaline ashe babu abinda ya kai shikwanciyar hankali, ke kuwa daga ke sai masoyinkiku biyu a gida ku rakashe kowa kokarin yafarantawa dan uwansa yake yi. Ke gidanki nasiminti ne kewayayye ai bello madu ya zuba sumunti a gidansa tal a lailaye da simunti kamar abirnin. Mu da muke gidan kasa ma muke jin dadinrayuwarmu balle ke'' hanna ta ce'' kai hajir ai dagidan simintin dana kasar duk dayane yanzu yakecemun mahaifiyarsa ta tubure lallai lallai bata yardata kaini gidansa ba sai dai in zauna a gidansu. Hajir ta zabura ta wurgar da marar da take kwasar tuwota mike tsaye ta rike haba da hannu tace'' hanname kika ce kina nufin yanzu gidan su bello za'akaiki? Lallai mun shiga uku mu masu kai amaryama balle ke da zaki zauna da ita. Hanna ra jawohannun hajir ta zaunar da ita tace'' hajir zauna mana muyi magana daga zaune me yasa kika cemun shiga uku wani abune ? Hajir tayi ajiyar zuciyata koma ya ta zauna tace'' hanna bazan boye mikiba a gaskiya innar bello bata da haki saboda dukgarin nan babu wanda bai san bala'in inna hauleba har tafi iya abu matar babanki da kike bani labarinta don tun maigidanta yana nan bai rasu batake azabtar da kishiyarta indo wahalar duniyarnan yau idan kika je gidan indo da yayanta tamkarbayi ne a gidan. Debo ruwa ma a rafi ya ishekibayan zuwa gona da sassafe amma shi bello meyasa zai yi mana haka bayan yasa halin mahaifiyarsa ko da yake ba laifinsa bane don idanta saka musu kara basun isa su tsallake bamusamman bello yana yi mata ladabi sosai fiye dasauran kannanshi shine babba a gidan. Ina jin batsso yayi nisa da ita gani take komai ya samu yanzuke zai dinga dankawa gaba daya'' kafin hanna tace wani abu ahmed ne yayi sallama ya shigo sukaamsa masa gami dayi masa sannu da zuwa. Amurtuke ya amsa sannan ya juya ta kalli hajir tadaka mata tsawa yace. Ke hajir ki iya bakin kidanme kike kokarin rikita hanna akan aurenta dabello madu akanta aka fara zama da sirikai'' ya juya ya kalli hanna yace'' to saikin toshe kunnuwankishi aure dan hakuri ne kiji kiki ji ki gani kiki gani,ladabi da biyayya shi zai rabaki da masifa datakurawar surukarki. Kada ki yarda da 'yan zugamasu nuna miki kin hadu da masifar suruka mutumko shaidan ne yasan mai kyautata masa don haka idan kika bi inna haule sau da kafa dole ta dagamiki kafa. Bawai nace hajir tayi karya ba hakahalayyar inna haule take amma sai kinyi hakurikindaure kin mata biyayya zaki ga ashe duk abundaake fada maki ba haka take bama'' hanna tasunkuyar dakai kasa tace'' to kawu naji abunda ka fadamin zanyi amfani dashi na gode madalla'' tamike ta shiga daki. Ahmed ya juya ya kalli hajirwacce ta cika tayi fushi taf kamar zata fashe'' yashafa kumatunta yace'' ke kuma daga maganameye abun yin fushin'' hajir tace'' haba ahmed mekake nufi da ka ce kada hanna ta saurari yan zuga, kana nufin nice yar zugar kenan zan hanata yinaure ko? Ya ce a'a abunda naga laifinki shinemuddin kika sanar mata halin innar bello madu aizata tsorata kuma zata ji ta tsani surukarta daganan zaman lafiya babu kuma ni bello ne yafi banitausayi har cewa yayi ko zai fasa auren hanna ne saboda yasan tabbas zata hadu da halinmahaifiyarsa shi kuma a duniya abunda yaki jiniirin batawa hanna don yana sonta kamar yaddayake son rayuwarsa. Mun kada mun raya da innahauke ta hakura ta bar bello ya tare da amaryarsa agidansa taki fur wani uban ashar ta soka min ahe haushina take ji wai na dauki yata na bashi, ashetana so ta hadashi da wata shine yaki,Sum sum nayi na ficedaga gidan. Kuma wani abun bakin ciki shine belloyayi yayi ta yadda ya rushe bangarensa yayi nasiminti ya zagaye da katanga tace bai isa ba ana kasar zai saka amaryar tasa. Sai zana ya suyo yadanzagaye dakin su kwaya daya jal kuma abincinsu ahade dana yan gidan zasu dinga yi allah dai yakyauta mana nan mun dukufa da addu'a alah yadora shi akanta ta hakura ta barshi ya zauna agidansa hajir tace''amin nima zan taya hanna da addu'a amma caf wannan suruka ta hanna. Ai kogidan bazan taba takawa ba da sunan ziyara ni tunina yarinya tsoronta na ke ko gidan bana shigaallah ya sani banasan masifa. Duk hirar nan da sukeyi kakaf a kunnen hanna wacce ke daki tana jiyosu. Tayi ajiyar zuciya ta girgiza kai don tausayin kanta da kanta tace a ranta. Haka allah yaso danihaka zan kare a kunci, wahala da bakin ciki narabu da wahalar iya abu na fada wahalat innahaule allah kana sane dani, kasan halin da nakeciki kaine majibincin lamarina la'ila ha illa antasubhanaka inni kuntu minaz zalimin. Babana yayi gaskiya da yace babu mijin da zan aura da zairikeni amana in ba haisam ba. Baba baka sanyadda mukayi da haisam ba ka mutu ka barni akaninje in cewa haisam yazo ya aureni ka bashini, yayahaisam ya auri wacce yake so yar barni, baba kabarni a duniya baka san na rabu da haisam din bama. Ta rushe da kuka mai tsanani. Ta koma takwanta a tsakar dakin tana tunanin rayuwar dasuka yi da haisam shine farin cikinta a makarantabaya so ko kuda ta cijeta tattalinta wasa da dariyakullum har ya zuwa ranar rabuwarsu. Hanna tayikuka har ta gaji sannan ta mike don zuwa bandaki tayi alwala magariba. Ashe ta dade dayi bata saniba. Kamar yadda bello madu yace za'a kawo kefeda sauran kudade na al'ada an kawowa hanna lefeakwati uku kowacce a cike danma inna haule dukta rarrage kayan amma duk da haka masha allahan zuba mata kaya. A nan kauyen sai zancen kayan ake yi 'yan uwan hanna sai murna ake ammabanda ahmed domin ya tsorata da ganin yawanlefen nan yasan dole za'a zuba ido aga me kymaza'a kai dakin hanna.A matsayinsa na dan karamin malaminmakaranta firamare mai daukar dan karaninalbashi shi zai yiwa hanna gado, gara da kumaabincin 'yan biki gashi kuma a kurarren lokaci akasaka ranar bikin. Gashi duk danginsu shine maidama dama duk a jikinsa damgi suke nema. Yasan ko za'a taimaka masa da gudummawa bai wuce ayimasa fantekar alkaki da nakiya ba sai 'yankwanikan cin abinci wadanda suka daddage nezasu bashi setin samira. Da cin bashi da komaiahmed ya hada kudin gado mabi lamba one damadubinsa. Dan kudin da hajir take tarawa na dinkin hular da take ta bashi ya hada da sauran yargudummawar da ya samu ya sayi ledar daki dalabule shikenan sai kwanukan rabon abinci dasamira seti hudu aka haka aka jerawa hanna adaki. Bayan an sha biki an kai amarya dakinta tsaftsaf daidai karfinsu sai dai wani babban tashin hankali ahmed ta buga sama da kasa ya rasa kudinsiyama hanna gara. Don haka yace hajir da wasumatan suje su bawa inna haule hakuri insha allahukafin ta haihu za'a kawo mata gara don har ta farahabaici an kawo amarya babu gara. Kwanan hannauku cur tana rusar kuka bayan an kaita gidan miji . A ranar na hudun ne bello madu ya shigo dakintada jakar kayansa shi ma ya kauro gidan daga cangidansa. Da misalin karfe goma na dare gari yayishiru kowa yayi bacci abinka da rayuwar kauyeamma a zaune a gefen gado ya tarar da hanna tayitagumi tana tunani ido yayi mata jawur a kumbure , yayi mata sallama ta shigo. Ta daga kai da sauri tadube shi sannan ta amsa masa sallamar da yayimata. Ya shigo ya ajiye jakarsa a gefen akwatinantayazo kusa da ita ya zauna yana mai yi matamurmushi da nuna farin cikinsa a fili, ya dubikwayar idanuwanta yaga jawur don tsananin kuka da tasha yi yace'' hanna kukan ne har ya zamarmiki da idanuwanki haka ? Don allah ki daina kuka,hanna ni mai kaunarki ne bazan cutar dake ba'' tasake rushewa da kuka yasa hannu ya jawotajikinsa sai yaga tayi sauri ta zabura ta mike tsaye,Wannan zabura ta Hanna ta bawa Bellomamaki kamar wanda ya dona mata wuta, ya miketsaye yasa hannu zai rukota. Hanna tayi sauri tajada baya tana kokarin ta fice waje. Bello ya ce'' a.ahar waje zaki fice to na kyaleki zo ki zauna bazansake taba ki ba'' sannan hanna ta dawo tazo ta zauna a kasa kan ledar dake shimfide a tsakardakin ta hada kai da gwiwa tana kuka tamkarranta zai fita. Wannan kuka na hanna ya tayarwada bello hankali ji yake tamkar tana soka masawuka a zuciyarsa idan tana zubar da hawayen nan.Ya nisa sannan yace Hanna kiyi hakuri dan allah ki daina kuka meke damunki ne ? Nifa yanxumijinkine ki daina guduna kuna ina da hakkinakanki muddin kina guduna kuma kina kuka kinatayar min da hankali.Nace kiyi shiru kinki ki daina.Ko kina so inyi fushi dake Allah yayi fushi dakeMala'ikun allah su dinga la'antarki har sai gari ya waye? Hanna ta dago da sauri ta kalleshi yace yayakike kallona? Gaskiya nake fada miki ai duk macenda take gudun mijinta Allah da mala'ikunsa zasudinga la'antarta har sai gari ya waye ko kin yaddaki halaka ? Hanna ta girgiza kai tace bana so nahalaka'' yace ''to in ba kyaso ki halaka zo nan kusa dani ki zauna muyi yira. Cikin sheshshekan kukaHanna tace"kawu na zalunci kaina, na kumazalunceka da ban fada ma gaskiyar abunda yakedamuna ba. Kawu na kasance ina cikin wani hali natsananin damuwa wanda har nake tunanin bazaniya auren kowa ba. To amma dole nasan za'a yi min aure shi yasa na hakura na amince na aureka atunanina zan iya daurewa in zauna amma yanzubayan da akayi auren ciwon da yake damuna yadawo min danye bana jin zan iya zaman aure har insami aljannar da kowacce mace take nema akarkashin tafin kafar mijinki ta hanyar biyayyar aure. Kawu kayi hakuri ka yafemin dan allah karufa min asiri. Ka sauwakemin mu zauna haka batare da kowa ya sani ba, saboda sai in halaka idanmuka zauna a haka da igiyar auren ka. Bello yabude baki yana kallon Hanna can ya taso yazogabanta ya durkusa ya rike hannunta cikin yar siririyar murya mai dauke da tsananin dimaucewayace'' Hanna., fadamin ni kawunkine mai shirintaimakonki ta kowacce hanya kada kiji tsoronfadamin ko mene ne '' ta janye hannunta a hankalita share hawayenta tace '' idan bakamantaba a labarin dana baku a garinmu nace nayimakarantar sakandire da taimakon yaya Haisamson yaya haisam ne ya zame min dafi a zuciyatawanda dafin nan zai iya zamra min ajalina. Kawubello inason haisam harni ma kaina ina mamakin yadda kayi zuciyata ta kamu da sonshi haka nayiaddu'ar don allah ya goge mun , nayi azumi nayikukan kullum akan allah ya yaye min amma kamarkaramin ake . Daga karshe sai nake addu'ar allahya dauki raina da in dauwama a haka amma kaganni har yanxu a haka na rasa yadda zanyi'' ta rushe da kuka. Bello yayi shiru yana kallonta shimacan ya nisa ya ce'l hanna me yasa nazakiyi addu'arallah ya hadki da haisam ba kuyi aure kike addu'arallah ya yaye miki sonsa ko kua allah ya daukiranki? Hanna ta goge hawaye tace:: haisam yayiaure a ranar da mahaifina ya rasu'' bello madu ya gyara ya zauna a gaban hanna ya lankwashe kafadon jin labarin wannan rikirkitaccen al.amarin nahanna. Hanna bata boye maiba ta bashi labarintadana haisam tun daga ranar da babanta ya kaitamakaranta har ranar gidansu ta iske shi zai tafidaurin aurensa, daga karshe tace'' ashe yaya haisam ba sona yake ba taimako kawai yayi min nikuma zuciyata ta kamu da tsantsar kaunarsa donhaka ne a koda yaushe nake addu,ar allah yayayemun sonsa bana addu.ar haisam yazo yaaureni. Bello madu yayi murmushi karfin hali yace''haisam yana sonki yana kaunarki sosai fiye dani kaina da duk wni mai sonki a duniya. Akwai watamatsalar da tasa bai aurekiba hanna'' hanna cikeda mamaki ta kurawa bello ido tace me yasa kacehaka me ka gani daka fadi haka?'' bello yace''saboda ke yarinya ce shi yasa baza ki fahimcihakan ba, kuma nasan irin yadda kike hanna bawai haka ta taba faruwa akaina ba a.a inakwatanta nima rayuwata zata iya shiga irin wannanhalin da kika shiga idan na rasaki saboda kecewacce na taba jin ina so a duniya. Ni na yadda naamince zanci gaba da zama dake a haka amatsayinki na matata amma babu zancen saki a tsakanina dake saidai mutuwa ta rabamu sabodasanda nake miki, hanna da ace haisam yana jirankibayyi aure ba da zan daukeki ina kaiki wajenshiinaura miki shi don kiyi rayuwa cikin farin ciki, ni indawo gida in zauna ciwon son da nake miki yakasheni na yadda indai na ceto rayuwarki. Amma yanzu da yake haisam yayi aure kiyi hakuri. A cikinkashi dari bisa dari da kike yiwa haisam, ki daure kibani kashi daya a cikin dari har karshenrayuwarmu ta aure na gode. Hanna ki daure kicigaba da zama dani a haka kada ki barni ni dakeduka muyi biyu babu, kin rasa haisam ni kuma in rasaki'' yasa hannu ya jawo jikinsa zai rungumetatayi sauri ta mike tsaye ta juya masa baya. Ya tashi asanyaye yaje ya rufe kofa ya datse da makulli. Yayinda hanna taji wannan rana tamkar ranar damahaifinta ya rasu ta kuma rasa haisam yau gata adaki zata kwanta gado daya da wani a matsayin mijinta ba haisam ba, hawaye yaci gaba da tsiyayomata daga idanuwanta. Bello yaxo ya rungumetata bayanta yana mai sunbatar kunnuwanta dagefen kumatunta cikin sanyayyiyar murya hannatace'' a matsayinka na mijina akan babu yaddazanyi ka sami GANGAR JIKINA amma ruhi, zuciyata na wajen haisam.'' bai iya bata wannan amsan bacimak ya dauketa ya dorata a tsakiyar gado. Hannata shide tama fita hayyacinta saboda tsananin bakinciki yau gani ga wani daban zai fara saninta 'yamace kafin haisam wannan bakin cikin ne yayimata yawa yasa ta fita hayyacinta ma iya cewa suma tayi amma gogan naka baima lura ba ji yakeyau tamkar an masa albishir da gidan aljanna gashiya auri hanna harma ta mallaka masa GANGAR JIKINTA.A ranar da hanna ta cika sati guda ta fara saninhalin uwar mijinta ashe da kara take yi mata. Dasassafe ko tashi daga bacci basu yiba Inna Hauletayi dirar mikiya a bakin kofan dakinsu tana bugunkofar da karfi tana fadin a tashi haka baccin ya isaduk inda sati yayi an gama cin amarci bakunta ta kare kin zama 'yar gida fito ki dora dumame. Indozataje rafi debo ruwa.Firgigit Hanna ta mike ta dirodaga kan gado ta bude kofa ta fito. Ta durkusa harkasa ta gaishe da Inna Haule. A yatsune ta amsatace'' a tafi wajen murhu a dora dumame ga dawada gero can idan kuka karya kumallo keda indo ku surfa''. Bello yaji tamkar yayi ihu saboda takaiciyasan Hanna kuma ta shiga uku ta lalace kamanyadda amaryar Babansa Indo take dandana wahalakullum kamar baiwa.Ya tashi zaune ya rike kaitausayin Hanna zuciyarsa da tunani ina zai samomafita kafin ta zama baiwa, to amma babu wata mafita tunda har yau har waye war gobe innaHaule taki amince masa ya koma gidansa shidamatarsa. Da ya isheta ma da maganar sai tace dukranar daya sake rokonta akan wannan bukata tasaAllah ya isa kuma zata tsine masa, don haka Belloyaja bakinsa yayi gum. Haka hanna ta kasance tana yin iya kokarinta na ganin ta farantama uwarmijinta tana binta sau da kafa amma a banza innahaule bata gani. A koda yaushe zagin hanna taketana cewa.A yaushe zagin hanna take tana cewa aurendaba gara ma ai bai cika aure ba. Wai hanna tamallake mata da don da sai yayi sati biyu,uku baizogarin ba daga wajen aikimsa amma yanxu bayasati guda, zantuttuka barkatai marasa ma'ana daina nuna tsana tsagoranta. To wannan al.amari yasa hanna ta sake fitar da rai daga samun zaman lafiyaa rayuwarta, inna haule halinta daya da iya abukoma tafi iya abu ko uwarka ka yanka musu kadafa ka basu bazsu gode maka ba. Sai dai kawaiidan abun ya isheta ta shiga daki tayi kuka ta gaji.Idan bello madu ya dawo ya ganta a wannan hali sai ya shiga lallashinta yana bata hakurin nan nasababu abinda yake karama hanna banda takaici.Abu daya ya gano lagonta in har yana so tayidariya a duk halin bacin ran da take shine yacemata haisam. Haka yake sakata a gaba yace dolesai ta bashi labarin haisam. A koda yaushe hanna na kirga kwanikin yaushe bello zai dawo dagawaje aiki saboda dashine kawai take hira mai dadihar tayi dariya hirar ita ce hirar haisam.. Hanna daindo ne suke surfe a yau, inna haule ta fita unguwashine ma suka samu suna yar hira. Duk da indo tagirmewa hanna amma duk da haka bata fi shekaru ashirin da shida ba a matsayin suruka take a wajenhanna tunda matar baban mijinta ce. Amma doletasa suka zama kawaye. Hanna na bakace dusar,indo tana tikar dawa a turmi. Indo ta tsagaita dadakan tace'' hanna sai dai hakuri ni harna saba dawannan bauta haka Allah ya rubuto mana rayuwarmu. Hanna tayi ajiyar zuciya tace '' Allahyana barin bawanshi a halin daya so ya ganshi.Amma duk abubuwan da inna kemun bayadamuna irin duk abunda muke yi mata bata ganidubi fa irin aikin da mukeyi kamar zamu mutuyanzu idan tazo cewa zatayi munyi ha'inci bata surfu ba. Ga zagin da take yimin akan gara ni narasa yadda zanyi da rayuwata. Indo ta ajiye tabaryatace'' ai waike kina nufin duk abinda ake baki saniba a gidan nan yau? Hanna ta ajiye faifan dakehannunta ta tattara hankalinta gaba daya a wajenindo tana jiran taji me yake faruwa. Indo tace '' ko da yake kin tafi debo ruwa dazu da sassafe ni innahaule tasa na shifa dakinki na miko mataakwatinan aurenki guda biyu wadanda baki dinkakayan ciki ba tasa almajiri ya daukar mata wai zatakai wani gida ajiya tunda ba.ayi mii gara ba sumabaza ki daura lefansu ba. Daman wata uku ta daukar miki a kawo gara gashi yanzu kin shigawata hudu da aure . Don haka da zarar bello yadawo zata sa ya sakeki, lefen kuma ta kaiwa watayarinyar a daura masa aure da wacce zata kawomata gara. Kuma kinsan bello babu yadda zaiyiidan ta sashi a gaba tace '' ya sake ki . Hawaye ne sur yake zuba daga idanuwanta hanna ta mike dagudu ta shiga daki ta tara wayan an kwasheakwatina sai kwaya daya 'yar karamar kaya kalauku ne ta dinka a lefen su suka rage sai saurantsofaffain kayanta nada gasunan a kasa an watsarmata. Sai ta kwanta a kan gado ta fara rusar kuka hanna ta kware wajen iya kuka dan ko gasar masuiya kuka akaje ta duniya ina ganin ita zata zo tadaya. Can ba dadewwa inna haule ta dawo ta tarada indo ce kadai take aikin abincin rana tace'' inahanna? Indo tace'' ciwan ciki take tana daki. Taleka ta tarar da hanna sharkaf cikin kuka sai tace.'' babu wani ciwan ciki ba ciwan cikiba ko ciwannakuda kike kin bar gidan nan bazan iya ba harkartalauci anyi biki ko gara babu lefan dana dauke neshine yasa bakin ciki ya kwantar dake. Haka hannata yini cur a kwance babu ci babu sha sai kukaAllah cikin ikonsa sai ya jeho mata Bello da yamma kwanansa biyu ral da tafiya ba zato ba tsammanihanna taji sallamansa ya shigo, furgigit tayi ta tashizaune kallo daya yayi mata yasan akwai abindaaka yi mata har tasha kuka. Yaje da sauri ya zaunaa kusa da ita ya jawota jikinsa ya tambayeta mekedamunta take kuka. Ta amsa masa da ba komai . Ya ce yasan dole da wani abu kar ta boye masa ta fadamasa gaskiya, sai tace cikin tane ke ciwo, yayi shirushi dai ya jita ne kawai amma bai gamsu ba. Sai canaka jima hankalinsa yakai wajen akwatina yagabasa nan yace hanna ina akwatinanki suke? Tayishiru can tace inna ta kwashe takai ajiya wai tunda ba'yimin gara ba wata zata kaiwa ta aura maka itani ka sakeni. Sai ta rushe da kuka. Bello ya cije bakidon tsananin bakin ciki yayi shiru ya kasa maganasai yasa hannu yana goge mata hawaye ya nisayace. Daina kuka kece baki sani ba na baw ahmedkudin da zai saya mika gata kakaf yanzu ma cikon kudin da zai karasa sayyar na kawo masa. Damanyanzu zan koma wajen aiki tunda ina da aikin dare.Daman inna bata ganni ba ance tana makwabtabari inyi sauri in tafi baza ta san nazo garin bamaballe tayi min maganar sai ince Ahmed suyi kokarisu kawo garar gobe kinga an kashe bakinta kafin in dawo. Ya rungumeta hanna ya sambacikumatunta yace '' bazan sake kiba hanna ina sonkida yawa ki kwantar da hankalinki kinji ko, sannanya fice yana sauri ya tafi. Hanna ta bishi da kalloyayin da zuciya kece mata'' ba haisam kadai ba bello madu ma maisonki ne hanna ki kaunace shi.'' haka kuwa akayiwashe gari da misalin karfe uku na yamma saihanna taji an doso cikin gidan kamar a mafarkitaga kartan maza suna ta ajiye buhunhuna a kofar dakin inna haule . Mata suna ta shigowa dafantekun alkaki, nakiya dibulan da sauransu.Wannan al.amari ya bawa inna haule mamaki,nauyi da kunya saboda sunyi mata ba zata duk tabigari tana fadin ba.ayiwa hanna gara ba kuma bazasu iya yiba kwatsam sai ga gara wacce ko 'yayan attajiran garin ba'a taba yi musu gara mai yawanbuhunhunan haka ba. Nan dai inna haule ta haufara.ar borin kunya tana cewa ashe kuna tafe ku kaki sanar min nima in gayyato yan uwana suxo sutayani karbar irin wannan abin alhairi sannunku dazuwa ku shigo daki mana ya zaku zauna a waje. Hanna dibo tabarminki dana indo a shinfida baki.Ai da kun sanarmin zaku zo da nasa anyi mukugirke girke da soye soye irin wannan abin arzikihaka'' yan uwan hanna suka ce'' babu komai ai bazama muka zo yi ba mun kawo gara gata nan,zamu koma don yarmu ta sami salama a zamanta na aure da mijinta'' suma suka yaba mata ba dadi.Washe gari inna haule da sassafe taje ta debowahanna akwatinanta ta kawo mata amma ankwashe wasu kayan da yawa babu ta kumagargadi hanna kada ta sake ta fadawa danginta komijinta tayi shiru da bakinta. Da bello madu ya dawo faran faran inna haule ta kira shi ta nunamasa gara har tana cewa'' allah sarki ashe bakaramin shiri suke yiba shi yasa basu kawo dawuri ba irin wannan yawan gara sai kace yarsarkin noma ka auro '' bello yayi dariya ya ce'' Allahya sanya alheri ya bamu zaman lafiya'' ya nufi dakin hanna, bayan tayi masa sannu da zuwa ta kawomasa abinci da ruwa yasha sai ya jawo akwatinanya bude kamar yadda ya zarga tabbas mahaifiyarsazata kwashe wasu kayan haka kuwa ya gani takwashe kaya da yawa. Ya waiga ya kalli hanna saita sunkuyar da kanta kasa bata ce masa komai ba... Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 2 Posted by ANaM Dorayi on 03:14 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Yace '' hanna an kwashe miki lefenki ko? Kiyihakuri zan suyo miki wasu insha Allah idan muka yialbashi wani watan'' hanna ta dago cikin ladabi datattausar murya tace'' ni na yafe duniya da lahira basai ka biyani ba wahalar zata yi maka yawa. Kawubello babu abinda zance maka sai godiya da wannan gara daka yimin Allah ya saka da alheridomin ka kwatar min yancina tun daga ranar daaka kawo inna bata sake yimin gori ba. Yanzu zanyizaman farin ciki a gidan aurena: yayai murmushiyace'' farin cikin ki shine nawa Hanna, Allah ya karasanya ki a farin ciki fiye dana yanzu'' tace amin na gode. Karshen wata nayi da bello ya dau albashi saida ya sisiyawa hanna kayayyakinta damahaifiyarsa ta kwashe cikin dare ya kawowahanna a boye yace ai hakkintane dole ya biya ta.Hanna tayi godiya ta karba haka hanna da bellosuka kasance yana kyautata mata a boye komai ya gani na sakawa kona marmari sai ya suyo mata dadaddare ya shigo mata dashi ya bata a boye ba taredaya bari mahaifiyarsa ta gani ba. Bello yana karason hanna saboda ladabinta hankali da nutsuwada uwa uba tsananin hakurinta da tawakkali itakuwa hanna har yau har wayewar gobe ta kasa masanya gurbin haisam ta mayar da bello zuciyarta.Idan bacci take yi tana kwance da bello ammamafarkin haisam take. Idan tunani take yi haisamkawai take hangowa a zuciyarta. Tana kokarin tamayar da soyayyar da take yiwa haisam kan bellosaboda ita ma ta saka masa da soyayyar, sabida irin kyautata mata da yake amma abu ya faskara hakadai take dagewa tana nunawa bello tana sonsawanda a zuciyarta ba haka bane. Wasu lokuta dayawa idan suka tashi da safe. Bello yakan ce matayaya haisam? Don jiya kina kiransa a mafarki.Hakika hanna duk sanda ta kwanta mafarkin haisam take yi ashe har ambatonsa take a fili.Saboda tsananin son da bello yake yi mata ya yardaya amince kuma zai zauna da ita a haka. Bai tabanuna mata bacin ransa ba. Ita kuma hanna sai tajitausayinsa ya kama ta nauyi da kunyarsa talullubeta. Amma yaya zata yi tunda GANGAR JIKINTA YA AURA ZUCIYARTA na wajen haisam.Matsalar gara ta wuce tsakaninta da surukarta saikuma matsalar da inna haule ta dakko ta dorawahanna ita ce har yanzu hanna ko batan wata batayiba balle ta samu ciki fada da gori a wajen innahaule babu dare babu rana. Bello yayi kokari ya wayar mata dakai akan cewa ba laifin hanna baneciki Allah ke badawa amma abu yaci tura inna hauletaki ta saurarawa hanna cewa take ga sa'anninaurenta nan dukka ciki garesu wata bakwaibakwai tunda yanzu watan hanna bakwai da aure.Yau hanna tun karfe biyun dare take kai kawo a tsakar gida bacci ya gagari idanuwanta. Duk budeidon da bello zayyi sai yaga hanna tana fita ko tanashigowa cikin dakin kaman a mafarki yake ganinta. Can yaji ana kiraye kirayen sallar asuba tayi. Yasahannu ta laluba gefensa yaji hann bata nan. Yayifirgigit ya tashi ya fito tsakar gida ya hango hanna a gaban murhu tana hura wuta ya karasa inda takeyace.' Hanna yau lafiyarkikalau kuwa tun dare kike shige da fice kinki kikwanta yanxu da asubar nan wutar me kikehurawa? Hanna ta danyi murmushi tace'' kawu kamanta yau da duku duku oganka yace zai aiko damota za kuje Agadas shine nake dora maka ruwan wanka naji yau garin da sanyi sanyi''Yayi murmushiya ce'' Ai jinsa nayi kawai meye abun turo mota daduku duku sai kace zamubar kasar'' Hanna tace''Agadas ai da nisa shi yasa kuma wata kila bakwana zakuyiba ko ? Yace' Gaskiya agadas da nisaba kuma cikin garin zamu shiga ba local government zamu je ina ganin wajen 450 Km nekuma bana jin zamu kwana ziyarar aiki zai kaimucan mu kuma yan rakiya'' Hanna tace '' Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Ina jin kiran assalatukafin ruwan yayi zafi ga buta ka fara yin yin Sallah ?Ta mika masa buta ta durkusa har kasa. Bello ya tsaya yana kallonta kawai saboda wata tsantsarsoyayyarta ce take kara sarke masa zuciya.Musamman wannan kulawa da ladabi da Hannatake masa, ya karbi butar ya shiga bandaki, kafinya idar da sallar Hanna ta hada masa ruwa wanka .Ya tashi ya shiga wanka. Kafin ya fito ta debo wankakkaun kayansa data wanke ta goge masa tadora akan gado ta goge masa takalmin da zai sakamar yadda tasaba masa kullum. Bayan yakammala yana goge gogensa da yan shafe shafesai ya dauko kayan da Hanna ta fitar masa ya saka.Tazo tana balle masa maballin wuyan rigarsa. Yayi murmushi yace'' Hanna na gode da irin wannahidima da kulawa da kike nunamin wannan yasaina kara sonki dari bisa dari, idan akwai soyyya datafi dari bisa dari ina miki Hanna sai dai ni anyakuwa na sami kwaya dayan nan kacal da nake so asanmin a cikin darin da ake yiwa haisam ?Cikin kunya hanna tace'' Haba daya kacal ai kafiguda daya'' yace '' a.a zancen gaskiya muke, nawaaka karamin ? Tayi dariya tace'' kawu ka wucegoma ma zaka kai sha biyar'' su duka suka tuntsireda dariya. Yace '' to tunda a wata bakwai na samigoma sha biyar nan da shekara bakwai zan iya tadda haisam'' suka sake tuntsirewa da dariya.Muryar inna haule ce ta katse musu dariyar da sukeyi tana bakin kofar dakinsu tana cewa'' tun dazumagana nake muku baku jini ba kun shige dakikuna tuntsira dariya da duku dukun safiyar nan tomotar ofishinku ce tazo suna ta kwankwasa gida . Daman Hanna abinda kika sani kenan ki shiga dakida miji kina dariya aikin kenan ciki fal kashi, babugurbin kwanciyar Da sai gurbin tarin kashi'' Hannatayi kasake yayi sanyi fara.ar da take yi ta koma cikiranta ya baci damin da ana siyar da ciki da ta suyohaka kuma da a wani waje ake nemoshi da taje ta nemo duk wahala koda kuwa zata mutu ne. Ko tahuta da zagin da gorin da ake yi mata. Bello yayiajiyar zuciya yace'' inna gani nan zuwa shiryawanake'' ta wuce ta tafi tana tsaki tana cewa'' Kaje kadawo dai daga tafiyar kazo mu zauna muyimaganar saboda bazai yuba, in zuba muku ido haka kawai aure wata bakwai kenan babu ciki baalamarsa kaina da kafafuwana turawa yarinyaabinci nake sai dai taci tayi kashi kawai. Ai ba dantazo ta cika mana shadda muka aurota ba mumamuna so muga dan jariri a gidanmu. Tunda tashanye ka ta asurce ka baka ganin lefinta to ni bata asurceni ba dole ka karo aure idan ma baza kasake taba, kai dole ma ka sake ta ka auro maihaihuwa don daki daya garemu a gidan nan'' Harinna haule tayi nisa ta juyo ta dawo ta tsaya a kofardakinsu Hanna tace'' Hanna kiyi ki fito daga dakinnan yau duk ke zaki yi aikin gidan nan shara wanke wanke surfe da girki ki fara debo ruwatukunna idan kin cika randunan gidan kakaf sai kifara aikin gida da yamma kuma kije gona ki tsinkowake da gyada dan sun nuna. Yau wacce kukeaikin tare indo aikenta zanyi magarya wajenkawata. Tunda ba ciki garekiba ba goyo ba ai wannan aikin bazai gagarekiba, sai dai idan kinjikashi sai kiyi a gonar tunda cikinki sai kashi babuhaihuwa. Kinga kuwa kashin naki ya zamar mintaki a gonar kinga kin taimaka kema'' Bello maduya fisata baisan sanda yace'' Haba inna ki dainayiwa hanna gorin haihuwa ba laifinta bane rashin haihuwa Allah ne yake bayarwa inna dama haryanzu Hanna ce take debo ruwa a rafi ina almajiriindana dauko aiki nace zan dinga biyansa. Ita taji daaikin gidan su kuna almajiran suje gonar. Hannatasa hannu ta toshe masa baki tace '' yi shiru karkasa taji haushina, mahaifiyarka ce babu komai duk zanyi aikin. Inna Haule ta rike baki tace'' inyedannan ka fara fada in fada dani akan matarkalallai abun babba ne jeka ka dawo ka sameni donwallahi ina ganin zamanka ya kare da wannanyarinyar mai kama da tumatir ina ganin rabaka takesotayi da kowa a duniya har dani dana haifeka . Ba'a haiyacinka kake ba na sani bayinka bane. Tatafi tana surutanta dai barkatai. Hawaye yana zubashar daga idon Hanna. Bello yasa hannu ya gogemata zuciyarsa cike da tsananin tausayinta ammayafi jin tausayin kansa da kansa. Saboda zaifi hannashiga wani hali,idanmahaifiyarsa tasa ya saketa don shine yafi sontafiye da yadda take sinsa idan ya rabu da hanna yarabu da farin cikin rayuwarsa. Kalma daya ce yasanidan yafadawa Hanna duk irin bacin ran da takezata yi dariya idan ya ambaci sunan Haisam . Yayi dan murmushi ya kalleta yace'' Hanna dama ace ayanzu kina da ciki ki haifanmun da namiji in sakamasa suna haisam. Hanna ta dago ta dubeshiidanuwanta a cike da hawaye sunyi jawur donkuka amma saida murmushi ya subuce mata a taketaji zuciyarta ta fara dan hucewa daga tsananin tafasar da take yi saboda kunar maganganun dainna Haule ta fada mata. Hanna taji wani dan sanyi aranta wani abu ya dasu a zuciyarta da bello yace ''dama ace ana da ciki ta haifi da namiji ya saka masasuna Haisam taji dama ace hakan faru mana. Ammadata tuna yanxu ma haka al'ada take don haka zancen ciki ma babu shi sai ta sake rushewa dakuka. Bello ya jawota ya rungumeta akirjinsa yanashafa lallausan gashinta yace'' Hanna lallai yauranki ya baci sosai har in kira miki Haisam ammakici gaba da kuka kiyi hakuri ki yafewa innata mucigaba da yi mata addu'a Allah yasa ta gane gaskiya Allah ya cusa mata soyayyarki a ranta. Hannatayiajiyar zuciya tace amin'' amma ka tayani addu'aAllah ya bani ciki kafin karshen watan nan inaganin haka zai saka soyayyata a zuciyar inna. Belloyace amin ya Allah, zan dukufa da addu'a kema kiyiAllah ya amsa mana. Ya goge matahawayen idanuwanta ya sumbaci kumtunta yace'' Haisamsunan danmu fa. Hanna ta kyalkyale da dariya tarufe ido sai taji wani farin ciki ya lullubeta. Tatsugunna ta jawo takalminsa ta fara saka masa akafa tana sake goge masa da tsumma. Ta feshemasa jikinsa da turare tace'' Kawu bello Allah ya kiyaye hanya kuje lafiya ku dawo lafiya. Yace aminHanna Allah yasa nazo na sameki lafiya cikin farinciki'' yana tafiya yana waiwayan hanna, itama ta fitohar bakin kofar dakin ta tsaya tana daga masahannu har ya shiga dakin mahaifiyarsa sannanhanna ta koma daki. A zaune a gefen gado Bello ya iske mahaifiyarsa tana tunani tana gayda kai yadurkusa ya gaisheta ta amsa a fusace ta fara masfada tace'' to dannan abunda nake so dakai shinekarka yadda kayimin musu akan duk hukuncindana yanke akanka ina nemar maka aure a gidandagacin garinnan yar sarauta ka dace ka aura tubda ka makalewa Hanna baza ka iya sakinta bato ta zauna anan gidan tare dani ita kuma waccamidan anyi aure sai a kaita gidan ka. Bello ya dagakai ya kalleta zuciyarsa cike da bakin ciki.Gidan da yasha magiya ta yarda akai Hanna takiyau gata da bakinta tana cewa yayi aure yakaimatarsa can amma banda Hanna ba. To ashe hannadin ta tsana kawai . Ya nisa yace inna me zai hanamu tare mu duka da amarya da hanna duk inhadasu acan din'' Ta girgiza kaia tace '' nace maka karka yimin musu ko? Haka naga dama, tashi kajeka dawo din mu karasa maganar amma idan kamatsa akan sai ka mayar da hanna gidanka zaka saince ka sake ta don wallahi hanna baza ta tare awancan gidan va sai dai idan bani na haifeka ba. Kobayan raina ka kaita can Allah ya isa'' Bello ya rike kai don takaici can yace'' Naji inna na gode, danAllah ki yafemin duk abunda nayi miki, idan na batamiki rai a rayuwata gaba daya''Tayi dariya tace ''Babu abunda ka taba yimin wallahi ko musun madaka tarka kake mun bayin kanka bane ta shanyeka ne na yafe maka Allah yayi maka albarka Bello ya mike ya fita hawaye ne shar yake fita dagaidanuwansa . Yana fitowa hanna tana jika gero tayisharkaf da hawaye daga gani ta gama jin dukmaganganun da suke yi. Kallo daya yayi mata yajihawaye ya sake kece masa. Yazo ya wuce tagabanta yace'' Hanna kiyi hakuri, ki sake yin hakuri, Allah yana tare da mai hakuri'' ta bishi dakallo tana hawaye yana waiwayanta yana hawayehar ya fice . Tayi shiru tana sauraren karar motarsuhar suka yi nisa ta daina jin karar motar, ta rushe dakuka tana cewa a ranta'' A bakin ciki ashe zandauwama? Yanzu aure inna zata sa kawu Bello zaiyi ya tareda amaryarsa agidansa ni abarni anan, meyasa inna ta tsaneni ? Me nayi mata tatsaneni? Meyasa kowaya tsaneni a duniyarnan ? Ubangijinayana sane dani, Allah kasan halin da nake ciki,Allahka fitar dani, Allah kaine abin godiya. Bayanfitar Bello madu da kamar awa guda. A lokacin hanna tana surfa gero, inna haule tana tsakar gidatana cin dumamen tuwo, indo kuwa daga wanka tafito zata shirya ta tafi magarya inda inna Haule zataaiketa. Suka ji ,Mota tururus ta tsaya a kofar gidansu.Wani ma'aikacine mai sanye da kayan 'yan sanda,yayi sallama ya shigo ba tare daya gaishe suba. Yace '' Nan ne gidan su custom Bello madu ko @inna haule ta tsaya dacin tuwonta tace '' Nan neamma baya na waye yake nemansa? Yace inazuwa'' ya fice, gaban hanna ya hau faduwa . Daf-daf daman tun jiya ta kasa bacci saifaduwar gaba take. Jingine tabarya da take surfe ta tsaya. Kawai ji suka yi ana cewa' ku kamada karfiwajen kafadan zaku rike inna haule ta zabura ta mike da gudu ta lekoHanna ma ta biyota da sauri idanuwansu sukagane musu wannan gagarimin tashin hankalin,Gawar bello madu ce ake shigowa da ita. Allahyayi masa rasuwa a sanadiyar hatsarin motar dayaritsa dasu yanzu-yanzun nan suna hawa hanyarsuta tafiya Agadas wata babbar mota ce tazo gwaramusu suka kutsa ta tsakiyar motar cikin ikon Allahbello ne kawai ya rasu, sauran sun sami munanan raunika suna asibiti. Hanna ta fadi ta suma,yayin da inna haule take neman tube kayan jikntadon gigicewa sai da aka rirriketa. kafin kace kwabogida ya cika yayi makil da 'yan uwa da makwabtamaza da mata. Ani masa wanka, an suturtashi ankaishi an binne kamar yadda sharia musulunci ta tanada. bello ya tafi ya bar rikici gidansa kuma shitasa ta kare a duniya domin rikicin duniya da mairai akeyi duk wani rai saiya dandana mutuwa Allahyasa mu cika da imani, amin. hanna tayiwa belloaddu'ar har yawun bakinta ya kame, idan ta ya gajida addu'ar ta rushe da kuka tayi ta huta haka dai har akayi sadakar bakwai 'yan zaman makoki sukawatse aka bar 'yan gida. yayin da bacci yakegagarar idanuwansu, kamar yadda inna haule takekuka cikin dare haka hanna ma sai ta laluba kusada ita taji ita kadai babu bello sai ta tashi tayi kukahar ta godewa Allah. kaico hanneta rasa kowa a duniya. hanna bata shiga. watamatsala batabangaran ci ko sha ko aikin gida ba har ta fitadaga takabarta.sai bayan ta fita daga takaba an fara zancenrabon gado sannan inna haule ta daka tsalle ta diretace babu abunda za'a bawa hanna na gadondanta tunda hanna ba haihuwatayiba da bello saidai ta hada 'yan komatsanta ta bar musu gida.kawu Ahamed yaji haushi sosai ya kuma lashi takobin ko sama da kasa zata hadesai ya kwatarwa'yarsa hanna hakkinta a tumuli takaba shari'ar shida inna haule har kotin koli idn bata bari an rabagadon nan da hanna ba. yace kuma babu indahanna zataje a gidan zata zauna sbd bello yana dagado a gidan ubansa, inna haule kuma tace ita kuwa baza ta bayar da dukkiyar belloba sai dai suzuba. makudan kudi kuwa aka kawo daga wajenaikin su bello, gashi da filaye da wannan tafkekengidan nan daya sha suminti da bulo. inna haulekuwa tace duk natae banda hanna ko sisi baza tabata ba tunda ko kwai bata saka a gidan ba. tashin hankali ya tabbata a zuciyar hanna ta rasa yaddazata yi da rayuwarta da kawunta zai hakura ya bariinna haule ta rike dukiyar bello dukka ba sai anraba da ita ba. duniyar nawa take wanda yatara ma ya tafi yabarta kowa ma mutuwa zaiyi. dukwani hango jin dadin. rayuwarduniya yagoge a zuciyar hanna babu abunda take bege sai mutuwatazo ta dauketa ta tafi ta hutaitama. daga gidankawu ahamed dake aiko mata da abincin dare darana. tafi tafiya suma wata rana basa aiko mata donyau da gobe sai Allah. hanna ta fara fitar dazannuwan daurawarta da kwanukanta tana siyarwa snnn taci abinci. wata rana da yamma daindo sunje rafi sun debo ruw suna tafe suna hira saisuka ji hassan me yekuwa yana sanarwa yanacewa "yekuwa. jama'a ga wata sanarwa, mai girmadagacin garin nan yace a sanar muku matawadanda mazansu suka rasu suka barsu da suzo fadarsa yanzun nan. ma'aikata daga nigeria sunzomusu da tallafin taimako. gwamnatin jihar kano anigeria ta aiko da taimakon kudi za'a raba musu jaridomin su rike kansu da marayin 'ya'yansu. ammakada wata ta kuskurataje idan ba mijinta bane yamutu, sai wacce mijinta ya mutu idon ta zunguri hana tace hanna muje wajen taron nan ko Allah zaisa mu dace. hanna ta rike baki tace babu ruwanmuyanzu idan mukaje ai mun shiga 3 a wajen innnacewa zatayi munje. mun tona musu asiri aci muka jemu tambaye tako zata yadda. a hanya sukadingahaduwa damata wadanda mazansu suka rasu suna ta tafiya gidan dakaci don karbarwannan tallafi mai tsoka. kowacce tagasu hannasai tace au, baza ku taho fada ku karbiwannantallafi ba daga nig fa bakin suka zo, indotace gaskiya hanna in baza ki ba ni zanje sbd idanmukakuskuramukaje gida inna haule baza ta barmu ba.amma idan mun riga munje mun karbobabu yadda zata yi damu fada ne dai da zagi yazama jiki. hanna tace to mu shigagidan. adama muajiye ruwa muje din daman gudun fadan inna nake,to kobabu abundamu kai ma kullum zagin mu takemuje kawai, suka shiga gidan adama suka ajiye ruwan da yake kansu suka nufi fada wajen taron.mata ne makil akan layi suma su hana sukajekarshen suka tsaya. wata kyakkyawar mata ce azaune akan kujera da tebur a gabanta an dorawasu fles akan teburin. kallo daya zakayi wa matarkasan tana cikin daula fatar jikintamulmul sumul. dukda matar ba fara bace amma ba baka bacekalarta mai kyau kayan jikinta kuwa ko ba'a gayamaka ba leshin zai doshi dubu hamshin sarkargwal da dankunneta da zubbunan gwal reras ahannunta guda hudu sai sheki sukeyi.matar maifaraa'a gata bata kyamar talakwa sai gaggaisawa dasu take suna yin hannu. tace. kowacce tazogabanta ta rubuta sunanta don asan yawansukuma nawa ya cancanta a basu. kowacce ta hauzara ido sbd basu iya rubuta sunanta. matar taceyanxu duk cikinku babu wacce ta iya rubutu tazo ta taimka min mu rubuta sunayenku?Hanna tayi shiru kamr tace ta iya amma gudunsurutun 'yan garin nan kar ace ta cika nuna iyawasai tayi shiru. Indo ta zungureta ta hanna bakn iyarubutu baki rubuta mana Hanna tace a'a indo baburuwana a samu wani yazo yayi dan kar ace nazogarinku na zake. Matar ta sake cewa To tunda babu wacce ta iya rubutu ina ganin ba zaiyu mu aiwatarda aikin da zamu aiwatar ba a yau sai mun nemowacce ta iya rubutu sannan saboda da mata zallamukeso mu kafa kungiyar dole mace ce zata zo tarubutu mana sunayen indo da taga kiri-kiri zasurasa bata san snda tace A'a ranki ya dade ga hanna ta iya rubutu" sauran suka hau cewa hannataimaka mana ke kuwa ashe daman kin iya rubuturubutamana karmu rasa Matar tace wacece hanna?Ta fito tazo nan Hanna taje gaban teburin matar tatsaya tace gani ranki y dade. Matr ta kalli hanna smada kasa wata burgujejyar doguwar riga wacce aka dinkintada wani wagambari mai kauri irin nddinnan itama kanwar kkrta ce ta bata, gashintatufke a tsakiyar ki tai gammo dashi da zasu deboruwa sai wani yalallen gyale baki ta yana akanta datakalminta dan madina akafarta. Matar tayimurmushi tace yaya sunanki? Hanna tace sunana Hanna Abubakar imam" matar tace HannaAbubakar kin iyarubutu? Hanna tace na iya ranki yadade, matar tace ko da yake ku anan french kukeyiba turanci ba ko irin na 'yan nig? Hanna tace ni nafiiya turancin nig, french din kadan-kadan na iyamijina yana koy min mtar taace , ta jawo kujera kizo nan kusa dani ki dinga rubuta sunayen su, ki fararubuta sunan ki sannan ki rubuta sunayen sauran.Hanna ta zauna tana rubutu sunayen matan nandaya bayan daya suna tahowa a layi. Ta gamatubuta sunayen sai magaruba tayi sai aka tsayar dashawarar sai gobe da safe su kra taruwa dan a raba musu tallafin sukanufi gidanjen su, matarkuma gidan dakci aka kaita a can zata kwana,namijin kuma da sukazo shima aka kaishi wanigida aka suke shi tunda dare yayi dokin gobe tayisu koma fada. Hann da indo kuwa sai suka haufaduwar gab suna shirya kalmar da zasu furta wajen kare kansu daga fadan inna haule. Aikuwadaga shigarsu gida ta fara yi musu fada donlabari ya kai mata cewar anga su hanna a fadasunje karbar jari. Tana cewa dole Hanna ki barmingidana sbd so kike ki koywaindo kinji da fitinawanda da bata iyaba, ki tafi can gidan ku acan ake yunwa ake neman jari mu nan Allah ya rufa manaasiri,kema indo tunda wanda ya du nuyinki ke da'ya'yankiya rasu bello ne damn yace shi zai dingaciyar dku gashi ya mutu dole kema asan yaddaxa'ayi idan bangaren gidanku zaku siyarmin to,idan ma wani zaku siyarwa dai duk daya ki karbi kudinki ki kada 'ya'ynki ku koma can Tawa localgobernment grinku. Ba zaku zo ban haife ku bakusamun hawon jini tunda kun hallaka mazan nakuni dai ku kyale ni. Washe gari da sassafe su hnnasuka tashi suka hu aiyukan gidan,bayn sun gaamsuka leka ko ina basu ga inna haule ba ta shiga makwabtasai suka debi bokitansu suka cewamasa'ud dan gidan indo in inna tazo yace mata suntfi deboruwa . A tamfar. Maikyau hanna ta daurabasu tsaya a ko ina ba sai a fada wajen taro, sunmadanmakara don ynzu tar da rabi wjen taro, sunmadan mkra don ynxu tara da rbi tayi suka ajiye bokitansu a lungu sukaje wajen taron matr ta. KalliHanna tyi murmushi tace hanna ke muke jira kifarakiran sunaye in rarraba muku kudin . Hanna tagaisheta faram faram da fara'a sannan ta krbitakardar ta. Fara kirn suna tace Hanna abubakariman ce ta farko, matar tace to ki kira sunayen daya bayan daya suzo subi layi sai kwai in dingamimmika musu kudin a layi Hanna ta fara kirnsunayen, kowace tan zuwa tana shiga layi kamaaryadda sunayen suke a jikin takrdar,byn hanna takammala kiran sunayen sai matr t mike tace tomadalla Assalamu Alaikum jam'a su duka sukace wa'alaikussalm tce ni sunana Haj Hindatu umardaga kano state nigeria. Nazo nan grin mai sunaDashi karkashin karamar hukumar mgarya a.Janhuriyar niger don in kawowa 'yan uwana matatallafi da taimako yaddamatan da suke da mazasuke samun taimako daga wajen mazajensu to ku da baku damazasai kusamu san'ar da zakutaimakawa kanku da marayin 'ya'yanku. Sukasatafi raf'-raf suna cewa Allah ya saka da alheri mungode hajiya hindatu. Ta cigaba da cewa dagagwannatin jihar kno matar maigirma gwamanjihaar kano ta bude wta kungiya wacce za'a dinga taimakwa matan da mazansu suka rasu sukabarsu. Shine taga ya dace mu shigo makwabciyarkasarmu Niger suma mu hada kai da gwiwamutaimaka musu saboda Abunda yayi nigeria shiyayiniger duk uwa daya uba daya muke, tafi sukahauyi suna murna suna cewa Allah ya kiyaye Nigeriada gwannatin jihar kano Hajiya Hindatuumar taci gaba da cewa yanxu anan garin zamukirkiro wani suna mu saka wa wannankungiyatamu. Don mucigaba da turo muku tallafi tako ina daga kasarmu. Bani za bawa kungiyar nansuna bku d knku ykmt ku saka mata suna. Nan dai wannan tace a sa mata kaza wacce tace asa mt kazadaga karshe di. Suka tsayr da shawarra akan asawa kungyar sun hindatu umar, tayi darya tace a'aba sunana za'a sa ba sbd wata kila baz ku sakeganinaba saidai kuga an turo muku wata sbdmuma acan 'yan kungiyar muna da yawa idan aka turoni yaugobe wata za'a turo muku. Amma yanzutunda ga wacce taiya rubutu da karatu hanna itazata dinga wakiltarku idan ta kama mahar cannigeriazata dinga zuwa tana karbo muku tallafi inaganin idan kun amince asawa kungiyar sunnhanna. Gaba daya suka hau cewa mun amince asa sunan HANNA,Dagakarshe matar ta jawowata jaka ta fara mikamusu damin kudi kowcce kudin data samu idanaka kiyasta dakudin nigeria zaiyi kimanin nairadubu sha biyar-biyar. Bayan kowacceta karbataceba'a kare ba.akwai atamfofi da wasu kudadenda za'a sakebasu shima daga gwannatin nigeria saidai basu zo dakudin yanzu ba amma idan zaiyusu nada wata daga cikinsu da zataje ta wakilcesudan taga waje tacigaba da zuwa su sai suka hadabaki suna cewa mun wakilta hannaa matsayinwakilyarmu. Hjy hindatu ta juya ta kalli hanna tacekin amince hanna zaki bini nigeria kidinga karbo musu taimakon? Hanna tayi murmushi ta ce hjymezai hana sai in biki din akan haka sukayi sallamacewar hanna zata bi hjy hindatu kano don karbomusu wasu tallafin masu yawa,kafin hanna tabimatar saida taje da sauri gidan kawu ahmad tashaidamasa duk sha'awarda sukayanke akanta ya amince ya kumayi mata fatan Allah yasa su dauketaaiki ma acan tayi yace idan da sarari tajemakarantarsu takarbo sakamakon jarabawarta tanemi aiki ko Allah yasa ta dace. Ta rabakudintagida 2 ta bashi rabi. Ta sake rabanata gida 2tabawa matarsa hajir. Kogidan inna haule bataje ba dauko kayanta kawai ta fada motar su hjy hindatuumar sai tafiya daman hjy hindatu tayi. Sallamadagaci dasauran hakiman garin tabasu kudi masuyawa sumata sanar musu zata tafi da hanna dontasake karbo musu wasu kudaden taimako. Sunyimurnasosai sun shi albarka sunyi musu fatan Allah yakiyaye hanya. Mutumin da sukazo dashimai sunashehu shine yake tuka motr hjy hindatu a baya tazauna hanna ce ta zauna a gidan gaba, motar kirarhumma jeef dindimemiyar motamai dauke darundumemyar rikoda an saka sauti mai tashi a hnklsai sanyayyiyarna'urar sanyi ce ke dukan jikin hanna. Cikin motar ma abun kallo ne lallausankujerun motar su suka sa hanna ta nutsu komagana bata iyayi,tace a ranta Allah ya baku duniya wannanmota ce kawai ba gida ba, Allah mai azurta wandayaso sun hau titi dodar suna zuba gudu a titi saihanyar kan karfe 3 ma a ciki garin kano tayi musutafiya suke kamar bayi sukeyi ba sbd babu watakura ko gjy irin ta matafiya a tare dasu. Hanna sai kaallon kano takeyi galala komai yaci gaba bakamar lkcn da ta zo ba. Babu abinda ya fado mata arai sai ranar data zo wajen haisam zuwanta kanona farko kenan kuma bata taba ska ran sakedawowa ba ashe zata dawo yanzu Allah ya kawodalili. Ta dinga kallon haanyoyi ko zata gane gidan su haisam amma ina ba tama gane hanyar ba balleta gane gidan. Haism haism take kira a zuciyartayayin da kwalla ta cika mata idanuwanta. Tamadubi hjy hindatu take kallonta tace hanna yayadai naga kamar kwalla ta cika miki ido ko iskar ACce tyi miki yawa a ido a rage? Hanna tace a'a babu komai suka cigab da tfy can hjy hindatu tace hannaga garinmu fa, kano kenan kin taba zuw kano netunda naga kamar a nigeria kikayi karatu? Hannatace nan FGGC kazure nayi na taba zuwa kano saudaya sheraka 2 da suka wuce amma bazn iya tunaina ne unguwar dana zo ba, sulemanu cresent sunan unguwar , hjy hindatu tace oh sulemncresent sunan unguwar ai bamu da nis sosai ynxumun ahmdu bello way zamu bi ta wajejen dai ni asokoto rd farm center nake zan nuna miki kwanarhanna tace to suka cigaba da tafiya.Daidai get din wani tsantsereren katafaren gdamotar su hanna ta tsaya yayin da mai gadin ya tasoda sauri yazo ya bude musu. Hjy hindatu ta kallihnna tce hanna nan gidana ne ina so muyi sallamuci abinci mu huta wajen gobesai in kaiki wajenkungiyar subki tallafi a kaiki can garin naku ko? Hanna tace babu komi na gode hanna taga duniyawannan gida shine ake kira aljannar duniya sbdkana shiga farfagiyar gidn wasu fulawoyi ne anzagaye wani dan tudu yana ta bulbulo da tsuntsayemsu kyau aka watsa a farfagiyar gidan sunt t yawocan gefe kuma wajen wnke ne (swimmingpool) an kewye da wasu kujerun hutawa cn gefe kumawjen wsannin ne ma motsajiki (games) wajenbsket ball, tble tannis, football da sauransu. Iskuma gawta tafkekiyar kofa wacce zata kaika cikingidan. Daga can bay kuma boyi quarters ce itamakamar wani katfaran gidan. Arziki ma anan ai ba'a magn kai kce a turai kake ba'a nigeria ba. Hjyhindatu ta yukura zata fita dagcikin mota ta juya takalli hanna wacce ke zune tayi turus tace hnna fitoman hanna tj kofar zata bude ta kasa sai da hjyhindatu ta fito daga kujerar baya tabude mata tawaje snn hanna ta fito, gidan ya baw hnna sha'awakwrai da gaske. Tace hjiya gidanki yayi minkyau wlh, ta kalli hnn tayi murmushi tace nagodehanna.Wani dogon saurayi ne kyakkyawa a gefe azaune akan wata kujerar roba yayi tahumu ya rikekai. Hjy hindatu taje ta sameshi tana zulayarsa tacemijin me akayi maka yau? Kana ganina ko ka dagokayimin magana ko budurwarce ta baka maka rai?Daga nan hanna ta tantance kanin mijinta ne wasan kanin miji take yi masa, ya dago a sanyaye ba fara'ada kyar ya kalleta yace antynah muje daga cikimuyi mgn. Hjy hindatu t kyal kylle da dariya tace kaidalla rago nasan fada ku kayi kai da ummi dukydda kayi. Yace wannan me sauki ne muje ciki dai,ya juya ya halli hanna yace anty wacece wannan? Tace yar niger ce yace niger? Daman niger kike jeyau kwana 7 bakya nan ? Tace eh ehmuje ciki dai,hanna zo mu shigo ciki. Suka isa wani tafkeken falowanda zan iya kiransa aljinnar dunita anan hjyhindatu ta ajiye jakarta akan kujera ta kshingidadon gjy. Tace da hanna zo ki zauna bakuwa kema kin gaji hanna tayi murmushi dukka snsan jikintaya dau sanyin na'auraa, a fakaice kallon alatun dasuke jifge a falon take take tana tambayar zuciyartaabunda bata sani ba bata taba gani ba. Saurayinyaje wjen wata (telephone) waya da take sakale ajikin bango ya dauka yana latsa wasu lambobi can da aka jima yace" hello hjy ga aunty ta dawo ashewai niger taje. Hjy hindatu ta tshi zune tace lhhajiyrku kake gayawaa ashe niger naje damanhaka kake kai in an gaya maka magana sai kafada? Yazo a sanyaye ya zauna akan kujera yaceaunty dole fa hjy tsn kin dawo kuma in kika je tunda neman ki ake yi tuntuni "hajiya hindatu tacehjyr a asibiti take ko kuma a ofis? Yaya mai jikin inata tambayarka baka bani amsa ba? Yace yana canyaji sauki tace bari. Inje inyi sallah inje in duboshi,hour yanzu basu sallameshi? Yana premier hospitalko Aminu kani aaka mayr dashi? Ya ce yana can dai. Tace wai meke damunka ne duk da kyaar kkemagana na lura. Hanna tace wani ne bashi da lfy?Allah ya sawake. Hjy hindatu tace wlh mai gidanane bashi da lfy yana asibiti. Hanna ta girgiza kai tacekai kai Allah ya sawake masa, ciwon ya tsananta nehaka har da kwanciya a asibiti me ya same shi? Tace ciwon a zuciyarsa yake ciwo ne sosai yakefama wallahi hanna. Hanna tace zuciya? Is tarableAllah ya bashi lfy. Ramlah tace amin shigo gabandaki muyi sallah ko azahar bamuyi ba gashi 3da rabi yanzu la'asar ta kusa. Hanna na biye da itahar wani katafaran daki mai dauke da wani kayataccen gado a ciki dakin kuma da wanikyataccen bandaki. Hjy hindtu tace hnna ta shigabandaki tayi alwalla idan ta fito sai ta shiga . Hannata shiga bandaki sai da tasha kallo ta gaji sannantayi alwalla ta fito. Hjy hindatu mata shiga ta dauroalwalla.Suna idar da sallar azahar sai kwai suka yi l'asardon lokaci yayi hnna na tahiyar karshe hjy hindatuta idar tana jan carbi suka juyo na rafsa kukakamar na mutuwa a babban flo a guje hjy hindatuta fita hanna kuma ta hau sauri tana so ta idar tajeitama taga meke faruwa hanna taji ihun ya kara karuwa da hjy hndatu ta fita kuka wiwi sukeyi.Hanna ta fita da sauri ta iske mata makil a falo anata kuka. Hanna tayi kasake tana kallonsu bata sanme ya faru b balle tasan me zata ce musu. Hjyhindatu ce ta taso tazo ta kama hannun hamma takawo ta tsakiyar matan nan wadanda suka doshi su ashirin. Hanna ta durkusa akan kafet ta gaishesuwata kamillliyr datijuwa mai kyau ta dago da luhu- luhun idanuwanta ta dubi hanna ta juya ta kalli hjyhindtu tace ramlah wacece wannan? Tce wannanitace hannar haism. Su duka suka bude ido da bakisuka ce hanna, hanna ce wannan ina kike nemota? Ta rushe da kuka tace har niger naje na nemota saigba daya ka rushe da kuka. Hanna ta kasa ganeabunda ake nufi, knta ya daure abunya batamamaki. Tce meke faruwa, a ina nake anan? Hajhindatu ta goge hawaye tace hanna nan kano ne.Ta nuna wannan dattijuwar matar tace wannan itace mahaifiyr haisam! Hisam! Haisam haj hindatuta ce haism. Ta nuna wannan saurayin tce wannanizziddin kanin haisam ne, ni kuma ba sunana hjhindatu ba, sunana ramlah nice matar hasamhanna ta zabura ta mike tsaye tace ramlah, mekefaruwa, me nayi miki? Ramlh ta jawo hannun hanna ta zaunar da ita tace zuna hnna zan bki lbrnhism ynxun nan, hanna ta koma ta zauna asanyaye ta tattara hankalinta baki daya a sauraronramlah,Ramlah ta sharbehawayen da suka cika mata ido tace hanna, hisan,yana sonki, haisam ne mai sonki, babu wani maisonki a duniya irin hisam. Haisam yafi kowakaunarki a cikin duk masu sonki a duniya hannatace ramlah meyasa kika ce haka? Ramlah tace abunda yasa nace haka shine haisam bai taba yinsoyayya ba sai akanki, bai taba ganin wata 'yamace ba a duniya da yaji yana sonta kamarkihanna, hanna ta dago ta kalli ramlah tace ammahaisam ke ya faraa kafin ma mu hdu dashi houryayi miki alkawarin zai aureki. Ramlah ta girgiza kai tace hiasam ya sanni tuntuni amma ba sona yakeba. Allah ya jarabeni da tsananin son haisam tunmuna america idan sunje hutu gidnmu. Nashasanarwa mahaifiyata sai tace kada ma in fara bazaiyiwu ba, saboda mhaifiyar haisam kaawarta cetasha gaya mata cewa haisam bashi da ra'ayin soyayya yace shi bai taba jin yana son wata bakuma yana ganin bazai taba ji ba, har muka dawokasar nan. Amma naki hakuria naci gba da cusasoyayyar haisam a zucyata, na dinga kokarinnunawa haisam irin soyayyar da nakeyi masaamma sai yake nuna min baisan abunda nake nufi ba. Da nag haka sai na dinga bin ta hanyr iyayenmudon na sami haisam, da farko mahaifina na samunasa masa kuka cewar in ba'a bani haisam b xankashe kaina. Mahaifin ya lallashe ni ya ce duk maisauki ne zi sami mahaifin haisam. Haka kuwa akayimhaifina yaje ya sami abokinsa mahaifin haisam ya shaida masa bukatata. Sbd da sanin raa'ayinhaisam akan soyayya bai amsa masa ki tsaye basida yace zai tuntubi haisam zai kuma yi shawarada mahaifiyar haisam kusan shekara guda bamujiwata cikekkiyar msa ba daga gidansu haisam to sainasan haisam yaki amincewa ne yasa babu wata cikekkiyar amsa da naji game da bukatata akannifa har yanxu ina son haisam, babu irn kalmar damhaifina bai furta min b wajen wayar min da kaiakan in cire son haisam, in so msu sona ga sunnbarktai suna zuwa, naki nace lallai-lallai sai haisam,Nazo nyi yjin ikin cin binci naki ci naki sha naakaura daki sai kuka. Iyayena suna ta lallashina nkicanj ra'yina. Shi kuwa hisam bai san ma abindanakeyi ba, yn can jami'a yana karatunsa. Kawrkirauda kanwata nake aike da wasika in shaidwhaisam halin da nake ciki amma bai taba bani amsar wasikata ba. Ko dda naje gidansu bayacemin komai koda zamu yini tare ko uffan bazaicemin ba. Haka idan yazo gidanmu wajen auwalyayna abokinsaa idan muka gaisa babu binda zaisake cemin ko hira nake musu bai cika sa baki ba.D mahaifina yaga na dmu sosai da son haisam shine ya sake samun mahaifin haisam suka zaunasukayi magana sosai mahaaifina y nunaa bacinransa yace b yadda za'ayi suce haisam yakiamincewa tunda bashi ya hifesu ba, susukahaifeshi in har suna so zasu san yadda zasu sshi yaamince dole. Gudun kada abokantarsu ta baci mahaifin hisam y kira haisam yace ko yaki. Koh yaso is ya aureni, da farko mahaifiyarsa taki tacebayayiwa a yiwa namiji auren dole abarshi tundayce bashi da ra'ayin soyayya gashi yanzun kara2yake a lkcn yana shekararsa ta karshe a jami'a.Mahifiyar hisam tag dai abun zai koma tashin hnkl tsakanin ta da mahaifana da kuma mijinta sai taamince tace ayi auren, taci gaba da lallaba haisamakan ya yarda ya iya bikin. Da aka zo sa ranarauren yy habib sai aka had damu. Aka sa ranaraurenmu shera daya dai daii lkcn da haisam zaigama bautar kasa ni kuma na gama sakandire sai ayi bikin. Har lkcn da ka sa mana rana haisam baitaba zuwa gidanmu ba da sunan yazo zance. Nicekullum nake yi masa waya musamman da tsakrdare. Yan amsa mun wayar amma wani lkc sai yyibarcinsa m ya barni a layin wayar ina magana nikadi. Hak a cikin hirarrakin da muke akwai wasu tambayoyi da nake yi msa bi tba amsa mun ba sidiyyi shiru. Tambyoyin kuwa shine hisam ynxunkuw kana jin sona a zuciyarka? Meyas baka zuwgidanmu znce? Idan ban ganka b ko naji muryarkabana iya barci kaifa? Baya amsamin duk watatambay data jibanci soyayya, n sni kuma n gane haisam b sona yake ba kiri kiri amma idona ya rufetunda ni ina sonsa zan iya zama dashi a haka.Haisan yana bautar kasa. FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama sai ranar daurin aure a bda dasadaki in zama matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na sami wani na aura don shi kuma sai nan dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa. Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka zuba mana ido Sai addu'a.Haisan yana bautar kasa. FGGC kazaure ina gidainaa jirns ya gama sai ranar daurin aure a bda dasadaki in zama matarsa kwi ya rage. Kwatsam sahaisam ya kammala bautar kasa sai yace shifa yakammala butar kasa sai yace shifa ba ynzu za'ayibikin ba ayi na yay habib tunda shine babba ayi namu daga bya. Aka yarda da bukatar haisamtunda lallabashi akeyi akayi bikin yaya habib. Iskwi mukaji haisam ya koma FGGC kazaure amatsayin cikakken malami wi shi koyarwa yakesoyayi shiyasa ya nemo ikin can, nace na yarda ayibikin zan iya binsa kazaure mu zauna, hk dai haisan yayi tayi mana hanya hanya yaki yarda yibikin. Da yaga an takur masa ance sai ya barokazaure ya dawo kano ga kamfanin babansa ananzaiyi aiki ayi bikin mu kuma shi yace shi ya aminceidn na sami wani na aura don shi kuma sai nan dashekara 5. Nace na yarda zan jira shi in shiga jami'a kafin nan nima na kare sai muyi auren kawai. Ranmahaifina ya baci mahaifiyatata zazzgeni tace bazanjira shi ba sai kace bani da zuciya wanne irin so newannan. A lokacin akwai wani saurayi nai sunaDalhatu dan jarida ne yana sona sosai. Yana so yaaureni nace ni bana sonsa bazan aureshi ba daidai lkcn nan an turashi BBC london yace idan anyibikinmu sai. Ya tafi dani can london nayi kara2jami'ata, naki fur. Babu irin nasihar da iyayena basuyimin ba da lallashi naki ji nifa idan ba haisan basaidai in fsa aure. Iyayen haisan. Ma sunyi iya.Kokarinsu wajen tlastawa. Haisam ya dawo yazo ayi. Bikinan namu sai ya daina zuwa wkend din mada yake zuwa kwata kwata. To. Kowa. Ya rasa.Yadda zaiyi damu suka zuba mana ido Sai addu'a.Na shiga jami'a a nan kano BUK ina karantar.Bangaran lbrn 'yan jarida (mass com) ina Karatunaina jiran haisam na sami samari kalakala akwaikyawawan da suka fi. Haisan kyau nesa ba kusaba, akwai masuarzikin da suka fi haisam, masusona fiye da haisan amma. Na kisu ni sai haisam don bazan mant ba har mahifiyt tke cemun zakiauri haisam in n takura masa mma bazaki samisoyayyar da kike nema ba. Nce idan anyi auren zaisoni ai. Nasa kanwata rauda ta binciko. Mun wanneirin buri ne haisam ya kudira a FGGC kazaure yakeso y cika kamr ydda kullum ake cewa, rauda tace ai wata yarinyace year jinsu mai suna hanna yacekanwarsa ce tana jin sbd it yaki barin mkrntr nasrauda taci gaba da lura d binda yake gudanatsakanin hasam da hanna kuna ji 4 (ss1) rauda tzomun da cikekken bayani game da binciken danasata tayimun. Tace abu ya tabbata haisan son hanna yakeyi,duk mkrt an sani zance ya fito fili. Tabani lbrn irin gwagwarmayar da akayi tsakaninhaisam da malai masu takurawa hnna da dalbaimasu takura miki yaya habib ma ya fada manayadda sukayi da haisam har hisam ya wawaroadda kamar dabawa masa, yaya habib yace haisam sai addu'a sbd kamar ya zautu a son wata yrny donhaka nema yaki dawowa.Raina ya baci sosai da naji nce haisam yana sonwta, na lashi takobin ko wacece wannan hanna saina ga krshent ko a ina take, shine nabi direban muda zai dauko rauda ranar hutu don inga wacecewannan hanna? Kuma 'yar waye? Dame ta fini dahaisam yafi sonta dani? In kuma ja mata kunne akan ta rabu da mijina, don alkcn yadda nakeji zaniya hallaka duk wanda yake kokarin ya rabani dahaisam, naje mkrt na tarat bakya nan ance suhaisam sun tafi dake sai muka biki garinku mukatarar bakya nan sai mahaifinki. Na fadimagangannu iri iri a cikin bacin rai sbd mahaifinki ya rabaki da mkrtr don ki rabu da haisam, haisanbai bar kazaure ba is da kika gama mkrt da sati 2snn ya dwo gida da kaynsa, mahaifinsa na ganinsacewa yayi haisan har ka cika burin daka kudira kadawo? Haisam yayi murmushi yace eh baba,mahaifiyarsa tace idan baka gama cikawa ba ka koma ka gama ka dawo ramlah na jirnaka ayi bikinku, haisan yace ya gama saidai kuma yazo wajensuneman alfarma guda daya donAllah su taimakamasa , suk bukaci haism daya fadi abunda yake soya fada inshaa Allahu idan bta fi karfinsu ba zasuyimasa sai ya zauna ya basu lbrn ki tas tun daga ranar da aka kawo ki mkrt har halinda kike ciki agidanku, ya kuma bayyana musu tsananin son dayake miki yace su taimake shi su bashi izini yahadamu mu 2 ya aura sbd kece rywrsa zai iya shigawani hali idan suka ki amincewa masa, bai rufebakinsa ba mahaifinsa ya daka masa tsawa yace bazai yuba karma ya sake yi musu wata magiya.Mahaifiyarsa ma tace in har ita ta dauki cikins wata9 ta hifeshi yasha nononta har ya girma to bataamince masa ya auri hanna ba.Kwana 2 haisam ya kara ramewa kullum kagnshi yana tunani kallo 1 zakyi masa kasan yanacikin wani hali na tsananin damuwa, ya daina ci yadaina sha balle yayi hira da mutane mahaifinsa dayaga haka sai ya kira shi yce yaje ya sameni yayimin bayani akan ko zan yadda ya auremu mu 2 idan na mince to zaije ya sami. Matarsa mahaifiyahaisam ya lallashet ta yarje masa, haisam ya samenia lambun gidan mu da yamma. Yake cewa intaimakeshi in ceto rayuwarsa ya auremu mu 2 ni dake, na kekashe kasa nace ban yarda ba, hism yadurkusa gwiwoynsa 2 a kasa yana rokona ina duba girman Allah da tsknin iyayensa da iyayenatun suna yar in barshi ya aureki yayi min alkawarizaiyi adalci a tsakanin mu kawai don ya ciro hannadaga cikin wahala ta dwo wajensa ba don yafisonta ba a kaina. Mahaifansa sunce in har naamince suma sun yarda ya aure mu mu 2. Nace har abada bazan taba amincewa ba. Hawaye ne yakezubowa daga idanuwan haisam yana rokonaamma naki fur.Ramlah ta sharbe hawaye tacigba da cewa.Bayan anyi hak haisam ya hkr akyi bikinmu ranardaurin aure ma haisam kuma yake ko. Bidiyo kasetan nuna babu abinda zaka gani a idanuwanhaisam sai hawaye, anyi biki an kaini gidana kowaya watse aka barni da haism. Babu binda haisam yake saidai y zauna a falo yayi shiru yan tunani saiinyi mgn sau gom haisam baya sanin binda nakecewa yana can yana tunani. Hira wannan ba mayida haisam balle zncen wata soyayya. Ina alkunyaina sharewa a matsayin na sabuwar amrya baikamata in dinga binsa shi namiji bai bini ba. To. In hour znyi sati ban shiga bangarens ba bazaizo indanake ba, gaisuwa ce kawai take hadani da haisam,bayan mun gaisa sai kllo da ido ko abinci na kaimasa baya ci sai dai ruwan shayi kwai yake sh, tunyan lekawa ofis wajen aikinsa kmfanin babansaanan yake aiki harm ya daina zuwa kwata kwata. Yaynsa habib yayi fdn har ya gaji ya kyale shiabokansa gaba 1 mgn suke meke damun hsam yacanja gaba 1 bay zuwa wajensu babu. Walwalabayason yin mgn ko sunje wajensa. Nim har wnnabu na haisam ya fara damuwa, inyi wanka inacaba ado amma haisam baisan nayi ba, is muyini a zaune haisam bai dago ki ya klli fuskata ba balle yaga jan baki da hodar dana shafa balle yaga fari daidon da nake yi masa da kallon soyayyar da nakeyimsa, in tkace miki. Munyi wta 4 cur da haisam. Hkko hnnu n bai taba rikewa ba blle ya shiga dakina.Is da abun ya isheni nayi yaji n tafi gidansu naje na sami mahaifiyrrsa na shaida mata halinda muke cikida haisam, ina kuka kamar xan mutu. T lallashenitace in daina kuk muka tafi gidan ni da ita mukasami haisam a zaune a flonsa. Kan kujerar dayasaba zama yayi tagumi. Yana tunani kamar ydda yasaba. Hjyr sa tayi masa fad sosai ta shada masa gara ya ski jikinsa ya dwo da walwalarsa zmansa danidram kuma har abada baza ta yarje masa yaje yaauro wata hanna ba. Bayn nan ne haism ya yardaya shiga daki na da daddare wani babban takaici.Ma muna kwance tre yana kirana da sunan hanna.Nayi fadan nayi fushin saidai ya bani hkr yace mantawa yayi gobe. Ma haka. Jikina ya fara sanyina fara sarewa na fara fitar da rai akan smunsoyayyar haisam yayi nisa sosai a fagen son hanna.Kullum sai ske dulmiya yke a tunanin hannah,baya cn abincin kirki ba'a hira dashi sidai gashi nanne kawi yana kano amma zuciyarsa tan babbanmutum garinku. Wasu lokutan da ymma yakn shigalambu yan busa wani dan karfe dogo kamr naazurfa da nayi bincke aka ce bun busrki ne akwai wsu tsakiyoyi. Akwatinsa suma wasu lokutn yandauko su ya baz a gdo da wani hoto tun. Kuna jjs 1ke da rauda kanwat da nusaiba haisam natsakiyarku shim ya kura ido yana kallo in takicemiki soyayya ta fr zautar da haisam ni kuma inagefe ina son maso wani, ni da dutse duk dya nake a cikin gidan. A haka muka shekara da hisam saimuyi wta 3 snn nake samu ya shiga dakina, tokoda ya shigo ma ba farnta min zaiyi ba dagakarshe sunan hanna zai dinga kirana. Nyi fad, nyiyji har na gaji haisan bay tnkamin balle ya bini bikoidan nayi yaji, da kaina nake zuw in dawo. Ban sami kulawar haisam ba, bbu soyayyarsa. Akwaiabinci , ga kudi da duk wani bu najin dadin duniyakatafaren gida, galla-gallan motoci duk waccenakeso it xn shiga. Mahifiyar haisam ce take yiminsutura. Ba'a yin wata gud is ta aiko min da dinkunahaka mahaifinsa ya budemin account. Banki yana turomin da kudi, yay hbib duk wata yake siyominkyn abinci komai da komai. Mahaifana knsu dakafarsu kudi suke bani suna kara rokona inci gabada hkrn zma da mjina tunda ni nace nji n gani inasonsa haka. Amma dukka gatn da surukaina sukeyimin da iyayena duk a banza ne ba dadin rywta nkeji b tund na rasa soyyyar mijina. Kowa ya rsakan haisam an rasa yadd za'a kamo bakin zrenbare a ware mana matsalar mu. Wani lkcmahaifiyata t kirani take shwarta ta ko zan hkr dawnn aure inzo in auri mai sona shima yaje ya aurowacce yakeso nace I ni ko da xan mutu gara inci gab da zama da haisam a haka sbd tsananin son danake yi masa.Haka nci gba da zam d hisam, kullum a cikintunani yake hour zuciyarsa ta samu matsala yakwanta ciwo likitoci suka ce lallai lallai haisam yancikin mtsananciyar damuwa ta tunani da kunci dolea dinga kwantar masa da hnkl don har zuciyrsa takamu da ciwo sbd damuw, bamu Da maganin wannan matsalar ta haisam sbd kece maganintsananin sonki shi yke damunsa. Don haka ciwonhaism yaci gaba da yaduwa kusan kullum a asibitihaisam yake daya ya dawo gida sai ciwo ya tashi amayar dashi asibiti haisam ya rame yayi duhu abintusayi. Wani abin mamaki a karkashin filonsa na asibiti abun busrki ne da tskiyoyinki yke ywo dasu.Likitoci sunyi sunyi da haisam ya rage damuwa sbdsamun lfyr zuciyrsa abu ya faskara. Akwai lkcn dahisam yayi wta 2 a kwanace premier clinic jikinbabu sauki saida aka mayar dashi aminu kanoteaching hospital amma in yanzu kaga haisam zaka dauka kafin ka fita bakin kofar dakin zi mutu sbdtsananin jin jiki da yake. Numfaninsa sama samadakyar abun tausayi,Hanna ta rushe da kuka gaba 1 wajen sai akafara hawaye, ramlah ma hawayen da take ya karakaruwa. Taci gaba da cewa nafi kow sanintakamaimai maye ke damun haisam ina ta zarginkaina nice silr wannan ciwon na haisam tunda nicena raba shi da abar kaunars. Da naga haka sai na yankewa kaina shawarar kawai in shiga gari dukinda hannah take inje in nemo wa haisam sbd itacekadai soyayyar da xan nunawa haisam amatsayina na mai tsananin sonsa banason in rrasashi gaba 1, gara na nemo msa maganin wannanciwo da yaki warkewa fiye da shekara 1 yana fama. Ban bari kowa ya sani ba, bn shawarci kowa ba nashirya tsaf da kayana da guzurina da direbana nashirya fita neman hanna, na yiwa surukaina daiyayena sallam akan zanje kd gidan wata kawatada mijinta ya rasu inyi mata ta'aziya kwana 2 kawizanyi, mahaifiyata ta nemi ta hanani tfy sbd ga jikin haisam yayi tsanani yana kwance a asibiti yaya za'yiince xanyi bulaguro duk da ma dai bani bace nakezaman jinyarsa kaninsaa ne izziddin damahaifiyarsa ai is suga ban damu dashi ba harkatama na tafi, nasan hakan data fada gsky ne baikamata in tafin ba amma nace ni dai zanje ba dadewa zanyi ba. Tayimin fatan Allah ya kiyayehanya sai na dawo na tafi.Kowa ya gyara zama dan yaji ci lbr cike da mmkda tausayin ramlah kowa ya zuba mata ido yanakllo musamman hanna. A zuciyata cewa tke waishin ko mafarki nake ne bad gaske bane ni ramlahta nemowa haisam, yi zanga haisam kenan? IkonAllah, Allah mai girma, Allah na gode maka, ko bazan auri haisam ba in ganshi ma nagode waAllah. Ramlah taci gaba da cewa "babban mutumgarinku na nufa na rasa gidan naku ma sai damuka yi tambaya don bn manta sunan mahaifinkiba mallam habu, nace yana da ya hanna wata farakamar da farko basu gane ki ba da hnne suka fi sanin ki ashe ko yar baba nace kece sannan akakaimu gidn naku she mahifinki ma ya rasu? Hannata gyada kai tace yafi shekaru 2 ma da rasuwa.Ramlah tace Allah ya jikansa. Mahaifiyar haisambabu abinda take iya cewa sai kuka kawai takeyikamar ranta zai fita mahaifiyar ramlah ce take rike da ita tana lallashi itam kuka take. Ramlah tace saimatar babanki muka iske take cemin suma basusan inda kike ba, kanin mahaifiyar yazo ya duke kitun bayan rasuwar mahaifinki kun tafi ksarsuniger. Na tambaya wani nigertace Dashi sunangarin muka kwana sannan muka nufi garin Dashi. Na dan sha wuya kfin nagano inda kike. Munyikwana 2. Gidan wni bawan Allah a grin muna yiwamatansa kwatance sai can daya daga cikin matantace hnna matr marigyi bello mdu custom. Nacemijinta ya rasu ne? Sukace ya rasu harta fita dagatkaba, naji dadi da sukace a ynxu baki da miji don zan iya tahowa dake, to amma yaya zanyi gashibaki sanni ba yan wanki da yanuwn mijinki ba zasubari in taho da ke ba, na tambaye su 'ya'yankinawa yanxu? Suka ce baki taba haihuwa b watankibakwai d aure mijinki ya rasu ya barki, sai kawai natuno wata dabara nace to tunda mijinki ya rasu bari ince daga gwamnatin jihar kano matar gwamna taaikoni don in kafa wata kungiya da za'a tallafawamatan da mazajensu suka rasu suka barsu damarayin 'ya'ya. Haka kuwa akayi nasa aka rakanifadar maigari Ni da direbana muka hada bkimukace tare aka turo mu. Dajin hak mi gri da jam'ar gari yasa akyi shela aka tar mana matan da mzansusuka rasu suka brsu. Kallo 1 nayimiki na gane. Ki,sbd na sanki a hotuna a wajen raudah kanwata tunkun aji 1 har aji 6. Tund nasan kin iya rubutusauran basu iya ba, nace to wacece tazo ta rubutasunan ta basu iya ba, nace to wacce ta iya tazo t ding rubutawa suka nun ku kika zo kika rubuta.Na babbaku taimakon da zn baku sannan nacetunda kin iya rubutu to ke zki dinga wakiltar sukina karbomusu taimako dga kano na nemi d kibiyoni kano, naci sa' kuwa 'yanuwanki sukaamince kika biyoni, don kawai in kawo ki wajen haisam.Wannan karon hann murmushi ne y kece matasbd tsananin farin ciki. Ta sake tattara hankalintawajen rmlh tana suaronta. Ramlah ta cigaba dahawaye tace hanna gaki a tsakiyar faalon gidanhaisam don kece kadai mganin da zaisa haisam yawarke daga wannan matsannancin ciwon zuciyar da yake fama dashi "ta sharbe hawaye tci gba dacewa Haisam ya sha wuy hanna a sanadiyyartsananin sonki, haisam ya rasa walwala a rywr sa asanadiyyr tsananin sonki. Haisam mi kaunar ki nefiye da duk wani mai sonki a duniya. Sai yu hnnataji amsar wnn klmomi data dde tan nemn dalilin da ke cewa haism yafi kowa sonta a duniya. Mahaifintane y fara fada mata, Bello madu ya fada mata haka,snn ramlh ta fad mata. Lallai na yarda haisam yafikowa sona. Hanna take fada a zuciyarta. Ramlah tasake rushewa da kuka mai tsanani tace ban barshikuma ya auri wacce yke so ba. Hanna ta matso na rungume ramlah tana lallashinta tana bata hjr itamakukan tkeyi, ramlah tace hanna dole nayi kukadole na dauwama a cikin bakin ciki har karrshenryw ta sbd halin wahala da bakin ciki dana jefahaism na cuceshi na cuci kaina. Hanna tce antyramlah daina cewa haka Allah ya rubuto sai anyi haka amma bake kikasa haka ta faru ba, ramlah tadago kalli hanna tace haisam ya sha wuya, kullumyan tunani kamar ya zautu don wni lokaci sai kagayayi murmushi yace hanna kenan tsananin tunaninki da yakeyi. Ni dai ina tare da GANGAR JIKINhaisam ne amma zuciyarsa na wajenki. Ramlah ta sake rushewa da kuka tce GANGAR JIKINSA NAAURA zuciyarsa na wajenki hanna. Ke kadai cemaganin ciwon nan na haisam hanna kece kawaizai gani ya warke.Hanna tasa hannu tana gogewa ramlah hawayecan cikin zuciyarta kuma cike take da farinciki datadade bataji irinsa ba cikin sanyin murya tace yanzuina yaya haisam din yake, ku kaini in ga jikin nasa.Gaba daya falon suka dauki kuka mai tsummazuciya. Hanna cike da mamakin meyasa suka sake rushewa da kuka kuma. Hnna ta dubi Ramlah tacelfy kuka sake rushewa da kuka? Ramlah ta dafakafadar hanna tace hanna saidai kiyi hkr Allahyayiwa haism rasuwa jiya yya habib yayo waya.Zasu taho d gawar a yau da daddare zasu iso.Hanna ta zabura ta mike tsaye yayin da zuciyarta ta far dukan 3 3 kanta ya fara sarawa kamar zai fasheta dora hannu aka yayin da jiri ya dauke ta ta komata zauna, ramlah ta riketa. Izzidin kanin haisam neya katse hanna daga tunanin da take ciki yazogabanta ya durkusa yana mai tsananin kuka dahawaye yace ni nake jinyarsa yace min duk ranar dana ganki na baki wannan. Ya mikowa hannatsakiyoyinta da abun busarta. Cikin snyin jiki tasaahnnu ta karba tana jujjuyawa ta gansu gr dasukamar yau ya karba daga wajenta. Sai ta tuno ranarda aka kai ta makaranta tan zaune akan akwati,haisam n kn benci yana mata tambayoyi har ya krbi wadnnn tsakiyoyin, sai hawye ya dinga digowadaga idanuwanta.izzidin ya ce bayan tfyr ramlahjikin yaya haisam ya rikice sosai har aman jiniyakeyi. Ashe yaya habib yana ta cuku cuku zai fitadashi turai. Bayan tafiyar ramlah da kwana 2 yayahabib ya tafi dashi londonRanar da suka isa da daddare Allah yayi ikonsayaya haisam ya rasu. Gingirim hanna ta tsaya tanakallon izzidin tamkar wata gunki. Izzidin yaci gabada cewa yaya habib yn kuka yayi waya yace yau dadaddare gashi nan zai juyo da gawar haisam shinewannan taron da kika gani ana jiran isowar su muke. Kiyi hkr hanna haka Allah ya rubuta miki.Haisam yasha wuya a sandiyar sonki. Kowa yayishiru ba abinda kakeji a falon sai sautin shesshekarkuka kowa keyi. Can hanna ta rushe da kuka tanacewa Innalillahi da inna ilaihir raji'un haka Allah yarubuta min haka Allah yaso ya ganni nagode wa Allah. Yanxu babu babana, babu mijina bello madu,babu haisam din da nake sa ran xan ganshi dukdaran dadewa. Hanna ta rusa kuka tana bada lbrnrywr ta tun ranar da mahaifinta ya kaita mkrnt sukagamu da haisam har izuwa aurenta da bello madu,har izuwa rana irin ta yau da aka bata lbrn mutuwar haisam. Tace ta dauka ita kadai kehaukarta Haisam yana can da matarsa ya manta daita tunda yace ya cika burin daya kudira akai nainyi karatu ya dawo gida yanzun zai cika alkawarindaya dauka. Sai na dauka haisam ya manta da watahanna ashe ina nan like a ransa. Hanna kuka wiwi Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100 GANGARJIKINSA NA AURA 2 Part 3 Posted by ANaM Dorayi on 04:41 PM, 30-Apr-15 Under: Gangarjikinsa ta Aura Jama'ar dake cike a falon iyayensa da iyayenramlah danginsa da dangin ramlah da makabtaduk sukaji tausayin hanna fiye da kansu da kansu.Hanna ke akayi wa mutuwa.inji mahaifiyar haisamyace min hjy ku barni na auri hanna, hjy hanna ceryw ta amma naki fur ashe kuwa da gaske yake gashi yanxun babu shi ina ma yana da rai yazoyaga hanna, sai duk falon aka dauki kuka gabadaya.Hanna ta kankame tsakiyoyinta da abun busarta acikin gyalenta ta mike ta dakyar tana hadahanya tana tafiya dakyar ta nufi wani daki ashedakin haisam ne, can lungu gado ta shige tayizauna yayin da idanunwanta suka fada kan wanikaton hoton haisam dake like a jikin bangon dakin yyi kyau sosai yana dariya a hoton. Taji gabanta yayanke ya fadi ta kurawa hoton ido kem yayin dataji wani ruwa dga hancinta yana zurara ta cikinkanta numfashin ta na kokarin dauke mata abundazata iya tunawa kenan , ashe suma tayi, Amratukanwar haisam aka turo dakin tazo taga wanni hali hanna take ciki karta nemi ta halaka kanta. Saikuwa tazo ta ganta ta jingine a lungun gado azaune ido babu baki sai fari ta kafe. Amratu takwalla ihu sai duk aka shigo aka tara hanna cikinwannan hali. Ba'ayi wata wata ba aka daukota anasalati aka yayyafa mata ruwa ta farfado.Tana bude ido taga dandazon jama'a har sunfina dazu mata da maza an idar da sallah magaribaan sake taruwa ana jiran isowar gawar haisam.Kofar gida cike yake taf da maza. Hanna tayi salatita tashi ta zauna tana tunanin a ina take ko daimafarkin ne, amma ta murtsike idon ta goge ruwan dake fuskrta taga zahiri ne ba mafarki bane haisamya rasu , ya rasu da gaske ne. Hanna taji sai sannuakeyi mata yayin da taji wasu na tambaya itacehanna? Wannan ce hanna? Wadanda suka zoyanzu kenan. Hanna tace a zuciyarta wato kowama ya sanni kenan kamar yadda nima acan duk wanda ya sanni yasan haisam,KARSHE Hanna ta matsa kusa da mahaifiyar haisam ta zaunasai taji mahaifiyr haisam tasa hnnu ta goge matahawaye, tace mata hanna yi hkr Allah ya kaddarahaka fatana ki din da yiwa Haisam addu'a kinji ko,Allah ya jikansa ya gafrta masa. Allah ya hadaki damai sonki fiye da gafrta masa. Allah ya hadki da mai sonki fiye da yadda haisam yake sonki. Hanna tagirgiza kai tace har abada ba'yi ba, baza ayi bakuma hjy, na rasa mai sona nima na rasa wandanakeso. Sai su duka suka rushe da kuka. Kanhanna akn cinyar mahaifiyr haisam tana kukakamar ta shiga cikinta don tsananin son da taji tana yi mata tamkar haisam tunda ita ta haifi haisam. Itamahaifiyar haisam ta dafa knta jin hanna taketamkar haisan ita tunda haisam na son hanna itamaharga Allah taji hanna ta shiga ranta. Amma aikingamaa ya gama haisan din daya hada ya tafi yabarsu, Can Hanna ta dago tace zanje inyi sallar mgariba?Hjy haisam tace eh jeki kiyi. Hanna ta mike dakyarga tsananin faduwar gaba da ciwon kai, ita kantabazata iya musulta yadda takeji a wannan rana ba.Ta shiga dakin ta kalli wajen da hoton haisam yakemanne taga an cire shi sai ta wuce ta shiga bandaki ta dauro alwalla tazo ta fara sallah. Bayan ta idar dasallar magariba ta tashi ta fara jero nafiloli sai tajigaba daya an dau salati tun daga yan kofar gidahar matan dake falo sai taji ana cewa sun iso, an isoda gawar. Tana tsaye tan sallah sai taji ta sulmuye tazauna kafarta ta kasa daukarta gbanta ya yanke ya fadi. Taji duk tsikar jikinta tana tashi, kukan da yakizuwa dazu ya kece mata tamkar ranta zai fita. Cantaji salatin da akeyi ya lafa sai ta rike bango ta tashitsaye dakyar don ta fita falon taje taga gawr abunkaunarta don idan taga fuskarsa yanzu ita ce kadaizata dinga tunawa har karshen rayuwarta. Duk dama taji a jikinta itama ba dadewa zata yi ba aduniya zata bi haisam dinta. Tunda damuwa datunani ne ya kashe haisam a shekara 2 ita yanzuyadda takeji ya linka yadda haisam yakeji don hakazuciyarta ta iya fashewa a wata 3 ta mutu ta huta.Tana tafiy a hankali don karta fadi.har ta fita daga dakin, tana fitowa taga gaba daya daruruwanmutanen da suke zazzaune a falon sun juyo sunakallonta gaba dayansu. Idonta ya dira akan watafuska wacce take tunanin ba gaskiya take gani bagizo ne. Kash!! Anan zan dakata mu hadu aGANGAR JIKINSA TA AURALittafi na 3 Naku ANaM Dorayi,Nagode da karfafamin gwiwan da kukeyi, Allah yabani ikon kammala 3 kamar yanda na kammala 1en 2...Bye! Zaharaddeen Shomar Whatsapp 08168575100

Post a Comment

0 Comments

Contact Form

Name

Email *

Message *

Translate

LATEST POST