ads:::

YARE BIYU

YARE BIYU {2tribes} na ILILEE ~1~ NOTE:wannan labarin 'kagagge ne,kuma ban rubutashi ba, domin cin fuska ko kuma cin zarafi ga ko wani {YARE} ba! NOTE: Kuma zan yi amfani da yaruka daban-daban[hausa,yoruba,pidgin english & english] wajen rubuta wannan labari mai suna YARE BIYU,afuwan ga wanda hakan zai zame masu ba'kon al'amari! SADAUKARWA GA: all the tribes in the whole nigeria! Asha karatu lafiya my lovely fans...... ¤ ¤ ¤ In the name of ALLAH the compassionate ,the merciful! * * * Tsaye take gaban wardrobe 'kirar royal furnitures,hannunta ri'ke da handle d'in 'kofar wardrobe d'in,jikinta lullu6e da guntun towel ,wanda hakan na nuni fitowarta kenan daga wanka,duba ta kai ga tufafin dake jere reras acikin wardrobe d'in ,dogon tsa'ki taja bayan ta zabgawa kayan harara,tace'chai! Oluwa i don suffer,which kind wahala come be this,person no fit wear better cloth for this palace[fada],everyday na ankara,gown,wrapper no even skirt or trouser,abeg i don tire oh' ,ta 'kara jan wani dogon tsa'ki! Hannu taji ansa an zagayeta ta baya ,ana sumbatar wuyanta,tsa'ki ta 'kara ja tace 'ohh OGA HITLER how many times wey i go tell you sey make your hands no dey touch my body ,na by force,i no dey do,abeg free me jorh',ta juyo a fusace tare da jan tsa'ki,turus tayi a lokacin da idanunta suka mata tozali da akasin hasasHannu taji ansa an zagayeta ta baya ,ana sumbatar wuyanta,tsa'ki ta 'kara ja tace 'ohh OGA HITLER how many times wey i go tell you sey make your hands no dey touch my body ,na by force,i no dey do,abeg free me jorh',ta juyo a fusace tare da jan tsa'ki,turus tayi a lokacin da idanunta suka mata tozali da akasin hasashenta! Nunashi tayi da yatsa tana cewa 'soltonu[SULTAN] How dare you carry your hand wey resemble ishono[ashana] touch my body,you dey craze? ,wetin bring you come my room this hot afternoon sef?' sultan ya marairace murya yana cewa 'please BOLAJI ,help my soul,i need to have sex with you urgently,cause i'm in need of your body,please bolaji help me,just name your price ,i will pay,but please just let me quench the sexual urge i have for you' ,bolaji ta dubeshi she'ke'ke sannan ta kwashe da dariya tana tafa hannayenta tace 'chai! see this cockcroach oh,you wan have sex with me 'bolaji' abi? ,i resemble ten ten naira ashawo wey dey patrol for lagos bridge?,ta 'kara yin dariya tana gyara zaman towel d'inta,sannan tace 'even your brother oga hitler wey be my husband,no fit have sex with me,talkless of you ,tiny agbaya ,mumu first class,abeg carry your wahala commot for here jare' ,sultan ya 'kara marairaicewa yana mai zuba ro'ko kamar maro'ki yana cewa 'please bolaji ....! A zafafe ta katseshi tana cewa 'you are wasting your time oh,soltonu,as you see me so,even my corpse you no fit have sex with,talkless of me wey i tanda stand for here!' Hannu Sultan yasa ya fisgota ta fad'o jikinsa ya kamkameta,ita kuwa bolaji ta sa ha'kora ta chafko kunnensa ,hakan yasa sultan yayi 'yar 'kara ya saketa yana mai shafa kunnensa ,a tsammaninsa ko ta gutsire masa kunnen ne! Sultan ya dubeta ransa a 6ace yace 'wallahi yau sai na kashe kishiruwar sha'awarki da nake kwana ,nake tashi da ita,ko da kuwa hakan zai zamo sanadiyar mutuwarki' ,ita kuwa bolaji ko a jikinta domin bata ma san meye fad'a ba,hannu tasa ta gyara d'aurin towel d'inta,tana harararsa! Sultan matsowa yayi gadan gadan da niyyar ya had'ata da bango,yana matsowa kuwa ,bolaji ta dun'kule hannu ta zuba masa naushi a ciki ,sultan hannu biyu yasa ya dafe cikinsa,domin naushin ya shigeshi matu'ka,har sai da 'kwalla ya zubo masa,a fusace ya shammaceta, ya dam'ki gashin kanta ya gwara kanta da wardrobe,hakan yasa ta sulale 'kasa a sume! Jin 'karar buga kan bolaji da sultan yayi da wardrobe ne yasa FULANI da ta zo wucewa ta gaban d'akin tare da hadimai tsayawa Jin 'karar buga kan bolaji da sultan yayi da wardrobe ne yasa FULANI da ta zo wucewa ta gaban d'akin tare da hadimai tsayawa chak! Fulani ta dubi hadiman tace 'ku dakata anan' ,gaba d'ayansu suka had'a baki wajen cewa 'toh ranki ya dad'e' sannan suka sunkuyar da kawunnansu! A 'kasaice fulani tasa hannu ta tura 'kofar d'akin bolaji ta shiga tana wurwurga idanu! Idanuwanta ne suka mata tozali da sultan dake 'ko'karin kunce tazuge zai afkawa bolaji dake kwance a sume! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/14, 6:39 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= {2tribes} na ILILEE ~3~ Cike da hanzari gami da zafin naman barde da kurtagu suka sa hannu suka cicci6i bolaji tare da turmusata cikin buhun! Fulani ta yi murmushi tace 'kuje ku sata a booth d'in highlander[mota] ,sannan ku cewa driver yana iya tafiya bayan kun amshe mu'kullin motar daga hannunsa! Barde da kurtagu suka amsa da 'angama ranki ya dad'e' sannan suka fice da bolaji dake cikin buhun! Fulani ta kai dubanta ga jakadiya tace'zamu fita mu dawo ,ko da su mai martaba sun riga mu dawowa, kice musu asibiti mukaje tare da sultan' 'angama ranki shi dad'e' cewar jakadiya mara'kisiya, fulani ta ce 'zaki iya tafiya' ,bayan jakadiya ta fice ,fulani ta dubi sultan da duk ya kasa magana ,mamakin mahaifiyarsa kawai yake! A fusace tace masa 'ayu ,sai ka taho muje,domin mu aiwatar da aikin da ke gaban mu' sultan baki na rawa yace 'umma me kike shirin aikatawa ga bolaji?' ,a kausashe ta amsa mai 'muje zaka gani,kuma bana bu'katar in 'kara jin kayi magana akan wannan ru'ba'b'biyar bayarabiyar! Wuce muje!' Jiki a sanyaye ya bi bayan fulani,suka nufi bayan gida,inda fulani ta bada umarnin ayi parking mota! Barde ne ya russuna yana cewa 'ranki ya dad'e an sallami direban[driver] ga mu'kullin motar' 'mi'kawa sultan mu'kullin!' amsar da fulani ta bawa barde kenan! Bayan barde ya mi'kawa sultan mu'kullin a ladabce sai fulani tace dasu 'kuje ku fito da guards car[motar dogarai] mu wuce,domin wajen gari zamu nufa!' 'angama ranki shi dad'e ' barde da kurtagu suka had'a baki wajen furtawa,sannan suka mi'ke a zafafe suka wuce domin cika umarnin Sarauniya fulani! Fulani ta dubi sultan tace'shiga mu tafi!' Bayan sun shiga motar ,sultan ya tayar da motar kenan,sai ga NAWWARA sanye da royal abaya ta iso kusa da motar cikin sassarfa,tana 'kwan'kwasa window side d'in fulani,fulani ta dubi sultan tace 'unlock the door lock' ,bayan ya aiwatar da haka,fulani ta bud'e kofar motar tana tambayar nawwara 'lafiya ,meye faru' ,nawwara tayi ya'ke ,sannan tayi narai narai da idanu tana cewa 'umma dan Allah zan bi ku' ,'toh shigo muje!' ¤ ¤ ¤ Tafe suke akan titi, Motar su[guards car] barde da kurtagu ne agaba ,sai motarsu fulani a baya! Da sun zo traffic ko checkpoint ake basu daman wucewa kasancewar duk abinda ya shafi masauratar sarki modibbo ba'a wasa ko kuma nuna ja ,domin gwamnatin nigeria kakaf tasan da kafuwar wannan masauratar mai d'imbin tarihi! Nawwara ta dubi fulani tace 'umma buhun menene na hango su barde sun sa a booth d'in motar nan' ,dariya fulani tayi sosai ,sannan tace'buhun mutuniyar taki ce,matar nisful hayat d'inki' ,nawwara tayi jim sannan tace 'umma kina nufin gwolaji[bolaji]ce d'aure a cikin buhun kamar himilin doya?' 'eh!' fulani ta bata amsa tare da labartawa nawwara abinda ya faru ! Nawwara ta jinjina lamarin tana cewa 'tir'kashi,amma wannan gwolajin [bolaji] anyi shegiya kuma shed'aniya ,ta asirce yaya HASH ya aurota,yau kuma akan sultan d'in tsafinta ya sauka,toh ta Allah ba tata ba',fulani ta ta6e baki tana cewa 'bar ni da tarikicen oduduwar mana,yau zanyi maganinta,idan ita NAJA'ATU bata kishin d'anta,toh ni ina kishin nawa d'an ,ya zama dole inyiwa tufkar hanci',nawwara tace 'hakane kam umma,domin umman yaya hash sai a slow wallahi,ta cika shiru shiru wallahi,in ba haka ba,ina yaya hash ina auran bayarabiya dan Allah,abin babu match ko kad'an, crossroad! Sannan ta jefi fulani da tambayar ' Yanzu umma ya zakiyi da gwolajin[bolajin]?' fulani ta amsa mata da 'muje zaki gani' ,sultan dake tu'ki ,uffan bai ce masu ba! Sai da suka iso wani daji dake wajen gari ,sannan fulani ta bada umarnin a tsaya! Gaba d'ayansu suka fito,dajin tsit ba kowa,sai kukan tsuntsaye kawai ake ji! Fulani ta bawa barde da kurtagu umarnin d'auko bolaji daga booth,bayan sun d'auko ta,fulani tace su fito da ita daga cikin buhun! Haka suka kunce buhun suka fito da ita ,duk ta ji'ke da gumi sharkaf! sanyayyar iskar daminar da ake yi ne ya bugeta,hakan ya zamo sanadiyar farkawar bolaji,ta bud'e idanunta a hankali tana mai salati tare da dafe goshinta da sultan ya buga da wardrobe d'azu! Jin muryar fulani tana cewa 'barde bani aska' yasa bolaji ta kai dubanta garesu tana mai tashi da 'kyar domin ta zauna,ganin kamar a daji suke yasa tasa hannu ta cire d'ankwalin da jakadiya ta tamke mata baki dashi d'azu,tana cewa 'mummy folani[fulani],anty nuwara[nawwara] wetin come bring us here,wetin happen?' Nawwara a fusace taja dogon tsaki tana cewa 'jibi yadda take gur'bata mana sunayen mu dan Allah' fulani tace ''kyale shegiya mana,mai suffar aljanu,idan bata gur6ata mana sunayenmu ba,taya za'a san cewa ita jikar oduduwa da sango ce' ta dubi barde da kurtagu bayan ta amshi askar! ta umarcesu da cewa'ku kamata ku ban'kare mini shegiya!' written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/14, 6:40 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= {2tribes} na ILILEE ~4~ Da sauri barde ya dam'ki 'kafafun bolaji ,kurtagu ya dam'ki hannayenta,suka ban'kare ta! Fulani gadan gadan ta yo kan fuskar bolaji hannunta ri'ke da askar, tana dariya tana seta mata askar akan fuskarta! Ganin hakan yasa bolaji ta fara tittirjewa domin kwace kanta daga ri'kon dasu barde suka mata! Muryarta na rawa a firgice tace 'wetin i do una?,wetin happen? ,kile fe se fun mi? Ahh mummy folani wetin you wan do me?' Fulani ta katseta ta hanyar cewa 'yimin shiru tubabbiya,wanda suka tsinci musulunci daga baya,domin duk wani YARE a fad'in nigeria in ba hausa/fulani ba,toh a arna nake kallonsu ko kuma tubabbu, ki tsaya in aiwatar da kud'iri na cikin sau'ki,domin wannan gur6atacciyar turancin naki ,ba fahimta nake ba,ehe'' Bolaji ta cigaba da tirjewa tana son 'kwatar kanta daga hannun kurtagu da barde,amma ina,ta kasa! Ta cigaba da magiya tana mai bawa fulani ha'kuri cikin harshen pigdin da yoruba, ta had'a ta da Allah da manzonsa [s.a.w]! Amma hakan bai yi tasiri ga fulani ba,sai ma karta mata askar tayi akan fuska tana cewa 'ashe kuma kun san Allah da manzonsa?' Ihu bolaji ta saka don azaba. Sultan ne ya matso yana cewa'haba umma,me zakiyi mata,laifin me tayi miki ne,da za ki salwantar mata da rayuwa,kar ki manta ita ma musulmace kamar mu' a fusace fulani ta amsa masa da cewa 'amma kuma YARE ce! Fulani ta cigaba da cewa'wannan shegiyar bayarabiyar ta zamo mata ga d'an na fi so a rayuwata,kuma ta zam o sanadiyar rushe auransa da nawwara kuma kyawun ba'kar fuskarta ne ya rud'eku da har hakan ya zamo sanadiyar da yayanka ya aurota ,kai kuma ka hai'ke mata,ALLAH ya ta'kaita, na bayyana ba tare da ka cika burinka akan ta ba,sultan na dad'e ina jiran wannan ranar da zan fitar da shegiyar nan daga rayuwarmu,domin a rayuwata idan akwai abinda na tsana toh ya biyo bayan YARE!' sultan ya marairaice murya yace 'umma toh me zai hana a sata a mota ta koma garinsu kawai ko kuma ki 'kyaleta ta shiga duniya' fulani ta harare shi ta amsa masa da cewa 'salon kuma kaddara ta 'kara had'a su ita da yayanka ko? ,kaga sultan ka 'kyaleni in aiwatar da abinda nayi niyya,kuma na 'kara jin kayi magana anan ko kuma ka nemi hanani abinda nayi niyya, sai na tsine maka albarka!',sannan ta juya ta dubi nawwara tana cewa 'matso ki danne min kanta yadda zanji dad'in kekketa mata shegiyar fuskar nan tata,in banda abin tsafi irin nasu na yarbawa,ina ba'kin mutum ina kyau ,yarinya sai kace aljana,gata dai ba'ka,amma sai shegen kyau!' Nawwara jiki na rawa ta dam'ki kan bolaji ta ri'ke tana cewa 'ni kaina sai dai in nuna mata hasken fata,amma kyau ta fini nesa ba kusa ba,kuma hakan ba 'karamin 'kona min rai yake ba' fulani kuwa tasa aska ta d'inga keta mata fuska! Bolaji sai ihu take don azaba tana bawa fulani ha'kuri,amma duk a banza ,sai da fulani tayi mata kaca-kaca da fuska,domin jini da nama ne kawai ke reto akan fuskar ,wanda hakan ya zamo sanadiyar sumewar bolaji dan tsabagen azaba Bolaji sai ihu take don azaba tana bawa fulani ha'kuri,amma duk a banza ,sai da fulani tayi mata kaca-kaca da fuska,domin jini da nama ne kawai ke reto akan fuskar ,wanda hakan ya zamo sanadiyar sumewar bolaji dan tsabagen azaba ! Sultan kauda kansa yayi gefe ,idanunsa cike da 'kwalla yana mai tir da wannan rashin imani! Ita kanta Nawwara ta tausayawa bolaji amma tsoron fulani da kuma soyayyar yaya hash ne yasa ta danne tausayin nata! Fulani tayi cilli da askar tare da goge hannunta da ya ca6e da jini a jikin kayan bolaji,sannan ta dubi su barde da kurtagu tana sauke numfashi tace' kuyi cilli da ita can ' tayi masu nuni ga wani wawaken ramin duwatsu dake nan gaba dasu ! Da hanzari suka cika umarnin fulani! Haka suka cillar da bolaji wacce fuskarta ya dawo tam'kar d'anyan naman shanu! Fulani ta umarcesu da su wuce su koma fada! Haka suka shige mota tare da ficewa daga jejin, suka bar bolaji kwance a tsakiyar duwatsu duk kanta da jikinta su farfashe sanadiyar gwabzuwa da d'inga yi da duwatsu! Written by : Abdulaziz ililee isma'il [10/14, 6:40 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= {2tribes} na ILILEE ~5~ Masarautar modibbo masarauta ce mai daraja da d'imbin tarihi a yankin Yabo dake jihar sokoto,anyi sarakuna da dama a wannan yankin har izuwa lokacin da sarautar da mulki ta dawo hannun SARKI ABBAS MODIBBO III! Wanda ya kasance d'an fari ga sarki ayuba modibbo II ! Sarki abbas yana da matan aure guda biyu! kasancewar masarautar modibbo wayayyen masarauta ce mai tafiya da yanayin zamani ,hakan yasa yin 'kwar'kwarori bai zamo tilas a wannan masarauta ba,uwar gidansa suwaiba tana da 'ya'yanta gudu takwas reras duk mata,sai kuma amaryarsa sailuba tana d'a guda d'aya tak namiji mai suna ATTAHIRU,kuma akwai zaman lafiya a tsakanin matan guda biyu,sai dai d'an abinda baza'a rasa ba na gulmace gulmace,tsegumi da munafirci irin na gidan sarauta! Attahiru ya kasance yaro mai 'kwazo da hazaka,domin sai da ya sauke alqur'ani ,sannan ya fara primary,yayi primary da secondary d'insa duk a jihar sokoto! Bayan ya kamalla secondary d'insa ya samu admission a usman d'anfodio university in da yaje ya karanci political science,bayan ya kamalla degree Bayan ya kamalla secondary d'insa ya samu admission a usman d'anfodio university in da yaje ya karanci political science,bayan ya kamalla degree d'insa! Sai aka turashi bautar 'kasa osun state! Mai martaba sarki abbas yaso attahiru yayi bautar 'kasar shi anan garuruwan hausawa,amma attahiru ya dage akan cewa bai da damuwa ko a ina ne zai iya zuwa yayi bautar 'kasarsa! Zaman attahiru a garin osun cikin 'kabilar yarbawa,zama ne na sanin darajar juna da mutunta juna,bai samu matsala da kowa ba ,har ya kamalla bautar 'kasar ya dawo sokoto inda ya rabu da 'yan gari n osun ,musamman mazauna yankin 'erin local govt' da kuma d'alibansa na 'F.G.C ERIN' suna masu kewar sa! A lokacin da ya dawo daga bautar 'kasar ne, mahaifiyarsa ta fara masa zancen aure domin duk yan uwansa[senior sisters d'insa] ko wacce tana gidan mijinta! A wannan lokacin ne saudat[fulani] wacce ta kamalla takabarta,ta dawo masarautar modibbo da zama! Fulani ta kasance d'iya ga 'kanwar mahaifiyar attahiru,mijinta ne ya rasu washegarin data tare a gidansa,bayan ta gama takaba ne,sailuba [mahaifiyar attahiru] ta umarceta da ta dawo fada da zama,kasancewar can gidan nasu babu mahaifiyarta [ta rasu] a gidan sai matan uba da 'yan uba! Soyayyar attahiru da fulani ya samo asaline a lokacin da ya dawo daga bautar 'kasa ya taddata a fada,inda sukayi amanna da junansu,ko da sailuba ta 'kara tuntu6ar attahiru da zancen aure,bai yi nauyin baki ba wajen cewa ya za6i fulani a matsayin matar da yake son aura! Mai martaba yayi na'am da za6in d'ansa ,haka zalika sailuba! Ba'a d'au wani dogon lokaci ba,magabatan attahiru da na fulani suka had'u aka d'aura auren su! A cikin fada aka yanki fegi aka cancand'a masu gidansu suka tare abinsu ,suna gudanar da rayuwarsu! Attahiru ya koma makarantar UDUS yayi degree d'insa na biyu wato masters! Bayan ya kamalla masters ya fad'a kasuwancin gwala gwalai ,wanda cikin shekaru 6 kacal yayi kud'i na fitar hankali,wanda hakan ya zamo sanadiyar fad'awarsa harkar siyasa,domin siyasa a nigeria sai da mai arziki ake damawa! Kuma alhamdulillah ya samu kar6uwa ,domin takarar gwamna ya fito ,akayi za6e ya kuma lashe za6en! Fulani kuwa har zuwa wannan lokaci ko 6atan wata bata ta6a yi ba! Governor Attahiru abbas modibbo ya kasance shugaba adali,mai ri'ko da gaskiya gami da amana,kuma mai kishin talakawa da kuma sanin darajarsu! Written by :abdulaziz ililee isma'il [10/14, 6:41 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= {2tribes} na ILILEE ~6~ An samu cigaba ta fanni daban daban a jihar sokoto a 'karkashin mulkin Gov.attahiru modibbo! A shekararsa ta biyu akan mulki ne, ya auri Naja'atu wacce ta kasance d'iya ga sarkin yankin dass dake jihar bauchi! Naja'atu ta kasance yarinya mai nutsuwa da alkunya,magana wuya yake mata,bata da tashin hankali ,gata da sanyin rai da kuma ha'kuri! Bayan ansha biki ta tare a sokoto government house,suna zaune lafiya da fulani,babu matsala ko kad'an a zaman nasu! Bayan Wata goma sha d'aya[11] da auran,naja'atu ta haifo santalalen d'anta ma'aboci kyawu da kwarjini! Kowa ya yi farinciki da wannan haihuwar musamman Attahiru da fulani! Ranar suna aka rad'awa yaro suna HASHIM! Watan hashim goma shad'aya ,naja'atu ta cireshi daga nono,ta had'a kayansa kakaf ta mi'kawa fulani shi kyauta! Fulani tayi murna da wannan kyauta da naja'atu tayi mata,domin har kuka sai da tayi,kuma daman Allah ya d'aura mata 'kaunar hashim tun ranar da aka haifeshi! Attahiru yayi ta shi wa naja'atu albarka! Hashim yana da shekara d'aya,tenure d'in mahaifinsa ta 'kare! Suka tattara suka bar state government house, bayan tsohon governor attahiru yayi handing over ga sabon governor! A wannan lokacin ne Allah yayi wa sarki abbas rasuwa! Sarauta da mulki ya dawo kan sarki attahiru modibbo ! Mai martaba sarki Ya cigaba da gudanar mulkinsa cikin aminci da adalci,domin su kansu al'ummar yankin na 'yabo' sun san cewa masarautar modibbo ta samu chanji da cigaba ba kad'an ba,domin ko ta fannin ginin masarautar an samu chanji,domin duk bayan shekara uku mai martaba yake sawa a canja komai na cikin masarautar izuwa tsari na zamani! Sai da yarima hashim ya shekara 5 ,sannan fulani ta samu juna biyu! Bayan wata goma ta haifo santalelen d'anta ,ranar suna ya ci sunan sarki abbas,amma da [SULTAN] ake kiransa! ¤¤¤¤¤BAYAN SHEKARU ASHIRIN [20] ¤¤¤¤¤! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/14, 6:42 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~7~ Ba'kar Mota 'kirar pathfinder akayi parking a harabar gidan ! Cike da hanzari royal chaffeur [direba] ya fito daga gidan gaba ya zo ya bud'e kofar gidan baya ! Saurayi,matashi ,maji 'karfi,mai kwarjini da kyawun fuska gami da kyawun sura ,wanda shekarunsa basu wuce ashirin da biyar[25] ba ya fito daga gidan bayan,yana sanye da uniform na sojoji wanda suka masa d'as a jikinsa! Wannan matashi ba kowa bane face 'CAPT.YARIMA HASHIM ATTAHIRU MODIBBO! A 'kasaice ya d'aga kansa ya dubi masarautar modibbo fuskarsa d'auke da murmushi,yana mai yaba tsarin palace d'in ,domin ko a 'kasashen larabawa sai haka! Cike da takun 'kasaita ya nufi hanyar cikin gida! Royal guards sai zubewa suke suna kwasar gaisuwa ,hannu kawai yake d'aga masu! Har ya iso 'kofar da zata sadashi da cikin palace d'in! A gaban 'kofar! ,Fulani ce tsaye tare da hadimai ,fuskarta d'auke da murmushi,ganin yarima hashim yasa ta ware hannayenta tana cewa 'come to me my prince charming,the soldier of the nation! The pride of the of the modibbo's palace! my soul dear,welcome home' Fad'awa yayi jikinta yana cewa 'my gorgeous umma! i miss you so much,dafatan na sameku lafiya' 'lafiya lau my souldear' fulani ta bashi amsa tare da jan hannunsa suka shige ciki,hadimai na biye dasu ,suna yiwa yarima hashim kirari,basu tsaya a ko ina ba sai a tsakiyar palace parlour wanda aka 'kawata da purple velvet royal chairs na zamani da curtains masu kyau! Fulani ta dubi hadiman tare da cewa 'kuje ku tabbatar da komai da yarima zai bu'kata a d'akinsa an tanada' ,'angama ranki ya dad'e' hadiman suka fad'i tare da wucewa domin cika umarnin fulani! Fulani takai dubanta ga hashim tana cewa 'my souldear yanzu ka je ka gaida ummun ku [naja'atu],bayan kun gaisa ,sai kaje da'kinka and freshen up,sannan kaje turaka ka gaida mahaifinku,after that kazo dinning ka ci dad'ad'an abinci dana dafa maka da hannuna' ,hashim yayi murmushi yace 'angama your majesty,your wish is my command' ,sannan ya wuce ya nufi hanyar da zai sadashi da bangaren mahaifiyarsa! Sultan ne ya tareshi yana cewa 'd'an gatan umma kenan,tun d'azu nake jiran isowarka,amma umma sai da ta rigani ganinka ' hashim yayi murmushi yana cewa 'naughty bro,ba dole ta rigaka,duk fad'in gidannan umma ta fi kowa 'kaunata ' ,sultan ya cafke da cewa 'ba sai an fad'a ba,by the way,welcome home big bro ,ya aiki da kuma fama da zaman daji' ,'alhamdulillah' hashim ya bashi amsa tare da cewa 'yaushe ka dawo daga malaysia?' 'shekaran jiya na dawo for good ,cause i'm done with my degree programme,yanzu haka service zan tafi in the next 2weeks domin har an aiko min da posting letter' ,hashim yace 'congrats bro,yanzu ka zama bigboy fah,ina sukayi posting d'inka?' ,'enugu!' sultan ya bashi amsa , hashim yace 'enugu kam is a nice place to be,zaka ji dad'in garin sosai' ,sannan ya ri'ke hannun sultan yana cewa 'muje ka rakani gun ummu in gaisheta!',hannunsu ri'ke da juna suka wuce part d'in ummu [naja'atu]! Written by [10/14, 6:43 PM] =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~8~ Zaune akan darduma suka riski ummu tana karatun al'qur'ani,neman waje sukayi suka zauna,har sai da ta idar,sannan tayi addu'a suka shafa tare,a sanyaye ta rufe al'qur'ani tare da kai dubanta ga sultan tana cewa 'd'ana kazo a dai dai kuwa,d'azunnan dama maka fura,duba fridge d'in can ka d'auko' ,sultan baki a washe ya nufi fridge d'in ya d'auko robar damammiyar furar ya dawo ya zauna yana mai cewa 'ummu you are the best mom on earth' ,murmushi kawai tayi ! Hashim ne yayi gyaran murya tare da cewa 'ummu ina wuni,dafatan na sameku lafia' ,'lafia lau,an dawo?' ummu ta fad'a ba tare da ta dubeshi ba ,'eh shigowata kenan ummu!' ,'toh madallah' abinda ta fad'i kenan sannan ta cigaba da jan sultan da hira,inda sabo hashim ya riga ya saba da halin ko in kula da ummu take nuna masa kasancewarsa d'an fari,domin tafi sakarwa sultan fuska tare da jansa ajiki,shi kuwa yafi samun kulawa a gun fulani! A haka ya fice ya bar ummu da sultan suna hira,sultan na shan fura! Da'kinsa ya nufa,yana shiga ya rage kayan jikinsa,ya fad'a bathroom yayi wanka tare da yin alwala,ya fito ya shirya cikin wata ba'kar jallabiya mai taushi,ya kuma gabatar da sallar zuhr,sannan ya fice ya nufi palace parlour! A kan dinning ya hango mai martaba,fulani,ummu da sultan suna cin abinci! Dinning Table d'in ya nufa ya zauna ba tare da yayi wa kowa magana ba,kasancewar idan suna cin abinci basa magana,jakadiya mara'kisiya ce tayi wa hadimar dake serving abinci nuni da ido datayi serving d'in yarima,da hanzari ta zuba masa abinci a plate kamar yadda ta zubawa kowa d'azu ,sannan taja gefe ta 'kame ,kamar yadda jakadiya ta 'kame a gun ita ma! Bayan sun ci sunyi nak ,sai suka d'unguma suka dawo restroom,inda yawanci suke zama suyi hira a tsakaninsu,bayan sun zazzauna,sai hashim ya russuna ya gaida mai martaba,mai martaba ya amsa masa da fara'a yana mai shafa masa kai yace 'd'azu ummanka take sanar dani dawowarka,dafatan babu matsala a can inda aka turaku kwantar da tarzomar' ,'alhamdulillah babu matsala' ,'toh Allah yayi maku albarka' ,fulani tayi caraf tace 'amin!', sultan yayi 'kwafa yace 'kaji su umma masu d'a' ,fulani ta harareshi tace 'fad'i ka 'kara fad'a da babban murya',ummu tayi murmushi ta shafa kan sultan tana cewa 'rabu dasu d'ana,kaima Allah yayi maka albarka' ,'amin ummu na' ,sultan ya fad'i tare da kwantar da kansa akan cinyarta ,yana mai yiwa hashim gwalo! Mai martaba yayi dariya yace 'ku da 'ya'yan naku baku da dama wallahi' ,sannan yayi gyaran murya yace 'hashim yaushe zaka koma? ' ,'on monday zan koma kaduna inyi reporting' 'jibi kenan?'mai martaba ya tambaya,'insha Allahu' hashim ya amsa,mai martaba yace' Allah ya kaimu ' sannan ya dubi sultan yace 'ranar talata ka shirya zamuje osun state,zan dubo company,MD yayi min waya akan cewa ma'aikatan company sun tafi yajin aiki,so zanje da kaina in ji dalili,in kuma kwantar masu da hankali ,in kuma shawo kan matsalar'',sultan yace 'toh Allah ya kaimu abba' ,fulani ta yamutsa fuska tace 'kaji tsiyar yarbawan kenan,duk garuruwan hausawan dake fad'in nigeria ,basu isheka bud'e company ba ,sai can garin su oduduwa da sango ka idanunka suka hango,i ga irin ta nan,da zaka bi shawarata da ka rufe kamfanin wallahi,ka dawo ko nan cikin sokoto ne ka bud'e wani' ,mai martaba yayi murmushi yace 'fulani kenan ban san meye had'aki da yarbawa ba,mutanennan na zauna dasu kuma naji dadin zama dasu a lokacin danayi bautar 'kasa a can ,hakan yasa na yanke shawarar bud'e kamfani acan yankin erin dake jihar osun,domin taimakawa talakawa mazauna wannan yankin samun aiki a kamfanin,saboda su sami abinda zasu ciyar da iyalansu,kuma naga inada kamfanin purewater da tumatir a kaduna,da kuma kano' ,fulani tasan in ta tsaya jin kalaman bakin mai martaba yanzunnan ranta ne zai 6aci ,zuciyarta ta buga a banza,domin akan posting d'in sultan da akayi zuwa garin enugu ,ta so yayi redeploying ya dawo nan arewa, amma mai martaba ya hana,domin shi zuciyarsa babu wannan 'kabilancin sam ! Numfashi ta sauke tace 'hmm Allah ya taimaka,amma su kansu YARE babu yaren dasuka tsana sama da hausa' ummu tayi murmushi tare da cewa 'haba yaya,ki daina fad'in haka ,dukkanmu d'aya muke a gun Allah' a haka suka cigaba da hira har lokacin sallar asr yayi,suka tashi domin suje su gabatar da sallah! [10/14, 6:45 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~9~ MODIBBO & SONS .CO kamfani ne da yayi fice a nigeria kasancewar suna da branches{reshe}a garuruwa daban daban a 'kasar nigeria MODIBBO & SONS .CO kamfani ne da yayi fice a nigeria kasancewar suna da branches{reshe}a garuruwa daban daban a 'kasar nigeria! Suna da kamfanin pure water a kano,kamfanin tumatir a kaduna,kamfanin auduga a katsina da sauransu! Duka kamfanonin mallakin masauratar modibbo ce 'kar'kashin jagoranci da mallakar sarki attahiru modibbo! Shekaru 10 da suka wuce ,mai martaba da kanshi yaje jihar osun ,yankin erin ,ya shaci fegi aka siyar masa ,ya bada kwangilar gina babban kamfanin manja [RED OIL COMPANY]! Bayan an gama gina wannan kamfanin!,a kamfanin an kwashi ma'aikata da dama tunda ga kan manyan ma'aikata masu takardu har izuwa 'kananun ma'aikata irinsu leburori da masu gadi musamman mazauna wannan yankin! Abdulrazak adebayo wanda aka fi sani da baba leji, ya kasance lebura a wannan kamfanin! Yana zaune da iyalansa a wannan yankin erin ,yana da matar aure guda d'aya mai suna riskatu,sai 'ya'yansa guda biyu mace da namiji! Namijin sunansa bamidele ,macen kuma sunanta BOLAJI! Wanda a yanzu haka shekarar bamidele 23 ,yayin da bolaji take da shekara goma sha takwas! Bamidele yana aji uku a secondary ya bar makarantar wato yayi dropping out ,sanadiyar babu da suke fama da ita,ya kama harkar sai da bunburutu wanda maami [riskatu] ta bashi jari! d'an abinda yake samowa a cinikin bunburutun,da shi suke samu su siyi abinci,albashin babalaji ba wani afki gareshi ba ,domin Allah ya had'asu da azzalumin shugaba a kamfanin,wanda sai ayi wata 5 ko 6 ,bai biya 'kananun ma'aikata ba! BOLAJI yarinya mai 'ko'kari da haza'ka,tanada garin jiki,ba'ka ce,amma tanada kyawun fuska da kyawun sura ,domin ko a yankin erin kafin a sami mace ba'ka mai irin kyawunta sai an tona! Ta kasance yarinya mafad'aciya idan an ta6ota,tana da zafi,kuma tana da sanyi a wasu lokutan,gata bata da tsoro ko kad'an,ta kasance ruwa mai sa 'kwai yayi tauri ,haka zalika mai sa dankali yayi laushi,tana tafiyar da mutum ne ta yadda ya tafiyar da ita! Yanzu haka tana ss3 a G.S.S ERIN ,suna zana jarabawar w.a.e.c wanda kud'in w.a.e.c da 'kyar aka had'a aka biya mata,domin tana 'kaunar karatu,bata san ta kasance kamar d'an uwanta bamidele! ¤¤¤¤ Da sallama ta shigo gidan hannunta ri'ke da qur'ani! Ta dubi maami dake faman sa'ka ashoke [sana'ar ta kenan] tace 'bawoni!' tana mai cire hijabinta ,maami ta dubeta tace 'ahh bolaji are you back ,welcome' ,'thank you oh maami,how your body' ,'i thank oluwa oh ' maami ta bata amsa, bolaji ta ja kujera ta zauna kusa da maami tana cewa 'maami mi! This your pregnancy eh,i wish make you born twins,boy and girl ,so that i will back one and hold one' ,maami tayi murmushi tace 'bolaji ahh ,you no dey shame,since the time wey you dey small i no get bele,na now wey you don grow finish,i com dey get another bele' ,bolaji ta dubi turtsetsen cikin da ke jikin mahaifiyarta haihuwar yau ko gobe,tayi murmushi tace 'na so God dey take do his miracle oh,me i just dey pray sey make you deliver safely' 'amin oh my daughter ,go kitchen carry your food chop oh' maami ta fad'i cike da kulawa ! Bolaji ta tashi taje ta d'auko abincin ta,sannan ta d'auko littafin jarabawar da zasuyi gobe tana ci tana karatu! Written by : Abdulaziz ililee isma'il Like · 2 · Reply · Report · Yesterday at 10:08am Aminatu Yusuf Sokoto =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~10~ Tana gama cin abinci,ta ajje littafin,ta nufi kitchen ta kwamfaci ruwa ta sha ,sannan ta had'a kan kwanuka ta fito ta wankesu tas ,sannan ta dawo ta zauna tana cigaba da duba littafinta ,maami tana mata sannu ta hanyar cewa 'ekhuse' ,bolaji ta amsa da 'eshe'! Babalaji ya shigo da sallama,gaba d'aya suka amsa ,bolaji taje ta amshi ledar hannunsa tana ce masa 'ekabo' ,babalaji ya amsa 'my daughter eshe',maami ta tashi da 'kyar tana gyara d'aurin zanin nata,tabarma ta shimfid'a masa,tana mai cewa babalaji 'ekabo' ,bayan ya zauna yana sauke ajiyar zuciya yace 'iya bolaji[maman bolaji] eshe oh,how body' ,'we thank God oh,my husband,how's your day,hope it went well' ,bolaji ta iso da ruwa a cikin kofin silva,ta russuna ta mi'kawa babanta,ya amsa ya shanye tas,bayan ya shanye ya dubi bolaji yana cewa 'thank you my daughter,may the almighty oluwa bless you' 'amin oh' bolaji da maami suka amsa! Babalaji ya dawo da dubansa ga maami yana mai cewa 'hmm,i'm tired oh,we the labourers have been standing at the company's entrance for the past 4hours waiting for our 7month salary to be paid to us,before we get back to work and call of the strike,but the payment did'nt take place,instead the manager told us to excersise patient,and we should come back on tuesday cause the owner of the company will come and tackle the problems!' ,maami ta dubi mijinta cike da tausayi tace 'this is wickedness,i don't know what this country is becoming,but no wahala,oluwa dey ,he dey watch and he's in control' ,babalaji ya amsa mata da 'na so oh,let's wait for the tuesday,we shall see' ,maami ta tashi ta d'auko masa abinci ta kawo masa,yana ci ,tana masa firfita tare da jan sa da hira! ¤¤¤¤ Ranar litinin misalin 7:30am hashim ya gama shiryawa,yayi sallama da iyayensa,direba ya saukeshi a airport,inda palace pilot ke jiransa,ya shiga private jet d'insu,suka d'aga kaduna! Misalin 'karfe 10 na dare ,mai martaba na zaune kishingid'e a d'akin fulani,kasancewar ranar girkinta ne! Fulani ta dubi mai martaba tare da cewa 'gobe ne tafiyar taku ko?' ,'insha Allah' mai martaba ya bata amsa,fulani ta gyara zama tana cewa 'abban hashim baka ganin cewa daraja da arzikin wannan masarauta ya wuce ace ka bud'e kamfani[compani es/factories] a garuruwa,ni a ganina sarauta da mulkin ka sun girmi hakan, ,musamman kamfanin pure water da aka bud'e a kano ,da kuma na manja da aka bud'e a garinsu oduduwa,bai kamaci wannan masarautar ba,da kuma kai kanka da ka kasance tsohon gwamna' ,mai martaba yayi murmushi wanda ya 'karawa fuskarsa kwarjini ,yace 'fulani kenan,ni ba kowa bane face d'an adam kamar kowa,wad'annan kamfanonin ba'a bud'e su domin samun kud'i ba ,an bud'esu ne saboda talakawa mazauna yankin da aka bud'e kamfanonin, su samu hanyar da zasu nemi halas da guminsu ta hanyar samun aiki a kamfanonin,kuma kinga a yanayin da 'kasar tamu take ciki,aiki yana yi wa matasa wuyar samu duk da kwalin degree d'insu,,kinga kenan samun aikin matasa a kamfanonina zai sa a rage samun matasa masu zaman banza da kashe wando [jobless youths],kuma da kike cewa masarautar nan ta girmi hakan,ta ina masarautar nan ta girmi haka,me kike d'au sarauta a duniyar nan ne?,mu da mutanen gari,musamman talakawa ,duk d'aya muke a gun Allah! sarauta da mulki sai sarautar ALLAH s.w.t 'malikul mulk',mabuwayi,gagara misali,wanda dukkan mu gaba d'ayan mu a 'karkashin ikonsa da mulkinsa muke! kuma kamfani yanzu na fara 'bud'ewa ,in akwai abinda yafi purewater 'kas'kanci idan har na samu dama sai na bud'e kamfaninsa,in har hakan zai zamo alkhairi ga al'ummar annabi muhammad [s.a.w],musamman talakawa! masarauta bata girmi yin ko wacce irin halastaciyyar sana'a ba,ko da kuwa wannan masarautar tana da daraja da arziki' ,jiki a sanyaye fulani tace 'ALLAH ya bada lada,ya kuma 'kara arziki,na fahimci manufarka,kuma ina fatan sauran sarakuna irinka zasu koyi da kai' ,mai martaba yace 'amin fulani,addu'arku kawai nake bu'kata a kullum,' ,haka suka cigaba hira na farantawa juna rai ,har izuwa lokacin da bacci ya riskesu! [10/14, 6:49 PM] ‪+234 810 476 6513‬: =YARE BIYU= {2tribes} na ILILEE ~2~ Tsawa fulani ta dakawa sultan tana mai cewa ' kar ka kuskura ka cire wandonka!' ,a tsorace sultan ya mi'ke tsaye jikinsa na rawa ya dubi fulani yana mai d'aure tazugensa a kunyace. Fulani ta zabga masa harara,sannan ta dubi bolaji dake kwance a yashe a sume,a fusace ta watsawa sultan tambayar 'meye sameta?' ,sultan ya hau inda inda yana sosa 'keya ya labarta mata abinda ya faru! Dogon tsa'ki fulani taja tana mai cewa 'toh jarababbe,ayu,duk matan hausa/fulani dake cikin fad'in garin nan basu isheka dannewa ba,sai wannan YAREN,yaren ma bayarabiya,ni na rasa meya ke rud'arku a tattare da ita da har hakan zai ja hankalinku gareta,wallahi ina ba'kin ciki in wayi gari inga wannan bayarabiyar yarinyar a gidannan,yayanka yaje ya kwasota a matsayin matar aurensa,kai kuma yau kazo zaka hai'ke mata ko?,wallahi ina daf da tsine maka albarka,domin bana fatan in had'a tsatso da YAREN da ba hausa/fulani ba,kuma naga kaima kana shirin bin sawun yayanka,tunda har ka fara kokarin yiwa wannan bayarabiya fyad'e,toh nan gaba ma ,bayarabiyar zaka auro d'ungurungum kaima' ,sultan baki na rawa yace 'umma ki yi ha'kuri,ita ma wannan tsautsayi ne ya kawo ni wajenta,kuma tunda ban aikata ba,shikenan bazan 'kara ba!' Tsaki fulani ta ja tana cewa 'ni ban hanaka neman matanka ba,amma bana son kayi mu'amala da YARE,ga yan mata kyawawa ,tsala tsala hausa/ fulani,ka nemesu mana,kuma wannan jinin oduduwar wallahi tallahi sai ta bar fadar nan a yau d'innan,domin zamanta a fadar ya 'kare a yau,tunda har ta kai ka fara hai'ke mata ,toh dole inyiwa tufkar hanci!' Ta juya ta fita daga d'akin tare da nufar gun hadiman data dakatar a waje! Dubansu tayi a kausashe tace 'kuna iya tafiya,ke kuma badiyya ki tsaya' ,sum sum sum suka watse,sai wacce ake kira da badiyya ce kawai ta tsaya,kanta a sunkuye tace 'ranki shi dad'e,ALLAH ya ja zamaninki' Fulani ta katseta da cewa 'ki hanzarta yanzu kije ki kirawomin mara'kisiya[jakadiya]' ,'an gama ranki shi dad'e' badiyya ta fad'i tare da barin wajen,cikin mintuna da basu wuce d'aya ba,sai ga kuyanga badiyya tare da jakadiya mara'kisiya! a gaban fulani ta rusuna tana zabga gaisuwa! Fulani da dubi ba'kin fuskarta tace 'su mai martaba basu dawo daga rangadi ba ko' ,'eh ranki shi dad'e ,sai zuwa yamma' mara'kisiya ta amsa. Fulani tace 'toh tashi kije ki kira min barde da kurtagu yanzunnan' sannan ta dubi badiyya tace'ke kuma biyo ni',da hanzari mara'kisiya ta tashi ta fice domin cika umarnin uwargijiyarta,ita kuma badiyya ta bi bayan fulani suka shiga d'akin bolaji! Sultan yana nan inda fulani ta barshi a tsaye ,hankalinsa a tashe ganin bolaji bata farfad'o ba! Fulani ta umarci kuyanga badiyya da ta d'auko doguwar riga ta sanyawa Fulani ta umarci kuyanga badiyya da ta d'auko doguwar riga ta sanyawa bolaji! Cikin minti biyu badiyya ta aikata hakan! Fulani tace mata 'zaki iya tafiya' ,a bakin 'kofa badiyya tayi kici6us da jakadiya mara'kisiya tare da barde da kurtagu,cike da azama badiyya ta koma gun fulani ta rusuna tana cewa 'ranki shi dad'e ,ga jakadiya ta iso da su barden' ,'ki ce masu su shigo',badiyya ta tashi taje ta fad'a masu sannan tayi tafiyarta ,jakadiya da su barden suka shigo da'kin suna masu mi'ka gaisuwa ga sultan da fulani ! A 'kasaice fulani ta dubi barde da kurtagu,tayi murmushi mai sanyi sannan tace 'wani aikin sirri nake so in yi daku,saboda ku ukun nan na aminta daku' ,gaba d'ayansu suka had'a baki wajen cewa 'godiya muke ranki shi dad'e ,kuma an gama ranki shi dad'e,umarninki kawai muke bid'a' fulani ta dubi kurtagu wanda ya kasance gamsasshen 'kato ne maji 'karfi ,tace 'ka je ka cewa direba ya fito da highlander mai duhun gilashi ya zagaya ta baya ya jira mu anan' ,'angama ranki shi dad'e' kurtagu ya bada amsa tare da ficewa cike da zafin nama ,sannan ta dubi barde mai 'kira kamar ta samudawan farko tace 'kai kuma buhu zakaje ka samo mai fad'i da girma yanzunnan' ,'an gama ranki ya dad'e' barde ya fad'a cikin katuwar muryarsa,sannan ya fice. Fulani ta dubi jakadiya dake dur'kushe a gun tace 'mara'kisiya nemo tsumma ,ki tamke min bakin bayarabiyar nan' ,da hanzari jakadiya ta kunce d'amarar da tayi da dankwali ,ta 'karasa ga bolaji dake kwance a sume ,ta d'aga kanta ta d'ora akan cinyarta sannan ta tamke bakinta da dankwali tamau! Bayan mintuna talatin sai ga barde ya shigo d'akin hannunsa ri'ke da 'katon buhu ,kurtagu shima ya shigo ya rusuna yanacewa' angama ranki shi dad'e' ,fulani ta murmusa tace 'madalla,yanzu ku had'u ku d'au wannan ku sata acikin buhun' tana mai nuna musu bolaji dake kwance a sume bakinta tamke da d'ankwali.... Written by :AB [10/15, 8:22 PM] : =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~10~ Tana gama cin abinci,ta ajje littafin,ta nufi kitchen ta kwamfaci ruwa ta sha ,sannan ta had'a kan kwanuka ta fito ta wankesu tas ,sannan ta dawo ta zauna tana cigaba da duba littafinta ,maami tana mata sannu ta hanyar cewa 'ekhuse' ,bolaji ta amsa da 'eshe'! Babalaji ya shigo da sallama,gaba d'aya suka amsa ,bolaji taje ta amshi ledar hannunsa tana ce masa 'ekabo' ,babalaji ya amsa 'my daughter eshe',maami ta tashi da 'kyar tana gyara d'aurin zanin nata,tabarma ta shimfid'a masa,tana mai cewa babalaji 'ekabo' ,bayan ya zauna yana sauke ajiyar zuciya yace 'iya bolaji[maman bolaji] eshe oh,how body' ,'we thank God oh,my husband,how's your day,hope it went well' ,bolaji ta iso da ruwa a cikin kofin silva,ta russuna ta mi'kawa babanta,ya amsa ya shanye tas,bayan ya shanye ya dubi bolaji yana cewa 'thank you my daughter,may the almighty oluwa bless you' 'amin oh' bolaji da maami suka amsa! Babalaji ya dawo da dubansa ga maami yana mai cewa 'hmm,i'm tired oh,we the labourers have been standing at the company's entrance for the past 4hours waiting for our 7month salary to be paid to us,before we get back to work and call of the strike,but the payment did'nt take place,instead the manager told us to excersise patient,and we should come back on tuesday cause the owner of the company will come and tackle the problems!' ,maami ta dubi mijinta cike da tausayi tace 'this is wickedness,i don't know what this country is becoming,but no wahala,oluwa dey ,he dey watch and he's in control' ,babalaji ya amsa mata da 'na so oh,let's wait for the tuesday,we shall see' ,maami ta tashi ta d'auko masa abinci ta kawo masa,yana ci ,tana masa firfita tare da jan sa da hira! ¤¤¤¤ Ranar litinin misalin 7:30am hashim ya gama shiryawa,yayi sallama da iyayensa,direba ya saukeshi a airport,inda palace pilot ke jiransa,ya shiga private jet d'insu,suka d'aga kaduna! Misalin 'karfe 10 na dare ,mai martaba na zaune kishingid'e a d'akin fulani,kasancewar ranar girkinta ne! Fulani ta dubi mai martaba tare da cewa 'gobe ne tafiyar taku ko?' ,'insha Allah' mai martaba ya bata amsa,fulani ta gyara zama tana cewa 'abban hashim baka ganin cewa daraja da arzikin wannan masarauta ya wuce ace ka bud'e kamfani[companies/factories] a garuruwa,ni a ganina sarauta da mulkin ka sun girmi hakan, ,musamman kamfanin pure water da aka bud'e a kano ,da kuma na manja da aka bud'e a garinsu oduduwa,bai kamaci wannan masarautar ba,da kuma kai kanka da ka kasance tsohon gwamna' ,mai martaba yayi murmushi wanda ya 'karawa fuskarsa kwarjini ,yace 'fulani kenan,ni ba kowa bane face d'an adam kamar kowa,wad'annan kamfanonin ba'a bud'e su domin samun kud'i ba ,an bud'esu ne saboda talakawa mazauna yankin da aka bud'e kamfanonin, su samu hanyar da zasu nemi halas da guminsu ta hanyar samun aiki a kamfanonin,kuma kinga a yanayin da 'kasar tamu take ciki,aiki yana yi wa matasa wuyar samu duk da kwalin degree d'insu,,kinga kenan samun aikin matasa a kamfanonina zai sa a rage samun matasa masu zaman banza da kashe wando[jobless youths],kuma da kike cewa masarautar nan ta girmi hakan,ta ina masarautar nan ta girmi haka,me kike d'au sarauta a duniyar nan ne?,mu da mutanen gari,musamman talakawa ,duk d'aya muke a gun Allah! sarauta da mulki sai sarautar ALLAH s.w.t 'malikul mulk',mabuwayi,gagara misali,wanda dukkan mu gaba d'ayan mu a 'karkashin ikonsa da mulkinsa muke! kuma kamfani yanzu na fara 'bud'ewa ,in akwai abinda yafi purewater 'kas'kanci idan har na samu dama sai na bud'e kamfaninsa,in har hakan zai zamo alkhairi ga al'ummar annabi muhammad [s.a.w],musamman talakawa! masarauta bata girmi yin ko wacce irin halastaciyyar sana'a ba,ko da kuwa wannan masarautar tana da daraja da arziki' ,jiki a sanyaye fulani tace 'ALLAH ya bada lada,ya kuma 'kara arziki,na fahimci manufarka,kuma ina fatan sauran sarakuna irinka zasu koyi da kai' ,mai martaba yace 'amin fulani,addu'arku kawai nake bu'kata a kullum,' ,haka suka cigaba hira na farantawa juna rai ,har izuwa lokacin da bacci ya riskesu! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/15, 8:54 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~11~ Washegari da misalin 'karfe 11:00am mai martaba yayi sallama da matansa! Ya kuma d'amka komai da ya shafi fada ga waziri! SULTAN BELLO AIRPORT mai martaba da sultan suka nufa bisa rakiyar fadawa da royal chambers[hakimai,galadima,su shamaki da dai sauransu]! Misalin 'karfe 12:00 na rana modibbo palace private jet ya nausa da mai martaba da sultan sararin samaniya izuwa birnin ikko [lagos] Misalin 'karfe 12:00 na rana modibbo palace private jet ya nausa da mai martaba da sultan sararin samaniya izuwa birnin ikko [lagos]! Da isar su airport d'in jihar lagos ,suke iske an turo masu motoci daga masarautar osun state,da yake 'oba'[sarkin masarautar osun] ya san da zuwan mai martaba! Tafiyar awanni 'kalilan ne tsakanin lagos zuwa osun! Bayan sun d'an huta a masauratar osun,sun gabatar da sallar zuhr,sai suka wuce yankin 'erin' dake jihar osun, bisa rakiyar royal guards na osun's palace! ¤ ¤ ¤ ¤ Gaban gate d'in kamfanin manja na modibbo [MODIBBO RED OIL COMPANY ! Erin] cike yake ma'kil da 'kananan ma'aikatan da ba'a biya su albashinsu ba na tsawon wata bakwai tare da matayensu da 'ya'yayensu,suna masu zanga-zanga,hannayensu ri'ke da cardboard papers mai d'auke da rubutun 'WE N O GO GREE' ,'PAY US OUR SALARY' 'baro 'baro! Cikin wad'annan ma'aikata masu zanga zanga harda babalaji da iyalansa,da yake yau bolaji batada paper hakan yasa ta biyo mahaifinta,haka zalika maami duk da cikin dake jikinta hakan bai hanata biyo bayan mijinta ba domin nema masa ha'kkinsa ,bamidele shi ma yana nan tsaye cikin matasa irinsa,hannunsu ri'ke ganyen darbejiya sai ihu suke suna cewa 'we no go gree,pay our parents their 7months salary!' a gefe guda yan jarida ne suke d'aukan rahoton wannan zanga zangar[demonstrati a gefe guda yan jarida ne suke d'aukan rahoton wannan zanga zangar[demonstration]! A cikin wannan yanayin su mai martaba suka iso kamfani,bai zaci abin ya kai haka ba,domin da 'kyar aka samu ma'aikatan suka matsa daga gaban gate d'n shiga kamfanin! motocinsu suka samu daman wucewa izuwa cikin harabar kamfanin! Mai martaba bai jira an bud'e masa kofar mota ba yafito,sultan na biye dashi,MD dasauran manyan ma'aikata suka zo suna mi'ka gaisuwa! Mai martaba ya umarcesu da yana bu'katan ganawa da manyan shugabannin da aka wakilta a kamfanin domin gano silar wannan matsalar na rashin biyan 'kananun ma'aikata albashi,kuma yana son a kuma shawo kan matsalar! Zaune suke a conference room mai martaba yana tattaunawa dasu ! Bayan tattaunawar ne ,aka gano cewa ashe bursar[ma'aji] ne ya ke danne kud'in albashin 'kananun ma'aikata idan ance ya raba masu baya basu da kuma had'in bakin accountant! A take mai martaba yasa aka rubuta masu takardar kora daga kamfani! Sannan kuma yace wa MD Yaje yasa a bud'ewa ma'aikata gate su shigo domin ya kwantar masu da hankali ! Bayan securities sun bud'e masu gate sun shigo harabar kamfanin sun tsaya suna ifice ificensu! MD ne ri'ke da bututun magana yana mai umartarsu dasuyi shiru su saurari mai martaba,saboda yanzu komai yazo 'karshe ,domin mai martaba [founder of the company] da kansa zai gana dasu ! Bayan sun yi tsit ,Mai martaba ya amshi bututun[mic] ya fara masu magana cikin harshen turanci,yana mai 'kara basu ha'kuri,yan jarida suna gefe suna d'aukan hoto da rahoto! Maami ita ko in banda hararar mai martaba ba abinda takeyi,domin duk jawabin nan nasa ba fahimta take ba,gani take kamar harda sa hannunsa wajen rashin biyan 'kananun ma'aikata albashinsu har na tsawon wata 7! Dur'kusawa tayi da 'kyar tasa yatsu tana laluben dutse,can yatsunta suka dam'ko mata katon dutse a 'kasa ,mi'kewa tayi tsaye tayi jifa da dutsen,batare da kowa ya lura ba sai 'iya folake'[maman folake] dbke tsaye kusa da ita, sauran kuma gaba d'aya hankalinsu na ga mai martaba dake kwararo masu bayani dalla dalla! Mai martaba baiyi aune ba yaji saukar dutse a goshinsa,wanda hakan yayi sanadiyar fitar jini daga goshinsa,jinin kuwa ya 6ata masa farin tufafin dake jikinsa! Hannu yasa ya dafe goshin nasa sanadiyar zogin azaba da rad'ad'i da yaji! Tuni hankula suka tashi,sultan hankalinsa a tashe yayi kan mahaifinsa ,ya ri'ke shi,yana mai cewa MD ya kira ambulance! Security da royal guards[osun palace] suka raraki ma'aikatan da duka,tuni suka tarwatse kowa ya arce,bolaji,babalaji da bamidele suna ri'ke da maami,wacca take jan 'kafa da 'kyar a haka suka fice daga harabar kamfanin,maami ko zuciyarta wasai ,ita a ganinta tayi maganin azzalumi! Ni kuma ililee nace' hmm 'tsuliyar dodo ki ta6o!' written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/15, 8:55 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~12~ Motar ambulance ce ta shigo harabar kamfanin,a take male nurses suka fito daga motar,suka nufi wajen mai martaba domin shigar da shi cikin motar,bayan sun kwantar dashi ,likitan da aka zo dashi yayi masa treating d'in ciwo tare da yi masa dressing d'in ciwon! Bayan likitan ya gama yi masa treatment d'in! Ambulance d'in suka tarkata suka tafi ! ,mai martaba ya umarci royal guards dasu wuce dashi airport ,bayan ya jaddadawa MD cewa ya tabbatar ya biya ma'aikatannan albashinsu,kuma kar ya kuskura yaji anyi masu wani abu! Ta waya mai martaba yayi sallama da 'oba' domin basu biya ta fada [osun's palace] ba, airport d'in lagos,suka wuce,mai martaba da sultan suka haye modibbo's palace private jet, pilot ya d'aga dasu izuwa jihar sokoto! Suma royal guards suka juya suka koma jihar osun! ¤ ¤ ¤ Fulani ce ta taresu cike da fargaba ganin mai martaba goshinsa d'aure da plaster ,duba ta kai ga sultan tana mai tambayarsa 'lafiya? Meya sami goshin abbanku',mai martaba ya nemi gu ya zauna,sultan kuma ya labartawa fulani abinda ya faru,daman me neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki,nan fulani ta fara zuba bala'i kamar zata ari baki tana cewa 'kaga irin ta ko,tsiyar YARE kenan,in mutum yayi magana kuce an cika nuna kabilanci,a gaskiya idan akace mutum ba bahaushe bane ,toh yayi asara babba' ,ummu ce ta shigo rest room d'in ,domin yiwa mai martaba sannu da dawowa ,maganganun fulani ne yasa tayi turus tana tambayar lafiya ,fulani ta amshe da cewa 'ina lafiya kuwa,dubi goshinsa ki gani,mutanen oduduwa masu kashi a leda ,su ne sukaso su halaka mana shi,toh ta Allah ba tasu ba ,tubabbu kawai',mai martaba ne ya katseta ta hanyar cewa 'ya isa haka ,bana son in 'kara jin kin tada zancennan,tsautsayi ne ,kuma baya wuce ranarsa',ranta bai so ba,amma ba yadda ta iya,dole tayi shiru ,ummu kuwa tayiwa mai martaba sannu da zuwa ,takuma jajanta masa,sannan ta ja hannun sultan suka fice ,fulani kuwa ficewa tayi taje tasa hadimai su jera abinci akan dinning ,wato suyi setting table .saboda mai martaba zai zo yaci! ¤¤¤ Cikin dare fulani na zaune ita kad'ai a d'akinta,abin duniya ya isheta,'kiyayyar YARE na 'kara ruruwa a zuciyarta! kasancewar mai martaba yau a d'akin ummu yake! Hadimanta kuma suna zauna a gaban d'akin nata! Wayarta ta janyo domin bugawa hashim ! Ringing biyu Hashim ya d'auka , tun kafin yayi magana ,fulani ta fara cewa 'ina son ka d'ibi sojoji,gobe kuje yankin erin dake jihar osun,ku ci uban duk wani 'karamin ma'aikacin kamfanin abbanku' ,a tausashe hashim yace 'umma meye faru' ,nan fulani ta kwashe labari kamar yadda sultan ya labarta mata ta gaya masa,har da 'karin gishiri! Hashim wanda ransa ya gama 6aci da jin haka,allurar tasa ta motsa ,cikin 6acin rai yace 'ina abban yake,ya jikin nasa?' ,fulani ta amsa da 'da sauki,gashi can a kwance,kanshi ya suntume! ' sannan tace'my soul dear ya zama dole ka d'au mataki fa,ya kamata ka d'au fansa ga jinin abbanku da suka zubar' ,hashim ranshi a 6ace yace 'angama ,insha Allahu gobe da safe zamu tashi izuwa garin,zasu gane kurensu ,sai sun gane cewa ba'a ja da masauratar modibbo a zauna lafia' ,fulani tace 'thats my souldear ,the soldier of the nation,ALLAH ya kai ku lafiya' ,a haka sukayi sallama fulani tana mai 'kara zugasHashim wanda ransa ya gama 6aci da jin haka,allurar tasa ta motsa ,cikin 6acin rai yace 'ina abban yake,ya jikin nasa?' ,fulani ta amsa da 'da sauki,gashi can a kwance,kanshi ya suntume! ' sannan tace'my soul dear ya zama dole ka d'au mataki fa,ya kamata ka d'au fansa ga jinin abbanku da suka zubar',hashim ranshi a 6ace yace'angama insha Allahu,gobe da safe zamu tashi izuwa garin,zasu gane kurensu,sai sun gane cewa ba'a ja da masarautar modibbo a zauna lafiya',fulani tace'that's my souldear,the soldier of the nation ,ALLAH ya kai ku lafiya!' a haka sukayi sallama,tana mai 'kara zugashi! Bayan sun gama wayar ,ta ajje ,ta bi lafiyar gadonta,tayi kwanciyarta zuciyarta fari Tas! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/15, 8:56 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~13~ Tunda garin Allah ya waye maami take fama da ciwon na'kuda ,amma ahaka ta daure ta cije tana tsoran kar bolaji ta gane halin da take ciki,saboda gane hakan ,na iya sawa bolaji ta fasa zuwa makaranta! Bolaji ta fito daga d'akinta sanye da farin shirt long sleeve,sai guntun blue skirt daya wuce 'kaurinta,sai kuma blue baret[hula]data kifa akanta,kafarta sanye da farin safa da brown sandal,hannunta ri'ke da biro da pencil! Fuskarta d'auke da murmushi tayiwa Maami da babalaji sallama,sannan ta fice daga gidan! Murna kawai take , saboda yau zasu zana jarabawar 'karshe wato yoruba language! ¤¤¤ Misalin 'karfe 1:00 na rana convoy d'in gwanayen motocin Nigerian army guda goma,suka d'inga shigowa yankin 'erin'! Mutanen yankin sai bin motocin suke da kallo suna masu tambayar junansu 'lafiya!' MODIBBO RED OIL COMPANY motocin suka nufa,da isar su kamfanin, Gateman ya wangale masu gate jikinsa na rawa! Bayan sunyi parking motocin a harabar kamfanin! Sojoji ne d'auke da bindigu suka d'inga durowa daga motocin,fuskarsu babu alamun wasa! Capt.hashim ne jagoransu,domin shine a gaba,fuskarsa babu annuri ko kad'an ,jikinsa a murd'e a cikin kakin sojoji,wanda hakan ya bayyanar da mazantakarsa! MD ne ya fito daga cikin office d'insa jiki na rawa ya nufesu ,saboda ya shaida fuskar hashim! Hashim fuska a d'aure ya umarci MD da company securities da su fita su shaidawa mutanen mazauna yankin su fito daga gidajensu domin yana son yin magana dasu! Da hanzari MD da securities d'in suka fice daga kamfanin domin cika umarnin capt.hashim! Cikin awa d'aya [village square] ya cika ma'kil da mutanen yankin erin ,mata da maza ,yara da manya,duk a tsugune,kowa cikinsa ya d'uri ruwa ganin murd'a murd'an sojoji hannunsu ri'ke da bindigu ! Murya a kasaushe hashim ya fara magana yana cewa 'where are the red oil company workers who demonstrated[zanga zanga] yesterday with their families?' ,jiki na kyarma 'kananun ma'aikatan suka d'inga fitowa d'aya bayan d'aya,suna tsoron suyi wani abu yanzu asa bindiga bindigesu! Bayan sun gama fitowa ,hashim ya dubesu ya buga masu tsawa yana cewa 'who amongst you stoned my father?' ,baki na rawa ko wannensu ya fara cewa 'no be me oh' ,'ah i no know oh' ,tsawa ya 'kara buga masu yana cewa 'fetch the person out now,or else all of you will face my wrath',hakan yasa suka yi tsit,jiki na rawa! Iya folake ce ta d'aga hannu baki na rawa tace 'sir!' ,a fusace hashim ya dubeta yace 'WHAT?' , baki na rawa iya folake tace 'it's a woman that stoned your father' ,'who's she? ,where is she and her family?' ,hashim ya tambaya murya a kausashe! Iya folake jikinta na rawa tace 'the woman is 'iya bolaji',she and her family are not here,because she's in the state of labour ,her husband took her to the hospital an hour ago ,i even saw them when they were leaving for the hospital' ,hashim fuska a murtake yace'are you sure she's the one who stoned my father' ,iya folake tace 'i'm very sure sir' ,sannan ta d'ora yatsa akan harshenta tana cewa 'i swear i saw her with my 2 koro koro eyes ,when she picked the stone' ,nan wasu mata masu shaidar zur suka had'a baki suna cewa 'it's true sir,it's iya bolaji oh' Hashim ya umarcesu da su tashi su tafi ,amma iya folake da sauran matan da sukayi magana su tsaya! Haka suka tashi suka nufi gidajensu ,suna masu murna da ku6utar dasu da iya folake tayi,da yanzu a bindigesu a banza! Bayan kowa ya watse hashim ya dubesu yana cewa 'take us to the hospital,i hope it's not far?' iya ayomide ta amsa masa da cewa 'e no far oh,we fit trek go sef!' Hashim ya dubi sauran sojojin tare da ce masu 'lets go' ,haka suka d'unguma suka tafi,su iya folake a gaba suna yin jagora! Written by:ABDUL AZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~13~ Tunda garin Allah ya waye maami take fama da ciwon na'kuda ,amma ahaka ta daure ta cije tana tsoran kar bolaji ta gane halin da take ciki,saboda gane hakan ,na iya sawa bolaji ta fasa zuwa makaranta! Bolaji ta fito daga d'akinta sanye da farin shirt long sleeve,sai guntun blue skirt daya wuce 'kaurinta,sai kuma blue baret[hula]data kifa akanta,kafarta sanye da farin safa da brown sandal,hannunta ri'ke da biro da pencil! Fuskarta d'auke da murmushi tayiwa Maami da babalaji sallama,sannan ta fice daga gidan! Murna kawai take , saboda yau zasu zana jarabawar 'karshe wato yoruba language! ¤¤¤ Misalin 'karfe 1:00 na rana convoy d'in gwanayen motocin Nigerian army guda goma,suka d'inga shigowa yankin 'erin'! Mutanen yankin sai bin motocin suke da kallo suna masu tambayar junansu 'lafiya!' MODIBBO RED OIL COMPANY motocin suka nufa,da isar su kamfanin, Gateman ya wangale masu gate jikinsa na rawa! Bayan sunyi parking motocin a harabar kamfanin! Sojoji ne d'auke da bindigu suka d'inga durowa daga motocin,fuskarsu babu alamun wasa! Capt.hashim ne jagoransu,domin shine a gaba,fuskarsa babu annuri ko kad'an ,jikinsa a murd'e a cikin kakin sojoji,wanda hakan ya bayyanar da mazantakarsa! MD ne ya fito daga cikin office d'insa jiki na rawa ya nufesu ,saboda ya shaida fuskar hashim! Hashim fuska a d'aure ya umarci MD da company securities da su fita su shaidawa mutanen mazauna yankin su fito daga gidajensu domin yana son yin magana dasu! Da hanzari MD da securities d'in suka fice daga kamfanin domin cika umarnin capt.hashim! Cikin awa d'aya [village square] ya cika ma'kil da mutanen yankin erin ,mata da maza ,yara da manya,duk a tsugune,kowa cikinsa ya d'uri ruwa ganin murd'a murd'an sojoji hannunsu ri'ke da bindigu ! Murya a kasaushe hashim ya fara magana yana cewa 'where are the red oil company workers who demonstrated[zanga zanga] yesterday with their families?' ,jiki na kyarma 'kananun ma'aikatan suka d'inga fitowa d'aya bayan d'aya,suna tsoron suyi wani abu yanzu asa bindiga bindigesu! Bayan sun gama fitowa ,hashim ya dubesu ya buga masu tsawa yana cewa 'who amongst you stoned my father?' ,baki na rawa ko wannensu ya fara cewa 'no be me oh' ,'ah i no know oh' ,tsawa ya 'kara buga masu yana cewa 'fetch the person out now,or else all of you will face my wrath',hakan yasa suka yi tsit,jiki na rawa! Iya folake ce ta d'aga hannu baki na rawa tace 'sir!' ,a fusace hashim ya dubeta yace 'WHAT?' , baki na rawa iya folake tace 'it's a woman that stoned your father' ,'who's she? ,where is she and her family?' ,hashim ya tambaya murya a kausashe! Iya folake jikinta na rawa tace 'the woman is 'iya bolaji',she and her family are not here,because she's in the state of labour ,her husband took her to the hospital an hour ago ,i even saw them when they were leaving for the hospital' ,hashim fuska a murtake yace'are you sure she's the one who stoned my father' ,iya folake tace 'i'm very sure sir' ,sannan ta d'ora yatsa akan harshenta tana cewa 'i swear i saw her with my 2 koro koro eyes ,when she picked the stone' ,nan wasu mata masu shaidar zur suka had'a baki suna cewa 'it's true sir,it's iya bolaji oh' Hashim ya umarcesu da su tashi su tafi ,amma iya folake da sauran matan da sukayi magana su tsaya! Haka suka tashi suka nufi gidajensu ,suna masu murna da ku6utar dasu da iya folake tayi,da yanzu a bindigesu a banza! Bayan kowa ya watse hashim ya dubesu yana cewa 'take us to the hospital,i hope it's not far?' iya ayomide ta amsa masa da cewa 'e no far oh,we fit trek go sef!' Hashim ya dubi sauran sojojin tare da ce masu 'lets go' ,haka suka d'unguma suka tafi,su iya folake a gaba suna yin jagora! Written by:ABDUL AZIZ ILILEE ISMA'IL [10/15, 8:58 PM] =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~14~ Bolaji tana tsaye tare da 'kawayenta a harabar makarantar [G.S.S ERIN] ,fitowarsu kenan daga jarabawa sai hira suke suna murnar kamalla jarabawarsu ta 'karshe a yau ! Shigowar Wata matashiyar budurwa cikin harabar makarantar a guje tana mai kwatsawa bolaji kira tare wurwurga ido ,yasa hankalin kowa ya koma kanta! Bolaji ce ta tareta tana tambayarta da cewa 'ahh funmilayo wetin happen ,why are you shouting my name like this?' ,matashiyar da bolaji ta kira da funmilyo ta sauke numfashi tana haki tace 'bolaji,your mother was taken to the hospital....' ,da sauri bolaji ta katseta ta hanyar cewa 'which hospital was she taken to? ' ,funmilayo tana haki tare da kuma saita numfashi tace'ERIN MATERNITY and some sol...' ,bolaji bata bari funmilayo ta 'karasa zancenta ba,ta kwasa a guje ta fice daga makarantar! Gudu take kamar wacce zaki yake bin ta abaya! 'bauraniyar hanya [shortcut] bolaji ta bi,hakan yasa cikin minti 5 ta iso mataulacin asibitin da ko 'kwararren likita babu ballantana isasshun nurses! Sai haki take tana sauke ajiyar zuciya ,duk ta gama ji'kewa da gumi,a haka ta ja 'kafafunta ta shiga akurkin asibitin! Idanunta ne suka hango mata babalaji da bamidele a zaune,sun zabga uban tagumi,da hanzari bolaji ta tunkaresu cike da d'oki tana tambayarsu da cewa 'where's maami,has she deliver yet?' ,'not yet' bamidele ya bata amsa,babalaji yace 'she's in the labour room!' Da sauri bolaji ta fad'a dakin haihuwar [labour room] tana mai raba idanu! Maami ta hango kwance akan gado duk ta jike da gumi sai ihu take tana cewa 'olohun oh!',nurse d'aya ce tsaye akanta sai cewa take 'oya push abeg,you need to push oh,if not, you go suffer your self and the baby!' ,bolaji da gudu ta 'karasa ga mahaifiyarta tasa hannunta ta ri'ko hannun maami,tasa d'aya hannun tana goge mata gumin da yake tsastsafowa akan goshinta! Tana cewa 'maami kpele oh! all will be well,try and push! Maami ta runtse idanunta dan azaba,'karfinta duk ya gama 'karewa,haka ta daure ta cije ta yun'kura tayi wani irin nishi mai 'karfi' ,nurse fuskarta a washe tace 'oya keep pushing the baby's head is coming!' ¤¤¤ Babalaji da bamidele suna zaune a inda bolaji ta barsu, bakinsu d'auke da addu'a! Kawai sai gani sukayi iya folake da iya ayomide tare da wasu matan da sojoji suna shigowa harabar asibitin! Basu daina mamaki ba har suka iso inda suke azaune! Iya folake ce ta nuna babalaji da yatsa tana cewa 'na the woman husband be Iya folake ce ta nuna babalaji da yatsa tana cewa 'na the woman husband be this!' Hashim ya dubi babalaji ya daka masa tsawa yana cewa 'Mr man where's your wife'?' ,jiki na kyarma,baki na rawa ,babalaji yace 'she's in the labour room ,but what....' ,Hashim bai jira babalaji ya 'karasa maganarsa ba ya katseshi ta hanyar kai dubansa ga su iya folake yana cewa 'take us to the labour room!' A haka suka d'unguma gaba d'ayansu suka shiga d'akin haihuwar,su iya folake[jagora] suna gaba! Babalaji da bamidele suka rufa masu baya hankalinsu a tashe! Da shigarsu cikin d'akin ,hashim ya dubi iya folake yace 'where's she' ,da yatsa ta nuna masa maami dake kwance a kan gado tana mai yun'kurin haihuwa! Cike da zafin nama hashim ya nufi gadon tare da kwatsawa nurse d'in dake faman cewa maami 'oya push the baby's head is coming!'' wata mahaukaciyar tsawa yana cewa 'get lost woman' ,ganin jikinsa da khakin sojoji ,ga kuma sauran sojojin dake tsaye kikam fuskarsu babu annuri,hannunsu ri'ke da bindigu, yasa nurse d'in matsawa daga wajen jikinta na rawa! Bolaji ta kai dubanta ga hashim ,fuskarta d'auke da mamaki! Wani wawan mari mai amo da sauti Hashim ya kwad'awa maami a fuska yana cewa 'how dare you stoned my father'! Zafin marin ne yasa maami tayi wani irin 'ka'k'karfar sha'kuwar da yayi sanadiyar komawar jaririn dake shirin fitowa duniya! Suman tsaye bolaji tayi hannunta dai ri'ke da hannun maami! Su kansu iya folake sai da suka firgita da abinda capt.hashim yayiwa Su kansu iya folake sai da suka firgita da abinda capt.hashim yayiwa maami! Bolaji bata dawo hayyacinta ba sai da taji hannun maami ya su6uce daga hannunta 'sharaf!' Da hanzari ta kai dubanta ga maami wanda tuni numfashinta ya tsaya cak,jinkinta yayi sanyi ,idanunta sun 'kafe! Ganin haka yasa bolaji ta fashe da wani irin kuka mai zafi,tana jijjiga maami tana cewa 'no maami,please don't go,wake up please!',amma ina ,maami ta amsa kiran Allah! Bolaji ta kifa kanta akan 'kirjin maami tana mai rusa kuka! Ganin halin da maami ke ciki yasa Babalaji ya ri'ke 'kirjinsa tare da sulalewa 'kasa,bamidele ne yayi hanzarin taroshi ,tare da jijjigashi yana cewa 'baba,kilode!' ,amma ina, babalaji ya amsa kiran Allah ,sakamakon zuciyarsa da ta buga! Bamidele ya fashe da wani irin mahaukacin kuka yana cewa 'baba iis gone too!' created by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/15, 8:59 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~15~ Furucin bamidele ne yasa bolaji dake kwance akan gawar maami tana risgar kuka d'agowa tare da kai dubanta ga gawar babalaji da ke kwance a jikin bamidele! A fusace bolaji ta mi'ke tsaye cikin zafin nama ta tunkari hashim da ke tsaye 'kikam ko gezau bai motsa ba ,sojoji na bayansa ,fuskarsu a mutur'ke,hannunsu ri'ke da bindigu! Bolaji ta dage iya 'karfinta ta d'aga hannu tare da ware yatsunta guda biyar,ta zabgawa kumatun hashim mari gudu uku kyawawa,d'aya bayan d'aya,kuma hagu da dama! Ji kake GAU! GAU! GAU! Hashim yana tsaye 'kikam ko 'kadan marin bai sa ya motsa ba,yana tsaye daram saikace dutse! Da sauri sojoji su ka yo mata caaa da bindigarsu ! Hashim ya dakatar dasu ta hanyar d'aga musu hannunsa guda d'aya! Bolaji tasa hannu ta cakumi kwalar khakinsa,jajayen idanunta akan nasa,muryarta a kausashe ta fara ce masa ''who the hell are you?, what gave you the right to slap my mother?, what sort of crime did my mother commit,that you can't wait for her to give birth! if you don't have respect for womanhood ,you ought to have respect for motherhood? why is own your case different?'' Bolaji ta tambaya cikin karaji ,hannunta ri'ke da kwalar khakinsa ta maimata kalmar 'WHY?' Hashim ya rintse idanunsa gam,duk tsigar jikinsa ya tashi,gashin jikinsa duk suka mimmi'ke,jijiyoyin jikinsa duk suka kumbura! Bolaji ta cika masa kwalar khakinsa,ta fara dukan 'kirjinsa da hannunta duka biyun ,tana kuka tana cewa' You are heartless! Ruthless! You are so evil and mean! You are an imbecile,a monster!,you have no heart at all! Hashim bud'e idanunsa yayi da sukayi jajir ya d'amki hannayen bolaji da take dukan 'kirjansa dasu! Cike da zafin nama yayi watsi da ita,wanda hakan yayi sanadiyar fad'uwarta 'kasa,ta kuma buge goshinta da jikin gadon da gawar maami ke kwance! Tashi tayi zaune da 'kyar ,ta dafe goshinta tana mai cigaba da risgar kuka ,ta d'aga kanta ta dubi hashim da rinannun idanunta tace 'you are the cause of my parents death! may you live long so as to live your life in sadness and sorrow! you will never know happiness in your life,you will live your life in misery and pain..!' Hashim a fusace ya d'aga hannunsa a dun'kule da niyyar naushinta! Sai kuma ya fasa,yayi 'kwafa yace 'we shall see!' ,sannan ya juya ya dubi sojojin yace dasu 'lets go !', Bayan ficewarsu hashim daga d'akin ,su iya folake suka fashe da kuka suna masu tsinewa wad'annan sojojin,domin basu ta6a zaton haka daga garesu ba,sun zata cewa ganin iya bolaji a halin na'kuda zai sa su fasa aikata 'kudirinsu ! Jiki a sanyaye suka nufi bolaji suna lallashinta,suna kuma tsinewa wannan akurkin asibitin dake fama da rashin wadatattun ma'aikJiki a sanyaye suka nufi bolaji suna lallashinta,suna kuma tsinewa wannan akurkin asibitin dake fama da rashin wadatattun ma'aikata! Iya ayomide ce ta fita taje ta sanarwa da mutanen yankin ,mutuwar babalaji da maami! Cikin 'kan'kanin lokaci mutanen yankin suka zo asibitin da makara guda biyu , suka d'auki gawar maami da babalaji,suka kai gida,aka musu wanka ,aka yi musu suttura,aka sallacesu sannan aka sadasu da gidansu na gaskiya! Bolaji da bamidele sun sha kuka sosai,domin kowa ya tausayawa musu ! ¤¤¤¤ Wayar hashim ce tayi ringing ,sai da wayar ta kusan tsinkewa sannan hashim d'in ya amsa,yana amsawa kuwa,a d'aya bangaren fulani ce ta washe baki tana cewa 'my souldear,dafatan ka d'auki fansa ga jinin da mutanen oduduwa suka fitar daga goshin mahaifinka ko?', da 'eh' hashim ya bata amsa ,fulani tayi 'kasa da murya tana cewa 'yawwa my souldear,the soldier of the nation,yanzu abinda nake so da kai ,shine ina son kajawa MD da sauran ma'aikatan kamfanin kunnen da kada su kuskura mahaifinku yaji labarin zuwanka erin' ,hashim yace 'angama umma' ,fulani tace 'kasan halinsa na 'kaunar YARE da talakawa,yanzu yana samun labarin zuwanka ,zai tadawa mutane hankali a banza,kaima idan kunyi waya ,kada ma ka nuna masa cewa kasan da zancen mutanen oduduwa sun jefeshi da dutse',a haka sukayi sallamWayar hashim ce tayi ringing ,sai da wayar ta kusan tsinkewa sannan hashim d'in ya amsa,yana amsawa kuwa,a d'aya bangaren fulani ce ta washe baki tana cewa 'my souldear,dafatan ka d'auki fansa ga jinin da mutanen oduduwa suka fitar daga goshin mahaifinka ko?', da 'eh' hashim ya bata amsa ,fulani tayi 'kasa da murya tana cewa 'yawwa my souldear,the soldier of the nation,yanzu abinda nake so da kai ,shine ina son kajawa MD da sauran ma'aikatan kamfanin kunnen da kada su kuskura mahaifinku yaji labarin zuwanka erin' ,hashim yace 'angama umma' ,fulani tace 'kasan halinsa na 'kaunar YARE da talakawa,yanzu yana samun labarin zuwanka ,zai tadawa mutane hankali a banza,kaima idan kunyi waya ,kada ma ka nuna masa cewa kasan da zancen mutanen oduduwa sun jefeshi da dutse',a haka sukayi sallama! Hashim kuwa, ya cika umarnin fulani ,ta hanyar jawa MD da sauran ma'aikata kunne da kada su kuskura ya ji labarin cewa sun shaidawa mai martaba zuwansa da sojoji yankin erin,in ba haka ba zasu yabawa aya za'kinta' ,MD da sauran ma'aikata jiki na rawa suka amsa da 'toh!' Cikin dare hashim da sauran sojoji ,suka samu daji acikin yankin erin suka yada zango ,domin hashim ya buga waya can kaduna ya nemi izini akan cewa sai nan da kwana hud'u zasu dawo,domin basu gama da abinda ya kawosu yankin erin ba! A dajin suka kafa {tent},kuma duk abinda xasu bu'kata ,hashim ya amshi kud'i gu MD,sun je kasuwa sun siyo! Bayan sun gabatar da sallar isha ,kowannesu ya shige [tent] ya kwanta ,hashim zuciyarsa tafarfasa take ga abinda bolaji ta aiketa a gareshi ,domin tunda uwarsa ta haifeshi ,mace bata ta6a d'aga masa murya ba,balle kuma ace tasa hannu ta mareshi,ya zama dole ya koyawa bolaji hankali,saboda ba'a ta6a CAPT.YARIMA HASHIM ATTAHIRU MODIBBO! a kuma zauna lafiya ,ya zama dole ya d'au fansa ga marin da bolaji tayi masa! Yana mai shafa kumatunsa! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~15~ Furucin bamidele ne yasa bolaji dake kwance akan gawar maami tana risgar kuka d'agowa tare da kai dubanta ga gawar babalaji da ke kwance a jikin bamidele! A fusace bolaji ta mi'ke tsaye cikin zafin nama ta tunkari hashim da ke tsaye 'kikam ko gezau bai motsa ba ,sojoji na bayansa ,fuskarsu a mutur'ke,hannunsu ri'ke da bindigu! Bolaji ta dage iya 'karfinta ta d'aga hannu tare da ware yatsunta guda biyar,ta zabgawa kumatun hashim mari gudu uku kyawawa,d'aya bayan d'aya,kuma hagu da dama! Ji kake GAU! GAU! GAU! Hashim yana tsaye 'kikam ko 'kadan marin bai sa ya motsa ba,yana tsaye daram saikace dutse! Da sauri sojoji su ka yo mata caaa da bindigarsu ! Hashim ya dakatar dasu ta hanyar d'aga musu hannunsa guda d'aya! Bolaji tasa hannu ta cakumi kwalar khakinsa,jajayen idanunta akan nasa,muryarta a kausashe ta fara ce masa ''who the hell are you?, what gave you the right to slap my mother?, what sort of crime did my mother commit,that you can't wait for her to give birth! if you don't have respect for womanhood ,you ought to have respect for motherhood? why is own your case different?'' Bolaji ta tambaya cikin karaji ,hannunta ri'ke da kwalar khakinsa ta maimata kalmar 'WHY?' Hashim ya rintse idanunsa gam,duk tsigar jikinsa ya tashi,gashin jikinsa duk suka mimmi'ke,jijiyoyin jikinsa duk suka kumbura! Bolaji ta cika masa kwalar khakinsa,ta fara dukan 'kirjinsa da hannunta duka biyun ,tana kuka tana cewa' You are heartless! Ruthless! You are so evil and mean! You are an imbecile,a monster!,you have no heart at all! Hashim bud'e idanunsa yayi da sukayi jajir ya d'amki hannayen bolaji da take dukan 'kirjansa dasu! Cike da zafin nama yayi watsi da ita,wanda hakan yayi sanadiyar fad'uwarta 'kasa,ta kuma buge goshinta da jikin gadon da gawar maami ke kwance! Tashi tayi zaune da 'kyar ,ta dafe goshinta tana mai cigaba da risgar kuka ,ta d'aga kanta ta dubi hashim da rinannun idanunta tace 'you are the cause of my parents death! may you live long so as to live your life in sadness and sorrow! you will never know happiness in your life,you will live your life in misery and pain..!' Hashim a fusace ya d'aga hannunsa a dun'kule da niyyar naushinta! Sai kuma ya fasa,yayi 'kwafa yace 'we shall see!' ,sannan ya juya ya dubi sojojin yace dasu 'lets go !', Bayan ficewarsu hashim daga d'akin ,su iya folake suka fashe da kuka suna masu tsinewa wad'annan sojojin,domin basu ta6a zaton haka daga garesu ba,sun zata cewa ganin iya bolaji a halin na'kuda zai sa su fasa aikata 'kudirinsu ! Jiki a sanyaye suka nufi bolaji suna lallashinta,suna kuma tsinewa wannan akurkin asibitin dake fama da rashin wadatattun ma'aikJiki a sanyaye suka nufi bolaji suna lallashinta,suna kuma tsinewa wannan akurkin asibitin dake fama da rashin wadatattun ma'aikata! Iya ayomide ce ta fita taje ta sanarwa da mutanen yankin ,mutuwar babalaji da maami! Cikin 'kan'kanin lokaci mutanen yankin suka zo asibitin da makara guda biyu , suka d'auki gawar maami da babalaji,suka kai gida,aka musu wanka ,aka yi musu suttura,aka sallacesu sannan aka sadasu da gidansu na gaskiya! Bolaji da bamidele sun sha kuka sosai,domin kowa ya tausayawa musu ! ¤¤¤¤ Wayar hashim ce tayi ringing ,sai da wayar ta kusan tsinkewa sannan hashim d'in ya amsa,yana amsawa kuwa,a d'aya bangaren fulani ce ta washe baki tana cewa 'my souldear,dafatan ka d'auki fansa ga jinin da mutanen oduduwa suka fitar daga goshin mahaifinka ko?', da 'eh' hashim ya bata amsa ,fulani tayi 'kasa da murya tana cewa 'yawwa my souldear,the soldier of the nation,yanzu abinda nake so da kai ,shine ina son kajawa MD da sauran ma'aikatan kamfanin kunnen da kada su kuskura mahaifinku yaji labarin zuwanka erin' ,hashim yace 'angama umma' ,fulani tace 'kasan halinsa na 'kaunar YARE da talakawa,yanzu yana samun labarin zuwanka ,zai tadawa mutane hankali a banza,kaima idan kunyi waya ,kada ma ka nuna masa cewa kasan da zancen mutanen oduduwa sun jefeshi da dutse',a haka sukayi sallamWayar hashim ce tayi ringing ,sai da wayar ta kusan tsinkewa sannan hashim d'in ya amsa,yana amsawa kuwa,a d'aya bangaren fulani ce ta washe baki tana cewa 'my souldear,dafatan ka d'auki fansa ga jinin da mutanen oduduwa suka fitar daga goshin mahaifinka ko?', da 'eh' hashim ya bata amsa ,fulani tayi 'kasa da murya tana cewa 'yawwa my souldear,the soldier of the nation,yanzu abinda nake so da kai ,shine ina son kajawa MD da sauran ma'aikatan kamfanin kunnen da kada su kuskura mahaifinku yaji labarin zuwanka erin' ,hashim yace 'angama umma' ,fulani tace 'kasan halinsa na 'kaunar YARE da talakawa,yanzu yana samun labarin zuwanka ,zai tadawa mutane hankali a banza,kaima idan kunyi waya ,kada ma ka nuna masa cewa kasan da zancen mutanen oduduwa sun jefeshi da dutse',a haka sukayi sallama! Hashim kuwa, ya cika umarnin fulani ,ta hanyar jawa MD da sauran ma'aikata kunne da kada su kuskura ya ji labarin cewa sun shaidawa mai martaba zuwansa da sojoji yankin erin,in ba haka ba zasu yabawa aya za'kinta' ,MD da sauran ma'aikata jiki na rawa suka amsa da 'toh!' Cikin dare hashim da sauran sojoji ,suka samu daji acikin yankin erin suka yada zango ,domin hashim ya buga waya can kaduna ya nemi izini akan cewa sai nan da kwana hud'u zasu dawo,domin basu gama da abinda ya kawosu yankin erin ba! A dajin suka kafa {tent},kuma duk abinda xasu bu'kata ,hashim ya amshi kud'i gu MD,sun je kasuwa sun siyo! Bayan sun gabatar da sallar isha ,kowannesu ya shige [tent] ya kwanta ,hashim zuciyarsa tafarfasa take ga abinda bolaji ta aiketa a gareshi ,domin tunda uwarsa ta haifeshi ,mace bata ta6a d'aga masa murya ba,balle kuma ace tasa hannu ta mareshi,ya zama dole ya koyawa bolaji hankali,saboda ba'a ta6a CAPT.YARIMA HASHIM ATTAHIRU MODIBBO! a kuma zauna lafiya ,ya zama dole ya d'au fansa ga marin da bolaji tayi masa! Yana mai shafa kumatunsa! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 10:51 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~16~ Bolaji in banda kuka da ajiyar zuciya da yin addu'o'i babu abinda takeyi,kowa ya ganta sai ya tausaya mata duk ta 'kara yin duhu ta rame,haka zalika bamidele ya shiga wani hali sanadiyar rasuwar iyayensa,a haka suka cigaba da amsar gaisuwa har akayi sadakar Uku! Cikin dare bolaji da bamidele suna Zaune a tsakar gida tare da wasu dangin iyayensu wanda basu wuce guda goma ba! Kawai sai ganin sojoji sukayi sun fad'o gidan batare da sallama ba,wanda hakan yasa gaba d'ayansu suka tsure in an d'auke bolaji ! Tsoro ya bayyana 'karara akan fuskar bamidele wanda a yanzu in akwai abinda yake tsoro a duniya toh bai wuce soja ba! Gadan gadan sojojin sukayi kan bolaji dake zaune akan darduma sanye da hijab,ko kad'an bata tsorata ba! Cicci6arta sukayi,tare da ficewa da ita waje, batare da kowa yayi yun'kurin hanasu ba,ita kanta bolaji kallonsu kawai take taga iya gudun ruwansu,hakan yasa tayi lamo a hannunsu! Dajin da suka yada zango suka wuce da ita! Yan yankin erin suka fito daga gidanjensu, suna kallon yadda sojojin suka wuce da bolaji daji ,suna masu tausayawa mata,da kuma tsinewa capt.hashim a zukatansu,suna son taimakawa bolaji ,amma babu hali domin suna tsoron a harbesu! Capt.hashim yana zaune akan wani kututturen icce dake tsakiyar dajin,sanye yake da ba'kar body hug ,da kuma wandon khaki,fuskarsa babu annuri ko kad'an! Ko da sojojin suka iso gareshi,sai suka watsar da bolaji a gaban kafafunsa! Hashim ya d'aga kai ya dubesu yace 'leave us alone!',sannan ya dawo da dubansa ga bolaji wacce ta tashi zaune tana kakka6e hijabinta! Tsawa ya daka mata yana cewa 'hey! behave your self!' ,she'ke'ke ta tsaya kallonsa ,sannan ta kai dubanta ga dajin idanu,wanda hasken wata ne ya haska Tsawa ya daka mata yana cewa 'hey! behave your self!' ,she'ke'ke ta tsaya kallonsa ,sannan ta kai dubanta ga dajin idanu,wanda hasken wata ne ya haskake! Sannan tayi 'kwafa ta cigaba da kakka6e hijabinta ba tare da tasan me take kakka6ewa! Murya a kausashe hashim yace 'hey....' ,bolaji tayi saurin katseshi ta hanyar cewa 'abeg oh,free me jorh,na wetin,ahh the wickedness wey do me ,never do you? oya kill me too,make i go join my parent for heaven.....'' ,hashim ne ya katseta ta hanyar cewa 'keep your mouth shut! don't you have manners,i'm talking you are talking ,who is the master here! 'GOD!' ,bolaji ta bashi amsa tana mai tashi tsaye sannan ta she'ke da dariya wanda ya taho da zubar hawaye daga idanunta,tana tafa hannayenta tace'see who's talking about manners oh,manners my feet!' ,hashim a zafafe ya mi'ke ,idanunsa jajir ya nunata da yatsa yana cewa 'don't try to mess with me ,cause you don't know what i'm capable of doing to you!' ,bolaji ta chafke ta hanyar cewa 'you are capable of killing,so i'm not scared of you .cause you have done enough damage to my life,so what else are going to do ,to me? Kill me?' bolaji ta tambayeshi tana mai tsurawa idanunsa ido! Hashim zuciyarsa na tafasa yasa hannu d'aya ya fisgota ta fad'o kirjinsa,ya ri'keta gam! Bolaji tasa Hannu tana dukan 'kirjinsa tana cewa 'get your filthy hands off me,you imbecile! Animal! Monster! I said get your...!' A zafafe Hashim ya katseta ta hanyar manna mata pinklips d'insa akan nata...,hakan yasa numfashin bolaji ya tsaya cak! Sai da hashim yayi minti talatin yana kissing d'inta,sannan ya cikata ta fad'i 'kasa wanwar a sume ,ya wuce ya barta anan a kwance! Ya umarci sauran sojojin dasu fito da motoci ,saboda cikin daren nan yake son su koma kadunYa umarci sauran sojojin dasu fito da motoci ,saboda cikin daren nan yake son su koma kaduna! Da hanzari suka had'a komatsansu,suka watsa a motocinsu,sannan suka bar dajin suka d'au hanyar komawa kaduna ! Batare kowannensu ya bi takan Bolaji dake kwance a sume a tsakiyar dajin! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:01 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~17~ Ganin ficewar motocin sojoji daga dajin yasa mutanen yankin ,suka yanke shawarar shiga dajin domin nemo bolaji! Haka suka d'unguma hannunsu ri'ke da torchlight suka shiga dajin! A tsakiyar daji suka tadda bolaji yashe a kwance ,cikin hanzari suka sungumeta suka kaita gida,a d'akinta suka kwantar da ita! Iya folake ce ta yayyafawa bolaji ruwan tulu,ajiyar zuciya bolaji ta sauke ,tare da bud'e idanunta,ganin mutane sun tsaya cirko cirko suna ce mata 'kpele oh',yasa ta yi 'karfin halin tashi zaune tana murmushi,iya folake ce tayi caraf tace 'bolaji,wetin happen,wetin the devil did to you again?, murmushi bolaji tayi ta amsa da 'nothing,i just fainted due to stress',nan dai kowa yayi mata sannu ya fice! Bamidele ya matso yana cewa 'hope you are ok?, 'yes i'm ok' ,bolaji ta amsa masa,sannan yayi mata sannu ya fice bayan ya rufeta da bargo! Ficewarsa ke da wuya ,bolaji ta tashi zaune ta fara goge le6enta da hannunta ,tana mai tsinewa capt.hashim albarka,wanda a zuciyarta ta la'kaba masa suna 'OGA HITLER',domin ya cancanta da a kirashi da wannan suna,saboda rashin imaninsa,a haka ta kwanta idanunta na zubar da hawaye tana mai yiwa iyayenta addu'a a zuci! A haka gwanin sata ya saceta! Washegari taji labarin cewa capt.hashim da tawagarsa sun bar yankin a daren jiya! ¤¤¤ Ranar sadakar bakwai MD yazo gidansu bolaji yayi masu gaisuwa tare da basu albashin babalaji kamar yadda ya biya sauran 'kananun ma'aikata albashinsu! Sannan kuma ya jajanta musu ga abinda hashim ya aikata a garesu ,inda kuma ya fahimtar dasu cewa babu sa hannun mai martaba sam, da abinda hashim ya aikata a garesu,ya kuma sanar da bolaji wanene mai martaba? Wanene hashim! Anan take taji ta kamu da 'kaunar mai martaba da halayensa,yayin da 'kiyayyar hashim da halayensa suka 'kara ninkuwa a zuciyarta ¤¤¤ A yau sultan zai wuce enugu bautar 'kasa,fulani ce ta zaunar dashi a d'akinta tana mai yi masa magana kamar haka 'sultan ina son ka bud'e kunnuwanka kaji abinda zan fad'a maka da kyau,nasan cewa zuwanka malaysia karatu ne yasa ka zama gawurtaccen manemin mata',sultan a razane ya bud'e baki zaiyi magana ,fulani ta dakatar dashi ta hanyar cewa 'ka bari in dire tukun,kana mamakin yadda akayi nasani ko,ba abin mamaki bane idan nace maka inada mutanen dana wakilta su d'inga bibiyarka,domin naga kai kanada rawar kai ,ba kamar yayanka ba ,namiji managarci,wanda mace bata dameshi ba ko kad'an ,kuma gashi bashi da matsala,na yarda dashi d'ari bisa d'ari ' fulani ta cigaba da cewa 'duk ba wannan ba,yanzu abinda nakeso da kai shine ,kar ka kuskura ka nemi matan enugu,inyamurai masu 'karnin janaba,kai in ta'kaice maka kawai bana son ko da wasa ka kuskura ka nemi macen da ta kasance ba YAREN hausa/fulani ba,domin sa6awa hakan na nufin tabbatar tsinuwata akanka,tashi ka tafi ,ALLAH ya tsare ,ya kuma kareka daga musibar inyamurai masu mugun hali',jiki a sanyaye sultan ya mi'ke ya fice yana mamakin kiyayyar da mahaifiyarsa tayi wa YARE! A haka ya fito,royal chaffeur ya wuce dashi airport,ya hau jirgi ya wuce enugu, Bayan yayi sallama da ummu da mai martaba! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:02 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~18~ Kwanaki,satuttuka da watanni sun shud'e! Cikin ikon Allah Sultan ya fara gudanar da bautar 'kasarsa a jihar enugu,kuma da alamu kashedin da fulani tayi masa yayi tasiri a kansa! Bolaji da bamidele suna tafiyar da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali,da kuma taimakon Allah ,maraicinsu baisa sun ha'kura da cigaba da gudanar da rayuwarsu ba! kasancewar 'kudin albashin mahaifinsu da MD ya basu da d'an kauri,da kudin bolaji ta fara 'kananun sana'o'i a cikin gida,tana gasa doya,agada[plantain] da masara,kuma alhamdulillah tana ciniki Allah ya sawa sana'ar tata albarka ,yayin da bamidele ya cigaba da sana'arshi na siyar da bunburutu,basu nemi wani abu ba sun rasa! Yan yankin erin,sun yanke shawara sun had'a kai sun bawa bolaji da bamidele kyautar wani wawakaken gona bisa dalilin ganin cewa kamar ta sanadiyarsu ne mahaifansu suka rasa rayuwankansu! Sunyi farin ciki da wannan halaccin da yan yankin suka musu,kuma sunyi godiya! ¤¤¤ Hashim kuwa ko da suka isa kaduna, bai 'waiwayi ,masauratar modibbo,tsakaninsa da su waya,a kullum suka tambayeshi rashin zuwansa ,sai yace masu aiki ne yayi masa yawa! Hashim gaba d'aya ya susuce,ya zama tamkar mara lafiya,zuciyarsa kullum a kuntacce take,bai 'kara sanin wani abu wai shi farinciki ba tundaga ranar da ya mari maami,tunanin bolaji yayi masa katutu a zuciya,fuskarta kawai yake tunowa ,zuciyarsa tayi sanyi,a kullum yana 'karyata zuciyarsa ga abinda take bijiro masa akan bolaji! yayi takaici,yayi bakinciki ga kamuwar zuciyarsa da wannan cuta,ya kai kukansa ga Allah akan ya yaye masa wannan mugun ciwon,duk sujjadar da zaiyi a sallah,sai ya kai kukansa ga Allah ,amma duk a banza! Domin a yanzu ya gama amincewa Allah ne ya jarabceshi da wannan cuta a zuciya ,wanda maganin wannan ciwo ita ce BOLAJI! ¤¤¤ A yau hashim ya yanke shawarar zuwa garin sokoto! Cikin ikon Allah ya iso masarautar modibbo! Bayan ya gama gaisawa da mahaifansa,anyi hirar yaushe rabo,sannan fulani ta ja shi d'akinta ta sanar dashi cewa tayi masa mata ,d'iyar yayarta da suke uwa d'aya uba d'aya ,hashim ya tambaya ' umma wacece ita?' ,fulani ta amsa masa da 'NAWWARA ce,d'iyar anty mannira,last two weeks ta dawo daga U.s.a ,ta kamalla degree d'inta,my souldear na gaji da ganinka haka ba tare da kayi aure ba! Hashim ya numfasa yace'umma ina mai neman alfarmar da ki bani lokaci ,in yi tunani akai',fulani da fara'arta tace masa 'no problem my soul dear,take your time,kawai dai ina son kasan da zancen auranka da nawwara ne' ! Cikin dare hashim ya je ya samu mai martaba a falonsa shi kad'ai yana shirin zuwa d'akin ummu,bayan sun d'anyi barkwanci,sai hashim yayi gyaran murya ya fara cewa ' abba na zo ne akan yarinyar da nake son aure,ina neman alfarmar aje yankin erin ,a nema mini auranta! Mai martaba yayi mamakin jin kalaman hashim sosai sai ya dubi hashim d'in tare da jifansa da tambayar cewa 'ta yaya kuka had'u da ita?',hashim yan sosa 'keya yace 'mun had'u ne a lokacin da mukaje yankin kwantar da wata tarzoma,kuma munyi amanna da junanmu,itace ma tace in turo',mai martaba yace 'toh shikenan ,zamu je mu nemo maka auranta,ALLAH ya sanya alkhairi' ,'ameen,kuma ina neman alfarmar dan Allah kar ka sanar da ummata,saboda....' ,mai martaba ya katseshi ta hanyar cewa 'kar ka damu,in dai fulani ce,nasan ta yadda zan 6ullo mata,kar kaji komai' hashim yayi godiya suka yi sallama! ¤¤¤ A yau mai martaba ya had'a manyan mutanen da zasu masa rakiya zuwa garin osun,yankin erin,domin nemawa CAP.T YARIMA HASHIM auran BOLAJI! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~18~ Kwanaki,satuttuka da watanni sun shud'e! Cikin ikon Allah Sultan ya fara gudanar da bautar 'kasarsa a jihar enugu,kuma da alamu kashedin da fulani tayi masa yayi tasiri a kansa! Bolaji da bamidele suna tafiyar da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali,da kuma taimakon Allah ,maraicinsu baisa sun ha'kura da cigaba da gudanar da rayuwarsu ba! kasancewar 'kudin albashin mahaifinsu da MD ya basu da d'an kauri,da kudin bolaji ta fara 'kananun sana'o'i a cikin gida,tana gasa doya,agada[plantain] da masara,kuma alhamdulillah tana ciniki Allah ya sawa sana'ar tata albarka ,yayin da bamidele ya cigaba da sana'arshi na siyar da bunburutu,basu nemi wani abu ba sun rasa! Yan yankin erin,sun yanke shawara sun had'a kai sun bawa bolaji da bamidele kyautar wani wawakaken gona bisa dalilin ganin cewa kamar ta sanadiyarsu ne mahaifansu suka rasa rayuwankansu! Sunyi farin ciki da wannan halaccin da yan yankin suka musu,kuma sunyi godiya! ¤¤¤ Hashim kuwa ko da suka isa kaduna, bai 'waiwayi ,masauratar modibbo,tsakaninsa da su waya,a kullum suka tambayeshi rashin zuwansa ,sai yace masu aiki ne yayi masa yawa! Hashim gaba d'aya ya susuce,ya zama tamkar mara lafiya,zuciyarsa kullum a kuntacce take,bai 'kara sanin wani abu wai shi farinciki ba tundaga ranar da ya mari maami,tunanin bolaji yayi masa katutu a zuciya,fuskarta kawai yake tunowa ,zuciyarsa tayi sanyi,a kullum yana 'karyata zuciyarsa ga abinda take bijiro masa akan bolaji! yayi takaici,yayi bakinciki ga kamuwar zuciyarsa da wannan cuta,ya kai kukansa ga Allah akan ya yaye masa wannan mugun ciwon,duk sujjadar da zaiyi a sallah,sai ya kai kukansa ga Allah ,amma duk a banza! Domin a yanzu ya gama amincewa Allah ne ya jarabceshi da wannan cuta a zuciya ,wanda maganin wannan ciwo ita ce BOLAJI! ¤¤¤ A yau hashim ya yanke shawarar zuwa garin sokoto! Cikin ikon Allah ya iso masarautar modibbo! Bayan ya gama gaisawa da mahaifansa,anyi hirar yaushe rabo,sannan fulani ta ja shi d'akinta ta sanar dashi cewa tayi masa mata ,d'iyar yayarta da suke uwa d'aya uba d'aya ,hashim ya tambaya ' umma wacece ita?' ,fulani ta amsa masa da 'NAWWARA ce,d'iyar anty mannira,last two weeks ta dawo daga U.s.a ,ta kamalla degree d'inta,my souldear na gaji da ganinka haka ba tare da kayi aure ba! Hashim ya numfasa yace'umma ina mai neman alfarmar da ki bani lokaci ,in yi tunani akai',fulani da fara'arta tace masa 'no problem my soul dear,take your time,kawai dai ina son kasan da zancen auranka da nawwara ne' ! Cikin dare hashim ya je ya samu mai martaba a falonsa shi kad'ai yana shirin zuwa d'akin ummu,bayan sun d'anyi barkwanci,sai hashim yayi gyaran murya ya fara cewa ' abba na zo ne akan yarinyar da nake son aure,ina neman alfarmar aje yankin erin ,a nema mini auranta! Mai martaba yayi mamakin jin kalaman hashim sosai sai ya dubi hashim d'in tare da jifansa da tambayar cewa 'ta yaya kuka had'u da ita?',hashim yan sosa 'keya yace 'mun had'u ne a lokacin da mukaje yankin kwantar da wata tarzoma,kuma munyi amanna da junanmu,itace ma tace in turo',mai martaba yace 'toh shikenan ,zamu je mu nemo maka auranta,ALLAH ya sanya alkhairi' ,'ameen,kuma ina neman alfarmar dan Allah kar ka sanar da ummata,saboda....' ,mai martaba ya katseshi ta hanyar cewa 'kar ka damu,in dai fulani ce,nasan ta yadda zan 6ullo mata,kar kaji komai' hashim yayi godiya suka yi sallama! ¤¤¤ A yau mai martaba ya had'a manyan mutanen da zasu masa rakiya zuwa garin osun,yankin erin,domin nemawa CAP.T YARIMA HASHIM auran BOLAJI! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:09 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~19~ Cikin ikon Allah mai martaba da tawagarsa suka isa yankin Erin, bayan sun biya ta masauratar osun sun gaisa da oba! Kamfani suka fara nufa,anan mai martaba ya labartawa MD dalilin zuwan su ,MD yayi jim tare da jinjina lamarin ,sannan ya shaidawa su mai martaba cewan yasan gidansu yarinyar suje ya kaisu ! Bolaji tana zaune a tsakar gida tana gasa doya ,sai ganin bamidele tayi ya shigo gidan da hanzari,ya kuma sungumi kujerun katako[bamboo chairs ] ya fice dasu ,sannan ya dawo ya umarci bolaji da ta zubo roasted plantain a kwano mai kyau ta kawowa ba'ki a zaure,bolaji ta amsa da 'okay!' ,sannan ta shiga kicin ta d'auko plate mai kyau ,ta jera gashashiyar agada[plaintain] akai,sannan ta d'auko hijab ta sa,ta d'auki plate ta nufe zaure,ganin MD da wasu manyan manyan mutane sun sha alkyabba da nad'in rawani ,yasa ta sunkuyar da kanta,ta russuna ta gaishesu da turanci,suka amsa mata,ta ajje plate d'in a kan stool tare da tura stool d'in tsakiyarsu,sannan ta mi'ke ta koma cikin gida tana mamakin zuwan mutanen nan gidansu! MD ne yayi gyaran murya ya fara gabatar dasu mai martaba ga bamidele,bamidele ya 'kara gaishesu da turanci,MD ya kuma yiwa bamidele bayanin zuwan su mai martaba! Bamidele yayi jim ,sannan ya numfasa,yace musu shi bai san cewa akwai ala'kar so tsakinin bolaji da hashim ba,amma bara yaje ya kira ita bolajin aji ta bakinta! Bamidele ya tashi ya shiga cikin gida domin kiran bolaji! Bamidele ya dubi bolaji ya ta6e baki yace 'bolaji ,the people wey come ,na oga soldier people oh,they are here to ask for your hands in my marriage' ,bolaji ta karkace baki tana hura hanci tace 'you mean sey na oga hitler, the killer, people be that?' ,bamidele ya amsa mata 'yes oh,the guy go tell them say,na you tell am make they come ask for your hands in marriage...',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'wait oh,you mean say na his papa wan marry...' ,bamidele ya chafke da cewa 'no oh,na oga soldier send em ,make dem come ask for your hands in marriage for him!'',bolaji ta mi'ke a fusace tana cewa 'GOD FORBID bad thing,me bolaji,marry that imbecile,that idiot ,abeg bros wetin you come answer them with?' ,bamidele yace 'i tell them sey,make them wait hear your answer oh,coz me i no know sey you and oga soldier talk this matter',bolaji daman da hijabi ajikinta,ta dubi bamidele tace'oya lets go,make i answer them!' ¤¤¤ Bolaji kanta a sunkuye ta fara labartawa su mai martaba abinda ya faru ,tundaga zuwan hashim yankin izuwa ranar da ya barta a sume a daji ,bata 6oye masu komai ba,kuma ta d'ora da cewa 'MD was a witness'! Mai martaba idan ransa yayi dubu ya gama 6aci,ya dubi MD yace 'abinda yarinyar nan ta fad'a,gaskiya ne' ,MD ya amsa da cewa 'gaskiyane ranka ya dad'e,kuma yarima hashim ya ja mana kunne akan kar mu kuskura kaji labari',mai martaba ya numfasa tare da cewa 'tir'kashi,amma hashim ya mai damu 'kananun mutane wallahi,yasan da cewa ya tafka irin wannan aika aikar ,shine ya turo mu,muzo mu nema masa aure,zan yi maganinsa,da shi da uwartasa dake zugashi'',mai martaba ya dubi bolaji da bamidele ya jajanta masu ,ya kuma basu hakuri akan abinda hashim ya aikata agaresu! Mai martaba bai bar yankin erin ba,sai da ya tabbatar ya dam'kawa su bolaji Diyar maami,sannan kuma aka kira chairman d'in yankin ,ya d'amka masa kwangilar gyara da kuma d'aukar isassun ma'aikata a 'ERIN MATERNITY',wanda shine zai d'au nauyi! ¤¤¤ Sai wuraren dare su maimartaba suka iso masauratar modibbo! Hashim kuwa daman tunda suka tafi yake ta addu'a tare da jan carbi,yana mai jiran tsammani! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~19~ Cikin ikon Allah mai martaba da tawagarsa suka isa yankin Erin, bayan sun biya ta masauratar osun sun gaisa da oba! Kamfani suka fara nufa,anan mai martaba ya labartawa MD dalilin zuwan su ,MD yayi jim tare da jinjina lamarin ,sannan ya shaidawa su mai martaba cewan yasan gidansu yarinyar suje ya kaisu ! Bolaji tana zaune a tsakar gida tana gasa doya ,sai ganin bamidele tayi ya shigo gidan da hanzari,ya kuma sungumi kujerun katako[bamboo chairs ] ya fice dasu ,sannan ya dawo ya umarci bolaji da ta zubo roasted plantain a kwano mai kyau ta kawowa ba'ki a zaure,bolaji ta amsa da 'okay!' ,sannan ta shiga kicin ta d'auko plate mai kyau ,ta jera gashashiyar agada[plaintain] akai,sannan ta d'auko hijab ta sa,ta d'auki plate ta nufe zaure,ganin MD da wasu manyan manyan mutane sun sha alkyabba da nad'in rawani ,yasa ta sunkuyar da kanta,ta russuna ta gaishesu da turanci,suka amsa mata,ta ajje plate d'in a kan stool tare da tura stool d'in tsakiyarsu,sannan ta mi'ke ta koma cikin gida tana mamakin zuwan mutanen nan gidansu! MD ne yayi gyaran murya ya fara gabatar dasu mai martaba ga bamidele,bamidele ya 'kara gaishesu da turanci,MD ya kuma yiwa bamidele bayanin zuwan su mai martaba! Bamidele yayi jim ,sannan ya numfasa,yace musu shi bai san cewa akwai ala'kar so tsakinin bolaji da hashim ba,amma bara yaje ya kira ita bolajin aji ta bakinta! Bamidele ya tashi ya shiga cikin gida domin kiran bolaji! Bamidele ya dubi bolaji ya ta6e baki yace 'bolaji ,the people wey come ,na oga soldier people oh,they are here to ask for your hands in my marriage' ,bolaji ta karkace baki tana hura hanci tace 'you mean sey na oga hitler, the killer, people be that?' ,bamidele ya amsa mata 'yes oh,the guy go tell them say,na you tell am make they come ask for your hands in marriage...',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'wait oh,you mean say na his papa wan marry...' ,bamidele ya chafke da cewa 'no oh,na oga soldier send em ,make dem come ask for your hands in marriage for him!'',bolaji ta mi'ke a fusace tana cewa 'GOD FORBID bad thing,me bolaji,marry that imbecile,that idiot ,abeg bros wetin you come answer them with?' ,bamidele yace 'i tell them sey,make them wait hear your answer oh,coz me i no know sey you and oga soldier talk this matter',bolaji daman da hijabi ajikinta,ta dubi bamidele tace'oya lets go,make i answer them!' ¤¤¤ Bolaji kanta a sunkuye ta fara labartawa su mai martaba abinda ya faru ,tundaga zuwan hashim yankin izuwa ranar da ya barta a sume a daji ,bata 6oye masu komai ba,kuma ta d'ora da cewa 'MD was a witness'! Mai martaba idan ransa yayi dubu ya gama 6aci,ya dubi MD yace 'abinda yarinyar nan ta fad'a,gaskiya ne' ,MD ya amsa da cewa 'gaskiyane ranka ya dad'e,kuma yarima hashim ya ja mana kunne akan kar mu kuskura kaji labari',mai martaba ya numfasa tare da cewa 'tir'kashi,amma hashim ya mai damu 'kananun mutane wallahi,yasan da cewa ya tafka irin wannan aika aikar ,shine ya turo mu,muzo mu nema masa aure,zan yi maganinsa,da shi da uwartasa dake zugashi'',mai martaba ya dubi bolaji da bamidele ya jajanta masu ,ya kuma basu hakuri akan abinda hashim ya aikata agaresu! Mai martaba bai bar yankin erin ba,sai da ya tabbatar ya dam'kawa su bolaji Diyar maami,sannan kuma aka kira chairman d'in yankin ,ya d'amka masa kwangilar gyara da kuma d'aukar isassun ma'aikata a 'ERIN MATERNITY',wanda shine zai d'au nauyi! ¤¤¤ Sai wuraren dare su maimartaba suka iso masauratar modibbo! Hashim kuwa daman tunda suka tafi yake ta addu'a tare da jan carbi,yana mai jiran tsammani! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:10 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~20~ Ko dasu Maimartaba suka dawo ,bai nemi hashim ba,abinci kawai yaci,ya kuma gaisa da matansa ya wuce d'aki! Sai da aka shafe kwana uku ,hashim bai ji maimartaba yayi masa zancen ba,kuma kusan kullum suna tare,hakan yasa zuciyarsa ta shiga zullumi! A yau bayan sallar la'asar maimartaba da hashim suna dawowa daga masallacin dake cikin fada! mai martaba ya umarci hashim da su je lambu akwai tattaunawar da yake so suyi! Bayan sun zauna akan kujerun da aka 'kawata lambun da su ,sai mai martaba yayi gyaran murya yace 'hashim ,ka dubi girman Allah da manzonsa[S.A.W] ka sanar dani gaskiyar yadda akayi kuka had'u da yarinyar nan',Hashim hankalinsa duk ya gama tashi,yasan za'a rina,allura ta tono garma,ba tare da 6ata lokaci ba hashim ya labartawa mai martaba duk yadda akayi,tun daga ranar da fulani tayi masa waya,izuwa yanzu da zuciyarsa ta kamu da ciwon bolaji ,mai martaba yayi jim sannan ya dubi hashim ,murya tausashe ya fara cewa 'ka bani kunya hashim,kuma ka bani mamaki,kana d'an musulmi ka aikata irin wannan rashin tausayin,yaushe ka dawo haka,yaushe ka zamo namiji mara tausayi,wannan ba halinka bane sam,idan ita umman taka bata da hankali sai ka biye mata,ni wanene da baza'a jefeni ba,kuma naga tsautsayi baya wuce ranarsa' ,mai martaba ya cigaba da cewa 'toh ga irinta nan,tun ba'a je ko ina ba ,ka fara ganin illar biyewa zugar mace ,yanzu wa gari ya wayewa?,ita ta zugeka kaje ka aikata mugun aiki,tana can kwance cikin farinciki,babu abinda ya dameta,kai kuma ta barka da 'kunci a zuciya,kana fama da jinyar zuci,hashim a gaskiya ka tafka wauta,wanda bana fatan hakan ya kuma faruwa,aikin soja ba hauka bane'',hashim jiki a sanyaye yace 'abba wallahi nayi nadama sosai,nayi danasanin biyewa umma wajen aikata wannan aiki mafi muni a rayuwata,kuma tundaga ranar da hakan ta faru abba ban kuma sanin wani abu wai shi farin ciki ba,da zarar na kwanta ,sai wannan matar da na mara ta bayyana a cikin mafarki, yanzu burina kawai a duniya shine in mallaki bolaji a matsayin matar aurena,domin yin hakan kad'ai zai zamo silar dawowar farincikina ',mai martaba yayi murmushi yace 'd'ad'in gobe saurin zuwa,sakayyar Allah kenan,ba ta yadda ba ya iya zuwa ,hashim kai a ganinka yarinyar nan zata amince ta aureka,kar ka manta kaine silar mutuwar mahaifiyarta wanda hakan kuma ya zamo silar mutuwar mahaifinta,wallahi hashim ko nine yarinyar nan bazan aureka ba,amma ba'a ja da kaddara da kuma hukuncin Allah,kaje ka nemi soyayyarta, idan Allah ya kaddara matarka ce sai kaga hakan ya faru,in kuma akasin haka ne,sai kasa dangana',hashim kansa ya d'au zafi,domin bai san ta inda zai fara fuskantar bolaji da batu na soyayya ba,abun da kamar wuya! mai martaba ya katse masa tunaninsa ta hanyar cewa'kaga illar biyewa son zuciya da kuma zugar mace ko?,yanzu ka je ka nemi soyayya a gun yarinyar ,ALLAH na tare da kai,zan tayaka da addu'a ,idan ta amince zata aureka,zan shige maka gaba,ita kuma uwartaka ka kyaleta da halinta,da sannu zata gane kurenta,kuma na tabbata idan aurenka da yarinyar nan ya tabbata,toh hakan kad'ai ya isheta ishara,kuma ka cigaba da yi mata biyayya!' maimartaba ya cigaba da bashi baki yana masa nasiha ,ya kuma tunatar dashi akan azumi guda sittin da suka hau kanshi,da kuma biyan diya,wanda mai martaba ya sanar dashi cewa ya riga ya biya diyan da share[kaso] d'in kud'insa [hashim] dake RED OIL COMPANY ERIN! ¤¤¤ Washegari Misalin 'karfe 4:00pm ,hashim yayi parking ba'kar hilux jeep d'insa a gaban gate d'in kamfani,sanye yake da ba'kar polo shirt da denim jeans,he looks so casual but hot,wayarsa ya ciro ya bugawa MD cewan ya fito yana jiransa a gaban kamfani! MD ya fito ,yaga hashim zaune a cikin mota ,ya 'karasa sukayi musabaha yana tambayar hashim 'saukar yaushe?' ,hashim ya amsa masa da 'isowata kenan!',sannan ya cigaba da cewa 'nazo ka rakani ,in je in nemo soyayya a gun da bai dace ba' ,MD cike da mamaki ya jefeshi da tambayar 'me kake nufi ?' ,hashim yayi jim yace 'a karan kaina,in da ni nake da iko da zuciyata,bazan ta6a yarda zuciyata ta kamu da soyayyar yarinyarnan ba,domin she's just not my type,amma da yake jarabta ce Allah ya jarabci zuciyata da ciwon sonta,wanda nayi addu'a akan Allah ya yayemin,amma ko kad'an sonta bai ragu ba a zuciyata,sai ma 'karuwa da yake a kullum,MD azal ta hauni wallahi,nayi danasanin aikata abinda na aikata ga mahaifiyar yarinyar nan wallahi,ga shi yanzu ina fama',MD yayi jim tare da cewa 'ikon Allah kenan!',hashim yace 'shigo,muje ka rakani gidansu ' ,MD ya shiga motar ya zauna,hashim ya tayar da motar yana cewa 'ALLAH ya bani ikon cinye wannan jarabawar' ,MD ya a msa masa da 'amin! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:11 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~21~ Bolaji tana zauna ta zuba tagumi,tana kallon buhun irin masara da bamidele ya siyo jiya ,domin damina tana gab da saukowa,gonar da aka basu kyauta suke son su fara yin shuka! A yanzu bolaji ba komai take tunani ba ,illa ta yadda zasuyi su samo yan tayin aikin da zasu tayasu fara nome wannan gonar su kuma yi shuka ! Tunaninta ya katsene a lokacin da wani yaro yayi sallama tare da cewa 'ekaso aunty!' ,bolaji ta dubeshi fuskarta d'auke da murmushi ta amsa masa da 'ade! Eshe o',yaro daya amsa suna ade yace 'anty bola,some two men are calling you', 'two men calling me?' ,bolaji ta tambaya ,ade ya amsa da 'yes ,they are outside waiting',bolaji ta kunce mayafin da ta d'aura akai ta yafa akanta,daman sanye take ta da jar tshirt da ba'kin skirt,ta dubi ade tace 'oya lets go' MD idanunta suka mata tozali da ,fuskarta d'auke da murmushi ta gaisheshi ,ya amsa yana mai mata bayanin abinda ya kawo su,sai alokacin ta d'aga ido ta hango hashim hakimce a zaune a cikin mota,harara ta zabga masa ,sannan ta tsirtar da miyau ,ta dawo da dubanta ga MD ta katseshi ta hanyar cewa 'oga MD ,save your breath abeg,if the idiot himself no fit carry his leg come here and talk to me,then you people should just forget' ,ta juya da niyyar komawa gida ,MD ya dakatar da ita tare da bata hakurin ta tsaya! Bayan ta tsaya MD yaje gun hashim yace masa 'toh yalla6ai ,kamata yayi kaje da kanka fa,domin gimbiyar tace kazo da kanka' ,hashim ya yatsine fuska ,sannan yace 'alright!' ,MD yayi masa fatan alkhairi,sannan ya juya ya barsu anan,zai taka[trekking] ya koma kamfani! Hashim fuska a murtuke,hannayensa a cikin aljihu,yana takun 'kasaita ya 'karaso ga bolaji,wacce ta 'kura masa idanu ,tana mai tsine masa a zuciyarta! Yana isowa ,ya dubeta fuskarsa ba annuri,murya a ciki ciki yace 'i'm sorry' ,bolaji ta matso kunnenta tare da karkace hanci tace 'what do you just say' ,'i'm sorry!' ,hashim ya maimata a da'kile ,bolaji ta 'kara cewa 'abeg open mouth and talk,i no dey hear you' ,da 'karfi hashim ya maimaita kalmar 'i'm sorry ',bolaji ta kwashe da dariya har da 'kwalla,sannan tace 'you are sorry for what' ,hashim wanda zuciya ta fara ciwo shi ,amma ya danne yace 'i'm sorry for all i have done to you,i've realised my mistakes,i'm sorry ,please forgive me!',bolaji ta dubeshi ta 'kara kwashewa da dariya sannan tace 'oga hitler so soon,ok oh ,i don forgive oh ,but to forget no be small thing oh',sannan ta juya zata koma cikin gida! Hashim ya dakatar da ita ta hanyar cewa 'please wait!' ,bolaji ta juyo tana cewa 'ohh na wetin again?' ,hashim a da'kile yace 'i want you to marry me',bolaji ta dubeshi tayi masa kallon tsaf sannan tayi 'kwafa tace 'your people wey you send come, no reply you my message?',sannan tace 'wait oh ,why you marry me sef,i resemble person wey dey look for husband' ,hashim a 'kule ya amsa mata da cewa 'because my heart has unknowingly fell in love with you '! Bolaji ta kwashe da wata mahaukaciyar dariya sauran 'kiris ta kifa ,sannan cikin muryar dariya tace 'love,ahh,chai,man don suffer, this is abomination,me bolaji,you love me? ,make i marry you,i reject in the name of the mighty olohu' ,sannan ta cigaba da cewa 'wetin you take sef ,abi you take ogogoro[giya] before coming here!',tayi 'kwafa tare da tafa hannayenta, ta cigaba da cewa 'abeg oga hitler,carry your wahala commot for here ,if no be say na kill you come to kill me with your words wey resemble rotten pig meat'' Bolaji ta cigaba da surfa masa bala'i kala kala ,iri iri,ganin cewa baza tayi shiru ba,yasa hashim ya karya billenshi ya dur'kasa,fuskarsa a murtu'ke ,murya a tausashe yana mai cewa 'bolaji,i'm on my knees,please,help a weeping soul,a craving heart ,and accept me as your husband,i'm beggin you',bolaji ta dubeshi she'keke ,ta tsirtar da miyau,taja dogon tsaki ta shige gida ta bar CAPT.YARIMA HASHIM ATTAHIRU MODIBBO! a d'ur'kushe a kofar gidansu! Written by :ABDULAZIZ ILILEE [10/16, 11:12 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~22~ Hashim ya mi'ke tsaye tare da kakka6e wandonsa,yana mai mamakin kansa,wai yau shine har da dur'kusuwa mace ,macen ma bayarabiya,shi da mata basa gabansa ko kad'an,ikon Allah kenan,babu ta yadda Allah baya jarabtar bawansa! ¤¤¤ Bamidele ya dawo daga gun sana'arsa,a kofar gida ya tadda hashim kwance a cikin mota,ga dukkan alamu yayi nisa a duniyar tunani,domin yanayinsa kad'ai ya nuna haka! bamidele bai tanka shi ba,ya wuce cikin gida,ya tadda bolaji sai cika take tana batsewa,hakan yasa yaja bakinsa ya tsuke,bai yi gigin tambayarta ba,domin yasan halin 'kanwar tasa! Washegari da asuba bamidele ya fito zai tafi masallaci,turus yayi a lokacin da idanunsa suka masa tozali da hashim dake sallah akan darduma kusa da motarsa! Cike da mamaki bamidele ya wuce masallaci! Misalin karfe 8:00am na safe ,bamidele da bolaji suna karyawa,bamidele yayi gyaran murya,ya dubi bolaji tare da cewa 'oga soldier still dey outside oh',bolaji a fusace tace 'doing what?' ,'who knows,but it looks like he spent the night outside' bamidele ya amsa mata ,tare da tambayarta 'what happen,did you guys met yesterday',bolaji ta labarta masa yadda sukayi da hashim jiya,bamidele ya jinjina lamarin,jiki na rawa yace 'the guy truly loves you oh,better marry him oh,before he looses his temper and send us to our graves oh',bolaji ta dubi bamidele she'ke'ke sannan tayi 'kwafa tace'i no blame you sha',bamidele yace'no blame me oh,cause i dey fear that their gun oh!' A fusace bolaji ta dire kofin kokon dawan da take sha,ta suri hijab ta saka,sannan tayi hanyar ficewa daga gidan tana cewa 'make i go deal with that wizard!' Fitowar bolaji ne yasa hashim ya fito daga mota,ya nufi wajenta! Hannu akan 'kugu ta dubeshi ta ja dogon tsa'ki,sannan tace masa 'follow me!' Bolaji tana gaba Hashim na biye da ita ,har suka iso wawakeken gonar da mutanen yankin suka basu kyauta! Bolaji ta dubi hashim,sannan tayi dariyar mugunta ,tace ' i will accept you as a husband,if only you can clear all the grasses in this farm,make ridges,sow some seeds and harvest alot of maize!' Hashim ba tare da yayi magana ba ya juya ya koma ya d'au motarsa ya tafi! Bolaji kuwa me zatayi in ba dariya ba ,tana tafa hannayenta ta shige gida ,bamidele yana tambayarta meye faru,tana dariya ta labarta masa yadda sukayi da hashim, ta d'ora da cewa 'the mumu don go sef,idiot he think sey i be mumu like him',bamidele ya dubeta yace 'omo you bad oh!' ¤¤¤ Yau kimanin kwana uku kenan da tafiyar hashim,bolaji tana zaune a tsakar gida tana gasa agada [plaintain] tana rere wa'kar 'oruka',funmilayo ta fad'o gidan a sukwane ,bolaji ta dubeta tace 'ahh funmi,na wetin again',funmilayo ta kama ha6a tace 'wonders shall never end,abeg come and see wetin dey happen',bolaji tace 'wetin come dey happen?',funmilayo ta amsa mata da 'stand up and follow me,make we go,so that you can see for your self',bolaji ta sauke plantain d'in,sannan ta d'auko 'karamin hijab ta saka,sannan ta dubi funmilayo tace 'lets go',suna fita,bolaji ta datse gidan da kwad'o! Hannun funmilayo ri'ke da hannun bolaji suka iso gona! Turus! Bolaji tayi a lokacin da idanunta suka hango mata hashim sanye da ba'kar singlet da 3quarter na khaki,sai zufa yake yana aikin had'a kunya kunya [ridges] da fatanya! Bolaji ta d'aura hannu akan 'kirji tana cewa 'chai,which kind wahala be this?' Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:14 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~23~ Funmilayo ta dubi bolaji a mamakance tare da cewa 'wahala?,what sort of wahala?',bolaji ta sauke hannu daga kan 'kirjinta ,tare da jan numfashi,ta labartawa funmilayo yadda sukayi da hashim kwana uku da suka shud'e! Funmilayo ta kwashe da dariya tana cewa 'this is serious,a soldier and a son to the owner of the red oil company now a farmer?,that means the guy loves you so much',bolaji a fusace tace'but i don't love him',funmilayo ta watsar da hannayenta tana cewa'na you sabi,love him or not,you must fulfill the promise you make to him!' Hashim ne ya katse masu hirarsu,yana mai goge zufan da ya tsastsafo masa akan goshi da bayan hannunsa,ya dubi bolaji yace 'my better half ,in less than few hours i'll be done with making the ridges,so i want you to tell me what sort of seeds should i be planting',harara bolaji ta watsa masa ,ji take kamar ta sha'koshi! A da'kile tace masa 'alright ,go back to work,come and collect the seeds tommorow,in the morning',hashim ya murmusa tare da juyawa ya koma gonar ya cigaba da aikinsa! Funmilayo ta dubi bolaji bakinta a bud'e tace 'oboi,see muscle oh,the guy is so damn hot' ,bolaji fuskarta a murtuke tace 'ehen',funmilayo tacigaba da cewa' 'he's handsome,he smells nice,his pink lips looks soft and kissable,he's.....',bolaji ce ta katseta ta hanyar d'aka mata duka a baya tana cewa 'he's heartless,he's wicked',sannan ta cigaba da cewa 'oya lets go abeg,witch',funmilayo tana sosa bayanta,suka wuce gida! Bolaji zuciyarta a 'kuntace suka iso gida,jiki a sanyaye ta bud'e gidan ta shiga ,funmilayo tana mata tsiya ta wuce gida ita ma! ¤¤¤ Da yamma hashim ya gama yin kunya kunya ,shuka kawai ya rage,yana zaune akan wani 'karamin dutse yana mai da numfashi ,domin ya jigata matu'ka,MD ne ya 'karaso cikin gonar,yazo ya zauna kusa da hashim yana mai dafa kafad'arsa yace 'yalla'bai abinda nake ji a yankinan wai kazama manomi gaskiya ne?',hashim ya amsa masa da 'eh gaskiyane',MD yayi jim sannan yace 'ya kuka 'kare da bolaji,ranar dana barku tare',hashim ya labarta masa yadda sukayi sannan ya cigaba da cewa 'kaduna na wuce a ranar data ce zan nome gonar in yi shuka in girbe, na d'auki hutu,daga can na wuce sokoto na labartawa abba yadda mukayi da ita,abba yace shi babu ruwansa,ya rage nawa,daga nan nayi sallama da ummata akan zanje wani gari aiki,a wayata nayi googling yadda ake yin noma,shine na taho da fatanya,taki,insecticide da sauransu ,yau da asuba na iso yankin nan,shine kawai na fara aikin gonar,yanzu saura shuka,idan Allah ya kaimu gobe',MD ya jinjina lamarin yace 'ikon Allah',sannan MD ya cigaba da cewa 'ALLAH kar ka jarabcemu da irin wannan soyayyar',hashim ya amsa da 'amin,nima kaina ni na jawa kaina',MD yace 'toh tashi muje gidana ka kwana',hashim ya amsa da 'toh muje,naga an kusan kiran sallar maghrib,kuma bana son in sha ruwa a gonar nan',hashim ya dubeshi a mamakance yace 'azumi kake?,kuma kake aikin gona',hashim ya tashi tsaye yana cewa 'azumin 60 da ya hau kaina,na fara a yau',sannan ya wuce yashige motarsa,bayan ya jefa fatanya a booth,MD yashiga motar yana mai jinjina jarumtar hashim! Ko da Bamidele ya dawo daga gun sana'a,bolaji ta labarta masa dawowar hashim,dariya yayi yana mai ce mata ita ta jawowa kanta,aure kuma yazama dole ta auri hashim,tunda tayi masa al'kawarin hakan! ¤¤¤ Washegari hashim ya biya ta gidansu bolaji,ya amshi irin masarar da zai shuka, ya wuce gona! ¤¤¤ A kwana a tashi ba wuya a gun Allah,a yayin da damuna ta gama kutsowa ,a lokacin Masara ta fara fitar da 'ya'ya,zuciyar hashim cike da farin ciki,bolaji kuwa hankalinta a tashe,kullum ba'kin ciki na 'kara ruruwa a zuciyarta ,musamman idan funmilayo tazo tana labarta mata yadda hashim yake gudanar da aiki a gona! BAYAN WATA HUDU! Damina tayi albarka,Masara tayi kyau! Hashim ya kamalla azumi 60! Yau tun safe yake girbe masara tare da wasu samari da yan mata na yankin,wanda sabo ya shiga tsakaninsu da shi,musamman funmilayo da tafi kowa za'kal'kalewa! Buhunhuna masara 50 suka dire a kofar gidansu bolaji! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:16 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~24~ Bolaji tana tsalle da murna a tsakar gida bisa dalilin w.a.e.c d'inta da tayi kyau,domin ta cinye! Shigowar Funmilayo cikin gidan jikinta na rawa yasa bolaji ta katse rawar da takeyi tana mai duban funmilayo! Funmilayo ta dafa kafad'ar bolaji tana mai cewa 'bolaji,your charming prince is waiting for you outside',bolaji taja dogon tsa'ki tace 'you mean the charming farmer',funmilayo ta watsar da hannunta tana cewa 'whatever' ,sannan ta fisgi hannun bolaji tana cewa 'lets go outside!' Turus! Bolaji tayi a yayin da idanunta suka mata tozali da buhunhunan masara reras a kofar gidansu ,hashim yana tsaye,han nayensa a cikin aljihun 3qtr dinsa,ya watso mata sexy eyes d'insa yana wani irin murmushi! Cike da 'karfin hali ,bolaji ta fara kewaye buhunhunan masarar tana 'kirgawa d'aya bayan d'aya,har sai data 'kirga buhu guda hamsin,sai data kusan yin fitsari domin ta tsorata matu'ka ! Fuska kawai tayi,ta d'aga kanta sama ta 'kwalawa masu aiki ginin gidansu kira da su sauko su shigar da buhunhunan masaran! Bayan sun shige dasu tas ,bolaji ta juya da zummar shigewa gida,cike da zafin nama hashim ya dam'ko hannunta,ya fincikota ta fad'o kan 'kirjinsa,goshinta na bugun goshinsa,yasa hannunsa ya zagayeta! Idanunsa akan idanunta,Murya a tausashe yace 'it's time for you to fulfill the promise you made'','what promise?' ,bolaji ta tambaya tana mai kauda idanunta daga kan idanunsa ,a zafafe hashim ya amsa mata da cewa 'don't even try to pretend as if you don't know what i'm talking about',bolaji ta tsu'ke bakinta tana harararsa! Hashim yasa le6ensa a daidai kunnenta yana cewa 'will you marry? 'NO!' bolaji ta amsa masa ,'will you accept me as your husband?' hashim ya tambayeta ,bolaji ta amsa masa da 'NO'! Hannunsa yasa ya dam'ki hannunta da 'karfi ya murd'a,Yana mai cewa 'will you be my wife', bolaji wanda idanunta suka yi ja ,saboda murd'a hannunta da yayi,azabar data ji ne yasa ta amsa da 'YES ,I will be your wife,i will marry you and accept you as my husband' ,hashim yayi guntun murmushi yace 'thats all i wanted to hear from you',sannan ya cika mata hannu,hakan ya bata damar sa hannu ta ture 'kirjinsa ,ta raba kanta daga rungumar da yayi mata ,tana matsar 'kwalla! Juyawa tayi zata shiga gida ,hashim yace mata 'wait!' ,ta tsaya cak ,sannan ya cigaba da cewa 'me loving you,does not give you the right to toy with my feelings,be ready my better half,cause our wedding fatiha will take place by tommorow insha Allah' Bolaji ta juyo ta watsa masa harara ,taja dogon tsaki ta wuce cikin gida! Su funmilayo suka kwashe da dariya ,hashim ya ciro kud'i ya rarraba masu yana kuma masu godiya bisa tayashi girbi da sukayi! Hashim ya wuce gidan MD ,ya had'a kan kayansa kakaf domin gobe hutunsa da ya d'auka zai 'kare,kuma yana so a goben ya wuce da matarsa! Da yamma hashim da MD suka je gidansu bolaji ,suka aika aka masu sallama da bamidele ,bayan ya fito ,MD ya shaidawa bamidele kud'irinsu akan cewa gobe suke son a d'aura aure,hashim ya wuce da matarsa,tunda ya kamalla noma kamar yadda bolajin ta bu'kata,bamidele jiki na rawa ya amsa masu da bakomai,gobe su turo magabatansu a d'aura auren ya wuce da ita! Ko da bamidele ya shaidawa bolaji yadda sukayi dasu MD ,hankalinta ya tashi matu'ka tana ta cewa haba ya zaiyi mata haka,kar fa ya manta shine fa wanda yayi sanadin mutuwar iyayensu,taya zata aureshi! Bamidele ya nuna mata cewa shi ba ruwanshi,ita takama tasa d'an mutane noma tare da d'aukan al'kawarin aurensa idan yayi noman ,aure kam yazama dole ta auri oga soldier,domin bazai zuba mata ido ta sa6a alkawari ba,kuma oga soldier yana sonta matu'ka,idan ya rasata Allah kad'ai yasan abinda zai aikata a garesu,shikuma ba zai iya da jarabar sojoji ba! Hashim ya buga ya shaidawa mai martaba yadda sukayi da bamidele,mai martaba ya tayashi murna ya kuma ce masa suna nan tafe washegari insha Allah! Maimartaba ya shaidawa fulani cewa gobe zasuje su dawo da hashim! Fulani sai murna take,hakan yasa ta bugawa yayarta waya akan cewa a turo mata nawwara gobe da safe! ¤¤¤ Washegari misalin 'karfe 8 na safe mai martaba da tawagarsa suka wuce lagos daganan zasu wuce can osun yankin erin! 'karfe goma na safe nawwara ta iso fada ,fulani taji dadin isowarta,domin tana son wannan karon idan hashim ya dawo ayi bikinsa da nawwara kowa ya huta! Haka aka cigaba da gyare gyare da dafe dafe a cikin fada ,duk na tarbar cap.t Yarima hashim, bisa jagorancin fulani! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~24~ Bolaji tana tsalle da murna a tsakar gida bisa dalilin w.a.e.c d'inta da tayi kyau,domin ta cinye! Shigowar Funmilayo cikin gidan jikinta na rawa yasa bolaji ta katse rawar da takeyi tana mai duban funmilayo! Funmilayo ta dafa kafad'ar bolaji tana mai cewa 'bolaji,your charming prince is waiting for you outside',bolaji taja dogon tsa'ki tace 'you mean the charming farmer',funmilayo ta watsar da hannunta tana cewa 'whatever' ,sannan ta fisgi hannun bolaji tana cewa 'lets go outside!' Turus! Bolaji tayi a yayin da idanunta suka mata tozali da buhunhunan masara reras a kofar gidansu ,hashim yana tsaye,han nayensa a cikin aljihun 3qtr dinsa,ya watso mata sexy eyes d'insa yana wani irin murmushi! Cike da 'karfin hali ,bolaji ta fara kewaye buhunhunan masarar tana 'kirgawa d'aya bayan d'aya,har sai data 'kirga buhu guda hamsin,sai data kusan yin fitsari domin ta tsorata matu'ka ! Fuska kawai tayi,ta d'aga kanta sama ta 'kwalawa masu aiki ginin gidansu kira da su sauko su shigar da buhunhunan masaran! Bayan sun shige dasu tas ,bolaji ta juya da zummar shigewa gida,cike da zafin nama hashim ya dam'ko hannunta,ya fincikota ta fad'o kan 'kirjinsa,goshinta na bugun goshinsa,yasa hannunsa ya zagayeta! Idanunsa akan idanunta,Murya a tausashe yace 'it's time for you to fulfill the promise you made'','what promise?' ,bolaji ta tambaya tana mai kauda idanunta daga kan idanunsa ,a zafafe hashim ya amsa mata da cewa 'don't even try to pretend as if you don't know what i'm talking about',bolaji ta tsu'ke bakinta tana harararsa! Hashim yasa le6ensa a daidai kunnenta yana cewa 'will you marry? 'NO!' bolaji ta amsa masa ,'will you accept me as your husband?' hashim ya tambayeta ,bolaji ta amsa masa da 'NO'! Hannunsa yasa ya dam'ki hannunta da 'karfi ya murd'a,Yana mai cewa 'will you be my wife', bolaji wanda idanunta suka yi ja ,saboda murd'a hannunta da yayi,azabar data ji ne yasa ta amsa da 'YES ,I will be your wife,i will marry you and accept you as my husband' ,hashim yayi guntun murmushi yace 'thats all i wanted to hear from you',sannan ya cika mata hannu,hakan ya bata damar sa hannu ta ture 'kirjinsa ,ta raba kanta daga rungumar da yayi mata ,tana matsar 'kwalla! Juyawa tayi zata shiga gida ,hashim yace mata 'wait!' ,ta tsaya cak ,sannan ya cigaba da cewa 'me loving you,does not give you the right to toy with my feelings,be ready my better half,cause our wedding fatiha will take place by tommorow insha Allah' Bolaji ta juyo ta watsa masa harara ,taja dogon tsaki ta wuce cikin gida! Su funmilayo suka kwashe da dariya ,hashim ya ciro kud'i ya rarraba masu yana kuma masu godiya bisa tayashi girbi da sukayi! Hashim ya wuce gidan MD ,ya had'a kan kayansa kakaf domin gobe hutunsa da ya d'auka zai 'kare,kuma yana so a goben ya wuce da matarsa! Da yamma hashim da MD suka je gidansu bolaji ,suka aika aka masu sallama da bamidele ,bayan ya fito ,MD ya shaidawa bamidele kud'irinsu akan cewa gobe suke son a d'aura aure,hashim ya wuce da matarsa,tunda ya kamalla noma kamar yadda bolajin ta bu'kata,bamidele jiki na rawa ya amsa masu da bakomai,gobe su turo magabatansu a d'aura auren ya wuce da ita! Ko da bamidele ya shaidawa bolaji yadda sukayi dasu MD ,hankalinta ya tashi matu'ka tana ta cewa haba ya zaiyi mata haka,kar fa ya manta shine fa wanda yayi sanadin mutuwar iyayensu,taya zata aureshi! Bamidele ya nuna mata cewa shi ba ruwanshi,ita takama tasa d'an mutane noma tare da d'aukan al'kawarin aurensa idan yayi noman ,aure kam yazama dole ta auri oga soldier,domin bazai zuba mata ido ta sa6a alkawari ba,kuma oga soldier yana sonta matu'ka,idan ya rasata Allah kad'ai yasan abinda zai aikata a garesu,shikuma ba zai iya da jarabar sojoji ba! Hashim ya buga ya shaidawa mai martaba yadda sukayi da bamidele,mai martaba ya tayashi murna ya kuma ce masa suna nan tafe washegari insha Allah! Maimartaba ya shaidawa fulani cewa gobe zasuje su dawo da hashim! Fulani sai murna take,hakan yasa ta bugawa yayarta waya akan cewa a turo mata nawwara gobe da safe! ¤¤¤ Washegari misalin 'karfe 8 na safe mai martaba da tawagarsa suka wuce lagos daganan zasu wuce can osun yankin erin! 'karfe goma na safe nawwara ta iso fada ,fulani taji dadin isowarta,domin tana son wannan karon idan hashim ya dawo ayi bikinsa da nawwara kowa ya huta! Haka aka cigaba da gyare gyare da dafe dafe a cikin fada ,duk na tarbar cap.t Yarima hashim, bisa jagorancin fulani! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 11:17 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~25~ Misalin 'karfe 8:00 na safe hashim ya gama shiryawa cikin uniform,ya kuma had'a kayansa kakaf yasa a mota ,sannan yayiwa MD godiya ga bashi masauki da yayi a gidansa na tsawon watanni! Sannan suka d'unguma dashi da MD suka wuce gidansu bolaji a motarsa,domin a can 'kofar gidansu bolaji zasu jira isowar mai martaba! Bolaji kuwa ko rintsawa batayi ba,haka zalika bamidele,kwana sukayi yana bata baki ,da kuma hakuri akan aurenta da hashim! Su iya folake dasu iya ayomide da sauran mata sukayi gangami guda suka taho gidansu bolaji da sassafe,da isowar su kuwa suka fara cece kuce akan auran bolaji da hashim,taya zasu zuba ido a aurawa bahaushe bolaji,bahaushen da yayi sanadin mutuwar iyayenta! Bamidele ya koro masu bayani ga alkawarin da bolaji ta d'auka, amma mirsisi suka 'ki yarda! Hakan yayiwa bolaji dad'i sosai domin ko kad'an ba ta son aurenta da hashim ! Misalin 'karfe 12:00 na rana ,mai martaba da tawagarsa,tare da kuma oba [sarkin osun] da tashi tawagar suka iso 'kofar gidansu bolaji! Bamidele yaje ya kwashi gaisuwa a gunsu,ya kuma sanar dasu halin da ake ciki! Oba ya nemi 'karin bayani a gun mai martaba,mai martaba ya labarta masa abinda yasani game da tarihin had'uwar hashim da bolaji! Bayan Oba yaji wannan labari,a take ya nunawa hashim kuskurensa game da abinda ya aikita ga maami,sannan ya umarci bamidele ya turo masa bolaji da su iya folake! Oba ya dubesu yafara da basu ha'kuri ga abinda hashim ya aikata wanda faruwar hakan, mu'kaddari ne,kuma Allah ya riga ya 'kaddara mutuwar babalaji da maami a wannan ranar ko da kuwa hashim bai zo ba,sannan yayi masu nuni da sakayyar Allah akan hashim na jarabtarsa da Allah yayi da soyayyar bolaji! Oba ya cigaba da masu nasiha,har sai da jikinsu yayi sanyi! Mai martaba shima ya 'kara basu ha'kuri,sannan ya umarci hashim da ya nemi yafiyarsu! Hashim ya basu ha'kuri ya kuma nemi yafiyarsu,a take suka ha'kura suka fawallawa Allah lamarin,ita ko bolaji bataso faruwan hakan ba! Mai martaba ya ciro awarwaron zinare guda uku daga aljihun alkyabbarsa ya mi'kawa bolaji a matsayin sadakinta! Bolaji tana ji tana gani aka d'aura aurenta da hashim! Jiki a sanyaye ta shige cikin gida,bamidele ya bi bayanta ,yana shiga gidan,ya tarar da bolaji zaune a tsa'kar gida tana risgar kuka,bamidele ya zauna kusa da ita ,ya kamo hannunta yana bata hakuri,ya kuma yi mata nasiha sosai akan ta zauna lafia da mijinta da danginsa ,kuma yana da tabbacin cewa hashim bazai ta6a wula'kantata ba,tunda yana sonta! Hashim kuwa ya kwashe kayansa daga motarsa ya zuba a booth din motar da maimartaba sukazo da ita,sannan ya dam'kawa MD mu'kullin motar,wato ya bashi kyautar motar! A haka su iya folake da funmilayo suka shirya ta cikin buba da iro ,suka kafa mata d'aurin ashoke ,sannan suka lullu6eta da mayafi,suka fice da ita! A motar maimartaba suka sata,bolaji sai kuka take,shi kanshi bamidele ya tausaya mata ,jaka ya mi'ka mata mai dauke da takardunta da album d'inta! Maimartaba ,oba ,da hashim sukayi sallama da mutanen yankin bayan sun raba masu kud'i ,sannan suka shige mota,suka wuce tare da bolaji masarautar osun suna masu d'agawa yan yankin hannu! A masarautar osun ,kuyangu da hadimai suka gyara bolaji,sarauniya ta bada umarnin a shirya bolaji cikin leshi da ashoke masu kyau da tsad'a,da kuma yari da sar'ka na coral beads masu kyau da she'ki,sannan mai make up itama tayi nata aikin! Bolaji ita dai nata idanu,hannunta ri'ke da jakar da bamidele ya bata d'azu! ¤¤¤¤ Misalin 'karfe 5:00pm jirginsu mai martaba ya sauka a filin airport na sultan bello dake sokoto! Maimartaba ne a gaba wajen saukowa daga jirgi,sai hashim wanda yake rungume da bolaji,sai sauran tawagar sarki ! Royal chaffeurs daman suna jiransu da motoci a bud'e , mai martaba da hashim &bolaji suka shig mota d'aya,tawagar sarki suka shige sauran motocin,dogarawa hannunsu ri'ke da jakar bolaji dakuma jakar kayan hashim suma suka shige tasu motar! Motocin a jere [convoy] suka fice daga airport tare da wucewa yankin yabo,masarautar moddibo ,inda fulani da nawwara suke jiran isowar maimartaba da yarima cap.t hashim! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 12:16 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~26~ Fulani da nawwara sun shirya cikin kaya na alfarma,sai zuba 'kamshi suke,ita kuwa ummu ko a jikinta tunda ba sultan bane zai dawo,tana d'akinta tana karatun al'qur'ani! Bayan fulani ta tabbatar da kamalluwar komai tun kama daga abinci,abinsha,da kuma da'kin kwanansu,hatta ruwan wanka sai da tabbatar da ancika bath tubs da ruwan turare! Misalin 5:00pm motoci suka fara shigowa harabar masarautar modibbo! Da sauri royal guards suka bubbud'e masu 'kofofi suka fito,mai martaba ne ya fara fitowa sai hashim da bolaji,sai kuma sauran yan rakiya, bayan mai martaba ya sallami tawagarsa sun watse,sai ya maido da dubansa ga bolaji fuskarsa d'auke da murmushi yace ' welcome to our palace my daughter',kanta a sunkuye ta amsa da 'thank you sir',mai martaba ya dubi hashim yace 'kai kuma ko da munshiga ciki,kar ka kuskura ka shaidawa ummanka batun aurenka ,ko da kuwa ta tambayeka wacece ita,kar ka ce mata komai ,ka bari da kaina zan mata bayani idan mun huta',hashim ya amsa da 'angama ranka shi dade!' A haka suka d'unguma cikin gida bisa rakiyar royal guards wanda hannunsu ke ri'ke da jakar bolaji da hashim! A kofar shiga main palace palour suka tadda fulani da nawwara da hadimai suna jiransu,mai martaba ya amsa gaisuwar fulani da nawwara da sauran hadimai,sannan ya wuce ciki ya barsu! Bayan Wucewar maimartaba fulani tasa hannu ta rungumo hashim tana ce masa 'welcome home my souldear,my charming prince,the soldier of the nation! Murmushi hashim yayi yana cewa 'thank you my gorgeous mother ,dafatan na sameku lafiya', fulani ta amsa da 'lafiya lau' sannan ta nuna nawwara da yatsa tana cewa 'ga nawwara nan danake maka zancenta',nawwara cike da kwarkwasa da yanga,ta karkace hanci kamar wata kuturwa tana cewa 'welcome yaya hash,how's the journey',tana mai juya idanu! Hashim yasa hannu ya jawo bolaji[wacce kanta ke sunkuye] ,jikinsa yana mai cewa nawwara'the journey was awesome',sannan ya dubi bolaji tare da cewa 'lets go in,it seems like you are exhausted'! Fulani baki hangame ta dubi hashim sannan ta dubi bolajin da sai yanzu ta lura da ita,ta jinjina kanta kamar kad'angaruwa tana mai cewa 'souldear wace kuma wannan',hashim ya murmusa sannan ya 'kara rungumo bolaji ta gefensa da kyau ,sannan yace 'umma ,sunanta bolaji!' ,'gwalagwaji' fulani ta maimaita a firgice hannunta akan kirji ,hashim yace 'a'a bolaji sunanta,sauran bayani zakiji a gun abba anjima',sannan ya dubi bolaji yana ce mata 'meet my mother' ,bolaji ta d'ago idanunta ,fuskarta ba yabo ba fallasa tace'good evening ma',fulani kasa amsawa tayi domin kwata kwata noturan kanta sun kunce,ganin haka yasa hashim ya ja bolaji suka shige ciki tare da wucewa d'akinsa! Nawwara ce ta ta6a fulani,wanda hakan yasa fulani tayi firgigit ta dawo hayaccinta, kamar wacce ta tashi daga bacci,sannan ta sauke numfashi tana cewa 'tir'kashi,yau naga abinda zai hanani bacci',ta cigaba da cewa 'nawwara YARE fa idanuna suka gane mini',nawwara ta amsa da cewa 'ni ba wannan ba,ala'karsu da yaya hash nakeson insani ',fulani ta amsa da 'nima ban sani ba,amma mu jira muji sauran bayani a gun mai martaba kamar yadda souldear d'in ya fad'a,na tabbata zamu samu amsoshinmu acikin bayaninsa!' ¤¤¤ Bayan hadimai sun ajje jakar kayan bolaji da hashim sun fice,hashim dake zaune akan couch[kujera] ya dubi bolaji data tsaya a tsaye 'kerere tana 'karewa d'akin kallo,murya a tausashe hashim yace 'my better half,please sit down',harara ta watsa masa tare jan dogon tsaki ,hashim ya murmusa kawai ,a fusace ya fisgo hannunta ta fad'o kansa,ya gyara mata zamanta sosai akan cinyarsa,hannu yasa ya d'auko glasscup dake gefensa mai d'auke da ruwan sanyi,ya kai bakinta,sanin cewa yanzu zai murd'e mata hannu yasa ta fara shan ruwan ,kuma sanyin ruwan da ya ratsa ma'kogoranta yasa ta shanye ruwan tas! Hashim ya ajje cup din,sannan ya fara cire mata d'ankunne da sar'ka,ya kuma warware mata d'aurin ashoken dake kanta! Bolaji ji take kamar ta fasa ihu ,sai tsaki kawai take! Hashim ya tureta daga kan cinyarsa a hankali,ya zaunar da ita akan couch d'in,mi'kewa yayi yana cire kayan jikinsa,sai da ya saura daga shi sai singlet da boxer ,sannan ya shige toilet! Bolaji tayi 'kwafa ta tallafo kumatunta da hannu biyu ,tace 'chai,i don suffer,me bolaji don become oga hitler wife by force by fire,chai chai,na my mouth cause am,i go carry my big mouth promise am marriage if e go farm,i think sey the mumu no go fit farm,see the wahala wey this promise come land me into,but no lele,GOD dey' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~26~ Fulani da nawwara sun shirya cikin kaya na alfarma,sai zuba 'kamshi suke,ita kuwa ummu ko a jikinta tunda ba sultan bane zai dawo,tana d'akinta tana karatun al'qur'ani! Bayan fulani ta tabbatar da kamalluwar komai tun kama daga abinci,abinsha,da kuma da'kin kwanansu,hatta ruwan wanka sai da tabbatar da ancika bath tubs da ruwan turare! Misalin 5:00pm motoci suka fara shigowa harabar masarautar modibbo! Da sauri royal guards suka bubbud'e masu 'kofofi suka fito,mai martaba ne ya fara fitowa sai hashim da bolaji,sai kuma sauran yan rakiya, bayan mai martaba ya sallami tawagarsa sun watse,sai ya maido da dubansa ga bolaji fuskarsa d'auke da murmushi yace ' welcome to our palace my daughter',kanta a sunkuye ta amsa da 'thank you sir',mai martaba ya dubi hashim yace 'kai kuma ko da munshiga ciki,kar ka kuskura ka shaidawa ummanka batun aurenka ,ko da kuwa ta tambayeka wacece ita,kar ka ce mata komai ,ka bari da kaina zan mata bayani idan mun huta',hashim ya amsa da 'angama ranka shi dade!' A haka suka d'unguma cikin gida bisa rakiyar royal guards wanda hannunsu ke ri'ke da jakar bolaji da hashim! A kofar shiga main palace palour suka tadda fulani da nawwara da hadimai suna jiransu,mai martaba ya amsa gaisuwar fulani da nawwara da sauran hadimai,sannan ya wuce ciki ya barsu! Bayan Wucewar maimartaba fulani tasa hannu ta rungumo hashim tana ce masa 'welcome home my souldear,my charming prince,the soldier of the nation! Murmushi hashim yayi yana cewa 'thank you my gorgeous mother ,dafatan na sameku lafiya', fulani ta amsa da 'lafiya lau' sannan ta nuna nawwara da yatsa tana cewa 'ga nawwara nan danake maka zancenta',nawwara cike da kwarkwasa da yanga,ta karkace hanci kamar wata kuturwa tana cewa 'welcome yaya hash,how's the journey',tana mai juya idanu! Hashim yasa hannu ya jawo bolaji[wacce kanta ke sunkuye] ,jikinsa yana mai cewa nawwara'the journey was awesome',sannan ya dubi bolaji tare da cewa 'lets go in,it seems like you are exhausted'! Fulani baki hangame ta dubi hashim sannan ta dubi bolajin da sai yanzu ta lura da ita,ta jinjina kanta kamar kad'angaruwa tana mai cewa 'souldear wace kuma wannan',hashim ya murmusa sannan ya 'kara rungumo bolaji ta gefensa da kyau ,sannan yace 'umma ,sunanta bolaji!' ,'gwalagwaji' fulani ta maimaita a firgice hannunta akan kirji ,hashim yace 'a'a bolaji sunanta,sauran bayani zakiji a gun abba anjima',sannan ya dubi bolaji yana ce mata 'meet my mother' ,bolaji ta d'ago idanunta ,fuskarta ba yabo ba fallasa tace'good evening ma',fulani kasa amsawa tayi domin kwata kwata noturan kanta sun kunce,ganin haka yasa hashim ya ja bolaji suka shige ciki tare da wucewa d'akinsa! Nawwara ce ta ta6a fulani,wanda hakan yasa fulani tayi firgigit ta dawo hayaccinta, kamar wacce ta tashi daga bacci,sannan ta sauke numfashi tana cewa 'tir'kashi,yau naga abinda zai hanani bacci',ta cigaba da cewa 'nawwara YARE fa idanuna suka gane mini',nawwara ta amsa da cewa 'ni ba wannan ba,ala'karsu da yaya hash nakeson insani ',fulani ta amsa da 'nima ban sani ba,amma mu jira muji sauran bayani a gun mai martaba kamar yadda souldear d'in ya fad'a,na tabbata zamu samu amsoshinmu acikin bayaninsa!' ¤¤¤ Bayan hadimai sun ajje jakar kayan bolaji da hashim sun fice,hashim dake zaune akan couch[kujera] ya dubi bolaji data tsaya a tsaye 'kerere tana 'karewa d'akin kallo,murya a tausashe hashim yace 'my better half,please sit down',harara ta watsa masa tare jan dogon tsaki ,hashim ya murmusa kawai ,a fusace ya fisgo hannunta ta fad'o kansa,ya gyara mata zamanta sosai akan cinyarsa,hannu yasa ya d'auko glasscup dake gefensa mai d'auke da ruwan sanyi,ya kai bakinta,sanin cewa yanzu zai murd'e mata hannu yasa ta fara shan ruwan ,kuma sanyin ruwan da ya ratsa ma'kogoranta yasa ta shanye ruwan tas! Hashim ya ajje cup din,sannan ya fara cire mata d'ankunne da sar'ka,ya kuma warware mata d'aurin ashoken dake kanta! Bolaji ji take kamar ta fasa ihu ,sai tsaki kawai take! Hashim ya tureta daga kan cinyarsa a hankali,ya zaunar da ita akan couch d'in,mi'kewa yayi yana cire kayan jikinsa,sai da ya saura daga shi sai singlet da boxer ,sannan ya shige toilet! Bolaji tayi 'kwafa ta tallafo kumatunta da hannu biyu ,tace 'chai,i don suffer,me bolaji don become oga hitler wife by force by fire,chai chai,na my mouth cause am,i go carry my big mouth promise am marriage if e go farm,i think sey the mumu no go fit farm,see the wahala wey this promise come land me into,but no lele,GOD dey' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 12:22 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~27~ Fitowar hashim daga toilet ne ya katsewa bolaji zancen da take,d'agowa tayi takai duba gareshi,sauran 'kiris ta sume lokacin da idanunta suka mata tozali da hashim sanye da towel kawai a 'kugu,jikinsa smooth babu d'igon tabo,faffad'an kirjinsa a cike tam yake da tsoka amma babu suma,cikinsa a tsu'ke wanda six packs suka 'kawata,bolaji ita kanta tasan hashim namiji ne mai kyau da tsarin halitta! Hashim ne ya 'karaso ya hure mata idanu,tayi firgigit ta dawo hayaccinta,ta harareshi taja tsaki,bai bi takanta ba,ya tayata cire kayan jikinta,ya cicci6eta ya kai ta toilet,ya fito ya shirya cikin wata ba'kar jallabiya ! Bolaji ta fito daga toilet ,jikinta rufe da towel,hashim ya mi'ka mata jallabiya ta saka,sannan ta jawo jakarta ta ciro hijab tasaka,sannan ta d'aura zanin leshin da ta cire! Hashim ya jasu sallar maghrib,bayan sun iddar ya ja hannunta suka fice ! A kan dinning suka iske maimartaba,fulani,ummu da nawwara! Kujera hashim ya jawo, bolaji ta zauna,sannan shi ma ya zauna a kujerar dake kusa da kujerar bolaji,kuyanga ta yi serving d'insu ! Misalin 'karfe 8:50pm na dare,maimartaba yana zaune da fulani da ummu a restroom! Mai martaba yayi gyaran murya ya fara yiwa fulani fad'a akan abinda tasa hashim yaje ya aikita,fulani ta tsure tana bashi ha'kuri,mai martaba yayi mata tatas ,sannan kuma ya labarta masu komai da yasani game da ala'kar hashim da bolaji har izuwa aurensu a yau,suka taho da ita! Fulani 'kiris ya rage zuciyarta ta tarwatse,amma haka ta tattaro nutsuwa da fara'a ta shimfid'a akan fuskarta tanuna tsantsan murnarta ga auren hashim da bolaji! Ummu itama taji dad'in wannan aure a zuciyarta ,amma a fili sai tayi addu'a kawai! Kasancewar ummu ke da girki,hakan yasa fulani ta mi'ke ta fice ta nufi d'akinta! Hashim ya gama shigar da duk wani informations ta laptop d'insa,kasancewar gobe zai wuce liberia inda aka turasu wani aiki har na tsawon wata d'aya,kuma sunada damar tafiya da matayensu at thier own risk,bayan ya gama da laptop d'in,kashewa yayi ya mi'ke ya cire kayan jikinsa ya rage daga shi sai boxers,sannan ya nufi gun bolaji wacce ke kwance akan darduma ,ta fara yin bacci,hannu yasa ya cicci6eta ya kaita kan gado ya kwantar ,ya rage mata kayan jikinta,ya tofe su da addu'a tare da kankameta,ya kashe wutar bedside lamp ,a haka har bacci ya kwashesu! Fulani tana shiga d'aki ta d'au waya ta kira nawwara! Nawwara ta shigo d'akin tana cewa 'umma lafiya?','ina lafiya kuwa,hashimu ya auro jinin oduduwa da sango',fulani ta bawa nawwara amsa! Nawwara hannun akan 'kirji ta 'kwalalo idanu tace'aure?','kwarai kuwa aure dai da kika sani' sannan fulani ta labartawa nawwara komai kamar yadda mai martaba ya labarta mata d'azunnan', nawwara ta jinjina kai tare da cewa 'noma!' lallai yaya hash wannan yarinya ta gama asirceshi',fulani tace'barni da shegiya,ni fa da maimartaba yayi min zancen,kasa yin zancenki nayi wallahi,domin nasan raina ne zai 6aci,wai ni hashim da abbansa zasu munafinta,ba laifinsu bane,laifin matsafiyar yarinyar ce ,yar gaban goshin sango ,amma dani take zancen,zata gane cewa shayi ruwane,a siyasance zanci ubanta,in kuma fitar da ita daga fadar nan ba tare da kowa a cikinsu ya lura ba,kema ya zama dole ki danne zuciyarki,ki nuna murnar ga wannan auren,domin yin haka kad'ai zaisa mu cimma burinmu akanta batare da kowa yagane 'kiyayyarmu gareta ba',nawwara tace'hakane umma,gaskiya kin kawo shawara mai kyau',fulani tayi murmushi tace'sai na nunawa wannan tsinanniyar cewa ni ba'kar masa ce ,tuyar iblisai,batare da na sanya boka ko malam a lamarin ba!' created by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 12:37 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~28~ Washegari da safe bayan gaba d'ayansu sun gama karyawa,fulani ta d'auko wasu royal abayas guda biyu ,ta 'kwan'kwasa d'akin yarima hashim! Hashim ya bud'e kofar ,ganin fulani ce yasa ya russuna yana cewa 'ina kwana',fulani da fara'arta ta amsa tana cewa'my souldear ango,aure babu gayata babu labari',hashim ya fara sosa 'keyarsa ,fulani tayi murmushi tace'ungo ka mi'kawa surukar tawa kafin anjima mu fita da ita mu had'o mata lefe' ,hashim ya amshi kayan yana cewa'godiya muke umma,amma fa umma tafiyar da zanyi zuwa liberia a yau da ita zan tafi,idan munje can zan had'a mata lefen'fulani ji tayi kamar ta sha'keshi ,a zuciyarta cewa take'huh zama da marasa kunya yasa d'ana ya zama mara kunya,ka tafi da ita can salon ka 'kunsa mata ciki ko,jiya ma ba yadda na iya ,hakan yasa na barku kuka kwana tare',a fili sai fulani ta amshe kayan daga hannunsa tana cewa'ayya toh shikenan, turo min ita,muje in tsuma maka ita ,yadda zakuji dad'in yin honeymoon d'in naku a can',hashim ji yayi kamar kasa ta tsage ya shige,a kunyace ya koma d'akin yacewa bolaji taje umma na kiranta! Bolaji sanye da jallabiyar hashim ta fito ,ta russuna,fulani taja hannunta tana cewa'my daughter,the beautiful damsel,stand up lets go to my room!' Suna shiga d'akinta ,fulani ta fara janta da zancen tafiya liberia,anan bolaji ta nuna mata cewa ita fa bata son tabi hashim! Fulani ta murmusa tana cewa 'da kinsan abinda zai sameki da kin tattara kin bi mijinki',sannan ta dafa bolaji tana cewa'my daughter,don't worry no one will force you to follow him,lie down and rest for now,i will talk to him',kasancewar mai martaba ya gabatar da kowa ga bolaji,hakan yasa bolaji ta rungume fulani tana cewa 'thank you mummy folani',fulani tace 'folanin uwarki,haka kawai zaki gur6atamin suna da shege harshenki na yare',bolaji tace 'what?',fulani tayi ya'ke tare da amsa mata da cewa 'i mean i love the way you pronounce my name',bolaji tayi murmushi ta kwanta akan gadon fulani ,kamar yadda fulanin ta umarceta' ¤¤ ¤ Misalin 'karfe 11:00am hashim ya gama shirin tafiya tsaf! fitowa yayi daga d'aki ya wuce bangaren mai martaba,anan yasamu ummansa da ummunsu ,ya russuna ya gaishesu suka amsa masa da fara'a,kanshi a sunkuye yace masu zasu wuce,maimartaba da ummu suka masa fatan alkhairi,a kunyace hashim ya dubi fulani yana cewa 'umma ina take,ta fito mu tafi',fulani ta murmusa tace'd'ana kenan,tana d'akina a kwance ,amma fa matar nan taka ta nuna min rashin son tafiyar nan,sai naga kawai me zai hana ka tafi kai kad'ai ka barta damu ,tunda wata d'aya kawai zakayi kadawo,kaga kenan kafin ka dawo ta riga ta gama sabawa da masauratar nan da kuma mutanenta,amma kana da damar tafiya da ita fah,tunda abar ikonka ce',hashim ya 'kas'kantar da kai yace'umma duk yadda kikace daidai ne,da ni da ita duk abun ikon ki ne,bara na wuce' ,fulani tace 'ALLAH ya kiyaye ya kuma tsare' ,a haka hashim yayi sallama dasu gabad'aya ya fice! 'Dakin fulani ya wuce ,anan ya tadda bolaji kwance akan gado,'karasawa yayi gareta ya ran'kwafa ya kwanta akanta,bolaji ta bud'e idanunta,a sanyaye hashim ya rad'a mata a kunne 'my better half,i'm leaving',turo baki bolaji tayi tare da kawar da kanta gefe,bakinsa yasa ya chafki bakinta,wannan karin jikinta yayi sanyi 'kalau,kwata kwata ba ta nemi ta janye bakinta ba,sai da ya gaji da kansa,sannan ya 'kyaleta,ya mi'ke tsaye,ya gyara zaman uniform d'insa sannan yace 'my better half take care of your self,if you need anything ask my mum',bolaji ta tashi zaune,ta turo bakinta tare da jan tsaki hashim yayi murmushi tare da juyawa zai fice! A daidai kofar ya juyo ya dubeta idanunsa jajir yace'i'm going to miss you my better half,and always remember that ,cap.t hashim love's you',bai jira amsarta ba ,ya fice tare da wucewa mota inda royal chaffeur ke jiransa,yana shiga mota r ya mannawa idanunsa ba'kin spec,royal chaffeur ya harba motar suka fice daga modibbo's palace,suka wuce airport,daga can hashim zai hau jirgi ya wuce liberia! Bolaji ta sauke numfashi,ta koma ta kwanta tana mai murnar rashin tafiyar hashim da ita ! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 12:38 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2trbes } na ILILEE ~29~ Misalin 'karfe 2:00 na rana ,fulani ,nawwara,da bolaji suka fice tare da royal guards,bayan fulani ta amshi ma'kudan kud'i a gun mai martaba! Siyayya wanda ya amsa suna siyayya fulani tayiwa bolaji sosai,wanda nawwara ita ce mai kan gaba wajen za6owa,sai da suka sha'ke akwatuna guda 24 da kaya,sannan suka dawo fada da kaya ni'ki ni'ki! Bolaji ta kasa cewa komai,sai murna take a yau tasamu madadin mahaifiyarta,fulani ta nuna mata so da gata ba kad'an ba,haka zalika nawwara! ¤¤¤ A kwana a tashi yau kwanan bolaji 20 a fada,wanda zuwa yanzu ta saba da mutanen fada,a kullum sai jakadiya mara'kisiya ta kaita gun ummu,ummu kuwa ba laifi tana jan bolaji a jiki tana hira da ita ,tare da bata shawarwari cikin harshen turanci! Bolaji abu d'aya ne bata saba dashi ba,shine d'aura zani ,kuma kusan duk tufafin da fulani ta kwaso mata atamfofi ne wanda fulani tasa a din'ka mata su zannuwa! ¤¤¤ A yau sultan ya kamalla bautar 'kasar sa ,kuma a yau sauran kwana uku hashim ya dawo! Tun safe ummu ta fara shirye shiryen tarbar sultan,itama ta nuna tata bajintar wajen sawa ayi gyare gyare da girke girke na tarbar d'anta! Misalin 'karfe 5:00 na yamma sultan ya iso fada,ummu tayi masa tarba mai kyau,inda ta d'inga mamakin haske da 'kibar da yayi kamar bashi ba! Da dare ,kasancewar ummu ke da girki,ta wuce sashin mai martaba! Sultan ya nufi sashin fulani ,a mini parlour d'inta ya tadda fulani bolaji, da nawwara,suna hira suna shan kayan itatuwa! Neman waje yayi ya zauna,suka gaisa da fulani da nawwara,sannan ya 'kurawa bolaji idanu,wanda maimartaba ya riga gabatar masu da junansu d'azu a gun cin abinci! Sultan yayi gyaran murya yace 'umma wai ita matar bros batajin hausa ne',fulani ta yatsine fuska tana cewa 'ka ta6ajin cewa oduduwa yana jin hausa?',bolaji tayi caraf jin fulani ta ambaci oduduwa, tace 'mummy folani,so you know oduduwa',fulani ta washe ha'kora tana cewa 'ba dole in san oduduwa ba,tunda ga irinsa a gabana',bolaji tace 'i beg your pardon',fulani tace 'what i said is that ,back then when i was in secondary school,i love the yoruba's so much,so i know alot about them',bolaji tayi dariya tana cewa 'excuse me',ta mi'ke tsaye ta wuce toilet d'in d'akin fulani! Tana fita fulani taja tsaki ,nawwara ta tayata ! Fulani tace'wallahi nagaji da nunawa wannan YAREN so,kullum nice magana cikin harshen turanci kamar d'iyar mango park',nawwara tace 'umma ke dai bari,gwolaji tana 'konamin rai,musamman idan ta ambaci sunayenmu' ,fulani tace 'kyale 'yar iskar mana,lokaci kawai nake jira in gabatar kudiri na akanta, kafin souldear ya dawo', nawwara ta amsa da 'ya kamata kam',sultan fuskarsa dauke mamaki ya dubi fulani yace 'umma me aibunta idan ta zamo YARE,zamanta matar bros ya kamata ace kin so ta tsakani da Allah',fulani ta aika masa da da'kuwa tana cewa 'tashi ka fice min daga d'aki,kafin yanzu in sauke maka kwandon tsinuwa akai',sum sum sum ya mi'ke ya fice! Fulani ta 'kara jan dogon tsa'ki tana cewa 'ya zama dole in fitar da yarinyar daga wannan masarauta' Sultan kuwa ya kamu da matsananciyar sha'awar bolaji,kyawunta da dirinta ne yake fisgar tunaninsa,wanda hakan yasa ya kasa jurewa ,ya fara neman mafita ga yadda zai kashe wutar sha'awar bolaji da ya addabi zuciyarsa! ¤¤¤ A yau maimartaba ya umarci fulani da naja'atu dasu shirya zasu fita rangadi,fulani ta tsiro da rashin lafiya,wanda hakan yasa maimartaba ya tafi da ummu[naja'atu] tare da royal chambers da royal guards! Fulani taji dad'in wannan fitar tasu! Sultan shima a wannan rana ya nufi d'akin bolaji domin gudanar da nasa 'kudirin,inda itama fulani tazo aiwatar tata kud'irin ,sai kuma ta tadda sultan [ku duba 1,2 3,]! CIGABAN LABARI..... *Ya rayuwar bolaji zata kasance a wannan dajin,mutuwa ko rayuwa? *Ya capt.hashim zai yi idan ya dawo ya tadda matarsa bata fada? *Me fulani zatace ga maimartaba da hashim akan 6acewar bolaji daga fada? *Shin kurtagu,barde,nawwara,sultan,da jakadiya zasu tona asirin fulani? Muje zuwa dai tare dani ILILEE ma'kir'kirin YARE BIYU ,domin samun amsoshinku! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 12:41 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~30~ A lokacin da fulani suka dawo fada,su maimartaba basu dawo ba,hakan ba 'karamin dad'i yayiwa fulani ba! kud'i ta d'auko ma'kudai ta bawa su barde da duk wani wanda yasa hannu a cikin fitar bolaji daga fada a yau ,in an d'auke nawwara da sultan,wanda su ja masu kunne tayi sosai akan kar taji kar ta gani,sannan ta wuce d'akin bolaji ,taje ta d'auko wata doguwar riga a cikin kayan bolaji da kuma awarwaronta guda uku na daham ,wanda maimartaba ya bawa bolaji a matsayin sadakin aurenta da hashim! Fulani ta wuce d'akinta ta 6oye kayan tana murnar faruwar abinda ta aikata ayau ,tana cewa a ranta 'nan gaba zakuyi naku aikin'! Daf da magriba mai martaba da ummu suka dawo daga rangadi, Fulani tayi masu tarba mai kyau! Bayan sallar isha,kowa ya hallara a gun cin abinci in an d'auke bolaji, bayan sun gama cin abincin,suka dawo restroom,maimartaba ya dubi fulani yace'ni ko ina yarinyar nan take,tunda muka dawo ban ganta ba',fulani ta marairaice murya tace'kasan gobe maigidanta zai dawo,shine d'azu mukayi mata gyaran jiki da fuska ni dasu nawwara,,toh gajiyane yasa kanta ciwo,tasha magani ta kwanta abinta,kuma dai da yake tana fashin sallah ne,hakan yasa tayi kwanciyarta'',maimartaba yace'ayya,ALLAH ya sawwake','amin' fulani ta amsa ,a haka suka cigaba da tattaunawa akan dawowar da hashim zai yi gobe! Sultan wanda hankalinsa gaba d'aya yana gun bolajin da suka baro kwance a daji,tashi yayi ya koma d'aki yana mai tunanin neman mafita ga yadda zaiyi ya ceto rayuwar bolaji! ¤¤¤ Bayan tafiyarsu fulani da awa d'aya,wasu ayarin mahauta da karnukansu suka zo wucewa ta dajin,ganin karnukansu sun nufi gun da bolaji ke yashe a kwance a dajin,yasa mahautan suka bi bayan karnukan nasu,ganin mace kwance fuska jina jina yasa sukayi mata chaa akai,sun tsorata matu'ka ga yanayin da suka tsinci fuskarta! Hannu suka sa suka cicci6eta suka yo bakin titi da ita suka kwantar da ita! 'Daya daga cikin mahautan ne ya tsaya akan titin yana mai d'aga hannunsa ga duk motar da ya gani tazo wucewa,amma fafur haka zasu wuce ba tare da sun tsaya ba! Wata ba'kar motace 'kirar vibe tazo wucewa a guje,har motar ta wuce mahaucin,sai kuma ta dawo da baya,sannan aka sauke gilasan motar! Wani Matashine ma'abocin kyau dake zaune kujerar dake kusa da kujerar direba ya dubi mahaucin yana cewa'bawan Allah lafiya kake tsaida mu',mahaucin yace 'ina lafiya kuwa yalla6ai,gawa muka tsinta a daji,shine muka yanke shawarar neman taimako gun irinku masu motoci,ku tafi da gawar asibitin cikin gari,ko a dace,iyalan mamacin suzo nema',matashin mai suna HISHAM yace'gawa kuma? A daji?','eh yalla6ai,sauko ka ganta ,macece ma,inaga wani naman daji ne ya hallaka ta,saboda fuskarta ya nuna alamun faruwan hakan',hisham ya bud'e mota ya sauko tare da duban matashin dake zaune a mazaunin direba yana cewa 'bala sauko muje mugani',matashin da ya amsa suna bala yaja gajeran tsaki tare da cewa'haba oga ,me had'inmu da gawa kuma,wayasani ko kasheta sukayi,shine zasu 'ka'kaba mana ita',hisham ya daka masa tsawa da cewa'common get out from the car my friend',jiki na rawa bala ya fito,mahaucin yayi masu jagora suka 'karasa gun sauran mahautan dake tare da bolaji! Ganin fuskar bolaji tamkar d'anyar naman shanu ,yasa hisham da bala suka kauda kawunnansu bakunansu d'auke da salati! Hisham ya umarcesu dasu d'auki bolaji su sanya ta a mota,bayan sun kwantar da bolaji a motar,hisham ya dubesu yace yana bu'katar koda mutum d'aya ne a cikinsu ya bisu domin bada shaida,a take mutum biyu suka amince zasu bisu! Sauran mahautan sukayiwa hisham godiya,sannan sukayi sallama da juna suka wuce! Police station direct suka zarce ,anan hisham ya nuna masu I.Dcard d'insa,sannan yayi reporting cewa gawa suka tsinta a daji,suna bu'katar d'ansandar da zai rakasu asibiti sukai gawar! A take aka had'asu da d'ansanda guda d'aya ,bayan an tabbatar da bayanin nasa,ta hanyar tambayar sauran mahautan guda biyu! YABO CITY HOSPITAL suka zarce da bolaji domin mi'kata ga mortuary! ¤¤¤ Sultan kuwa ya yanke shawarar komawa dajin dasu ka baro bolaji ,a wannan dare,ba tare da kowa yasani ba,ya d'au mota ya fice daga fada,ko da ya isa dajin ,ya iske wayam babu bolaji babu labarinta! Jiki a sanyaye ya dawo fada ,yana mai tir da halinsa na neman mata,gashi ya jazawa 'yar mutane ,an salwantar da rayuwarta ta dalilinsa,a take ya d'au al'kawarin ba shi ba neman mata har abada! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/16, 7:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~31~ Da isar su hisham asibitin[YABO CITY HOSPITAL] ,suka zarce reception suka sanar da nurse on duty abinda ke tafe dasu,da hanzari ta had'asu da DR AYUBA wanda ya kasance aboki ga hisham! Bayan sun gaisa da junansu,sai hisham ya korowa abokinsa jawabi akan abinda ke tafe dasu! Dr ayuba ya jinjina namijin kokarin da sukayi wajen ganin sun kawo gawar bolaji motuary,sannan ya koma kan bolaji wacce take kwance tamkar matacciya yana bincike domin tabbatar da mutuwarta ,abin mamaki sai ya tsinci jijiyar hannunta[pulse] yana matsowa,wato dai da ranta ,a take ya bawa nurses umarni da su shigar da bolaji emergency room domin abata taimakon gaggawa! Dr ayuba ya shaidawa su hisham cewa tana da rai bata mutu ba,su kwantar da hankalinsu,da izinin Allah zasuyi iyaka bakin 'kokarinsu wajen ganin su ceto rayuwarta,yana gama fad'a masu haka ya shige emergency room! Hisham a take ya sallami mahautan da 'yansandan da suka taho tare,ya rage daga shi sai bala! Bayan awa biyu Dr.ayuba ya fito daga emergency room ya shaidawa hisham cewa 'everthing is going smoothly,munyi 'ko'karin daidaita numfashinta tare da treating ciwon dake kan fuskarta da duk wani external wounds dake jikinta,yanzu haka ansaka mata drip,muna jiran farfad'aworta domin mu 'kara bincike akanta ko tana da internal wounds',hisham ya dubi dr.ayuba yana cewa 'godiya nake ayuba,ALLAH ya saka da alkhairi',dr.ayuba yayi murmushi tare da dafa kafad'ar hisham yace'never mind hisham,ko da ace ba kaine ka kawota ba,iyaka abinda zamu iya yi mata kenan',sannan yace 'zaka iya tafiya dare yayi,i will handle everything,kar ka damu'! A haka sukayi sallama da juna,hisham da bala suka fice daga asibitin! ¤¤¤ Washegari misalin 'karfe 10 na safe fulani ta nufi turaka gun maimartaba bisa jagorancin jakadiya mara'kisiya ,hankalinta a tashe kamar dagaske ,da isar su turaka ,fulani ta shige ,bayan ta mi'ka gaisuwa ga maimartaba,sai ta d'ora da cewa' ni fa tun da asuba banga yarinyar nan ba a d'akinta,kuma nasa an dudduba ko ina a cikin fadar nan,amma ba'a ganta ba',maimartaba hankali a tashe yace 'tir'kashi ba'a ganta ba,toh ina taje?',fulani ta amsa da cewa 'nima tambayar da nake wa kaina kenan,amma fa ina ganin kamar guduwa tayi fa,domin a yadda na lura yarinyar bata son hashim ko kad'an'! A take maimartaba ya bawa royal guards umarnin cewa su fita su nemo bolaji a duk tashoshin dake jihar sokoto,sannan ya umarci sultan da yaje gidan sate comissioner of police,ya kai masa hotuna da duk wani details na bolaji! Hankalin kowa ya tashi a fada,nawwara ce taje ta binciko jakar bolaji ,ta ciro hotunanta guda biyu daga cikin album ,ta kaiwa sultan,ya tafi dasu gidan commissioner! Ita kuma nawwara ta wuce gidan radio da television ta bada cigiyar bolaji! Fulani sai kuka take tana cewa 'me zatacewa souldear idan ya dawo ya tadda matarsa bata nan! Ko da sultan ya isa gidan Commissioner da hotunan bolaji,ya kuma shaidawa commissioner sa'kon maimartaba ,a take commissioner ya tura yaransa da hotunan bolaji suje duk wani checkpoints da police depot dake jihar sokoto su bada cikiyar bolaji! Har 'karfe 2:00pm na rana,babu labarin bolaji,hankalin maimartaba duk ya gama tashi! Fulani duk idanunta sunyi jajir sai mita take tana cewa 'ku nemo min d'iyata',su jakadiya na lallashinta! Sultan da nawwara kuwa suna mamakin fulani,musamman sultan da yake ji kamar ya tona abinda mahaifiyarsa ta aikata ,amma yana tsoron abin da zai biyo baya,hakan yasa ya dage da addu'a akan Allah ya bayyana bolaji a duk inda take! Misalin 'karfe 3:00pm jirginsu CAPT.YARIMA HASHIM ya sauka a filin airport d'in SULTAN BELLO! Ganin babu motar fada a airport d'in,yasa ya yanke shawarar yin shatar taxi da zai kaishi masarautar moddibo! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:24 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~32~ Bayan Hashim ya sallami mai taxi ,sai ya d'auki jakarsa ya shige fada,da sauri royal guards suka tareshi tare da amshe jakarsa suna masa barka da zuwa! Cike da takun 'kasaita ya 'karasa ya shiga palace parlour yana mamakin sauyin fuskokin kowa ! A palace parlour ya iske su nawwara da jakadiya mara'kisiya da sauran hadimai,suna bawa fulani baki wacce ke rusa kuka! Shigowar hashim ne yasa fulani ta d'ago jajayen idanunta ta dubeshi,da hanzari ta tashi ta fad'a jikinsa,tare da rushewa da wani kukan tana fad'in cewa'my souldear ta gudu,ta tafi,ba'a ganta ba,kaje ka dawo min da ita',hashim hankalinsa a tashe ya janye fulani daga jikinsa a hankali,ya dubeta tare da watsa mata tambayoyi kamar haka, 'wacece ta gudu? Wacece ta tafi? Wacece ba'a gani ba? Umma wacece?' 'MATARKA!' fulani ta bashi amsa ,muryarta na rawa ta labarta masa abinda yafaru ['karya da gaskiya]! A take idanun hashim suka canza launi,tsigar jikinsa suka mi'ke,gashi da jijiyoyin jikinsa suka tashi! A fusace ya bar parlour ya wuce d'akinsu yana cewa 'my better half ,where are you? I'm back',yana shiga d'akin ya nufi wardrobe ya bud'e ya d'auko jakar kayan bolaji data zo dashi, ya ciro iro da buban data sanya ranar dasu ka taho,ya rungume kayan yana fad'in 'please don't do this to me,you have punish me enough,my better half where are you ?,where have you hidden?,please come out,your husband is back!' Ganin cewa dagaske fa bolaji bata d'akin,yasa ajje kayan tare da mi'kewa ya wuce part d'in maimartaba! A nan ya tadda ummu da sultan suna jajanta lamarin! Sultan ne ya taso ya rungume hashim yana cewa'welcome back bigbro,kaga cewa ba'a zo an d'auko ka daga airport ba ko,yau mun tashi da wani mugun tashin hankali ne thats why,your wife is no where to be found' ,hashim ya katseshi ta hanyar cewa 'any news about her ,me ake ciki,wani mataki kuka d'auka da 'batan matata',sultan ya labarta masa halin da ake ciki a yanzu,har yanzu dai babu labarinta! Mai martaba ya dubi hashim tare da ce masa 'zo nan hashim',hashim ya 'karasa ga maimartaba! Maimartaba ya jawoshi jikinsa ya rungume yana bugun bayansa a hankali yana cewa 'hashim kayi ha'kuri,ka fawwalawa Allah lammuranka,ka d'auka cewa faruwar hakan kaddara ce,duk inda take Allah zai bayyana mana ita,jikina yana bani cewa ba guduwa tayi ba,amma bana zargin kowa akan hakan,ALLAH kad'ai ne masanin komai',hashim 'kwalla ya cika masa idanu,zuciyarsa na tafasa,ya kasa cewa komai ,sai ajiyar zuci yake saukewa! Ita kanta ummu a yau ta tausayawa d'an nata,'karasowa tayi tana shafa masa baya cikin sigar nuna tausayawarta gareshi! Maimartaba ya cigaba da bashi baki yana rarrashinsa! ¤¤¤ *HISHAM DAUDA BISHIR matashi ne d'an kimanin shekara 25 ,haifaffen d'an yankin yabo ne da ke jihar sokoto,d'a ne ga prof.dauda bishir da haj.hauwa! Ya kasance d'ansu na fari,yana da 'kanne mata guda biyu,zahra da zuhra! Yayi primary school d'insa a jihar sokoto,daga nan ya wuce N.M.S zaria ,anan ne suka had'u da hashim har suka 'kulla abota,bayan sun kamalla makarantar,sai hisham ya wuce 'kasar algeria yayi degree d'insa a bangaren international relations,yayin da hashim ya zarce N.D.A! Hakan yasa zumuncinsu yayi rauni,amma suna waya lokaci zuwa lokaci! A yanzu haka hisham yana aiki a non governmental organisation[N.G.O] mai suna 'Bieng human'! 'Kungiyar bieng human,kungiya ce da turawa suka samar don kwatarwa yan adam dake fad'in duniyarnan hakkinsu,yancinsu da kuma taimakawa marayu,gajiyayyu,da masu d'auke da cututtuka masu wuyar sha'ani! Wannan 'kungiya ta bieng human, duniya tasan da zamanta [worldwide org.]! Hisham ya kasance babban ma'aikaci a wannan 'kungiya,a branch d'insu ke jihar sokoto! Hisham ya kasance matashi kyakkawa,miskili ne na ajin farko,yana da ha'kuri da sanyin rai,gashi da son taimako! A yanzu haka yana zaune a gidansu,kuma aure baya gabansa tun bayan rasuwar masoyiyarsa MUJIBA ,wacce ta kasance d'iyar 'kanwar mahaifinshi,a gidansu ta girma kasancewarta marainiya,iyayenta sun rasu sakamakon hatsarin jirgin! Soyayya,aminci da sha'kuwa ya shiga tsakaninsu,har ta kai an masu baiko tare da sa masu rana! Ana gobe d'aurin aure,cikin dare ciwon ciki risketa ta amsa kiran ubangiji! Hisham yaji mutuwar mujiba,saboda har suma ya d'inga yi ,duk ya bi lalace ya tada hankalinsa,sai da akayi wata biyar da rasuwarta ya dawo daidai ya koma bakin aikinsa,amma zuciyarsa da ruhinsa suna masu bege da kewan MUJIBA! ¤¤¤ ko da bala direba ya sauke Hisham a gida ,a daren da suka kai bolaji asibiti,bai labartawa iyayensa da 'kannensa abinda ya faru ba! Washegari bala direba yazo ya kaishi office,sun biya ta asibiti ,amma dr.ayuba ya tabbatar masu da cewa bolaji bata farfad'o ba! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= { 2tribes } na ILILEE ~32~ Bayan Hashim ya sallami mai taxi ,sai ya d'auki jakarsa ya shige fada,da sauri royal guards suka tareshi tare da amshe jakarsa suna masa barka da zuwa! Cike da takun 'kasaita ya 'karasa ya shiga palace parlour yana mamakin sauyin fuskokin kowa ! A palace parlour ya iske su nawwara da jakadiya mara'kisiya da sauran hadimai,suna bawa fulani baki wacce ke rusa kuka! Shigowar hashim ne yasa fulani ta d'ago jajayen idanunta ta dubeshi,da hanzari ta tashi ta fad'a jikinsa,tare da rushewa da wani kukan tana fad'in cewa'my souldear ta gudu,ta tafi,ba'a ganta ba,kaje ka dawo min da ita',hashim hankalinsa a tashe ya janye fulani daga jikinsa a hankali,ya dubeta tare da watsa mata tambayoyi kamar haka, 'wacece ta gudu? Wacece ta tafi? Wacece ba'a gani ba? Umma wacece?' 'MATARKA!' fulani ta bashi amsa ,muryarta na rawa ta labarta masa abinda yafaru ['karya da gaskiya]! A take idanun hashim suka canza launi,tsigar jikinsa suka mi'ke,gashi da jijiyoyin jikinsa suka tashi! A fusace ya bar parlour ya wuce d'akinsu yana cewa 'my better half ,where are you? I'm back',yana shiga d'akin ya nufi wardrobe ya bud'e ya d'auko jakar kayan bolaji data zo dashi, ya ciro iro da buban data sanya ranar dasu ka taho,ya rungume kayan yana fad'in 'please don't do this to me,you have punish me enough,my better half where are you ?,where have you hidden?,please come out,your husband is back!' Ganin cewa dagaske fa bolaji bata d'akin,yasa ajje kayan tare da mi'kewa ya wuce part d'in maimartaba! A nan ya tadda ummu da sultan suna jajanta lamarin! Sultan ne ya taso ya rungume hashim yana cewa'welcome back bigbro,kaga cewa ba'a zo an d'auko ka daga airport ba ko,yau mun tashi da wani mugun tashin hankali ne thats why,your wife is no where to be found' ,hashim ya katseshi ta hanyar cewa 'any news about her ,me ake ciki,wani mataki kuka d'auka da 'batan matata',sultan ya labarta masa halin da ake ciki a yanzu,har yanzu dai babu labarinta! Mai martaba ya dubi hashim tare da ce masa 'zo nan hashim',hashim ya 'karasa ga maimartaba! Maimartaba ya jawoshi jikinsa ya rungume yana bugun bayansa a hankali yana cewa 'hashim kayi ha'kuri,ka fawwalawa Allah lammuranka,ka d'auka cewa faruwar hakan kaddara ce,duk inda take Allah zai bayyana mana ita,jikina yana bani cewa ba guduwa tayi ba,amma bana zargin kowa akan hakan,ALLAH kad'ai ne masanin komai',hashim 'kwalla ya cika masa idanu,zuciyarsa na tafasa,ya kasa cewa komai ,sai ajiyar zuci yake saukewa! Ita kanta ummu a yau ta tausayawa d'an nata,'karasowa tayi tana shafa masa baya cikin sigar nuna tausayawarta gareshi! Maimartaba ya cigaba da bashi baki yana rarrashinsa! ¤¤¤ *HISHAM DAUDA BISHIR matashi ne d'an kimanin shekara 25 ,haifaffen d'an yankin yabo ne da ke jihar sokoto,d'a ne ga prof.dauda bishir da haj.hauwa! Ya kasance d'ansu na fari,yana da 'kanne mata guda biyu,zahra da zuhra! Yayi primary school d'insa a jihar sokoto,daga nan ya wuce N.M.S zaria ,anan ne suka had'u da hashim har suka 'kulla abota,bayan sun kamalla makarantar,sai hisham ya wuce 'kasar algeria yayi degree d'insa a bangaren international relations,yayin da hashim ya zarce N.D.A! Hakan yasa zumuncinsu yayi rauni,amma suna waya lokaci zuwa lokaci! A yanzu haka hisham yana aiki a non governmental organisation[N.G.O] mai suna 'Bieng human'! 'Kungiyar bieng human,kungiya ce da turawa suka samar don kwatarwa yan adam dake fad'in duniyarnan hakkinsu,yancinsu da kuma taimakawa marayu,gajiyayyu,da masu d'auke da cututtuka masu wuyar sha'ani! Wannan 'kungiya ta bieng human, duniya tasan da zamanta [worldwide org.]! Hisham ya kasance babban ma'aikaci a wannan 'kungiya,a branch d'insu ke jihar sokoto! Hisham ya kasance matashi kyakkawa,miskili ne na ajin farko,yana da ha'kuri da sanyin rai,gashi da son taimako! A yanzu haka yana zaune a gidansu,kuma aure baya gabansa tun bayan rasuwar masoyiyarsa MUJIBA ,wacce ta kasance d'iyar 'kanwar mahaifinshi,a gidansu ta girma kasancewarta marainiya,iyayenta sun rasu sakamakon hatsarin jirgin! Soyayya,aminci da sha'kuwa ya shiga tsakaninsu,har ta kai an masu baiko tare da sa masu rana! Ana gobe d'aurin aure,cikin dare ciwon ciki risketa ta amsa kiran ubangiji! Hisham yaji mutuwar mujiba,saboda har suma ya d'inga yi ,duk ya bi lalace ya tada hankalinsa,sai da akayi wata biyar da rasuwarta ya dawo daidai ya koma bakin aikinsa,amma zuciyarsa da ruhinsa suna masu bege da kewan MUJIBA! ¤¤¤ ko da bala direba ya sauke Hisham a gida ,a daren da suka kai bolaji asibiti,bai labartawa iyayensa da 'kannensa abinda ya faru ba! Washegari bala direba yazo ya kaishi office,sun biya ta asibiti ,amma dr.ayuba ya tabbatar masu da cewa bolaji bata farfad'o ba! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:25 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~33~ *BAYAN KWANA UKU* Bolaji kuwa babu ita babu labarinta a fada ,domin har MD aka bugawa waya yaje can gidansu ya dubo ko taje can,amma babu labarinta,sai ma hankalinsu iya folake da bamidele da ya tashi,suna cewa shikenan bolaji ta shiga duniya sanadiyar 'kiyayyar aurenta da oga soldier! Hashim duk yabi ya tada hankalinsa,kullum yana rungume da kayanta da hotunanta yana cewa 'ban ta6a zata 'kiyayyarki gareni zai sa ki gujeni ba,na sha wahala akan sonki,na sha wahala kafin in samu ki aureni ,a lokacin dana aureki na zata 'karshen wahala ta yazo,ashe wasa farin girki,danasani na tafi dake,danasani ban tafi na barki ba,yanzu ta ina zan fara nemanki ,ta ina zan soma,please my better half come back to me'! Kowa a fada yana tausayawa hashim,duk yabi yayi sanyi,baya cin abinci,daga shan ruwa sai sallah! Fulani kuwa idan ta kalli hashim sai taji 'kiyayyar bolaji na 'kara ruruwa a zuciyarta! Hakan yasa ta 'kudiri anniyar d'aukar mataki na gaba akan lamarin! Sultan da nawwara suna masu tausayawa hashim matu'ka,amma ya zama dole su cigaba da biyewa fulani dan kaucewa makircinta! A can Erin sun dage addu'a akan Allah ya bayyana masu bolaji,haka zalika anan fada maimartaba yasa an tara malamai suna addu'a akan Allah ya bayyana bolaji ya kuma tsare ta a duk inda take ¤¤¤ kwanan bolaji goma a asibiti ta farfad'o fuskarta d'aure tam da bandeji ,idanunta kawai ake iya gani,Dr.ayuba ya bugawa hisham waya ya shaida masa farfad'owarta! Hisham da hanzari ya baro ofis yazo asibitin,bayan ya duba bolaji dake zaune tamkar gunki ba 'umh' ba 'uhm uhm'! Dr ayuba ya jashi ofis d'insa ,bayan sun zauna ,sai dr.ayuba yayi gyaran murya tare da duban hisham yace'toh Alhamdulillah patient d'in mu ta farfad'o,abu na gaba da za'ayi shine zamu had'u da sauran colleagues dina muyi sauran bincike akanta domin tabbatar da lafiyarta' ,hisham fuskarsa d'auke da murmushi yace 'nagode ayuba Allah ya saka da alkhairi',da 'amin' dr.ayuba ya amsa,suka cigaba da tattaunawa game da cigiyar bolajin da su kaga anayi a tv da kuma radio da newspaper akan cewa ta gudu,saboda har fada sukaje sukayiwa hashim jaje batare da sun san cewa itace a tare dasu ba! ¤¤¤ Dr.AYUBA ba kowa bane face yaya ga nawwara ,mahaifinsu d'aya ,uwa kuwa kowa da tasa,abotarsa da hisham ta samo asaline a jami'ar algeria,inda suka gano cewa mahaifarsu d'aya,duk da ba course d'insu d'aya ba,amma hakan bai hana sun 'kulla abota ba! Dr.ayuba ya kasance mutum mai tausayi a duk lokacin da bu'katar hakan ya taso,amma fa akan kud'i babu abinda bazai iya aikatawa ba,domin yanada masifar son kud'i! ¤¤¤ Hashim yana zaune a d'aki,yana rungume da album d'in bolaji a 'kirjinsa,ya takure a gu d'aya ,jijiyar kansa duk ya tashi,idanunsa jajir,a haka fulani ta shigo ta riskeshi tanemi gu ta zauna kusa dashi ta shafa kansa tana cewa'my souldear,kayi ha'kuri,nasan cewa its hard for you to get over her,amma ya zama dole ka manta da ita,tunda har izuwa yau ba'a ganta ba',sannan tayi 'kwafa tace'a gaskiya ta bani mamaki ,ban san cewa 'kiyayyarta gareka ya kai haka,na nuna mata so,gata da kulawa,amma haka tasa 'kafa ta shure ta gudu',hashim murya a sanyaye ya kwantar da kansa akan cinyar fulani yana cewa 'ni ban damu da guduwar datayi ba umma,all i want to know is tana ina ? ,wani hali take ciki a yanzu ? ,is she dead or alive?','wannan kuma Allah kad'ai ya sani' fulani ta bashi amsa sannan tace 'hashim ya zama dole ka fawwalawa Allah komai,ka d'inga cin abinci,ka ragewa kanka tunani' a haka fulani ta cigaba da bashi baki,ta aika aka kawo abinci ta ciyar dashi sannan ta fice ta bar shi ,bayan ta kwantar dashi! Fulani ta aika hadima badiyya ta kira mata barde da kurtagu,ta umarcesu dasu fito da mota kuma su shirya zasu fita! Fulani ta nemi izini gun maimartaba akan cewa zataje asibiti ,zata ga likita,mai martaba ya bata izini,ta shirya cikin shiga ta alfarma,ta sha'ke jakanta da kud'i masu kauri,sannan ta jefa doguwar riga da warwaron daham din bolaji a jakar ,ta fice ta shige motar ba tare da ta nemi rakiyar hadima ko d'aya ba,barde ya ja mota bayan ta bada umarnin su kaita YABO CITY HOSPITAL! Fulani ta dubi Dr.ayuba bayan ta ajje masa ma'kudan kud'i a gabansa akan table,Dr.ayuba ya zare idanu yana cewa 'ranki ya dad'e kud'in menene wannan?',fulani ta sauke ajiyar zuciya tare da marairaice murya tace 'ayuba ina son ka min wani aiki,wanda hakan kad'ai zai sa hashim ya dawo hayyacinsa ya manta da matarsa data gudu',Dr ayuba yace 'aiki ? Wani irin aiki?' ,fulani ta amsa masa da cewa 'gawar mace nake so ka bani,kuma ina son ka had'a mini fake D.N.A result' Created by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:25 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~34~ Cike da mamaki Dr ayuba ya maimaita kalmar 'gawar mace? ,fake D.N.A test result? ranki ya dad'e bangane ba,ki fahimtar dani' ,fulani ta marairaice murya tace 'ayuba ina son ka duba zumuncin dake tsakanina da mahaifiyarka wacce ta kasance kishiya ga 'yar uwata ,kasan halin da hashim yake ciki,duk yabi ya tada hankalinsa akan guduwar da matarsa tayi ,ya 'ki ci ,ya 'ki yin tawwakali,a ganina labarin mutuwarta kad'ai zai sa kowa ya ha'kura ya manta da ita a fada,wanda hakan zaisa hashim ya dawo hayyacinsa yayi tawwakali ya auri 'kanwarka nawwara,ayuba ka taimakeni ka ceci rayuwar d'ana!' Dr ayuba ya sauke ajiyar zuciya tare da kai duba gareta yace 'yanzu ya kike son ayi' ,fulani ta gyara zama tace 'yanzu dai gawar mace nake bu'kata da kuma fake D.N.A test result akan cewa jinin gawar yayi matching da jinin dake jikin warwaron daham guda uku da zan baka',Dr ayuba yayi jim sannan yace 'aikin fa da wuya,amma bakomai taimako ne,kuma wad'annan kud'in da kika ajje zasuyi amfani ,tashi muje motuary ki za6i gawa ,domin satin da ya wuce ankawo mana gawarwakin mutanen da sukayi hatsari akan titin zuwa kebbi daga sokoto!' fulani ta mi'ke suka fice ,bayan dr.ayuba ya kira wasu nurses guda biyu ya umarcesu da su biyoshi motuary! Da isar su motuary,Dr ayuba ya ciro kud'i ya bawa maigadin motuary,maigadi ya amshi kud'in yana washe ha'kora! Suka shige motuary d'in hancinsu rufe da mask! Suna shiga Dr ayuba ya umarci nurses d'in dasu bud'e gawarwakin mutanen dake cikin akwatin ajiyar gawa! Daya bayan d'ayan nurses suka fara bud'esu,a take fulani ta hango gawar mace mai duhun fata,wacce fuskarta ta dagargaje ,fulani batayi nauyin baki ba ta nuna gawar tana cewa 'wannan ce',Dr ayuba ya umarci nurses d'in da su fito da gawar su kwantar akan gadon dake d'akin [motuary]! Bayan sun kwantar da gawan,sai fulani tayiwa dr.ayuba nuni da idanu akan ya sallami nurses d'in sun tafi,Dr.ayuba ya dubesu yace 'you ladies can go',sum sum suka fice,suna fita fulani ta bud'e jakarta ta ciro doguwar rigar bolaji da ta d'auko ,ta yo kan gawar gadan gadan,da 'kyar da sid'in goshi ta sanyawa gawar doguwar rigar,sannan ta ciro awarwaron daham guda uku ta mi'kawa Dr.ayuba tana cewa 'ga wannan ka shafa musu jini, ka sanya su a cikin leda,sai kuma ka had'a fake D.N.A test result akan cewa jinin dake jikin awarwaron yayi matching da jinin gawar,yanzu zanje mota mu jiraka,kasan yadda zakayi kasa ambulance su biyo mu da gawar,inyaso mukaje fada zan d'orar',Dr.ayuba ya amshi awarwarayen[bangles] tare da cewa 'an gama ranki ya dad'e',fulani ta d'auki jakarta ita da dr.ayuba suka fice daga motuary d'in ,mota ta koma gun su kurtagu da barde,Dr.ayuba ya koma ofis dan aiwatar da abinda fulani ta saka shi! Bayan shud'ewar awa d'aya Dr.ayuba ya zo ya sami fulani a mota ya bata D.N.A test result tare da awarwarayen wanda aka shafesu da jini a cikin plastic bag! fulani ta amsa tana mai matse hawaye tace 'nagode ayuba,nagode da wannan taimakon da kayi min',Dr.ayuba yace 'bakomai ranki ya dad'e ,ga gawar can ansaka a motar ambulance,kuna iya tafiya',fulani tayi ta zabga masa godiya,a haka sukayi sallama ta shige mota ,kurtagu ya tada , suka fice daga asibitin,motar ambulance na biye dasu da gawa,har suka iso masarautar modibbo! Royal guards suka wangale gate ,motarsu fulani da ta ambulance suka shige! Bayan sun shiga ,direban motar ambulance da d'an uwansa suka fito daga mota suka bud'e bayan motar suka ciro gawar suka ajje a harabar fadar,ba tare da sunce uffan ba suka shige mota suka fice daga fada kamar yadda dr.ayuba ya umarcesu! Bayan motar ambulance ta fice,sai fulani ta dubi kurtagu da barde tace 'kuje ciki kuyi shelan cewa ga gawar matar hashim an kawo!', cike da girmamawa suka amsa da 'angama ranki shi dad'e',suka shige cikin fada dan cika umarnin fulani! Ba'a fi minti ashirin ba kowa ya fito harabar fada,mai martaba,ummu,hashim,nawwara,sultan sune a sahun gaba.suka 'karaso gun fulani dake dur'kushe a gaban gawa tana rusa kuka ,maimartaba ne yace 'fulani menene ya faru,dagaske ne cewa an kawo gawar yarinyar nan?',fulani murya a sha'ke da kuka tace 'dagaske ne ga tanan,gawarta ce,da naje asibiti ganin likita sai naga anzo wucewa da gawarta,ina ganinta sai jikina ya bani itace,duk da dai fuskarta ta salwanta,wanda hakan yasa basu gane cewa itace matar hashim da ake cigiya a kafafen yad'a labarai,dana bi diddigi sai nagano cewa ashe ta rasu ne ta sanadiyar hatsarin mota da ya ritsa da ita a hanyar fita daga garin nan,bayan tayi jinyar kwanaki',hashim ne ya matso kusa da gawar jiki asanyaye,hannunsa na rawa yasa ya bud'e farin mayafin da aka lullu6e gawar da shi,idanunsa na yin tozali da fuska gawar sai ya rintse idanu yana cewa 'ba ita ba ce!',fulani ta ciro ledar awarwarayen daham da D.N.A test result daga cikin jakarta ,tana kuka tana cewa 'kayi ha'kuri my souldear,nasan cewa da kyar ka amince,amma wallahi itace,gawarta ce,saboda sai dana tabbatar da itace' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:25 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~35~ Fulani ta mi'kawa maimartaba ledar awarwarayen da kuma fake D.N.A test result! Maimartaba ya amsa yana cewa 'tabbas wannan awarwarayen dana bata ne a matsayin sadakin aurenta,babu shakka gawarta ce',maimartaba ya dafa hashim yana cewa 'kayi ha'kuri kayi tawwakali,kulli nafsin za'ikatul maut,ALLAH da ya baka ita a matsayin matarka ,shi ya amshe abar sa,hashim kayi ha'kuri ,ka cinye wannan jarabawar,ka rungumi kaddara ka fawwalawa Allah komai',hashim a take wasu zafafen hawayen suka tsiyayo daga idanunsa ,ba tare da yace komai ba,ya tashi ya koma ciki hannunsa dafe da 'kirjinsa! Ummu ta tausayawa d'anta matu'ka,amma babu halin ta nuna haka saboda alkunya da 'kawaici! Fulani tana kuka ta umarci hadimai da su shigar da gawar bolaji domin ayi mata wanka da sutura a mi'kata gidanta na gaskiya! Bayan an shige da gawar,sai sultan da nawwara suka had'a ido tare da sauke ajiyar zuciya,saboda lamarin fulani ya matu'kar basu tsoro! Maimartaba ya umarci sultan da ya bugawa MD waya ,ya shaida masa rasuwar bolaji! Hashim ya koma d'aki ya takure gu d'aya,idanunsa sukayi jajir,jijiyoyin jikinsa duk suka kumbura,zuciyarsa na zafi da 'kuna,ALLAH kad'ai yasan irin halin da ya tsinci kansa a yanzu! Da maghriba bayan an binne gawar, ayarin su bamidele da iya folake,iya ayomide,funmilayo da sauransu suka iso fada bisa jagorancin MD da ya biya musu kud'in jirgi! Isowarsu ba 'karamin ba'kanta ran fulani yayi ba,amma haka ta daure ta cije ,ta tayasu kokawa ga mutuwar bolaji ,musamman da suka tadda an binneta sai kawai suka 6arke da wani sabon kukan,sai ihu suke suna cewa'dey don kill her oh,ahh oga soldier don send her go meet her parent oh,just the way he sent em to meet their fore fathers ',fulani sai basu baki take tana tayasu kukan,maimartaba ne ya basu ha'kuri sosai, ya kuma yi masu nasiha mai ratsa jiki,wanda hakan yasa jikinsu yayi sanyi ,suka fawwalawa Allah komai! Fulani ta bada umarnin akai su bangare guda a fada ayi musu masauki,kuma a tabbatar an basu kulawa! Washegari bayan an dawo daga sallar asuba,hashim sanye da farar jallabiya yana tafe dasu maimartaba,sultan,MD,da bamidele! Kawai sai ganin hashim sukayi ya yanke jiki ya fad'i ,bakinsa na fitar da aman jini guda guda! ¤¤¤ Dr ayuba ne ya fito daga I.C.U ,yana cire plastic gloves daga hannunsa,su maimartaba suka taso suna tambayarsa 'ya jikin hashim d'in? Meye sameshi' ,Dr.ayuba ya dubesu yace'muje office d'ina!' Bayan sun zazzauna a office d'in ,Dr.ayuba ya dubesu ya sauke ajiyar zuciya ,yace 'a gaskiya hashim yana cikin wani hali wanda Allah kad'ai ne zai iya fitar dashi',sultan bakinsa na rawa yace'doctor me kake nufi, please explain','a iyaka binciken mu akansa mun gano cewa yasamu attack due to shock and depression, wanda hakan yayi sanadiyar a yanzu he's in a state of coma' ,dr.ayuba yayi masu bayani! Maimartaba,sultan,MD,da bamidele suka had'a baki wajen maimaita kalmar 'COMA?' ,Dr ayuba yace'yes coma,wanda farfad'owarsa sai dai wani ikon Allah,amma za'a dad'e kafin ya farfad'o,because his condition is fatal,kuma ko ina zakuje dashi a duk asibitin fad'in duniyar nan,amsa d'aya ce guda d'aya 'addu'a!',maimartaba ya goge hawayen da ya zubo masa yana cewa 'innalillahi wa inna illaihi raji'un,ALLAH UBANGIJI YA TASHI KAFA'DARKA HASHIM,ya yaye maka kuma baka ikon cinye wannan jarabawar!' A take sultan ya fice daga ofis din,idanunsa na fitar da hawaye ya ciro waya yabugawa nawwara ya shaida mata halin da ake ciki! Ko dasu fulani suka iso asibitin ,anfito da hashim daga I.C.U ,an maidashi aminity! Hashim yana kwance dashi da matacce babu bambanci sai dai shi yana numfashi! Su iya folake sun tausaya masa matu'ka a lokacin da suka ganshi a kwance,fulani kasa hawaye tayi,sai kukan zuci take tana mai tausayawa d'anta! ¤¤¤ A harabar asibitin [YABO CITY HOSPITAL] Bala direba ya sauke hisham! Cike da takun 'kasaita ya fito ya shige asibitin ,a hanyarsa na zuwa ofis d'in Dr.ayuba ya had'u dasu maimartaba a zazzaune,ya rusuna ya gaidasu ya kuma yi musu gaisuwa,ya shige ofis d'in Dr ayuba! Yana shiga suka gaisa da Dr.ayuba sannan ya zauna yana cewa 'ayuba naga iyayen hashim a waje da zan shigo ofis dinnan ,mara lafiya suka kawo ne?',Dr.ayuba ya amsa da cewa 'hashim suka kawo d'azu da safe....{nan ya labarta masa komai game da rashin lafiyar yarima hashim },hisham ya nuna tausayarsa matu'ka sannan yace 'na tausaya masa Allah yabashi lafiya,ya kuma tashi kafad'arsa' ,sannan kuma yace'ya batun patient d'ina,kun gama bincikenku akanta',Dr.ayuba yayi gyaran murya sannan yace'mun gama duk wani bincike akanta ,kuma mun gano cewa,she has loss her memory!' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:27 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~36~ Hisham a d'imauce yace 'ayuba bangane ba',Dr ayuba yace 'toh dai a yadda bincikenmu ya nuna,ta buge akanta wanda hakan ya janyo brain d'inta ya samu matsala ,hakan kuma ya haifar mata da memory loss ' ,Hisham a sanyaye yace 'innalillahi wa inna illaihi raji'un,toh ni ya zanyi da ita,ni dana ke fatan ta murmure ta warke ,in ji labarinta da asalinta,saboda in sadata da garinsu da danginta!',sannan ya cigaba da cewa 'kuma fa har yanzu ban sanarwa dad da hajiya anything about her fa,basu ma san komai ba akan kawota asibiti danayi ba,its only my driver bala that know's about all this',Dr.ayuba ya gyara zamansa yace 'hisham ba wai fa tayi loosing memory d'inta forever bane,kuma naga tana fahimtar turanci,i spoke to her with english and she answered,ko nurses da turanci suke having conversation,so kaga some part of her memory tayi loosing,wanda muke fatan with time zatayi regaining sauran memory d'inta' ,hisham ya sauke ajiyar zuciya yace 'toh ayuba,ALLAH yasa memory d'in ya dawo gaba d'aya!',hisham ya mi'kawa dr.ayuba hannu sukayi musabaha ,yana mai cewa 'godiya nake Dr ,Allah yasaka da alkhairi'.Dr.ayuba yace 'amin and never mind hisham',hisham ya amshi bill ya fice daga ofis d'in ya wuce gun cashier yayi clearing bills ,sannan ya le'ka d'akin da aka kwantar da hashim ya jajantawa su fulani,ya fito ya le'ka d'akin da bolaji ke kwance fuska d'aure da bandeji ,bacci ya taddata tanayi hakan yasa ya tofa mata addu'o'i, ya fito daga d'akin tare da ficewa daga asibitin ya wuce gun aikinsa! Bayan sati biyu,aka rubutawa su maimartaba takardar sallamar hashim ,suka kwasheshi suka dawo dashi fada, ana kuma tsammanin jiran ranar da zai farfad'o! Dakinsa da bolaji aka kwantar dashi,inda fulani ta umarci hadimai da su had'a duk wani kayan bolaji su had'esu gu d'aya su saka a wardrobe su rufe! Aka cigaba da zaman makokin bolaji,hashim kuma yana kwance,tamkar kayi masa magana ya amsa! Kwanaki suka cigaba da tafiya ,a yayin da 'kawance na gamon jini ya 'kullu tsakanin funmilayo da nawwara,sai kuma soyayya mai 'karfi tsakanin nawwara da bamidele da suke gudanarwa ba tare da fulani ta lura ba,domin ita a yanzu takan lafiyar d'anta take wanda ke kwance tamkar matacce! A yau takama sadakar arba'in wato kwana arba'in da binne gawar da fulani ta kawo a matsayin gawar bolaji,kuma a yau ne su MD,bamidele dasu iya folake da funmilayo zasu koma osun state! Maimartaba ya had'a masu sha tara na arziki,nawwara da funmilayo da 'kyar aka raba su, suna kukan rabuwa ,haka zalika bamidele ya d'aukarwa nawwara al'kawari akan cewa zai dawo da magabatansa su nema masa auranta,kuma sunyi musayar lambobin juna,a haka suka rabu da mutanen fada suna masu kewan junansu! A 'bangaren bolaji kuwa duk raunikan dake jikinta sun warke sumul,kuma idan hisham yazo dubata suna d'an ta6a hira,a hirar tasu ne yake tambayarta da cewa 'what's your name,where are you from?,what tribe are you? ,ita kuma sai ta bashi amsa da 'i don't know',Dr.ayuba ne ya tsawatar masa da cewa ' kar ka nemi ka takurata da tambayoyi,ka 'kyaleta kawai,with time memory d'inta zai dawo,kar kace zakayi forcing d'inta by questioning her,let her face the future!',abinda ya rage a yanzu shine raunin fuskarta wanda a yau ne za'a cire mata bandejin dake d'aure a fuskarta! ¤¤¤ Dr.ayuba ya dubi hisham tare da cewa 'hisham akwai matsala fa dangane da fuskar yarinyar nan,her face is totally ruined and disfigured,her face looks scary' ,hisham cike da tausayawa,muryarsa a raunane yace 'ayuba ya za'ayi ,nifa lamarin yarinyar nan ya fara d'aure min kai,ga memory loss ,ga kuma wannan batun na fuska,nifa kawai zan had'ata da yan sanda,su kaita media akai cigiyarta ko danginta zasu bayyana',Dr ayuba yayi jim sannan yace 'hisham ka tuna fa cewa babu ta yadda za'a samu information akanta cause bata san wacece ita ba,kuma fuskarta is totally damaged,babu wanda zai ganeta ko da an kai cigiyarta media,danginta bazasu ta6a ganeta ba,hisham ka d'auka cewa kawai kaddara ce ta had'aka da yarinyar nan,kar ka gajiya ,kuma kar ka karaya,ka cigaba da taimakonta kar ka fasa,insha Allahu bazakayi dana sani ba,da zarar tayi regaining memory d'inta komai zai zo 'karshe insha Allahu',hisham yace 'yaushe zatayi regaining memory d'in?,yau ko gobe?,no one knows',dr ayuba ya dafa kafad'arsa yace 'kayi ha'kuri hisham,ALLAH na nan,mucigaba da addu'a kawai,kuma batun fuskar nata, why not kayi registering d'inta a N.G.O d'in da kake aiki,in Allah yasa an dace,sai kaga sunyi sponsoring d'inta,an tura ta abroad anyi mata surgery d'in',hisham ya sauke ajiyar zuciya yace 'zan jaraba in gani,may ALLAH see us through!',Dr.ayuba ya amsa da 'amin!' A haka suka nufi d'akin da bolaji take,a lokacin da hisham yayi tozali da fuskarta,a razane ya kauda kansa ,yana mai fad'in 'hasbunallahu wa ni'imal wakil!' ya tsorata matu'ka ga yadda fuskarta ya malkwad'e! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~36~ Hisham a d'imauce yace 'ayuba bangane ba',Dr ayuba yace 'toh dai a yadda bincikenmu ya nuna,ta buge akanta wanda hakan ya janyo brain d'inta ya samu matsala ,hakan kuma ya haifar mata da memory loss ' ,Hisham a sanyaye yace 'innalillahi wa inna illaihi raji'un,toh ni ya zanyi da ita,ni dana ke fatan ta murmure ta warke ,in ji labarinta da asalinta,saboda in sadata da garinsu da danginta!',sannan ya cigaba da cewa 'kuma fa har yanzu ban sanarwa dad da hajiya anything about her fa,basu ma san komai ba akan kawota asibiti danayi ba,its only my driver bala that know's about all this',Dr.ayuba ya gyara zamansa yace 'hisham ba wai fa tayi loosing memory d'inta forever bane,kuma naga tana fahimtar turanci,i spoke to her with english and she answered,ko nurses da turanci suke having conversation,so kaga some part of her memory tayi loosing,wanda muke fatan with time zatayi regaining sauran memory d'inta' ,hisham ya sauke ajiyar zuciya yace 'toh ayuba,ALLAH yasa memory d'in ya dawo gaba d'aya!',hisham ya mi'kawa dr.ayuba hannu sukayi musabaha ,yana mai cewa 'godiya nake Dr ,Allah yasaka da alkhairi'.Dr.ayuba yace 'amin and never mind hisham',hisham ya amshi bill ya fice daga ofis d'in ya wuce gun cashier yayi clearing bills ,sannan ya le'ka d'akin da aka kwantar da hashim ya jajantawa su fulani,ya fito ya le'ka d'akin da bolaji ke kwance fuska d'aure da bandeji ,bacci ya taddata tanayi hakan yasa ya tofa mata addu'o'i, ya fito daga d'akin tare da ficewa daga asibitin ya wuce gun aikinsa! Bayan sati biyu,aka rubutawa su maimartaba takardar sallamar hashim ,suka kwasheshi suka dawo dashi fada, ana kuma tsammanin jiran ranar da zai farfad'o! Dakinsa da bolaji aka kwantar dashi,inda fulani ta umarci hadimai da su had'a duk wani kayan bolaji su had'esu gu d'aya su saka a wardrobe su rufe! Aka cigaba da zaman makokin bolaji,hashim kuma yana kwance,tamkar kayi masa magana ya amsa! Kwanaki suka cigaba da tafiya ,a yayin da 'kawance na gamon jini ya 'kullu tsakanin funmilayo da nawwara,sai kuma soyayya mai 'karfi tsakanin nawwara da bamidele da suke gudanarwa ba tare da fulani ta lura ba,domin ita a yanzu takan lafiyar d'anta take wanda ke kwance tamkar matacce! A yau takama sadakar arba'in wato kwana arba'in da binne gawar da fulani ta kawo a matsayin gawar bolaji,kuma a yau ne su MD,bamidele dasu iya folake da funmilayo zasu koma osun state! Maimartaba ya had'a masu sha tara na arziki,nawwara da funmilayo da 'kyar aka raba su, suna kukan rabuwa ,haka zalika bamidele ya d'aukarwa nawwara al'kawari akan cewa zai dawo da magabatansa su nema masa auranta,kuma sunyi musayar lambobin juna,a haka suka rabu da mutanen fada suna masu kewan junansu! A 'bangaren bolaji kuwa duk raunikan dake jikinta sun warke sumul,kuma idan hisham yazo dubata suna d'an ta6a hira,a hirar tasu ne yake tambayarta da cewa 'what's your name,where are you from?,what tribe are you? ,ita kuma sai ta bashi amsa da 'i don't know',Dr.ayuba ne ya tsawatar masa da cewa ' kar ka nemi ka takurata da tambayoyi,ka 'kyaleta kawai,with time memory d'inta zai dawo,kar kace zakayi forcing d'inta by questioning her,let her face the future!',abinda ya rage a yanzu shine raunin fuskarta wanda a yau ne za'a cire mata bandejin dake d'aure a fuskarta! ¤¤¤ Dr.ayuba ya dubi hisham tare da cewa 'hisham akwai matsala fa dangane da fuskar yarinyar nan,her face is totally ruined and disfigured,her face looks scary' ,hisham cike da tausayawa,muryarsa a raunane yace 'ayuba ya za'ayi ,nifa lamarin yarinyar nan ya fara d'aure min kai,ga memory loss ,ga kuma wannan batun na fuska,nifa kawai zan had'ata da yan sanda,su kaita media akai cigiyarta ko danginta zasu bayyana',Dr ayuba yayi jim sannan yace 'hisham ka tuna fa cewa babu ta yadda za'a samu information akanta cause bata san wacece ita ba,kuma fuskarta is totally damaged,babu wanda zai ganeta ko da an kai cigiyarta media,danginta bazasu ta6a ganeta ba,hisham ka d'auka cewa kawai kaddara ce ta had'aka da yarinyar nan,kar ka gajiya ,kuma kar ka karaya,ka cigaba da taimakonta kar ka fasa,insha Allahu bazakayi dana sani ba,da zarar tayi regaining memory d'inta komai zai zo 'karshe insha Allahu',hisham yace 'yaushe zatayi regaining memory d'in?,yau ko gobe?,no one knows',dr ayuba ya dafa kafad'arsa yace 'kayi ha'kuri hisham,ALLAH na nan,mucigaba da addu'a kawai,kuma batun fuskar nata, why not kayi registering d'inta a N.G.O d'in da kake aiki,in Allah yasa an dace,sai kaga sunyi sponsoring d'inta,an tura ta abroad anyi mata surgery d'in',hisham ya sauke ajiyar zuciya yace 'zan jaraba in gani,may ALLAH see us through!',Dr.ayuba ya amsa da 'amin!' A haka suka nufi d'akin da bolaji take,a lokacin da hisham yayi tozali da fuskarta,a razane ya kauda kansa ,yana mai fad'in 'hasbunallahu wa ni'imal wakil!' ya tsorata matu'ka ga yadda fuskarta ya malkwad'e! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:28 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~37~ ¤¤¤ Fulani jiki a sanyaye ta shiga d'akin da Nawwara take,bayan ta nemi guri ta zauna akan couch[kujera],sai ta d'aga kai ta dubi nawwara dake zuba kayan cikin akwati! A sanyaye fulani ta kira sunanta,nawwara ta amsa da 'na'am' tana mai cigiba da sa kaya a cikin akwati ,fulani ta cigaba da cewa 'magana nazo nayi dake mai muhimmanci,amma kuma tukunna dai,naga kina had'a kaya,na meye?' ,nawwara ba tare da ta dubeta ba tace'gidanmu zan koma',fulani tace 'gida kuma nawwara,ni a ganina lokaci yayi da za 'a d'aura aurenki da hashim,saboda babu wanda ya cancanci ya kula dashi a halin da yake ciki a yanzu sai matarsa,kinga kenan yanzu ne zaki nuna masa so ta hanyar aurensa,ki bashi kulawa ,ki tsarkake shi da kuma sauran abubuwa,nagaji da ganin hadimai suna masa wannan aiki' ,nawwara ta tsaya cak tana duban fulani galala,sannan tayi murmushi tace 'ni kuyanga nawwara ce ta dace da wannan aikin ko?' sannan ta cigaba da cewa' soyayya da aure manya,kinga umma nifa banta6a son yaya hash ba,kawai na amince zan aureshi saboda kinyi min tayin aurensa a lokacin da bani da wani tsayayye,kuma ko da ace a yanzu zan auri yaya hash,toh wallahi bazan aureshi ba,mutumin dake kwance tamkar gawa,in aureshi in ce na auri wa ? Matacce?' ,fulani a fusace ta mi'ke tsaye tana cewa 'uwarki zaki aura,kaga yar iskar yarinya,ni zakiyi wa halin 'yan duniya?' ,nawwara ta amsa da cewa 'menayi miki?,dan na fad'a miki ra'ayina sai kiga ba'ki na,aure ne dai bazan auri yaya hash ba,kuma babu uban da zai tursasani in aure shi,ko da kuwa iyayena ne,kuma nasan cewa baza su ta6a tursasa ni akan in aikata abinda zuciyata bata so',nawwara ta zuge zip d'in akwatinta tana cewa 'in dai yaya hash ne, akai kasuwa ,ni dai nawwara bana so',fulani sauran 'kiris ta saki fitsari amma haka ta daure ta cije ,murya a sanyaye tace'nawwara kar ki min haka mana,kin san cewa fa duk abinda na aikata ,na aikata ne saboda cikar burinki na mallakar hashim...' ,nawwara tana yafa mayafi ta katseta ta hanyar cewa 'cikar burina ko kuma cikar burinki,kinga nifa dan Allah kar ki cika da surutu ,wai ana dolene,indai yaya hash ne bana so ,akai kasuwa,ko kuma ki aura masa kwarkwarori tunda ga kunyagai nan birjik a fada',fulani ta dafe kanta tana cewa 'na shiga uku','baki shiga komai ba tukun ,sai ranar da asirinki ya tonu,a ranar zaki shiga miliyan uku ,ba uku ba',fulani ta dubi nawwara tana nuna kanta da yatsa ,tace'ni kike jifa da irin wad'annan kalaman,nawwara ni?' ,nawwara ta kya6e baki tana gyara zaman hand bag d'inta a hannunta tace 'ke wacece? Ba kowa bace ke face makira,muguwa,mara imani da tausayi,shed'aniya,kuma insha Allahu sai Allah yayi mana katanga da kaidinki' ,fulani a fusace ranta a 6ace ta d'aga hannu zata kwashe fuskar nawwara da mari,nawwara tayi caraf ta ri'ke hannunta,tana mai girgiza kanta tace 'kar ki kuskura hannunki ya ta6ani da sunan duka,domin zan manta duk wata ala'ka dake tsakanin mu,in zage damtse in narka miki na jaki,dan haka ki kiyaye',sannan ta watsar da hannun fulanin,ta kuma nunata da yatsa tace 'kuma ina son in sanar dake cewa ,nan ba da jimawa ba insha Allahu , zan zamo mata ga bamidele' ,fulani murya na rawa tace 'ba....mu....ge...le?' ,nawwara ta amsa mata da cewa 'bamidele! yayan bolaji' ,fulani tana kifkifta idanuwa tace 'nawwara YARE zaki aura? Jinin oduduwa? Masu kashi a leda' ,nawwara ta amsa mata da cewa 'ke kika san wannan',fulani tace 'wallahi tallahi sai kinyi danasanin butulcin da kike shirin yi a gareni,sai na... ' ,nawwara ta katseta ta hanyar d'aga mata hannu tana cewa 'dakata! Butulci na nawa kuma,wallahi tallahi a shirye nake in tona asirinki ,in har kikayi 'yun'kurin 'bata lamarin aurena da bamidele,kuma ni zan nuna miki cewa ni 'yar zamani ce mai tarin sababbin kaidi,so inason ki iya takunki kawai ,ki 'kyaleni in auri za6in raina,ke kuma ki cigiba da rayuwarki a fada asirinki a rufe ,kafin ranar da za'ayi wal'kiya' ,nawwara taja akwatinta tayi hanyar fita daga d'akin,saida ta takai bakin 'kofa ta juyo tace 'wallahi nayi danasanin biye maki wajen aikata abinda muka aikata ga 'kanwar masoyina,kuma fa kar ki d'auka cewa bazan iya fasa 'kwai ba,kawai rashin sanin inda take ne a halin a yanzu zai hanani aikata hakan,kuma fasa 'kwan yana nufin kawo nakasu ga ala'kar mu da funmilayo da kuma masoyina' ,nawwara tayi dariya tace 'umma,amma ki rubuta ki ajje ,in har bolaji tana raye,kuma tana numfashi,toh ki sani cewa zata dawo da izinin Allah,kuma sai kin gama girban abinda kika shuka,duk da a yanzu ga d'an naki da kike balo'ko'ko akansa a kwance tamkar matacce,wannan kad'ai ya isheki ba'kinciki ayanzu,bisallam,sai kuma na kawo miki katin gayyatar aurena da muradin raina' ,nawwara bata jira amsarta ba ta fice janye da akwati,ba tare da tayiwa kowa sallama ba,ta fice daga fada,tayi shatar taxin da zai kaita gidan iyayenta! Fulani kuwa sulalewa tayi 'kasa wanwar akan mazaunanta,ta d'ora hannu aka tana cewa 'chai! Nawwara kin kasheni,kin gama dani!' ¤¤¤ Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:28 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~38~ Misalin 'karfe 10:00am na safe ,Zahra ri'ke da 'karamar jakar matafiya tana mai zubawa Hisham shagwa6a tana cewa 'yaya sham zamuyi missing d'inka wallahi,hope bazaka jima ba zaka dawo' ,hisham yayi murmushi yace 'zahra kenan,insha Allahu da zarar na kamalla abinda naje yi a can zan dawo' ,zuhra tace 'toh yaya Allah ubangiji ya taimaka,ya kuma tsare mana kai',zahra da hisham suka amsa da 'amin',a haka suka 'karasa main parlour inda Dad da hajiya ke zaune! Dad ya dubi hisham yana cewa 'har ka fito zaka wuce' ,hisham ya russuna yana cewa 'yes Dad ,12:00o'clock flight ne',hajiya ta dubeshi tace 'shine zaka tafi tun yanzu ,ka bari sai sha d'aya mana',hisham yana murmushi yace'hajiya zan biya office ne inyi clearing wasu files,daga can zan wuce',hajiya tace 'toh shikenan hisham Allah ya tsare ya kuma kiyaye,ALLAH kuma ya bada sa'a',Dad ya amshe da cewa'ALLAH kuma ya nuna mana ranar aurenka musha biki',hajiya dasu zuhra suka amsa da 'amin' suna dariya,hisham kuma sai sosa 'keya yake ,sai kuma jikinsu yayi sanyi dan tunowa da marigayiya mujiba,hakan yasa dariyar dake kan fuskarsu ya gushe,suka taru suka mata addu'a,sannan hisham yayi sallama dasu ya tashi ya fice harabar gidan, inda bala direba ke jiransa,zuhra da zahra suka masa rakiya zuwa bakin mota,bayan hisham ya shiga motar,bala ya tada mota ya fice bayan maigadi ya bud'e masu gate! [YABO CITY HOSPITAL] suka zarce bisa umarnin hisham! ¤¤¤ Dr ayuba ya mi'kawa hisham hannu sukayi musabaha sannan yace 'har zaku wuce ne?',hisham yace 'eh ina patient din taka take, ta fito mu tafi kar muyi missing flight',Dr.ayuba yace'na tura nurse taje ta taho da ita' sannan ya cigaba da cewa'a gaskiya hisham kayi namijin 'kokari sosai akan yarinyar nan wand Allah kad'ai ne zai biyaka' ,hisham yayi murmushi kawai,Dr.ayuba ya cigaba da cewa 'ALLAH ubangiji yasa ayi surgery d'in sucessfully,ba tare da an samu wani matsala ba',hisham ya amsa da 'amin' sannan yayi 'kwafa,fuskarsa d'auke da alamun tausayi yace 'ayuba nifa matsalata itace ,idan anyi surgery d'in mun dawo yaya zanyi da ita? ,ina zan kaita?' ,Dr ayuba ya dafa kafad'ar hisham yace'why not ka kaita gidanku kawai,in yaso sai ka yiwa su hajiya bayani kawai,nasan cewa bazasu 'ki ba,they will understand,tunda taimako ne they won't mind,kuma zamanta tare daku na d'an lokacine da zarar tayi regaining memory d'inta,shikenan fa' ,hisham ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa 'amma baka ganin cewa za'a samu....' shigowar Bolaji sanye da farar doguwar riga,kanta rufe da 'karamin hijab,tare da nurse ne ya katsewa hisham zancensa! Dr ayuba ya dubi bolaji wacce kanta ke sunkuye ,fuskarsa d'auke da murmushi yace'my patient,your flight is 12oclock,so you will be leaving by now,i wish you sucess',bolaji ta amsa da cewa 'thank you doctor,may Allah reward you!,sannan ta kai dubanta ga hisham tana cewa' likewise brother hisham i really appreciate your effort for giving me the chance to live again,although i don't really know who i am or know anything about my past,i have no words to express my gratitude towards you ',Dr.ayuba yayi murmushi ya katseta ta hanyar cewa 'the pleasure is mine,and my job is to save lives,so don't mind' ',hisham ya tashi ya amshi jakar kayanta[shine ya siya mata su] dake hannun nurse d'in da suka shigo tare,sannan ya dubi bolaji yace ' enough of the pleasantries ,shall we' yana mai nuna mata 'kofa! A haka bolaji tayi sallama da ma'aikatan asibitin,suna masu mata fatan alkhairi a rayuwa tare da mata fatan samun lafiya! Hisham yayi clearing duk wani bill ,sannan suka fice daga asibitin! ¤¤¤ Misalin 'karfe 12:05 jirgi ya d'aga dasu bolaji da hisham izuwa 'kasar america! Ko da jirgi ya sauka a filin AMERICAN AIRPORT,motar da aka turo daga N.G.O na Bieng human ne ,ya wuce da su 'GREENFIELD HOSPITAL ' dake Los angeles! ¤¤¤ Note: ga masu min comment da 'tnx' 'cgb' and 'nyc' please ku daina, bana bu'kata. ,all i want is for us 2 discuss about each chapter i posted,like what do u expct 2 happen next and what do u tink abt the chapter and so on,hakan zaisa in samu courage da zeal wajen ganin na 'kara 'kaimi gun posting a kai akai! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:29 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~39~ Suna isa asibitin[GREENFIELD HOSPITAL] , guest reception suka nufa,anan suka gabatar da salloli ,suka ci abinci ,sannan suka shiga cikin asibitin don ganin likitan da zai yiwa bolaji surgery! Dr.Nassif albert shine surgeon d'in da zai yiwa bolaji surgery,d'an asalin nigeria ne,haifaffen garin jos,ba musulmi bane,amma bahaushen jos ne,karatu ne ya kawoshi 'kasar america,bayan ya kamalla karatunsa,sai yayi housemanship d'insa a asibitin greenfield,daga nan sai suka ri'keshi saboda 'kwazonsa da haza'karsa,a yanzu haka shine 'kwararren plastic surgeon da asibitin ke ji da ta'kama! Kasancewar Dr.nassif yasan da zuwansu hisham da bolaji ,hakan yasa basu sha wahalar ganinsa ba,saboda duk wani info da details akansu, N.G.O [bieng human] sun riga sun turo asibitin,hatta kud'in aikin da za'ayi mata sun riga sun biya! Bayan Sun shiga wawakeken office d'in dr.nassif,sai Hisham ya mi'kawa Dr nassif hannu suka gaisa,dr.nassif fuskarsa d'auke da fara'a ya dubesu yace'you may sit down please' yana mai nuna musu kujera ,bayan sun zauna ,sai dr.nassif ya dubi bolaji wacce fuskarta ta malkwad'e yace 'maam! can we go over there so that i can examine your face' ,yana mai nuna mata wani gadon marasa lafiya dake cikin ofis d'in,bolaji ta mi'ke a sanyaye ta nufi gun gadon ta zauna,Dr.nassif ya sanya plastic gloves a hannunsa ,ya 'karasa gunta ya fara dube dubensa da gwaje gwaje akan mal'kwad'ad'd'iyar fuskarta da fulani tayiwa aika aika ,har na tsawon minti 30! Bayan dr.nassif ya gama wasu rubuce rubuce akan wani takarda,sai ya d'ago ya dubi bolaji sannan ya sauke idanunsa akan hisham yana mai cewa 'the surgery will take place by 8:00am tommorow morning and i hope you bring along the picture of the face we will be using for her surgery' ,hisham cike da mamaki yace 'picture? What picture?',Dr nassif ya cire spec d'insa yana cewa 'hisham ko?' ,hisham ya amsa da 'eh' ,dr.nassif ya jinjina kansa sannan ya cigaba da magana cikin harshen hausa wacce ke fita daga bakinsa tamkar turanci yana mai cewa'hisham ya zama dole ayiwa fuskarta total change over,cause her face is totally ruined and disfigured,ba ta yadda za'a iya gyara wani 'bangaren abar wani 'bangaren,saboda haka ya kamata muyi amfani da hoton fuskarta na asali yayin da zamuyi mata aikin!' bolaji ta 'kurawa bakin dr.nassif idanu kasancewar batajin me yake fad'a! Hisham ya goge gumin da ya feso masa akan goshi yana mai furzar da huci ,yace 'tir'kashi,likita akwai matsala fa,ita kanta bata san fuskarta ta asali ba,ballantana ni d'an rakiya',cike da mamaki dr nassif yace 'how comes?' ,a take hisham ya labarta masa lalurar bolaji na memory loss!' cike da tausayawa Dr nassif yace 'what a pity!' ,sannan ya cigaba da cewa 'toh babu matsala,za'a iya using wani face d'in for the surgery,in har kun amince' ,a take Dr.nassif ya bud'e drawer ya ciro wani 'katon album mai d'auke da hotuna ya mi'kawa hisham yana cewa 'ga album nan,kuje ku duba kuyi shawara ku za6i hoton fuskar da za muyi amfani dashi for her surgery',sannan ya dubi bolaji yace 'kar ki damu....' ,bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'i beg your pardon',hisham yayi murmushi yace 'doctor bata jin ko wani YARE a yanzu sai turanci',Dr nassif yace'oh sorry' cikin harshen turanci yayi mata bayani dalla dalla,bolaji tayi jim sannan tace 'no problem,i don't mind doctor,i will be okay with any face you use,all i want is to look good,i don't want to look scary anymore! A haka sukayi sallama,suka tafi! Masaukin da N.G.O ta tanadar masu aka kaisu! Bayan sun idar da sallar isha,sai hisham ya d'auko album suka fara dubawa shi da bolaji,yawanci hotunan arnan y'an matan black america ne da south africa,babu hoton musulma ko d'aya,a haka dai bolaji ta yanke hukunci ta za6i hoton wata black america! hisham ya dubeta yace 'are you okay with it' ,'yes i'm okay with it' ta bashi amsa ,hisham ya kwa6e baki yace 'alright then,since you are ok with it,no qualms',bolaji a sanyaye tace 'what about you?',hisham ya amsa da cewa 'i have no option,it's your face not mine,i only pray that the surgery would be done sucessfully!' Kasancewar suite[masauki] d'in yana d'auke da room and parlour da kuma toilet,hakan yasa hisham yayi kwanciyarsa akan kujerar falo,ita kuma bolaji tayi masa sai da safe ta wuce d'aki ta kwanta,tana mai yiwa hisham addu'a a ranta ,wanda tayiwa la'kabi da 'MY LIFE!' ¤¤¤ Washegari misalin 'karfe 8:30am Dr.nassif da sauran surgeons suka shigar da bolaji theatre! Hisham yana zaune akan restchairs dake jere a harabar gaban theatre d'in,yana mai cewa a zuciyarsa 'ta ya za'a sanyawa yarinyar nan fuskar arniya bayan kuma tana musulma ,gaskiya da sake','kana da hoton fuskar musulmar da za'a sanya mata in har ba internet zaka hau ka nemo ba',zuciyarsa ta bashi amsa! Wayarsa ya ciro daga gaban aljihunsa wanda hakan yayi sanadiyar fad'owar wallet d'insa,hannu yasa zai d'au wallet d'in,sai idanunsa suka masa tozali da hoton dake jikin wallet d'in! Written by :ABDULAZIZ iLILEE ISMA'IL [10/17, 8:29 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~40~ Murmushi ne ya su6cewa hisham,ya d'au wallet d'in,ya zare hoton yana mai cewa 'ALHAMDULILLAH ,bazan ta6a danasanin bada hoton fuskarki a sanya mata ba',zuciyarsa ce ta tunatar da shi cewa 'taya zaka bada hoton nan,bayan an riga an shigar da ita theatre,wata 'kila ma sun fara surgery.....',fitowar Dr.nassif daga theatre yana sauri ne ya katsewa hisham zancen zucin da yake,cike da hanzari hisham ya tareshi yana mai cewa 'doctor any problem?' ,Dr.nassif yayi murmushi yace 'no prolem at all,zanje office in d'auko hoton da zamuyi using for the surgery,i forget to pick it',hisham da sauri ya mi'kawa Dr.nassif hoton dake hannunsa yana mai cewa 'doctor ga wannan,ayi amfani da fuskar dake kan hoton please',Dr nassif ya amshi hoton ya duba yana cewa 'kana ganin babu matsala,kar ka manta cewa ta riga ta za6i hoton fuskar da za'a saka mata' ,hisham yace 'babu matsal doctor,i will explain everything to her after the surgery',Dr.nassif yace 'alright then,dafatan kuma wacce ke jikin hoton nan bata raye,domin ko hotunan fuskokin matan dana baku ku za6a,duk matattu ne' ,'eh wallahi bata raye,'yar uwata ce' hisham ya bashi amsa,Dr.nassif ya sauke ajiyar zuciya sannan yace 'alright it's ok,we will try our maximum best to make her face look exactly like this!',ko da dr.nassif ya gama fad'in haka,sai ya juyo ya koma theatre hannunsa ri'ke da hoton da hisham ya bashi! ¤¤¤ A 'bangaren Fulani tun bayan tafiyar nawwara, duniya tayi mata zafi,rashin farfad'owar hashim yana matu'kar d'aga mata hankali,musamman idan ta kalleshi taga yadda hadimai ke juyashi suna masa hidima tamkar matacce,a kullum Dr.ayuba yazo ya dubashi,amsa d'aya yake basu ''ku cigiba da addu'a,kar ku gajiya,at any time zai iya farfad'owa if Allah permits' ,maimartaba ya sa an tara malamai sunyi saukar al qur'ani mai girma,amma jikin hashim sai godiya,yana kwance tamkar gawa,zuciyarsa kad'ai ke bugawa a jikinsa,idanunsa bud'e kamar kayi masa magana ya amsa! A kullum fulani zama take a d'akinta tana risgar kuka tana mai cewa'danasani na barka da matarka ban raba ku ba,gashi nayi sanadiyar shigarka wannan mawuyacin hali,wanda da wuya ka sami macen da zata aureka,ta kuma yi d'awainiya da kai tsakani da Allah,wallahi na tabbata da bolaji tana fadar nan,babu abinda zai hanata d'awainiya da kai,duk da bata sonka,amma zata tausaya maka ,kuma kaci arzikina a gunta,ko kasancewarka mijinta zai sa taji tausayinka tayi d'awainiya da kai,ba tare da ta gajiya ba',wani lokacin kuma sai ta zabga uban tagumi tana zancen zuci kamar haka 'ina zan ganki bolaji,tayaya zan fara nemanki,bayan na tabbatarwa da duniya mutuwarki,kaicona ! Kaicona! Tir da mugun hali irin nawa,meye aibun bolaji?' 'zamantowarta YARE shine aibunta' zuciyarta ta bata amsa! Sultan kuwa ya fawallawa Allah lamuransa gaba d'aya,yayi watsi da mugun d'abi'arsa na neman mata,a yanzu haka yana aiki a [MODIBBO PETROLEUM] dake jihar sokoto a matsayin Managing director! A kullum idan yayi sallah sai ya nemi gafarar ubangiji,kuma sai yayi addu'a kamar haka'ya Allah ,idan har bolaji tana raye,ya Allah ka kareta da dukkan kariyarka,ya Allah ka bayyana mana ita a raye ko a mace,ya Allah ka tashi kafad'ar mijinta ka bashi lafiya,ya Allah ka tona asirin mahaifiyata!' A 'bangaren nawwara kuwa,soyayyarta da bamidele tayi 'karfi sosai,wanda a yanzu haka iyayenta sun san da zamansa,kuma sun bashi izinin ya turo magabatansa! Ko da Dr.ayuba ya tuntu6i nawwara akan zancen aurenta da hashim,sai ta nuna masa cewa 'ita daman ba son sa take ba,fulani ce kawai ke kid'anta kuma take taka rawarta!' ¤¤¤ *BAYAN WATA 'DAYA DA SATI BIYU* A yau Dr.nassif zai warwarewa bolaji bandejin dake d'aure akan fuskarta! Wata Nurse ce ta mi'kawa bolaji madubi a yayin da dr.nassif ya gama warware mata bandejin,ko da bolaji ta amshi madubin ta kalla,sai tasa hannu tana shafa fuskarta tana cewa 'wow! This face is beautiful',who's face is this? 'bolaji ta tambaya,hisham dake tsaye daga gefenta fuskarsa d'auke da murmushin jin dad'i,ya amsa mata da cewa 'it's MUJIBA'S face' ,'who's she?' bolaji ta kuma tambaya,'my late cousin',hisham ya bata amsa,sannan yacigaba da cewa 'from now on you will be called MUJIBA!',bolaji idanunta suka ciko da 'kwalla ta dubi hisham tana cewa 'i'm out of words,but all i'll say is thank you so much for giving me NEW LIFE! NEW FACE! NEW IDENTITY!,i really appreciate,may Allah reward you',hisham yayi murmushi yace 'the pleasure is mine mujiba,may you regain your memory soon!',a haka sukayi sallama dr.nassif da sauran ma'aikatan asibitin! Washegari misalin 'karfe 4:00pm jirgi ya sauke hisham da bolaji a filin airport d'in sultan bello! Hisham yayi wa bala direba waya yazo d'aukesu ya kaisu gida,cikin minti talatin bala direba ya iso airport ya d'aukesu ya wuce dasu gida,yana mai mamakin ganin fuskar mujiba akan fuskar yarinyar da suka d'auko a daji,a zuciyarsa yana mai jinjinawa hisham! THIS IS JUST THE BEGINING! ! ! Created by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 5:56 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~41~ Bala direba yana yin parking ,hisham da bolaji suka fito daga motar,hisham ya shige gaba,bolaji tana biye dashi,a haka suka nufi cikin gida,bugu d'aya hisham yayi wa 'kofar da zai sadasu da main parlour,zuhra ce ta bud'e 'kofar,ganin hisham ne yasa ta bud'e baki,fuskarta dau'ke da farinciki tace'welcome home yaya',hisham murmushi yayi tare da cewa'thank you',sannan ya shiga falon,zuhra ta bi bayansa ba tare da ta lura da bolaji ba! Hisham ya russuna ya gaishe da Dad dake zaune akan d'aya daga cikin kujerun da suka 'kawata falon,cike da fara'a ya amsa masa,yana mai ajje jaridar da yake karantawa,bala direba ne yayi sallama tare da shigo da kaya,a lokacin hisham ya juyo ya kai dubansa ga 'kofar shigowa falon,yana mai mamakin rashin shigowar bolaji,bala direba ne ya cewa bolaji 'bismillah ki shiga',yayin da yake 'ko'karin fita daga falon bayan ya ajje kayansu,jiki a sanyaye bolaji ta sanya 'kafa a falon,kanta a sunkuye,bakinta d'auke da sallama,hisham ya amsa mata sallamar yana mai cewa'come inside,and feel at home',bolaji ta d'ago kanta tare da watsawa hisham murmushi,a zabure daddy ya mi'ke da yayi tozali da fuskar bolaji,bakinshi na rawa ya furta harafin 'mu...ji...ba!','taratsatsa'!,'karar fashewar glass bowl mai d'auke da fruitsalad,da ya sulale daga hannun hajiya,sanadiyar ganin fuskar mujiba,mamaki,d'imuwa da firgici ya bayyana 'karara akan fuskarta,idanunta kuma 'kyam akan fuskar bolaji,bakinta d'auke da salati,zuhra kuwa wani tsalle ta buga,sai gata a kusa da zahra wacce take tsaye a dinning area,sanadiyar tagama jera abinci akan dinningtable d'in,rungume junansu sukayi,jikinsa na rawa,bakunansu na fad'in 'Allahuma ajirni.....',bolaji da hisham ko kad'an basuyi mamaki ba game da sauyin fuskokinsu hajiya ba,dad ne ya dubi hisham,cike da 'karfin hali yayi nuni ga bolaji da yatsa yana mai cewa'wacece wannan?,daga ina take?',hisham ya amsa masa da cewa'daddy ku zazzauna ku nutsu,in fayyace muku komai akanta',bayan kowannensu ya gayyato nutsuwa ya sanya a zuciya,sai suka zazzauna,a take hisham yayi gyaran murya ya labarta musu komai,tun daga had'uwarsa da bolaji har izuwa yau da suka dawo daga L.A[los angeles]! Hajiya ta sauke numfashi tare da cewa'kana nufin wannan wata ce daban d'auke da fuskar mujiba?',hisham ya amsa da cewa'eh',hajiya ta kama baki tare da jinjinawa lamarin tana fad'in'ALLAH ya kawo mu wani zamani',Dad yayi gyaran murya tare da cewa'ha'ki'ka kayi namijin 'ko'kari wajen ceto rayuwar wannan baiwar Allah,amma kayi kuskure daka sanya mata fuskar mujiba,domin ka 'kara dagula lamirinta gaba d'aya,kuma ga wani hanzari ba gudu ba,taya zamu zauna da ita ba tare da sanin ko wacece ita ba,taya zamu tabbatar da dawowar memory d'inta a duk lokacin da tayi regaining d'inshi,shin ita d'in matar aure ce?, budurwa ce?, Macuciya ce?,yar fashi ce?,karuwa ce?,duk bamu da wannan amsoshin hisham',dad yayi jim tare da kai dubansa ga mujiba yana cewa'd'an adam bashi da tabbas,kar mu zo mu zauna da ita da niyyar taimako,daga baya ta cucemu,ta bar mu da cizon yatsa',hajiya ta tareshi da cewa'alhaji tabbas zancenka dutse,amma ya zama dole ka cire duk wani fargaba daga cikin zuciyarka,tunda dai musulma ce,i shikenan,ALLAH zai dubi alkhairin da muka nufeta dashi,ya kuma ku6utar damu ya kare mu daga duk wani sharri dake tattare da ita',dad yace'shikenan hajiya kin gama magana,ALLAH UBANGIJI ya bata lafiya,ya kuma shiga tsakanin nagari da mugu',hisham ya amsa da cewa'amin',hajiya ta dubi su zuhra,tace'ku tashi ku kaita d'akin mujiba',zuhra ta mi'ke tare da jan hannun bolaji tana cewa'let's go',zahra kuma ta d'auki jakar bolaji da bala direba ya ajje d'azu,suka wuce d'akin mujiba,da ita bolaji,bayan tayi godiya sosai ga hajiya da dad! Dad ya dubi hajiya da hisham yace'toh ya zama dole musa ido ga zaman yarinyar nan a gidannan,kuma dole ta d'inga zama a d'aki,tare da sanya niqab a duk lokacin da zata fita,saboda gujewa had'uwa da wani a cikin dangi,kar a zata mujiba ce ta dawo daga lahira!',hajiya da hisham sukayi na'am da zancen Dad! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 5:57 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~42~ A kwana a tashi asarar mai rai,biki wanda ya amsa sunan biki akayi bayan an d'aura auren bamidele da nawwara,tun daga nan yankin yabo dake jihar sokoto zuwa yankin erin dake jihar osun! Farincikin Mallakar junansu a matsayin ma'aurata ya cigaba da wanzuwa a zukatansu har izuwa lokacin da nawwara ta tare a d'akin aurenta,wato gidansu bolaji! Sai muma muyi musu fatan zaman lafiya da kuma samun zuri'a d'ayyiba,ko da labari da kuma katin gayyatar auren nawwara da bamidele suka riski fulani,ba'kin ciki da takaici ne suka samu wawakaken gurbi a zuciyarta! ¤¤¤ A 'bangaren bolaji[mujiba] tana zaune cikin aminci ,yarda,kauna da tsantsar kulawa tare dasu hisham,babu abinda ta nema ta rasa,a kullum fatansu shine tayi regaining memory d'inta! Hisham yana jindadin yadda zahra da zuhra suka maida bolaji tamkar mujibar asali,hajiya ita kanta tana ji da bolaji,dad kuwa baya nuna banbanci ko kuma wariyar launin jini a tsakaninsu,ya d'auketa tamkar d'iyar cikinsa! Duk wani abu da ya shafi mujibar asali sai da su zuhra suka labartawa bolaji,tun daga rayuwarta a gidansu,soyayyarta da hisham,har izuwa rasuwarta,bolaji ta tausayawa hisham matu'ka,hakan yasa daraja da 'kimar hisham suka 'kara samun matsuguni a zuciyarta! Zuhra da zahra sun yi 'kokarin koyawa bolaji abubuwa dama,domin cikin watanni shida,sun koya mata abubuwa kamar haka YAREn hausa,girke girke,iya kwalliya da sauransu,kuma tare suke fita d'aukan karatu a duk lokacin da malaminsu yazo! Kamar kullum a yau bayan sun gama d'aukan karatu a gun malaminsu,sai suka nufi cikin gida,a falo suka iske hisham yana faman aiki da laptop,zuhra ce ta nufi gunshi tana cewa'yaya sham tunda yau babu inda zakaje,please ka taimaka ka kaimu salon mana',d'agowa yayi tare da cewa'ok zanyi wa bala direba waya yazo ya kaiku',zahra ta 'karasa kusa dashi,a shagwa6e tace'kai muke so ka kai mu,please yaya',hisham ya maida dubansa ga laptop d'insa tare da cewa'ba fa inda zan kaiku,ko ku bari bala direba ya kaiku,ko kuma ku ha'kura',zuhra da zahra a fusace suka mi'ke tare da wucewa d'akinsu suna masu kumburi tamkar alkubus! Bolaji ce tayi 'kasa 'kasa da murya,cikin hausarta mai gauraye da turanci tace'haba my life...',hisham ne ya katseta ta hanyar d'aga mata hannu yana cewa'please mujiba stop refering me as your life',bolaji ta tareshi da cewa'you deserve to be refered as my life,cause you gave me a newlife!',sannan ta cigaba da cewa'duk ba wannan ba,ka taimaka please ka kaimu salon,i'm pleading',hisham cike da si'kewa yace'ohh,i'm done talking,if you won't let bala to take you ladies to the salon,then just forget,cause i ain't driving you ladies to anywhere',bolaji idanunta ya ciko da 'kwalla tace'is this how you treat mujiba even when she pleads?,na san cewa i'm not ur mujiba,but i always try 2 be just like her saboda i'm having her face and name,hisham don't be so mean,just accept the fact that i'm mujiba,and accept my request',hisham ya katseta da cewa 'no! You are not mujiba,you are just who you are,so your request is been decline!',bolaji idanunta jajir,muryarta a da'kile tace'so be it',cike da sassarfa ta wuce d'akinta ,idanunta su na masu zubda hawaye,tana shiga ta ajje qur'aninta akan bedside,sannan ta fad'a kan gado tare da fashewa da kuka tana cewa'why hisham? Why ? ,why are you treating me this way?,why are you punishing my innocent heart?,all i wish for is to replace mujiba in your heart,hisham i love you ,i love you with all my innocent heart!,a fusace ta mi'ke,ta bud'e wardrobe ta ciro album d'in mujiba,ta bud'e tana kallon hotunan mujiba tana cewa'i always try to be just like you,i dress just the way you dressed,i use the perfume you used,i'm living in ur room,i try 2 be like you just 2 get the love of the man that loved you so much,the man that gave me your life,your name,your everything,but he only refuse to give me the love he gave to you ,why?',ta fashe da kuka mai tsuma xuciyar mai sauraro,zahra da zuhra ne suka dafata,cike da tausayawa zahra tace'mujiba don't try to be anyone else,just be your ownself',idanu jajir bolaji ta dubeta tace'my own self?,how can i be my own self,when i don't actually know who i am,all i know is i'm mujiba,i'm living her life,i'm wearing her face,i'm using her identity',zuhra ta rufe mata baki tana mai girgiza mata kai tana cewa'having or living mujiba's life does'nt give u the guarantee to have mujiba's love[hisham]!' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 5:58 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~43~ Zuhra da zahra suka cigaba da bata baki suna masu rarrashinta,ahaka hajiya ta shigo ta samesu,ganinsu a wannan yanayi yasa ta nemi jin ba'asi,a take zahra ta juye mata abinda ya wakana tsakaninsu da hisham,murmushi tayi sannan tace musu'ku je ku shirya,zan sashi ya kaiku',murna fal cikinsu zahra da zuhra suka fice daga da'kin domin suje dakinsu su shirya,hajiya ta dubi bolaji tace'mujiba tashi ki shirya,kin san sha'anin yayan naku wani lokacin sai an had'a da hakuri',bolaji tayi ya'ke tare da sunne kanta tace'alright ma!' Hisham babu yadda ya iya,haka ya ha'kura ya bi umarnin hajiya wacce tace'ka kaisu salon d'in,daga nan ka kaisu shopping,kuma ka jira su ka dawo dasu!' ko da ya kaisu salon d'in,zahra da zuhra suka fice daga motar suka bar bolaji da hisham,bolaji ta d'aga niqab d'inta,murya a sanyaye tace'hisham i'm sorry,nasan na 'bata maka rai d'azu,kayi ha'kuri ,i will never call u my life again,i will try my possible best to be myself',ganin bai da niyyar tanka mata,hakan yasa tasa hannu ta bud'e murfin motar ta fice,bayan ta sauke niqab d'inta! Bayan awanni uku,suka fito daga salon d'in,kowaccensu an mata gyaran gashi! YABO CITY MALL! hisham ya wuce dasu,bolaji kuwa ta saki ranta,ita dasu zuhra suka fara zagaye mall d'in,suna d'aukar abinda ransu ke so,suna jefawa cikin shopping basket,suna cikin zagayen ne,sai bolaji ta hango wasu love themed frames masu shegen kyau,barin su zuhra tayi a bangaren chocolates,ta nufi gun frames d'in,ta fara d'agasu tana dubawa,tana mai yaba kyawunsu a zuciyarta,wani d'an 'karamin red frame mai d'auke da rubutun love quotes ne yaja hankalinta,hakan yasa tasa hannu d'aya ta d'auko frame d'in, tana mai d'aga niqab d'inta da d'aya hannunta,ta fara karanta love quotes d'in tana murmushi,'wow! What a beautiful face',da sauri bolaji ta kai dubanta ga inda maganar tafito,wani matashin saurayi ne idanunta sukayi mata tozali da,fuskarsa d'auke da murmushi,ya jefata da wani irin kallo tare da cewa'a gaskiya kina da kyau',da sauri bolaji ta saukar da niqab d'inta tare da ajje frame d'in a mazauninsa,'tabbas kyawunki ya cancanci a killaceshi a cikin niqab', murmurshi mai sauti yayi tare da cigaba da cewa'zan so sanin sunanki,in da hali in samu address d'inki ,cox bazan so ki su'buce mini ba',bolaji bata tanka masa ba,ta juya da niyyar barin wajen,dakatar da ita yayi ta hanyar cewa'idan ke bazaki fad'a min sunanki ba,toh ni sunana ABBAS ATTAHIRU MODIBBO,kuma...',wani irin muguwar fad'uwar gaba ne ya riski bolaji,wanda ita kanta ba ta san dalili ba,da hanzari ta bar gun ba tare da ta tsaya jin sauran zancen nasa ba, 'karasawa tayi gun su zuhra,suka cigaba da siyayyarsu,bayan sun kamalla,sun je biyan kud'in,cashier ta nuna masu abbas tare da cewa'he has clear ur bills',sannan ta mi'kawa bolaji wani gift pack tare da cewa'this is for you',bolaji ta figi ledar siyayyarsu ta fice,zuhra ce ta amshi gift pack d'in,tare da d'agawa abbas hannu tace'thanks!',a mota zahra take tambayar bolaji ina ta san waccen had'ad'd'en gayen,ganin bata samu fuska ba yasa ta gimtse maganarta,zuhra ce ta rad'awa zahra cewa'ke malama,kiyi mana shiru,sanin kanki ne fa idan yaya ya san cewa wani ne ya biya kud'in kayannan,toh tabbas mun gama kad'ewa!' Ko da suka koma gida,bolaji ta zurfafa cikin kogin tunanin abbas,wanda ta rasa dalilin da yasa take jin fad'uwar gaba a duk lokacin da ya fad'o mata a rai! Hannu tasa ta janyo Gift pack d'in da zuhra ta bata,tana farkewa idanunta suka mata tozali da frame d'in data d'auka tana karantawa d'azu a mall,murmushi ne ya su6ce mata wanda bata san dalilinsa ba,rungume frame d'in tayi tana mai jin wani irin nutsuwa a tattare da ita! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 5:58 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~44~ Hisham yasa hannu ya fisge frame d'in daga hannunta, yana mai cewa'tun d'azu nake sallama,amma kin kasa amsawa saboda shagaltuwa da wannan',sannan ya kai duba ga frame d'in yana mai karanta rubutun dake rubuce a kai,yana gama karantawa ,ya had'e girar sama da 'kasa yana mai tambayar bolaji a fusace yana mai cewa'who the hell gave u this?',bolaji ta tsurawa fuskarsa ido tana mai mamakin sauyawarshi,ganin bata da niyyar bashi amsa,hakan yasa ya 'kara maimata tambayarsa a gareta,murmushi tayi tare da cewa'it was given 2 me by sme1 special,sme1.....',a fusace hisham ya dakatar da ita ,ta hanyar buga frame d'in a 'kasa,ya kuma sa 'kafa ya tattakeshi,har sai da frame d'in yayi rugu rugu,sannan ya nunata da yatsa yana mai cewa'this should be the first and the last time',sannan yasa kai ya fice daga d'akin,ya bar bolaji da tambayar kanta 'wai me hisham yake nufi ne?' Rashin samun amsa yasa ta tattara batunsa ta watsar! ¤¤¤ Sultan ya dubi ummu yana mai cewa'ummu naga matar aure fa',cike da zumud'i ummu tace'wacece ita?,a ina take?',sultan ya amsa da cewa'ban san sunanta ba,ban kuma san a inda take ba,a shopping mall na ganta',ummu ta jinjina lamarin tana mai cewa'lallai,abin naka azimun ne,baka san komai akanta ba,kake kuma cewa kaga matar da zaka aura,kai baka tunanin ko ita d'in matar aure ce?',da hanzari sultan ya tareta ta hanyar cewa'ni dai a gaskiya jikina ya bani ita d'in ba matar aure bace...',shigowar fulani ne yasa sultan yayi gum da bakinsa,ummu ce ta dubeta tana mai cewa'yawwa kin zo a daidai,d'an nawa fa ya ga matar aure','uhm 'yar wacce YAREN ya gano?',fulani ta tambaya bayan ta zauna,ummi ta bata amsa da cewa'ina ko zai sani,matar da ko sunanta bai sani ba',fulani tace'aww kice dai yaga matar gaibu,ALLAH shi kyauta',sannan ta cigaba da cewa'kowa da abinda ya dameshi,ni ta lafiyar d'ana nake,ya Allah ka tashi kafad'ar souldear',sultan ya amsa da 'amin' a zahiri,amma a zuciyarsa yana mai tir da halin mahaifiyarsa tare kuma da addu'ar 'ALLAH ya bayyana bolaji'! ¤¤¤ Fushi mai tsanani hisham yake da bolaji,tsakaninsa da ita gaisuwa,hakan kuwa ba 'karamin d'agawa bolaji hankali yayi ba,domin a da can ko ba komai yana shiga tsabgoginta,yanxu kuma yayi uwar watsi da lamarinta! Kamar kullum 'karfe 5:00pm hisham ya dawo daga ofis a gajiye,saboda sun yi aikin zuwa gidajen marayu domin basu tallafi daga N.G.O d'insu!,ganin babu kowa a falon yasa ya d'aga murya yana mai kiran zahra da zuhra,bolaji ce tafito daga d'akinta tana cewa'sannu da zuwa yaya,how's ur day?','fine' ya bata amsa a gajarce ,bayan ya zaune yana loosening necktie d'insa,'ina su zuhra?',ya tambayeta,'sun fita tare da hajiya' ta bashi amsa,hannu ya d'ora akan goshinsa yana mai cewa 'ohh i forgot,yau aka fara bikin cousin bara'atu',bolaji tace'yes they went 2 the wedding function',sannan ta wuce kitchen ta d'auko ruwa da fresh apple juice mai sanyi daga fridge ta jera akan tray ta had'a da cup ta kawo falon,ta tsiyaya masa ruwa a cup ta mi'ka masa tana mai cewa'i knw u must be thirsty and tired',ya 'karba ya shanye tas,sannan ta tsiyaya masa fresh apple juice tana mai cewa'can i ask u a question?',sai da ya shanye juice d'in sannan ya amsa mata da cewa'ask!', 'why do u broke the frame u saw me wit that day,and why are you still upset with me?'bolaji ta tambaya tana mai 'kura masa idanu,'cos u r like a sister 2me,i want u 2 focus on regaining ur memory,i dnt want u 2 start having boyfriends or any other sort of love relationship' ya bata amsa yana mai shan mur,murmushi bolaji tayi tare da cewa'whether i gain my memory or not,dole ne inyi aure,i'm woman,bazan dawamma a haka ba',hisham ya tare ta da cewa'wato kina nufin kenan aure kike so?',bolaji ta amsa da cewa'ko kad'an ba nufi na kenan ba,amma idan har nasamu mijin da zai aureni a haka,kuma zai iya acceptn d'ina a haka,toh me zai hana ni yin auren',hisham a fusace ya tare ta da cewa'in ma auren zakiyi mujiba,nine nan na cancanci in aure ki',cike da mamaki bolaji tace'ya za'ayi ka aureni bayan kuma baka sona',hisham ya sauke ajiyar xuciya sannan ya dubi bolaji yana mai cewa'mujiba tun ranar da muka tafi L.A na fara jin wani feelings a game dake,i never knew those feelings were love sai ranar da Dr nassif ya cire miki bandeji,na so na 6oye soyayyar danake miki har izuwa ranar da zakiyi regaining memory d'inki,ki san wacece ke,in maidaki gun danginki,domin ina gudun soyayya da Matar aure,saboda daga ni har ke bamu da tabbacin kina da aure ko babu,dawowar memory d'inki ne kad'ai zai warware mana komai',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa'ni ba matar aure bace,saboda jikina ya bani hakan,hisham kadaina shakku akaina,ni taka ce,mujibarka,i'm yours,my life is yours and you are my life!' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 5:59 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~45~ Hisham ya tari numfashin bolaji ta hanyar cewa 'alright amma duk da haka ya kamata mu jira ko nan da shekara d'aya ne kiyi regaining memory dinki,kar azo a aikata aikin dana sani! Bolaji tayi amanna da batun ,amma a zuciyarta ta kud'iri aniyar cewa ko da tayi regaining memory dinta,hisham will always be hers! * * * Tsaftacciyar Soyayya ce tayi karfi tsakanin bolaji(mujiba) da hisham wanda su kansu suna masu mamakin junansu ta yadda ko wannensu baya son yaga koda kud'a ya taba waninsu! zuhra da zahra sunji dadin faruwar wannan al'amari,haka zalika hajiya da daddy! A kullum addu'arsu shine 'Allah yasa mujiba(bolaji) tayi regaining memory dinta '! * * * A bangaren nawwara da mijinta bamidele,suna gudanar zallar soyayya a gidan aurensu ,wanda nawwara a kullum take mamakin wai itace da auren YARE ,Allah kenan! Tsakaninta da funmilayo kuwa ,aminci yana nan daram ,kuma a kullum sai bolaji ta fado mata a rai , ji take kamar ta shaidawa mijinta komai ,ta gaya masa gaskiya,amma zuciyarta tana kwa6arta da cewa kar ta kuskura ta yi wannan gangancin in har ba so take aurenta da bamidele ya zamo mushe ba ! *BAYAN WATANNI BAKWAI* A firgice bolaji ta farka daga bacci bakinta d'auke da salati ,jikinta sai kyarma yake, hannu ta dora akan goshinta saboda azabar radadi da kanta keyi mata ,a cikin wannan yanayi zuhra ta shigo ta sameta ,da hanzari ta karasa ga bolaji tana mai cewa 'menene mujiba? what's wrong?' , da kyar bolaji ta bud'e baki tace'kaina ne ke ciwo' ,zuhra tace'ayya bara na gayawa hajiya ,sai a kira doctor' ,tana gama fad'in haka ta tashi ta fita daga dakin ! Bayan shudewar minti biyar sai ga zuhra ta dawo dakin tare dasu hisham da hajiya ,hajiya ta rungumo bolaji tana mai cewa 'sannu mujiba' ,sannan ta dubi hisham tace ' bugawa doctor ayuba waya mana,yazo ya dubata',hisham murya a sanyaye yace 'na kira wayarsa amma not reachable', bolaji tace'dont mind ,ya ma daina ciwon,daman tun lastweek ne idan na kwanta bacci,sai nayi mafarkin da zaiyi sanadiyar farkawata da kuma ciwon kai!' ,gaba dayansu suka hada baki tare da cewa 'MAFARKI?' ,'wani irin mafarki ?' Hisham ya jefa mata tambayar,bolaji ta amsa masa da cewa 'wani katon gidane mai kyau da kayan alatu, sai kuma wani mutum a kwance a wani daki, rufe yake ruf da farin kyalle, macizai sunyi masa dabaibayi ,kalmar MY BETTER HALF yana fita daga bakinsa,da zarar nasa hannu zan yaye farin kyallen da ya rufe masa fuska ,sai na farka',sannan ta cigaba da cewa 'amma fa kar ku damu fa its just a dream! Hajiya tace'ya kamata dai kiga doctor domin........',bolaji ta katse hajiya ta hanyar cewa 'am fine wallahi,kar ku damu' ,hajiya tace'shikenan toh,sai ki tashi kishirya ,ki fito ki yi breakfast kafin malaminku ya iso " ,hajiya ta tashi ta fice ,zuhra da zahra suka bi bayanta ! Hisham ya dubi bolaji yace 'are you sure ba abin da ke damunki,ko dai still in kira doctor?', bolaji ta mi'ke tsaye tare da cewa ' i'm fine and ok ,dont mind my love',sannan ta fada'a toilet! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:19 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~46~ Cike da hanzari bolaji ta watsa ruwa ta fito ta shirya ,ta fita tayi breakfast a gurguje ,domin malam har ya iso! Misalin karfe 5:00pm hisham ya dawo daga wajen aiki , bolaji ta gabatar masa da abinci da abin sha ,bayan ya ci ya sha yayi hani'an sai ya wuce daki ya cire kayansa tare da watsa ruwa,batun mafarkin bolaji ne ya tsaya masa a rai ,domin anashi hasashen yana ganin tamkar mafarkin yana da ala'ka da asalin mujiba(bolaji),amma ko ma menene yana ganin ya zama tilas ya 'kara tarar ta da batun ,saboda sanin wacece ita da kuma asalinta ne kad'ai zai zamto sila ga cikar burinsu naganin sun zama ma'auratan juna! * * * A bangaren sultan kuwa tun daga ranar da suka hadu da mujiba(bolaji) a mall ya rasa sukuni ,gashi kuma watanni sun ja ,ya rasa ta inda zai fara nemanta,hakan yasa ya zama kamar wani zautacce ,duk inda yaga mace fuskarta dauke da niqab ,sai yasa hannu ya yaye niqab din ,akan haka har mari yasha ,da kuma duka daga gun mazajen wasu matan,amma duk da haka bai daddara ba ,domin har ila yau bai fidda tsammanin sake haduwa da ita ba! Capt. Yarima hashim ! Allah sarki! Har yanzu dai yana nan dai kwance tamkar matacce ,sai dai yayi haske ya 'kara kyau ,har yar 'kiba yayi! Fulani kuwa ta d'aura aure da kuka,takaici da kuma ba'kin ciki,a kullum ta dubi hashim sai ta zubda hawayen bakin ciki da tausayi,mai martaba da ummu a kullum nasiha suke mata da bada baki akan cewa 'cuta da waraka duk na Allah ne! * * * Misalin 8:50pm na dare Bayan Dad da hisham sun dawo daga masallaci ,a kitchen hisham ya iske bolaji ita dasu hajiya suna hada hadar had"a abincin dare ,dubanta yayi tare da cewa ' ina son muyi wata magana after we finish eating dinner' ,bolaji ta amsa da 'alright!'! Hajiya ta dubeshi tare da cewa 'd'an nema a gabana kake cewa d'iyata tazo zance gunka ko?', hisham yana sosa keya a kunyace ya amsa da cewa 'hajiya ba fa zance nace tazo guna muyi ba,magana zamuyi ,wato zamu dan tattauna ne....', yana gama fadin haka ya fice ,su zuhra da zahra suka kwashe da dariya ,zahra dake yanka kankana a bowl tace ' yaya sham kenan,ashe rana irin ta yau zata zo da zai kara yin soyayya da wata bayan marigayiya',zuhra ta cafke da cewa'ita ma wannan din dai mujibar ce dai,ko kinga bambamci ne?', zahra tace'babu wani bambamci ,kawai dai waccan ta rasu ,wannan kuma tana raye ',bolaji ta hararesu tare da cewa 'enough ,ya isa haka,ku ba kwa ganin abu ,ku ja bakinku kuyi shiru ko?,toh dai hisham is meant for mujiba, wether she or me..' ,hajiya ta amshe da cewa 'tell them my daughter,hisham naki ne' tare da yin murmushi,a take bolaji ta ryfe fuskarta domin taji kunya sosai,su zuhra kuwa sai tsokanarta suke,a haka dai suka kamalla hada dinner ! A balcony bolaji taje ta samu hisham yana jiranta,sallama tayi tare da mi'ka masa glass cup mai d'auke da ruwan dabino mai sanyi,amsa sallamar yayi tare da karban glass cup din yana cewa 'sai yanzu ?','i'm sorry dear,kayan da aka gama cin abinci dasu muka wanke',bolaji ta bashi amsa a sanyaye,hisham yace 'its ok,daman game da mafarkin nan nakeso in tambayeki',bolaji tace 'i'm all ears', hisham ya kurbi ruwan dabino sannan yace ' gidan da ki kace kin gani a mafarkin,ke a ganinki zaki iya tunawa ko kin san gidan ,as in a gaske?, 'no' bolaji ta amsa tare da cewa'but i don't know if gidan is related with my identity',hisham yace'may be ,amma a yanzu ina son ki min kwatancen yadda gidan yake ,as in the building and everything',bolaji tayi jim tana tunani sannan ta yatsine fuska tare da cewa 'toh dai the house is huge ,something like a mansion or a castle..' sai kuma tayi caraf tace 'why not in zana maka gidan kawai ,i can draw it!',hisham ya yi dariya tare da cewa 'are you sure that u can draw it' ,'yes my love ,i can ,or are u trying to under estimate me?' ,hisham ya gimtse dariyarsa tare da cewa 'no my dear,lets go to the study room! suna shiga studyroom hisham ya dauko farar cardboard paper da biro bic ,ya mika mata biro din tare da spreading cardboard paper din akan table,sannan yace 'oya mujiba start drawing',bolaji kuwa ta takarkare ta fara zane ,sai da ta shafe minti 20 ta rasa me zata zana ,hisham kuwa yana gefe yana gumtse dariyarsa,wutar nepar da aka d'auke ne yasa bolaji ta gimtse idanunta ,a take gidan da take mafarki ya bayyana a bangon kwakwaluwarta(brain) ,hakan yasa a take yatsun hannunta suka fara sarrafa biro , zanen gidan ta fara tiryan tiryan,hisham kuwa ganin an dauke nepa yasa ya ciro waya daga aljihunsa ya kunna musu haske,ganin bolaji ta dage tana zane idanunta a rufe yasa yayi mutuwar tsaye yana duban fuskarta ta hasken da wayarsa ke fitarwa ,bolaji na gama zana gidan,ta bud'e idanunta,a take nepa suka dawo da wuta,dubanta takai ga hisham tare da cewa 'yes ! Ga gidan na zana',idanunsa hisham ya kai ga zanen yana mai 'karewa hoton zanen gidan kallo,idanuwansa ya ware don tsabagen mamaki,bakinsa na rawa ya furta kalmar 'MO..DIBBO..'S PA...LACE!' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~47~ Fuskarta dauke da alamun tambaya ta dubi hisham tana mai tambayarsa cewa 'shin daman akwai wannan gidan a gaske?', yatsanta na nuni ga zanen da tayi,hisham ya amsa da cewa'tabbas akwai wannan gida gaske ,kuma wannan gida babban masarauta ce dake cikin yankin yabo,to cut the story short ,few days back naje palace din dubo abokina wanda kusan lokaci daya aka kwantar dashi da ke a asibiti ,yanzu haka he is still in coma ,dalilin mutuwar matarsa!',sai kuma hisham yaja numfashi tare da cigaba da cewa 'duk ba wannan ba ,wai shin meye had'inki da masarautar modibbo da har zaki ga masarautar a mafarkin ki?',bolaji ta amsa da cewa 'nima amsar tambayar da zuciyata take muradin samu kenan',sai kuma ta cigaba da cewa 'baka ganin wannan masarautar tana da ala'ka da asalina ,zan iya kasancewa d'iya ko kuma .....',hisham ya katseta ta hanyar cewa 'sai dai ki kasance baiwa ko kuma kuyanga ,domin babu d'iya a wannan masarauta,asali ma yaya maza guda biyu ...(nan ya kwashe takaitaccen labarin asalin masarautar modibbo da ya sani ,ya labartawa bolaji)! Bolaji ta numfasa sannan tace'shikenan kawai,mafarki ba gaskiya bane....',hisham ya tari numfashinta ta hanyar cewa'tabbas mafarki ba gaskiya bane ,amma ni a hasashena ina ganin cewa akwai wani boyayyen al'amari game da mafarkinki,ya zama dole ni da ke mu kai ziyara ga masauratar ,'kila ziyartar masarautar ya zama sanadin dawowar memory dinki',bolaji ta yarfa hannayenta tare da cewa 'alright,sai kasa mana rana muje ', hisham ya dubi agogon wayarsa sannan yace'shikenan yanzu dare yayi muje mu kwanta,ranar lahadi insha Allah sai muje,amma fa ina son wannan maganar ya zama sirri a tsakaninmu,saboda ina son mu bi komai a sannu',bolaji ta amsa da 'toh my dear',hisham ya dauki cardboard paper din ya nad'e,sannan suka fice daga study room din! *RANAR LAHADI* Misalin karfe 10 na safe bolaji sanye take cikin doguwar baby pink abaya tare da hijab rose pink,sai kuma niqab ,hisham a shirye yashigo falo tare da duban bolaji yana cewa'are you set?',bolaji ta amsa da 'yes',hajiya ta dubesu tace 'wai shin ku biyu zakuje asibitin,idan ni bazakuje dani ba ,ko zahra ce sai ta raka ku....',hisham ya katse hajiya ta hanyar cewa 'hajiya wai shin baki yarda dani bane ?',hajiya ta girgiza kanta tana cewa 'ba wani abu nake nufi ba,kuje kawai ,Allah ya tsare',bolaji da hisham suka amsa da 'amin',zahra da zuhra suka musu rakiya izuwa harabar gidan ,hisham ya fito da mota ,bolaji ta shiga ta zauna ,bala direba ya bude gate,hisham ya harba mota waje ,sai masarautar modibbo! Hisham ya dubi bolaji da tayi shiru tunda suka hau kan titi,sai yayi gyaran murya tare da jifanta da tambayar 'are you nervous?',murya a sanyaye bolaji ta amsa da cewa 'no i'm just scared','scared' hisham ya maimaita,bolaji ta amsa da 'yes i'm scared ,coz bansan me zamuje mu tarar ba,ina tsoron rasaka hisham,ina tsoron inyi regaining memory dina ,inzo in kasance ni baiwace mai munin asali',gefen hanya hisham ya samu yayi parking ,sannan ya dubi bolaji tare da sa hannu ya daga niqab din dake kan fuskarta,ganin hawaye acikin idanunta yasa yace'mujiba me kike tsoro ,idan kin kasance baiwa ,toh meye zai faru?,bolaji ta amsa da cewa 'shin hajiya da dad zasu kyaleka ka auri baiwa',hisham yayi murmushi mai ciwo sannan yace 'mujiba kenan,baki san yadda nake jinki a zuciyata bane,shiyasa kike fadan haka,amma ina son ki sani cewa ni hisham naki ne har abada,haka zalika ke tawa ce,mutuwa ce kad'ai zata iya rabamu mujiba ',sannan yace 'ki share hawayenki ,you have to be strong,saboda regaining memory dinki kadai me zai sa mu mallaki junanmu a matsayin ma'aurata,kuma a shirye nake in fuskanci ko wanne irin hukunci a kanki,in har hukuncin bai zo da kaddarar rabuwar mu ba ,mujiba ina tare da ke,kuma zan cigaba da kasancewa tare da ke a ko da yaushe',bolaji tayi murmushi tare da goge hawayen idanunta tace 'nagode my life,you mean alot to me,i will forever be grateful to you!', hisham yayi murmushi sannan ya tada mota suka cigaba tafiya,suna masu bayyanawa juna SO ! Written by: ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~48~ Ko da suka iso gaban fada sai bolaji taji kanta yana juyawa ,jiri na d'ibar ta ,hakan ya janyo sanadiyar fitar 'innalillahi wa inna ilaihi raji'un' daga bakinta ,hisham ya dubeta yana cewa 'lafia mujiba?',da kyar ta iya budan baki tace 'kaina yake min wani iri',da sauri hisham ya samu waje nesa da fada yayi parking tare da juyowaya fuskanci mujiba ,wacca tuni ta sume ,ganin alamu bata motsi yasa ya yaye mata niqab dinta ,tare da dauko ruwa a back seat ,ya shafa mata a fuska,ajiyar zuciya ta sauke tare da bude idanunta ,hisham cike da tausayawa yace 'sannu!' bolaji ta amsa da 'yawwa','do u remember anything?' Hisham ya tambaya ,bolaji ta amsa da 'no,but its like am gettin a little flashback,shiyasa kaina ya dinga min wani iri da naga palace din',hisham yace 'toh yanzu ya zaayi mu shiga ciki ko kuma mu koma gida nr ?,coz ina tsoron kar brain dinki ya takura',bolaji tace 'kar ka damu my love ,tabbas gidannan yana da alaka da my past and identity,amma ba zan iya tabbatar da haka ba sai nayi rayuwa acikin gidan, wanda a hankali zan gano wacece ni?',hisham yayi jim yana tunani ,sai kuma ya sauke ajiyar zuciya sannan yace'eh toh hakane kam,da ace asalin fuskarki gareki da ko hoto sai nayi miki in shiga in nuna musu ko shin zasu san wacece ke ,amma yanzu matsalar shine ta yaya zaki yi rayuwa a gidan ?,gaba dayansu suka yi shiru suna masu tunanin mafita ,bayan minti 30,sai kawai hisham ya tada mota tare da cewa' muje ciki i will come up with a plan'!,mujiba tasa hannu ta cire niqab din ,ta ajje a gefe,a yayin da hisham ya iso gate palace yana horn,royal guards suka fito ,ganim cewa shine sai aka bude masa gate ya shiga da motarsa ,bayan yayi parking,suka fito daga motar,guest parlour aka yi musu izinin shiga ,bayan sun zauna sai hisham ya nemi izinin a yi musu iso gun fulani,ita kuwa bolaji ware idanu ta yi tana kallon duniya,sai da suka shafe minti 40 suna zaman jira ,sannan kuyanga badiyya tazo tayi musu jagora zuwa royal parlour ,suna shiga fulani da ummu suka tadda a zaune ,ganin hisham ya russuna yana mika gaisuwa ,hakan yasa bolaji itama ta russuna tana mika tata gaisuwar,fulani ta amsa cike da fara'a tana cewa 'tashi ku zauna mana ,ashe kaine kazo ' hisham kuwa a kasan ya zauna ,haka yasa ita ma bolaji ta zauna tana mai zare idanu,tufafin dake jikin fulani da ummu ne suka bata shaawa,ummu ta dubesu tana cewa 'sannu hisham,kana kokari zuwa duba abokinka,Allah ya bada lada',cike da ladabi hisham ya amsa da 'amin',fulani kuwa tace 'duk cikin abokan souldear wannan kad'ai ke zuwa dubashi lokaci zuwa lokaci,daman baka sanin masoyanka zai musiba ta sameka ",sannan ta kai dubanta ga bolaji tana mai tambayar hisham 'wannan kanwarka ce?', hisham ya amsa da 'eh kanwata ce',fulani tayi murmushi tare da yafito bolaji tana cewa 'yan mata zo nan kusa dani ki zauna', a kunyace bolaji ta zo ta zauna tana mai jin nauyi ,ummu tace 'yanmata ya sunanki?', 'mujiba' bolaji ta amsa ,fulani tace 'lallai kin amsa sunanki',ummu tayi murmushi ,hisham yayi gyaran murya,yana mai kara russunawa ,ya dubi fulani tare da cewa 'ranki ya dade daman wata y'ar alfarma nazo nema ',fulani tace 'alfarma ?wacce iri?',hisham ya kara russunuwa cikin tsara kalamai daki daki yace 'daman wannan 'kanwar tawa ce za'ayi wa aure,shi wanda za'a aura mata d'ane ga yayan mahifinmu ,ita kuma bata sonshi sabida dan giya ne,amma iyayenmu sun rantse sai anyi auren,ita kuma rannan sai naji hirarsu ita da kawayenta tana cewa zata gudu ta bar gida in yaso ta shiga duniya, ni kuma naga da akan hakan ya faru gwara na nema mata mafita ,shine a yau na yanke shawara muzo in nema mata aiki a nan,in yaso sai tayi zamanta a fada tana muku hidima ,nasan cewa idan ba a ganta ba zaa hakura da zancen auren,idan komai ya lafa sai nazo in dauketa in maidata gida',ummu cike da tausayawa tace 'Allah sarki ,dan uwa mai dadi',fulani tayi caraf tace 'yanzu wannan zukekiyar yarinyar za'a yiwa auren dole a wannan zamanin ,lallai wasu iyayen akwai karfin hali', sannan ta dafa bolaji tana cewa 'kayi tunani mai kyau da ka kawota nan,amma fa baza'a amshe ta a matsayin hadima ba',hisham ya zare idanu cike da fargabar wargajewar plan dinsa ,zai bude baki yayi magana fulani ta katseshi ta hanyar cewa 'kar ka samu damuwa ka bar min ita ,zan ri'keta tamkar d'iyar dana haifa!' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~49~ Hisham me zaiyi in ba ya fara zuba godiya ba,ummu cewa take 'kar ka damu d'a na kowa ne',ita kuwa bolaji mamaki ne yayi mata dirar mikiya bata taba tsammanin cewa komai zai zo da sauki haka ba,jin muryar hisham yana cewa 'toh ranki ya dade bara ni na tafi ,godiya nake sosai ,Allah ya saka da alkhairi',tsam bolaji ta mi'ke tana cewa 'muje in raka ka yaya' ,fulani tayi murmushi tare da cewa 'sannu mai yaya',sannan ta dubi hisham tace'ka gaida gida',sai kuma hisham ya kara yin kasa da kai yana cewa 'insha Allah gobe zan kawo mata kaya da sauran abubuwan da....',da sauri fulani ta katseshi tare da cewa 'haba kai kuwa meye zata nema a fadar nan ta rasa ,kai dai kawai je ka abunka',hisham ya kara yin godiya sannan ya fice ,bolaji tana biye dashi,suna isa gun mota ,bolaji ta fara tafa hannayenta tare da cewa 'bravo my love!',sannan ta cigaba da cewa 'kana ganin cewa babu matsala kuwa domin ni ina shakkar wannan amincewar gaggawa matar nan tayi na zamana a gidannan',hisham yayi murmushi tare da cewa'mujiba kar ki damu ,be optimistic mana,ni nan na yarda dasu kuma sanin kanki ne cewa bazan barki a gun da za'a cutar dake ba ,kuma ko ma menene ki sa a ranki cewa muna yi komai ne domin cikar burin mu na mallakar junanmu a matsayin ma'aurata',bolaji ta ja numfashi tare da cewa 'toh shikenan Allah ya shige mana gaba ,amma fa idan naga babu wani cigaba game da regaining memory dina ,toh a gaskiya kazo ka dauke ni',hisham yace 'kar ki damu ,i will be coming to see u time to time,so u dont have to worry,insha Allah zamu dace ',bolaji tace 'toh yanzu in ka koma gida me zaka cewa su hajiya idan sun tambayeka ina nake',hisham ya amsa da cewa 'kar ki damu ,i will deal with that',sannan ya bude mota yasa hannu ya dauko wani kwali daga backseat ya mikawa bolaji yana cewa 'ga waya nan ,na hada komai,zamu dinga communating,sannan kuma pls ki kula min da kanki ,ki kuma rike min amanar zuciyarki ',bolaji ta amshi kwalin tana cewa 'thanks dear,kuma insha Allah zan rike maka amanar zuciyata ,ka cire shakku da waswasi a zuciyarka domin zuciyata taka ce kai kadai,ni taka ce ',a haka sukayi sallama ya shiga mota ya tayar ,royal guards suke bude masa gate ya fice,bolaji ta juya ta koma ciki zuciyarta dauke da kewar su zahra da zuhra! A ranar Fulani da kanta takai bolaji gun mai martaba tare da yi masa bayani game da ita,kasancewar mai martaba yasan wanene hisham tunda yana zuwa duba hashim lokaci lokaci ,kuma ya yaba da nutsuwarsa ,shiyasa ya amince tare da yin amanna da zamanta a gidan! Fulani kuwa dakin da nawwara ta zauna tasa aka gyarawa bolaji,sannan ta umarci jakadiya mara'kisiya da suje dakin hashim su kwaso kayan(lefen) bolaji daga wardrobe ,su zo su jera a wardrobe din dakin mujiba(bolaji) domin tayi amfani dasu! Sultan kuwa bai san wainar da ake toyawa ba a wannan ranar kasancewar tun safe ya fita neman matar aurensa wato mujiba(bolaji),sai yamma ya dawo a gajiye likis ,dakinsa ya wuce ya watsa ruwa sannan yabsakaya marasa nauyi,a lokacin kuwa bolaji tana sabon dakinta ,tana warwara da sa'ka game da yadda zata fara tunkarar abubuwan da zasu sa tayi regaining memory dinta ,daga karshe ta yanke shawarar shiga cikin hadimai da kuyangu,hakan yasa ta yanke shawarar shiga cikinsu a wannan rana sukayi girki tare ,fulani tayi kokarin hanata amma hakan ya gagara domin ta nuna mata cewa she loves what she's doing! Bayan sallar isha gaba dayansu in an dauke hashim dake kwance a daki sai kuma sultan wanda bai karaso ba suka hadu akan dinning domin cin abincin dare ,jakadiya marakisiya tare da bolaji sukayi serving ,sannan bolaji ta zauna kusa da kujerar fulani ,suka fara cin abinci,a lokacin sultan ya karaso ya zauna ,bayan jakadiya tayi serving dinsa ya fara cin abinci ba tare da ya lura da bolaji ba kasancewar yunwar da ya kwaso ,ita kuwa bolaji tun shigowarsa ta gane fuskarsa ,kuma sai da gabanta ya yanke ya fadi ! ,sultan kuwa sai da ya fara koshi sannan ya lura da mujiba (bolaji),sauran kiris ya saki kofin juice din da yake kwankwada saboda rikicewa,mamaki da dimuwa ,amma a take ya tattaro nutsuwarsa yayi watsi da rikicewar da yayi ,amma ya kasa dauke idanunsa akan ta ,gani ya ke tamkar in ya dauke idanunsa zata bacewa ganinsa ,ji yake tamkar a mafarki yake ganinta, ganin ta tashi tana taya su jakadiya kwashe plates yasa ya dawo hayyacinsa ,a lokacin ya lura ashe su mai martaba sun bar wajen ,ita ma bolaji juyawa tayi hannunta dauke da cups ta wuce kitchen,cike da zafin nama ya bi bayanta,a kitchen ya isketa ,a take ya bawa royal maids umarni da su fice daga kitchem din,sum sum suka fuce ya rage daga shi sai bolaji ,ganin kowa ya fice yasa bolaji ita ma tayi hanyar fita,cike da zafin nama sultan ya ri'ke mata hannu,cak ta tsaya ba tare da ta juyo ba,hakan yasa shi ya juya ya fuskanceta,hannunta ta fisge daga hannunsa ,ta fara ja da baya zuciyarta na dukan tara tara ,shi kuwa bin ta ya dinga yi yana mai jifanta da kallon so,har sai da bayanta ya hadu da bangon kitchen din,hakan ya bashi daman sa hannunsa ya kewayeta ta hanyar dora hannunsa akan bangon,bolaji kuwa duk tagama tsorata domin babu ta yadda zata iya guduwa,goshinsa ya daura akan goshinta bakinsa na furta kalmara 'kin bani wahala!' Written by;ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/17, 8:21 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~50~ Bolaji ta rintse idanunta tare da kauda fuskarta tana cewa 'please ka bani hanya in wuce',sultan yayi murmushi yace'in matsa kije ina?,bazan bari wannan karin ki subuce min ba ,ba tare da kin gaya min sunanki ba',shiru bolaji tayi ba tare da tanka masa ba,hakan yasa sultan yace'zamu kwana a haka kenan',kallonsa tayi da idanunta da suka canza launi suka koma jajawur ,murya a raunane tace'mujiba',murmushi yayi tare da cewa'ina sonki mujiba, Ban taba son wata diya mace ba a rayuwata sai ke,mujiba i love you,loving you was the best thing that has ever happen to me,mujiba i love u! mujiba i love u !!! mujiba i love u !!! ,yana gama fadin haka ,ya yi murmushi tare da bata hanya ta wuce,da sauri ta fice daga kitchen d'in ,sultan yabi bayanta ,murna fal cikin zuciyarsa yau gashi ga mujiba a gida daya,d'akin ummu yaje,itace ta labarta masa batun zaman mujiba(bolaji) a fada ,shima anan yake shaidamata itace matar aurensa dayake basu labarin ya gani kwanaki,ummu ta tayashi murna sannan tayi masa alkawarin nema masa aurenta idan har tana sonshi kuma zata amince ta aureshi,kuma a yanzu ya kamata ya nemi soyayyarta kafin ta koma gaban iyayenta,cike da murna ya wuce dakinsa, a ranar yayi bacci har da munshari ! * * * A bangaren hisham kuwa ,ko da ya iso gida ,hajiya ta nemi dalilin rashin dawowar mujiba(bolaji),sai cewa yayi" muna zuwa asibitin,bayan ta shaidawa doctor ayuba abun dake damunta ,sai ya bada umarnin sai dai a wuce da ita abuja gun wani kwararren doctor din kwakwaluwa domin ciwon kanta ya shafi brain dinta ne ,shine kawai sai nayi waya office ,aka turo officers daga can NGO , daman sune suka dauki nauyin duk wani health issue dinta,yanzu haka sun wuce da ita abuja',hajiya ta kama baki tace 'yanzu daga zuwa asibiti sai tafiya abuja ,kuma kai baka rakata ba, kuma baka biyo ta gida ku tafi damu ba?',hisham ya marairaice tare da cewa 'haba hajiya naga fa lokacin dana tsinto ta ni da officers din ne muka keta hazo da ita muka je har kasar waje domin neman lafiyarta....',hajiya ta katseshi ta hanyar cewa 'naga lokacin she was'nt part of the family ,and she was'nt our responsibility,but a yanzu she is...',hisham yace'alright naji please ki kwantar da hankalinki mujiba is safe ,zata dawo ',hajiya ta amsa da cewa 'shikenan daman kai ka kawota ,idan ma maidata kayi in da ka daukota,matsalarka ce ',a lokacin dad ya tsoma baki ta hanyar cewa 'daman abinda ya kamata kisa a ranki kenan tun ranar da ya kawo ta ,shi ke da iko da ita,amanarsa ce,mu yan taya riko ne,Allah ya bata lafia ,yasa kuma sa ayi komai a sa'a',hajiya ta amsa da 'amin',zuhra da zahra kewar mujiba(bolaji) duk yayi musu katutu a zuciya,ji suke tamkar ta tafi kenan,bazata kuma dawo wa ba,kamar yadda mujibar asali ta tafi ta barsu! A haka zancen mujiba ya mutu a gidan,washegari hisham ya shaida musu cewa an wuce da mujiba(bolaji) u.s.a domin further treatment,ci kanka babu wanda yace masa,shi kansa bai ji dadi ba,amma ya zama tilas hakan ya faru domin cikar burinsu shi da bolaji na muradin mallakar junansu a matsayin ma'aurata,kuma duk ranar da mujiba (bolaji)tayi regaining memory dinta ,ranar zai shaida musu gaskiyar inda mujiba taje ,amma for now he has to keep this as a secret ! * * * Washegari da safe bayan an gama yin breakfast ,fulani taja hannun bolaji ta kai ta dakin da hashim yake kwance ,suna shiga dakin gaban bolaji ya tsinke ya fadi domin tabbas in bata manta ba wannan shine dakin da tagani a mafarkinta,fulani ce ta katse mata tunaninta ta hanyar cewa 'mujiba zan baki wani gajeran labari ,wanda nake fatan zaki share min hawayena,ki kuma cika min burina na ganin cewa souldear yayi aure',sannan ta cigaba da cewa 'wannan da kika gani a kwance sunansa hashim,d'ana ne kuma ina kaunarsa fiye da kowa a duniyar nan ,rayuwarsa ta lalace ne a lokacin da ya auro YARE wato BAYARABIYA a matsayin matarsa ,duk yadda na kai da tsanar YARE haka na hakura ya aureta domin naga yana mata wani irin mahaukacin so wanda daga alamu, asiri tayi masa ,haka muka zauna da ita cikin aminci da yarda ,amma duk da haka sai tayi mana butulci ta gudu ,sai daga baya aka tsinto gawarta wanda sanadiyar ganin gawarta hashim ya zama haka ya shiga wannan halin na matacce a raye ,naso aura masa diyar yayata amma fafur ta ki amincewa saboda taganshi a haka',fulani ta goge hawayen idanunta tare da dafa kafadar bolaji tace 'ina son ki share min hawayena ,ki auri d'ana ,domin a jiya ina dora idanuna a kanki jikina ya bani cewa kaddara ce ta kawo min ke ,kuma ke ce zaki share min hawayena,bazan miki tilas ba,amma kije kiyi tunani,kuma ina son ki dinga shigowa kina kula dashi ,a haka sha'kuwa zai shiga tsakaninku,domin ina son aje a nema masa auren ki a ranar da kika koma gidanku',fulani tana gama fadin haka ,ta fice ta bar bolaji a tsaye tana warwara da sa'ka ,ita a yanzu danasanin zuwanta take yi,wannan wani irin azal ne ,ga abbas(sultan) da yace yana sonta,ga kuma wannan hashim din da uwarsa take son kakaba mata shi,ga kuma masoyinta hisham da tayi wa alkawari,shin menene mafita ? Ta tambayi kanta tare da cewa 'ya Allah ka dawo min da memory dina domin sanin ko ni wacece? '! A daki ummu ta iske fulani ,bayan sun dan taba hira ,sai ummu tayi gyaran murya tare da cewa 'maganar d'ana nazo yi miki,ashe mujiba ce matar aurensa da ya gani rannan yake bamu labari,shine nace yanzu me zai hana idan mujiba ta koma gidansu aje anema masa aurenta ,domin a gaskiya yarinyar ta kwanta min',Fulani tayi kasake tana kallon ummu ,sannan tayi kwafa tace 'kin ga rabu da shashashan yaron nan,ni na riga nayiwa d'ana kamun mujiba ,sanadiyar da yasa na amshi amanarta kenan a jiya ,domin mujiba da my souldear ta dace',ummu da mamaki ya cikata tace 'haba fulani wani irin magana ne haka ?,ya zaayi a hana mai lafiya auren mujiba sannan abawa mara lafiyan da ba'a san ranar da zai warke ba aurenta...',fulani ta katseta ta hanyar cewa 'hashim dina zai warke ,ni nasan zai warke ,kuma shi zai auri mujiba,kuma shi sultan din zai zo ya sameni,idan ma shine ya turoki zanyi maganinsa ,ya zama dole ya hakura da mujiba idan har ni dinnan ina da iko dashi' ummu idan ranta yayi dubu ya baci domin lamarin fulani ya fara bata mamaki ,hakan yasa ta mike tsaye a fusace tare da cewa 'fulani ya isa haka,ke a kullum kin fi son ki yanke hukunci ba tare da kinyi la'akari da abin da zaije ya dawo ba,toh tunda abin yazama iko da tutiya,naga nima hashim d'ana ne ko,kuma nice na dau cikinsa na kuma haife,toh ki ji da kyau idan har ina da iko akan hashim to wallahi bazai auri mujiba ba,sultan ne zai aureta',ita ma fulani ta mike tsaye tare da cewa 'haka zalika shi ma sultan bazai aureta ba idan har ni ce uwarsa kuma idan har zan gaya masa ya bi,toh bazai auri mujiba ba,my souldear ne zai aureta,ki rubuta ki ajje!' Written by: ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/18, 7:18 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~51~ Fulani na gama fadin haka ta mike tsaye ta fice daga dakin! Jiki a sanyaye Bolaji ta dubi hashim dake kwance idanunsa a bude tamkar kayi masa magana ya amsa ,fes fes dashi ,sai taji kawai ya bata tausayi,ta kuma kare godewa Allah da ya barta da lafiyarta har take iya sarrafa gangar jikinta,a cikin wannan yanayi kuyanga badiyya ta shigo dakin ta sameta ,murya a sanyaye ta dubi bolaji tare da cewa 'ranki shi dade,yarima sultan ne yake bukatar ganinki a lambu','me zanyi masa ?',bolaji ta tambayeta ,'ban sani ba,yace dai in taho da ke','bazataje ba',fulani ta bada amsa ,sannan ta bawa badiyya umarnin fita daga dakin! Fulani ta dubi bolaji tare da cewa 'menene tsakaninki da sultan?,'babu!' Bolaji ta bata amsa ,fulani ta cigaba da cewa'toh ina son hakan ya cigaba da kasancewa tsakaninku,domin bana bukatar soyayya tayi tasiri a tsakaninku ,kamar yadda na gaya miki dazu hashim zan nemawa aurenki da zarar yayanki ya maida ki gida',bolaji kasa tankawa tayi hakan yasa ta fice ,tana isa dakinta ,wayar da hisham ya bata ya fara ringing ,jikinta na rawa ta dauki wayar ta amsa tare da yi masa sallama,bayan ya amsa sai ya jefeta da tambayar'yanaji muryarki haka',ta budi baki da niyyar labarta masa abinda ya faru ,sai wata zuciyarta ta kwa'beta da cewa'kar ki dagawa bawan Allah hankali,tunda ke kanki kinsan cewa ta shi ce ke,da zarar yazo ya daukeki kun koma gida shikenan',sai kawai tace 'daga bacci na tashi,yasu hajiya da zuhra"',hisham ya amsa da 'duk suna lafia ,sai dai fa duk sunyi fushi dani,gani suke tamkar na rabaki dasu',bolaji tace'ayya nima nan i'm already missing them,but soon zan dawo garesu',sannan suka cigaba da hirar so, daga karshe sukayi sallama ! Sultan ne yayi sallama ya shigo dakin,bolaji ta amsa tare da janyo hijab ta sa,idanu ya watsa mata yana mai jifanta da wani irin shu'umin murmushi,sannan yayi gyaran murya tare da cewa 'mujiba kenan,meyesa kike son wahalar da zuciyata ne ,ni mai kaunarki ne,ki bani dama',bolaji ko kallonsa batayi ba bare yasa ran zata amsa masa! Fulani ce ta shigo dakin dalilin tasa jakadiya tazo ta sanar da ita a duk lokacin da taga shigowar sultan dakin mujiba(bolaji)! Murya a kausashe fulani ta kira sunansa tare da cewa 'kai sultan ka fita idanuna in rufe ,ummunka bata fada maka sakona ba ,toh hashim zan aurawa mujiba,domin kai baka dace da ita ba,kuma in kace zaka yi jayayya ga hukuncin dana yanke ,wallahi zan tsine maka albarka ka bi duniya',bolaji ce ta mike a razane tare da cewa'hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya zama dole in bar muku gida,haka kawai daga jiya zuwa yanzu zuwana ya fara haifar da fitina',fulani ta dubeta tace 'ki kwantar da hankalinki mujiba,babu in da zakije ,kiyi zamanki har izuwa ranar da yayanki zai zo ya tafi dake ',sannan ta maida dubanta ga sultan tace 'kai kuma dafatan zaka daina takura mata,ka fita daga harkarta ,ita ma ba sonka take ba',a fusace sultan ya bar dakin ba tare da yace uffan ba,hakan ya bawa fulani daman rarrashin bolaji,amma fafur bolaji taki amincewa da zaman fadan,daga karshe sai tace zata koma bangarensu kuyangu da zama,fulani ta amince! A kwana a tashi yau satin bolaji daya a fada ,ita da kuyanga badiyya sun zama kawayen juna ,tare suke zama suyi hira kasancewar dakinsu daya,fulani bata daina jan bolaji a jiki ba ,domin a kullum sai ta aika an kira mata ita,haka zalika ummu ita ma tana jan bolaji a jiki tana yi mata nasiha a ko dayaushe akan ta guji son zuciya ,kuma ta dinga sanya Allah a lamarinta tare da neman zabinsa a ko dayaushe,hisham kuwa suna waya akai akai ,kuma a kullum sai ya tambayeta ko an dace ,ita kuma sai tace masa har yanzu shiru no response! Sultan kuwa takanas yaje ya samu fulani a daki ya shaida mata cewa 'wallahi tallahi idan har kika cigaba da shiga tsakanina da soyayyar mujiba wallahi nima zan shiga tsakaninki da mai martaba da hashim wajen tona asirin abunda kika aikata ga bolaji',fulani bata san lokacin da ta dauke fuskar sultan da mari ba,shi kuwa yayi murmushi tare da cewa 'ni dai nagama magana,ki fitar da kanki daga sha'ani na da mujiba',dalilin da yasa fulani tayi sanyi tare da fitar da kanta daga tsabgar sultan,tana ji tana gani sultan ya fara neman soyayyar mujiba(bolaji),duk da ita ma bolaji bata bashi fuska ba,dawowar memory dinta ne ya dameta! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~51~ Fulani na gama fadin haka ta mike tsaye ta fice daga dakin! Jiki a sanyaye Bolaji ta dubi hashim dake kwance idanunsa a bude tamkar kayi masa magana ya amsa ,fes fes dashi ,sai taji kawai ya bata tausayi,ta kuma kare godewa Allah da ya barta da lafiyarta har take iya sarrafa gangar jikinta,a cikin wannan yanayi kuyanga badiyya ta shigo dakin ta sameta ,murya a sanyaye ta dubi bolaji tare da cewa 'ranki shi dade,yarima sultan ne yake bukatar ganinki a lambu','me zanyi masa ?',bolaji ta tambayeta ,'ban sani ba,yace dai in taho da ke','bazataje ba',fulani ta bada amsa ,sannan ta bawa badiyya umarnin fita daga dakin! Fulani ta dubi bolaji tare da cewa 'menene tsakaninki da sultan?,'babu!' Bolaji ta bata amsa ,fulani ta cigaba da cewa'toh ina son hakan ya cigaba da kasancewa tsakaninku,domin bana bukatar soyayya tayi tasiri a tsakaninku ,kamar yadda na gaya miki dazu hashim zan nemawa aurenki da zarar yayanki ya maida ki gida',bolaji kasa tankawa tayi hakan yasa ta fice ,tana isa dakinta ,wayar da hisham ya bata ya fara ringing ,jikinta na rawa ta dauki wayar ta amsa tare da yi masa sallama,bayan ya amsa sai ya jefeta da tambayar'yanaji muryarki haka',ta budi baki da niyyar labarta masa abinda ya faru ,sai wata zuciyarta ta kwa'beta da cewa'kar ki dagawa bawan Allah hankali,tunda ke kanki kinsan cewa ta shi ce ke,da zarar yazo ya daukeki kun koma gida shikenan',sai kawai tace 'daga bacci na tashi,yasu hajiya da zuhra"',hisham ya amsa da 'duk suna lafia ,sai dai fa duk sunyi fushi dani,gani suke tamkar na rabaki dasu',bolaji tace'ayya nima nan i'm already missing them,but soon zan dawo garesu',sannan suka cigaba da hirar so, daga karshe sukayi sallama ! Sultan ne yayi sallama ya shigo dakin,bolaji ta amsa tare da janyo hijab ta sa,idanu ya watsa mata yana mai jifanta da wani irin shu'umin murmushi,sannan yayi gyaran murya tare da cewa 'mujiba kenan,meyesa kike son wahalar da zuciyata ne ,ni mai kaunarki ne,ki bani dama',bolaji ko kallonsa batayi ba bare yasa ran zata amsa masa! Fulani ce ta shigo dakin dalilin tasa jakadiya tazo ta sanar da ita a duk lokacin da taga shigowar sultan dakin mujiba(bolaji)! Murya a kausashe fulani ta kira sunansa tare da cewa 'kai sultan ka fita idanuna in rufe ,ummunka bata fada maka sakona ba ,toh hashim zan aurawa mujiba,domin kai baka dace da ita ba,kuma in kace zaka yi jayayya ga hukuncin dana yanke ,wallahi zan tsine maka albarka ka bi duniya',bolaji ce ta mike a razane tare da cewa'hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya zama dole in bar muku gida,haka kawai daga jiya zuwa yanzu zuwana ya fara haifar da fitina',fulani ta dubeta tace 'ki kwantar da hankalinki mujiba,babu in da zakije ,kiyi zamanki har izuwa ranar da yayanki zai zo ya tafi dake ',sannan ta maida dubanta ga sultan tace 'kai kuma dafatan zaka daina takura mata,ka fita daga harkarta ,ita ma ba sonka take ba',a fusace sultan ya bar dakin ba tare da yace uffan ba,hakan ya bawa fulani daman rarrashin bolaji,amma fafur bolaji taki amincewa da zaman fadan,daga karshe sai tace zata koma bangarensu kuyangu da zama,fulani ta amince! A kwana a tashi yau satin bolaji daya a fada ,ita da kuyanga badiyya sun zama kawayen juna ,tare suke zama suyi hira kasancewar dakinsu daya,fulani bata daina jan bolaji a jiki ba ,domin a kullum sai ta aika an kira mata ita,haka zalika ummu ita ma tana jan bolaji a jiki tana yi mata nasiha a ko dayaushe akan ta guji son zuciya ,kuma ta dinga sanya Allah a lamarinta tare da neman zabinsa a ko dayaushe,hisham kuwa suna waya akai akai ,kuma a kullum sai ya tambayeta ko an dace ,ita kuma sai tace masa har yanzu shiru no response! Sultan kuwa takanas yaje ya samu fulani a daki ya shaida mata cewa 'wallahi tallahi idan har kika cigaba da shiga tsakanina da soyayyar mujiba wallahi nima zan shiga tsakaninki da mai martaba da hashim wajen tona asirin abunda kika aikata ga bolaji',fulani bata san lokacin da ta dauke fuskar sultan da mari ba,shi kuwa yayi murmushi tare da cewa 'ni dai nagama magana,ki fitar da kanki daga sha'ani na da mujiba',dalilin da yasa fulani tayi sanyi tare da fitar da kanta daga tsabgar sultan,tana ji tana gani sultan ya fara neman soyayyar mujiba(bolaji),duk da ita ma bolaji bata bashi fuska ba,dawowar memory dinta ne ya dameta! Written by:ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/18, 7:19 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~52~ Kamar kullum cikin dare bolaji da badiyya suna kwance suna hira kafin bacci ya riskesu ,sai bolaji ta tashi ta shiga toilet din dake cikin dakin, bayan shigarta da second 40,sai taji kamar motsi irin na fitar numfashin wahala,da hanzari ta gama abinda take ta fito ,me zata gani kuwa ,badiyya ta gani kwance ,barde ya rufe mata baki da hannunsa yana kokarin keta mata haddi ,tuni kan bolaji yafara juyawa wadansu al'amura da suka taba shudewa a rayuwarta a baya suka dinga dawo mata (wato arangamarta da sultan a ranar da zai mata fyade) amma hakan bai hanata yunkurin dauko wani katon wood flower vase dake gefen wardrobe din dakin, tare da sakarwa barde shi akai ,ji kake tum! ,hakan ya biyo da daukewar numfashinsa ba tare da ya kai ga cimma burinsa ba akan badiyya ,bolaji kuwa juwa ce ta dauketa ,hakan yasa ita ma ta fadi a wajen a sume! Badiyya kuwa rudewa kam ta gama yi ,domin rasa yadda zatayi dasu tayi,da kyar ta samu ta tattaro nutsuwarta ta shiga toilet da debo ruwa tazo ta shafawa bolaji a fuska,bolaji ta sauke ajiyar zuciya tare da mikewa zaune tana dafe da kanta ta dubi badiyya tare da cewa 'ina BOLAJI? MATAR HASHIM?,badiyya ta bude baki cike da mamaki tare da cewa 'mujiba wacce irin tambaya ce wannan ,meye had'inki da ita?',bolaji ta dubeta tare da cewa 'wannan bai shafeki ba ki gaya min gaskiya',sai badiyya tace 'toh matar yarima dai guduwa tayi a hanyarta na guduwa hatsari ya riskesu, hakan yayi sanadiyar mutuwarta',bolaji tayi murmushi mai kama da yake sannan tacee'shikenan yanzu ki je bangaren royal guards ki kirawo su ,su zo su fice da wannan',jiki na rawa badiyya ta fice taje ta kira su kurtagu da sauransu ,sukazo suka fice da barde wanda har yanzu bai farfado ba! Bayan an fice dashi sai bolaji ta dubi badiyya bayan ko wannensu ya zauna akan gadonsa,murya a sanyaye bolaji ta fara cewa'badiyya a yadda na daukeki a kwanakin nan,ban taba zatan zaki yi min karya ba ,amma bara na fayyace miki wani boyayyen al'amari a game dani',badiyya jiki a mace ta rafka tagumi tare da zubawa bakin bolaji na mujiya',bolaji ta cigaba da cewa 'faruwar al'amarin da ya wakana tsakaninki da barde a d'azu yasa hakan ya zama sanadiyar dawowar memory dina ,wanda na rasashi na tsawon lokaci ta dalilin jefar dani dasu barde da kurtagu sukayi a daji mai tattare da tarin duwatsu.....',badiyya cike da mamaki ta katse bolaji ta hanyar cewa 'ke kuwa mujiba meye hadaki da barde da kurtagu,naga baki dade da zuwa fadar nan ba..',bolaji tayi murmushi wanda ya taho da zubar hawaye sannan tace 'badiyya ki nutsu kiji labarin da zan baki domin BOLAJI ce a gabanki mai dauke da fuskar MUJIBA'(nan ta kwashe labarin yadda suka kwashe da sultan a ranar da yazo yi mata fyad'e,da kuma lokacin data farfado ta ganta a hannunsu barde ,har izuwa lokacin da fulani ta fara yanka mata fuska da aska wanda hakan yayi sanadiyar sumarta ,kuma bata kara sanin in da kanta yake ba sai ranar data farfad'o a matsayin wacce tayi loosing memory dinta,zamanta a asibitin,tafiyarta kasar waje tare da hisham domin gyara mata fuska,canjin fuskarta,rayuwarta a gidansu hisham da kuma zuwanta fada domin sanin ko wacece ita,soyayyar da sultan yake ikirarin yake mata da kuma auren hashim da fulani take so tayi ),badiyya mamaki ne ya cikata ,domin tabbas zancen mujiba(bolaji) akwai kamshin gaskiya ,amma duk da haka sai tayi ajiyar zuciya tare da cewa 'toh a gaskiya mujiba ranar da matar yarima aka ce ta bata a fada ,bazan manta ba a ranar mu kazo wucewa tare da fulani ta gaban dakinsu,sai kawai mukaji karar bugu,sai fulani ta bamu umarnin tsayawa sai ita ta shiga ciki,bayan wasu mintuna sai tafito ta sallami kowa tace ni in tsaya ,sannan ta bani umarnin in kirawo jakadiya,a gaban idonaa ta umarci jakadiya akan taje ta kirawo mata barde da kurtagu,ni kuma tace in biyota cikin dakin,da muka shiga na hango matar yarima a kwance daure da towel cikin rashin hayyacci,sai kuma sultan a tsaye a gefe cikin yanayi na tashin hankali,ni dai umarni fulani ta bani wai in sanyawa matar yarima doguwar riga,ina gama saka mata tace min na tafi. toh nidai daga lokacin sai zancen bacewarta ne ya ne ya karade fada(ta labarta dawowar hashim,kawo gawar da fulani da tayi a matsayin gawar bolaji da kuma shiga coman da hashim yayi sanadiyar ganin gawar)',badiyya ta tsurawa bolaji idanu kamar tana son karanto wani abu a tattare da ita ,sannan tace 'toh yanzu dai abin nufi kenan a nan shine fulani,nawwara ,jakadiya,barde da kurtagu suna da sa hannu wajen kawar da matar yarima daga fadar nan?', ',sai kuma tayi ajiyar zuciya tare da dafe kuncinta sannan ta cigaba da cewa ' idan har kece matar yarima ,toh gawar waye fulani ta kawo a matsayin gawar Bolaji?' Bolaji tabata amsa da cewa 'amsar da nima nake neman amsarta kenan,amma a yanzu ya zama dole ki yarda dani ,wallahi tallahi nice bolaji matar hashim',a take ta bawa badiyya labarin asalinta ,jifan da maami tayiwa maimartaba,fansar hashim...........har izuwa aurensu ! Badiyya tayi jim tare da yin wasu tunane tunane sannan tace 'toh ranki shi dade idan ni na amince cewa kece matar yarima ,taya zaki gamsar da sauran mutane har su yarda cewa ke din ce',bolaji tashi tayi daga kan gadonta tazo kusa da badiyya ta zauna ,sai ta dafata tare da cewa 'ni duk wannan bai dameni ba ,abin da ya dameni shine auren hashim dake kaine ..' Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/18, 7:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~53~ Badiyya ta katseta ta hanyar cewa 'auren dake kanki ba matsala bane ,domin mijinki kawai zaki komawa,dadin abun ma ,bakiyi aure kan aure ba',bolaji ta share hawayen daya zubo mata tare da cewa 'ya zanyi da hisham,me zance masa ,ta ina zan fara shaida masa cewa ni matar aure ce ',sannan ta dubi badiyya cikin ido tare da cewa 'wallahi badiyya da babu auren hashim akaina ,babu abinda zai hanani auren hisham,domin hisham ya cancanci in aureshi,kinga ni wallahi da hashim zai sawwake min dana huta ,domin hisham .....',badiyya ta tare numfashinta tare da cewa 'dakata ranki shi dade kar ki ma soma wannan zancen ,ki fa tuna ke matar aure ce ,kuma ko ba komai ya kamata ki bawa aure darajar sa,kuma yarima yana sonki ,ni a ganina duk wani masoyinki ya biyo bayan yarima ,kuma ko ba komai yakamata yarima ya samu tausayawa daga gareki', bolaji ta yi jim sannan tace 'har ga Allah na tausayawa hashim musamman ayanzu da yake kwance tamkar matacce',badiyya tace 'addu'a zaki cigaba dayi masa ,Allah ya tashi kafadarshi....' , bolaji ta amsa da 'amin',tare da kuma tambayar badiyya da cewa 'ina nawwara kuwa?,zan so in ganta.. ',badiyya tayi kwafa tare da cewa'nawwara ta zama sirikar ki domin yayanki take aure ,tana can garinku',bolaji ta ware idanu tare da cewa 'kina nufin nawwara ta zama matar bamidele?",nan badiyya ta kwashe labarin soyayyar nawwara da bamidele da kuma tawayen da nawwara tayi wa fulani da sauransu ta labartawa bolaji! Bolaji ta jinjina lamarin tare da cewa 'amma ya kamata ace nawwara ta shaidawa mijinta gaskiyar al'amari game da bacewata daga fada',badiyya tace 'tabbas da ace ta fada mai gaskiya,ina ga da har yanzu ana kan bincike domin nasan bazai dau abin da wasa ba,amma inaga ita ma shirun tayi kamar yadda sauran sukayi shiru',bolaji ta amshe da cewa'amma kuwa da nawwara taci amanar so...',badiyya ta katseta ta hanyar cewa'kar kiga laifinta,domin zai iya yiwuwa tayi shiru ne bisa rashin sanin kina raye ko a mace ,kuma sanin kanmu ne aurenta da yayanki zai iya zama matacce da zarar ta gaya masa gaskiya,kinga kenan soyayya ce zata sa ta gimtse bakinta domin masoyi yana iya yin komai don ganin bai rasa masoyinsa ba',bolaji tace 'kuma hakane',sannan to dora da cewa 'toh ni dai yanzu na rasa yadda zanyi ,ta ina zanfara fuskantar gyara rayuwata da fulani ta rugurguza mini da makircinta? ',badiyya ta dubeta tare da cewa'ranki shi dade....!',bolaji ta dakatar da ita ta hanyar cewa 'kicigiba da kirana mujiba kawai',badiyya tace 'toh ',sannan ta cigaba da cewa 'da farko ya kamata mijinki ya ci darajar aure ya samu kulawarki,domin kulawarki gareshi zai iya zamowa silar tashinsa ',bolaji tace 'toh zan jarraba,hisham kuma fa ya zanyi dashi',badiyya tace kawai ki gaya masa gaskiya,saboda....',bolaji ta tari numfashinta ta hanyar cewa'bazan iya ba ,bazan iya jurar ganin hisham cikin tashin hankali da bakin ciki ba,ya rasa mujiba a karo na farko,da wani idon zan dubeshi kuma da wani bakin zan shaida masa cewa ya rasa mujiba a karo na biyu',sannan ta fashe da kuka mai tsuma zuciya domin har ga Allah zuciyarta na kaunar hisham,cike da tausayawa badiyya tace 'toh Allah ya kawo miki mafita a cikin wannan al'amarin,tabbas hisham ya cancanci a tausaya masa',sannan tace 'game da sultan kuwa kawai ki watsar da lamarinsa .....',bolaji ta amshe da cewa 'kyaleni dashi zanyi maganinsa ,wallahi sai na wahalar dashi,sai na dandana masa bakinciki,sai rayuwarsa ta salwanta kamar yadda ya zama sila ga salwantar tawa rayuwar',badiyya ta jinjina al'amarin sannan tace 'toh mu barwa gobe komai ,domin dare yayi sosai ,ya kamata mu kwanta haka ',bolaji ta tashi ta koma kan gadonta ta kwanta ,zuciyarta na tufka da warwara,badiyya ta kashe wuta sannan ta kwanta ita ma ,bayan minti daya sai badiyya tace 'kinyi bacci?', da "a'a",bolaji ta amsa ,sai badiyya tace'kinsan me yake bani mamaki?',bolaji tace'sai kin fada',badiyya tace 'kin bar fada a matsayin BAYARABIYA ,gashi kuma kin dawo a matsayin BAHAUSHIYA!',bolaji tace'ikon ALLAH kenan',badiyya tace'tabbas zancenki dutse,babu ta yadda Allah baya tsarawa bawansa lamarinsa,ke d'aya kin zama mai suna biyu',bolaji tace 'da kuma YARE BIYU! a haka gwanin sata ya sace su! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/18, 7:20 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~54~ Washegari da safe bayan an gama yin breakfast ,bolaji taje daki ta samu fulani,ko da tashiga fulani ta dubeta tare da yin murmushi tace'mujiba yaya dai?',bolaji ta gimtse bakin cikinta tare da shimfida wani irin malalacin murmushi akan fuskarta tace' magana nake son muyi in bazaki damu ba',fulani ta sallami ko wacce kuyanga dake cikin dakin ,sannan ta dubi bolaji tace'ke nake sauraro',bayan sun zauna akan couch,bolaji tayi gyaran murya tare da cewa'game da batun hashim ne,na amince zan aure shi.....',fulani murna fal cikinta ta rungumo bolaji tana cewa ' wallahi mujiba kin gama yimin komai....... ',bolaji ta katseta ta hanyar cewa'ina son kulawarsa ya dawo hannuna,kuma zan koma dakinsa da kwana',fulani tayi jim kamar tana tunani ,bolaji ta katse mata tunani ta hanyar cewa'me kike tunani?,ko kina tsoro ne?',fulani tayi zuru ba tare da tanka mata ba,bolaji tayi murmushin yake tare da kada kanta sannan tace.'ki kwantar da hankali ,babu abinda zai faru tsakanina da hashim,ki yarda dani,ki cire zargi daga zuciyarki,bazan cutar dashi ba', fulani tace'nifa ba zargin komai nake ba,na yarda da hashim ko dayake da lafia mace bata dameshi ba ,balle kuma yanzu da baida lafia,kawai abin da nake tsoro shine kar mai martaba yaji kina kwana a dakin,muzo mu shiga uku',bolaji ta dubeta tare da cewa a zuci 'zaki shiga miliyan uku ne a ranar da asirinki ya tonu',amma a zahiri sai tace 'shikenan zan dinga kula dashi kawai ,domin ina son in shaku da mijin da zan aura ',fulani tace'shikenan mujiba,kinga kenan da zarar kin koma gida sai ayi zancen aurenku',nan suka cigaba da hira fulani tana mai bawa mujiba(bolaji) labarin (karya da gaskiya)bolaji! Ganin hirar bazata kare ba yasa tayiwa fulani sallama,hakan yasa fulani tace 'muje in rakaki dakin hashim',suna shiga dakin suka tadda hadimai maza guda uku da suke kula dashi ,suna goge masa jiki da towel da ruwan dumi,daga vest sai short knicker ne a jikinsa,duk sunyi kalar datti ,kwalla ya cikowa bolaji a ido,a wayance ta goge ,sannan ta dubi fulani tace 'kice musu su tafi',fulani cike da mamaki ta umarci hadiman da su fice,sannan bolaji tace mata ''ke ma ki fita!' ,fulani cike da takaici tace'in fita inje ina?',sai bolaji ta juya da niyyar fita ,fulani ta tsaidata tare da cewa 'haba mujiba,kar muyi haka da ke,ina zaki je','fita zanyi daga dakin tunda har yanzu baki aminta dani ba,ina son kasancewa da mijina,domin babu wanda ya dace ya bashi kulawa face ni matarsa',fulani ta maimaita kalmar 'mijinki? matarshi?',bolaji ta amsa da cewa'matarsa mana,tunda shine mijin da zan aura ,ya kamata tun yanzu in fara koyan yadda zan kula da shi tun kafin muyi aure,idan kuma baki aminta dani ba shikenan,sai na bar miki danki kawai,naga macen da zata aureshi a haka',fulani ba tace uffan ba ,da hanzari ta fice daga dakin! Tana fita bolaji ta sawa kofar dakin key ,sannan ta wuce toilet din dake cikin dakin, ta hado ruwan dumi a bowl tare da zuba antibacterial da bathing perfume ,sannan ta zo ta ajje a gefen gadon da hashim ke kwance ,cike da tausayawa tasa karfinta ta cire masa singlet din da short nicker,sannan tasa towel a ruwan tana goge masa jikinsa ,hawaye na zuba daga idanunta,yau oga hitler ne a kwance tamkar matacce ,inda ranka... A haka tagama gogeshi,sannan ta dauko masa singlet da vest masu kyau ta feshesu da turare ta saka masa,ta shafa masa lotion,ta taje masa kai,ta gyara masa kwanciyarsa ,ta maida bowl da towel din toilet,sannan ta dawo ta kwanta a gefensa tana mai shafa masa kai ,bakinta na karanto addu'o'i tana tofa masa ! *BAYAN SATI DAYA* Sultan rayuwa tayi masa dadi mujiba ta amshi tayin soyayyarsa bisa sharadin ya daina nuna mata so da kulawa,kuam ya daina zuwa gunta abangaren cikin gida,saboda kar mahifiyarsa (fulani)ta sa musu ido,shi kuwa ya aminci,daman burinsa mujiba ta soshi,amma duk dare sai yaje gunta bangaren bayi sunyi zance, ita kuwa bolaji tayi hakan ne saboda ta wahalar da zuciyarsa,domin tasan cewa ko da maza sun kare a duniya bazata auri sultan ba! A bangaren hisham kuwa ya je wani seminar a abuja,yana trying wayar bolaji a kashe,hankalinsa duk ya tashi,kuma gashi sai nan da kwana biyar zai dawo! Kulawa sosai bolaji take bawa hashim ,ta gogeshi,ta chanja masa vest da shortnicker ,ta wankesu a toilet ta shanya,ta yanke masa farata,bata barin hadimai da kuyangu su shigo dakin ,badiyya kadai ke shigowa ita ma shara da goge goge takeyi ta fita,fulani kuwa ta yaba da kulawar da mujiba(bolaji) take bawa hashim! Bolaji kuwa a dakin take wuni,tayi sallah ,ta ci abincinta,sai dare take komawa bangaren bayi,domin in ta gama yi masa duk abinda ya dace ,sai ta sawa kofar dakin key ,ta zo ta kwanta a gefensa tana masa hira,da surutai,ko kuma ta kwanta a kan kirjinsa ,wani lokacin har bacci ne yake dauketa! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/18, 7:21 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~55~ Yau ma kamar kullum bayan ta gama yiwa hashim duk abinda zata yi masa ,sai ta hau kan gadon ta kwanta gefensa tana mai shafa masa kai ,tana masa hira ahaka bacci ya dauketa,ba tare da ta sawa kofar dakin key ba! Ummu ce ta shigo bakinta dauke da sallama,kasancewar bata cika yawo da hadimai ba acikin gida,ganin bolaji kwance akan kirjin hashim yasa ta fara jero salati,sanadiyar hakan yasa bolaji ta tashi a firgice,ganin ummu a tsaye da kuma alamun bacin rai akan fuskarta,yasa ta sauko daga kan gadon tana mai sunkuyar da kanta! Ummu ta dubeta sannan tace'mujiba wacce irin rayuwa ce wannan?,me ya kai ki kwanciya tare da namijin da ba muharraminki ba?',bolaji shiru tayi ta kasa cewa uffan,hakan yasa ummu ta cigaba da cewa'ya zama dole ki bar fadar nan a yau,domin zamanki acikinsa babu amfani....',bolaji ta tari numfashinta ta hanyar cewa 'ranki shi dade meye aibu aciki,don na bawa yarima kulawan da yake bukata ,meye aibu don na zamo mace me yin aikin lada....','lada ko zunubi?,muharraminki ne?,wannan ba hakkin ki bane kuma ba aikinki bane ,baki da wata hujja mujiba ,ki tashi kawai ki fice ,kuma ki shirya komawa gidan iyayenki a yau',bolaji idanunta ya ciko da kwalla tare da juyawa ta dubi hashim dake kwance tace'OGA HITLER please wake up and make everything clear,you are my only hope now ,ka tashi ka sake ni ,i want to be free,i want hisham to be my husband',tana gama fadin haka ta tashi ta fice daga dakin ba tare da ta dubi ummu ,wacce mamaki ne yayi mata dirar mikiya 'wacece mujiba ?,wacce irin alaka ce tsakaninta da hashim da hisham?',tabbas mujiba ce kadai zata bata amsoshin tambayoyin da zuciyarta suke bujiro mata ,jiki a sanyaye ta fuce daga dakin ba tare da ta lura da hashim dake motsa yatsunshi da kuma bakinsa dake furta 'my better half' a sanyaye! Bolaji ta labartawa badiyya abinda ya faru ,badiyya ta bata shawaran akan ta shaidawa ummu gaskiyar wacece ita! Fulani ce ta iske hashim a zaune ya dafe kansa da hannu biyu ,sauran kadan numfashinta ya dauke saboda murna,da gudu ta karasa gareshi ta rungumeshi tare da cewa'Alhamdulillah my souldear has recovered',idanunta na zubar da hawayen farin ciki! Kafin ace me,fada ya karade da murnar farfadowar yarima hashim,dr.ayuba yazo ya dubashi tare da tabbatar musu da cewa babu matsala sai dai sanadiyar dadewar da yayi a kwance yasa ba zai iya tafiya da kafafunsa ba ayanzu, sai nan da dan wasu lokutan kafar zai warware ya fara tafiya , amma sai dai using wheelchair for now,kafin ya warware gaba daya! Hashim kuwa bai da zance sai na bolaji ,ita kuwa fulani cewa take 'ta mutu ,kawai ka hakura da ita,zan aura maka mujiba', hashim sai ya dubeta yace'No !,my better half is alive,i felt her presence!' ,bolaji kuwa da labarin farfadowar hashim ya isketa ,sai da tayi nafila raka'a biyu tana mai godewa Allah ! Badiyya ce ta shigo ta sameta tare da ce mata 'mujiba ranki shi dade na nemanki '',bolaji ta tashi ta bi bayanta,a daki suka iske ummu ,bayan badiyya ta basu waje,sai ummu tayi gyaran murya tare da cewa 'mujiba ki gaya min gaskiya ,wacece ke ,meye alakar ki da hisham ,yayanki ne wanda kuka fito ciki daya ko kuma me ?',mujiba murya a sanyaye tace 'babu alaka ta jini tsakanina da hisham ,sai alakar so,wanda nake zaki zamto sila ga cikar burinmu na zama ma'aurata ta hanyar sanya hashim ya sake ni ',ummu ta dubi bolaji cike da mamaki tace 'ya sake ki ?,dama akwai wani aure ne a tsakaninku wanda ni ban san da zamansa',bolaji tayi murmushi mai ciwo tare da cewa 'zan baki labarina tun daga haduwata(oga hitler) da hashim,har izuwa dalilin da yasa hisham ya kawo ni fada a matsayin kanwarsa',a take bolaji ta labartawa ummu( naja'atu ) komai da ya shafi rayuwarta ,sannan ta dora da cewa 'nasan bai zama lallai ki yarda dani ba saboda nazo da wata fuska,suna da kuma YARE daban,amma ina son ki fara bincike da kanki ,zaki ji labarin haduwarmu da hashim har izuwa aurenmu daga bakin MD ,sannan kuma ki tuntubi sultan da batun bacewa ta daga fada ,duk da ba zaima lallai ya fada miki gaskiya ba !',ummu kanta ne ya kulle gaba daya domin dama can ba ta san da batun daukar fansa da hashim da yaje yi a yankin Erin! Tirkashi fulani kin gama salwantar min da rayuwar ya'yana ! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 11:46 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~56~ Ummu a take ta nemi number din MD ta kira ,ba tare da bata lokaci ba ya labartawa ummu komai dangane da haduwar bolaji da hashim har izuwa aurensu ,bayan sun gama magana , sai ta cigaba da sake saken yadda zata bullowa al'amarin ,amma ta rasa mafita saboda rashin kwakwarrar hujja domin kuwa idan har mujiba ce bolaji ,toh gawar wacece fulani ta kawo a matsayin gawar bolaji! A bangaren bolaji kuwa dakinsu ta wuce tare da janyo wayarta ,tana kunnawa messages din hisham suka dinga shigowa ,ba ta kai ga dagawa ba ,sai ga kiransa ya shigo,cike da tausayi ta amsa wayar tare da karawa akan kunnenta tana mai yi masa sallama,ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa '.mujiba meya faru ne kullum wayarki a kashe idan na kiraki ',bolaji tayi murmushi tare da cewa ''tsabgogi ne sukayi min yawa shiyasa ma wayar nake mantawa da ita ,yasu hajiya da zuhra ,ina zahra ?,nayi missing dinsu sosai',hisham yace'suna nan lafia ,ni kuma bakiyi missing dina ba ko?',murmushi kawai tayi mai sauti ,hisham yacigaba da cewa 'ba na gari naje abuja seminar amma gobe insha Allahu zan dawo ,da zarar na dawo zan zo in ganki ,hope kuma an dace ?',bolaji ta amsa da cewa 'sai dai goben in kazo kawai ",sannan kuma sai tace masa 'abokinka ya warke fa ,dazu naji labarin wai ya farfado',hisham yayi murna sosai ,a haka sukayi sallama da junansu akan gobe zai zo ,bolaji ta dubi wayar idanunta na fitar da wasu zafafan hawaye soyayyar hisham da kuma tausayinsa ne yake nukurkusar zuciyarta! Washe gari fada aka tashi da shiryen shiryen walimar(DINNER) farfadowar hashim,bisa umarnin fulani,dafe dafe kawai akeyi da gyare gyare ,palace event hall yasha ado da decorations,duk wani abu da ake buqata tundaga kan mutanen da za a gayyata da kuma abinda za'a ci asha duk is in order ,abin gwanin sha'awa sai wanda ya gani! Bolaji ita ma ba'a barta a baya duk da yawaitar faduwar gaban da ta ke yi hakan bai hanata shiga cikinsu badiyya ta tayasu aiki ba,suna cikin yin aikin ne ,sultan ya aiko a kirawo masa ita ,jiki a sanyaye ta je ta same shi a palace parlour ,murmushi yayi mata tare da mi'ka mata wata katuwar leda ,tare da cewa 'take this ,i want you to wear them for todays event ,i hope you love it ',bolaji ta amshi ledar tare da cewa' thanks ',sannan ta wuce dakinsu ta ajje ledar ba tare da ta bude ba, sannan ta dawo kitchen suka cigaba da baking and frying ! Ummu kuwa kanta ne ya dau chaji daga jiya zuwa yau,daga karshe kawai ta yo alwala tare da yin sallah raka'a biyu tare da rokon Allah ya bayyana duk wani boyayyen al'amari ,ya kuma bayyana gaskiya a duk inda take ,a haka tasamu zuciyarta tayi sanyi tare da kuma fawallawa Allah lamarin fulani da sultan! Misalin karfe 7:00pm angama duk wani shirye shirye ,palace event hall ya zama ready,guest sun fara isowa ,manyan mutane sun fara hallara ! Bolaji ta fito daga wanka ,ta shafa body lotion,badiyya ta tayata taje kanta tare da yi mata packing,a lokacin ta tuna da ledar da sultan ya bata dazu, daukawa tayi ta bude ,red dinner gown ne mai adon crystal stones ,hannunsa dogo ne,sai kuma red velvet turban shima anyi masa ado da stones,da kuma high heel shoe silver mai adon cystal stones da kuma box of diamond earring and wristwatch, badiyya ta saki baki tana yaba kyawun kayan ,tare da tambayar bolaji da cewa 'ke kuwa mujiba ina kika samo wadannan kaya haka',bolaji ta dubeta tare da cewa 'sultan ne ya bani su dazu....',,badiyya ta tabe baki tare da cewa 'ban san meye hujjarki na kula wannan yaron ba ,ko da kuwa fansa kike san dauka akansa bai dace ki amshi soyayyarsa tare da kuma kayansa ba',bolaji tayi murmushi tare da cewa 'laifine idan na amshi kyauta daga gun kanin miji na',badiyya zata bata amsa kenan wata kuyanga tayi sallama tashigo dakin tare da cewa 'badiyya kizo jakadiya na nemanmu agun taron walima ', daman a shirye take,kawai sai ta tashi ta fice , bolaji ta shirya cikin gown din ,kayan sun amshe ta sosai,light and flawless make up kawai tayi powder ta murzawa fuskarta sannan ta shafa gloss a lebanta ,tayi kyau sosai ',ta saka earring da wrist watch ,sannan ta sanya takalmin,ko da ta kalli kanta madubi ita ma ta yaba da kyawun fuskar mujiba,murmushi tayiwa kanta sannan ta fice daga dakin! A parlour suka hadu da fulani ta ci ado da leshi da gold ,ga kuma alkyabba ,hadimai na biye da ita ,fulani ta dakata tare da duban mujiba tace 'wow kin yi kyau mujiba '',bolaji tayi murumshi tare da sunkuyar da kanta ,fulani tace 'kije ku taho tare da souldear ,angama shiryashi ',fulani nagama fadin haka ta bar wajen ita da hadimai suka wuce wajen walima ! Bolaji ta wuce dakinsu(ita da hashim),a shirye ta iske hashim zaune akan wheel chair ,yayi kyau sosai har ya gaji da kyau,bolaji ta karasa ta gaishe shi tare da taya shi murnar samun lafiyarsa ,murmushi yayi mata tarea dacewa 'all thanks to you mujiba ,you just acted like my late wife ,nagode sosai da kulawarki gareni ,amma ina son in tambayeki wani abu mana?', bolaji tace 'ina sauraronka ',hashim yace 'taya kika san cewa matata tana kirana da oga hitler?',bolaji tayi murmushi tare da cewa 'ummanka ce ta bani labarin ka da matarka ,saboda tanason in maye gurbinta a wajenka....',hashim ya katseta ta hanyar cewa 'i'm sorry to say mujiba ,a gaskiya no one can replace my better half,she's irreplaceable in my heart ,ita kadai ce macen da na fara so a rayuwata ,kuma itace ta karshe ,you can act like her but you can never be her,i will keep on loving my better till my last breath ,so bazan iya aurenki ba mujiba, saboda na daukar wa kaina alkwawarin ni da aure har abada ,tun da na rasa mata ta ,babu wacce zata iya maye mini gurbinta a zuciyata ',sannan ya goge kwallan daya zubo masa daga ido , sannan yace'bakin ciki na daya a duniya rashin samun soyayyarta a gareni.....',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'Allah ya jikanta ya rahamsheta,muje we are running late....',sannan ta turashi akan wheelchair sukafice daga dakin! Palace event hall ya cika ya batse da manyan mutane tun daga kan sarakuna har izuwa gwamnoni da kuma business tycoons ,a gaban kofar shiga hall din sultan ne a tsaye sanye da redvelvet suede suit tare da farin shirt da black cover shoe ,yayi kyau sosai,su bolaji na isowa ya tare su da murmushi sannan ya durkusa ya rungume hashim yana cewa 'bro u look handsome',hashim ya buga bayansa tare da cewa 'thanks ',sultan ya mike tsaye ya dubi bolaji cike da shauki ya matsa kusa da ita yana mai mata rada a kunne da cewa 'wow you look gorgeous,magnificent,beautifull and elegant my love ',matsawa tayi kadan tare da cewa 'all thanks to you ',hannunsa ya dora akan wheelchair din suka tura hashim ,a daidai lokacin hisham ya iso gun bisa jagorancin royal guard ! kiran sunan mujiba yayi ,hakan yasa ta juyo ,murmushi yayi mata tare da mikawa sultan hannu sukayi musabaha ,sannan ya durkusa gaban hashim sukayi musbaha tare da rungume juna suna masu murnar ganin junansu ,hashim cike da murna yace 'hisham kenan tunda muka gama NMS muka watsar da junanmu ',sultan ya katsesu ta hanyar cewa 'save all that for some other time ,the guest are waiting ! A haka su hudu suka dunguma suka shiga hall din! Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 11:47 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~57~ Suna shiga hall din kallo ya dawo kansu ,kasancewar spotlight din daya haskaka su, a haka suka karasa table din da'aka tanadar musu ,kasancewar the hall is decorated with round tables masu dauke da sixchairs,bayan ko wannensu ya zauna ,hashim shima aka gyara masa zamansa akan wheelchair,sai governor na wannan lokacin ne ya hau stage ya bude taro da addu'a tare da taya mai martaba da iyalansa murnar farfadowar yarima hashim,mai martaba shi ma ya fita yayi nasa jawabin tare da yin godiya ga Allah ,haka zalika ummu da fulani su ma sun hau stage sunyi nasu jawabin,daga nan sai hadimai suka fara serving ,bayan angama refreshment,firstlady din garin sokoto ta fito ta bada tarihin masarautar modibbo ,daga nan sultan ya fita shima ya bada tarihin hashim ,sai kuma hisham ya tura hashim zuwa stage din,sultan ya bashi mic ,da farko yayi godiya sosai ga Allah,iyayensa da kuma guests din suka hallarci wannan taro ,sannan kuma ya bukaci ayiwa marigayiya bolaji addua tare da kuma yi wa kowa fatan komawa gida lafia!, hisham ne ya tura shi suka koma mazauninsu ,masu daukan hoto sunayi masu video taping suma sunayi ,yayan manya kuwa sai selfie suke ana dorawa a instagaram ,sultan ya amshi mic tare da cewa " i want to make an important announcement but please i want mujiba to come forward to the stage',bolaji gabanta ne ya fadi ,gashi an kuma haskota da spotlight ,hisham ne yayi mata murmushi tare da yi mata alamun cewa tashi kije ,domin ko kadan bai kawo komai a ransa ba ,hakan yasa bolaji ta tashi ta tafi stage ,kowa ya yaba da class and charisma dinta,domin kayanta sunyi mata kyau matu'ka ,sultan ne ya dubeta yayi murmushi sannan ya dawo da kallonsa ga jama'a yana cewa 'this is mujiba ,the love of my life,the half that completes me ,my wife to be insha Allah .......',hisham hankalinsa ya tashi,idanunsa sukayi jajawur saboda wani irin zazzafan kishi dake nukurkusarsa,ranshi a bace ya tashi ya fita daga hall din ba tare da yayi wa hashim sallama ba ,akan stage kuwa sultan yayiwa wata hadima alamu da hannunsa ,hadima ta karaso rike da wani farantin gwal a hannunta mai dauke da ring box,sultan ya bude box din ya ciro diamond ring din,sannan ya durkusa a gaban bolaji ,tuni hall aka fara tafi ,yan mata da samari suka fara daukansu hoto ,fulani idan ranta yayi dubu yaa baci,,sultan ya kamo hannun bolaji yana cewa 'mujiba i want you to be my mrs,i want you to be the mother of my children,i want you to complete me and spend the rest of ur life with me ,mujiba will you marry me ?",bolaji ta fisge hannunta ,tare da cewa 'No ,i will not and will never marry you',sannan ta juya ta sauka daga kan stage din,tare da ficewa daga hall din gaba daya,sultan kuwa mutuwar tsugunne yayi ! Bolaji tana fita daga hall ,hisham ya tareta sannan ya damki hannunta ya jata zuwa inda yayi parking motarsa ,idanu jajir ya dubeta tare da kama kafadarta yana cewa 'mujiba menene tsakaninki da sultan?',bolaji jikinta na rawa saboda ta tsorata da yanayinsa tace 'wallahi tallahi babu wani abu tsakanina dashi ....',hisham yace 'toh shikenan,shiga mota mu koma gida,zamanki a palace dinnan ya kare,domin bazan zuba ido wani kato ya kwacemin ke ba ....',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'hisham kayi hakuri bazan iya bin ka ba',hisham ransa a bace yace 'saboda ki zauna da masoyinki ko ?,saboda kin samu wanda ya fini ko ?.... ',bolaji idanunta suka fara tsiyayar hawaye saboda kalaman hisham sun soki zuciyarta ,murya a raunane tace 'hisham try and understand my memory is back ,ni matar aure ce ,hashim ne mijina ',hisham mutuwar tsaye yayi ,baki bude ya tsaya kallon bolaji ,sannan kawai ya kwashe da dariya wanda yazo da zubar hawaye yace 'mujiba kenan ,ta nan kika bullo ,daman tsintacciyar mage bata mage ,kwadayi da son zuciya sunyi miki jagora wajen alakanta kanki da hashim a matsayin matarsa ta aure ,mujiba kin bani mamaki ,wato kwadayin dukiya da daular sarauta sun sa zaki gujeni.... ',mamaki ne ya kama bolaji ,cike da firgici ta bude bakinta tana cewa'hisham...',dakatar da ita yayi ta hanyar cewa 'baki da abin da zaki ce min mujiba ,everything is crystal cleared to me ,nagode mujiba ,rayuwa ce',bai jira jin ta bakinta ba ,ya fada cikin mota ,ya tayar yayi reverse ,guards suka bude mai gate ,ya fice a guje! . Bolaji kuka ne ya kwace mata sosai,kalaman hisham suna dada yi mata kuwwa a kwanyarta!,jiki a sanyaye ta koma cikin gida ! A parlour tayi kicibis da fulani ,fulani ta rungumota tare da cewa 'mujiba kinyi min daidai da kikayi denying proposal din sultan ,da yardar Allah baki da mijin da ya wuce souldear ',bolaji ba tace uffan ba ta wuce kitchen tana matsar kwalla ,badiyya ce tashigo kitchen din ,ganin bolaji tana kuka yasa takarasa gareta tare da dafata tana cewa 'lallai sultan yayi rashin hankali ,amma koma menene laifinki ne da kika amshi soyayyarsa.....',wasu hadimai da kuyangu ne suka shigo kitchen din da kayan wanke wanke niki niki ,hakan yasa badiyya tayi shiru ,su kuwa cewa suke ' a gaskiya mujiba kin yi ganganci ,kowa ganin rashin kyautawarki yake yi,sultan guda ya nemi aurenki amma ki watsa masa kasa a ido ....,ko kallo basu isheta ba balle ta tanka musu,sultan ne yashigo kitchen din a birkice ,sannan ya umarci kowa ya fice daga kitchen din ,he wants to be left alone with mujiba ,bayan kowa ya fice ,sai sultan ya dubi bolaji idanunsa na zubda hawaye yace 'why mujiba ? Please why ?',uffan batace ba ta yi hanyar ficewa daga kitchen din,hannunta ya damko yana cewa 'babu inda zaki sai kin gaya min dalilin da yasa kikayi denying proposal dina ',idanu jajir ta dubeshi tare da cewa 'saboda bana sonka ,na tsaneka ,na tsaneka sultan',sultan baki bude ya tsaya kallonta ,cike da takaici bolaji tace 'ka cika min hannu na ',sultan ya tattaro duk wani jarumta da ya rage , tare da cewa 'bazan cika ki ba ,har sai kinyi accepting proposal dina,ko kuma mu dawwama a haka ni dake ',ganin da gaske yake bazai cikata ba ,hakan yasa idanunta suka fara nema mataa mafita,hango wuka tayi a kusa dasu , daya hannunta tasa ta dau wukar sannan ta dora wukar akan hannunta da ya rike tana cewa'wallahi tallahi mujiba can cut her hand and give it to you,but you can never have her " ,sannan ta fara dadirawa hannunta wukar ,ganin jini ya fara fita yasa sultan ya cikata ,yana mai mamakin mujiba ,ita kuwa ta yar da wukar tare da ficewa daga kitchen bayan taja wani dogon tsaki.... Written by: ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 11:47 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~58~ Da Taimakon Allah hisham ya isa gida ,yana shiga ciki, ya zarce dakinsa ,ya rasa me yake masa dadi a duniya ,wai shi mujiba zatayiwa haka ,amma babu damuwa daman he saw it coming tunda ta kashe wayarta baya samunta yasan da walakin,yayi kuka sosai ,sannan ya tashi yayo alwala ya gabatar da sallah hakan yasa yaji sanyi a zuciyarshi,daga karshe sai ya kashe wayarsa gaba daya ,yayi kwanciyarsa ba tare da ya nemi kowa ba ! A bangaren bolaji kuwa ,daki ta shiga ,ta dauko wayarta ta fara neman wayar hisham ba tare da tabi ta kan ciwon dake hannunta ba ,'the number u r trying to call is currently switch off",amsar da matar network ke bata kenan,ta buga yafi sau ashirin ,amma amsa daya take maimaita mata,jiki a sanyaye ta watsar da wayar,tare da fashewa da kuka mai ciwo, cikin wannan yanayi badiyya ta shigo ta sameta ,"ke kuwa mujiba lafia kike kuka kamar wacce aka ce mata anjima zata mutu ta shiga jahannama","badiyya ina zan sa kaina ,hisham ya juya min baya.....(nan ta kwashe labarin yadda suka kwashe dashi dazu,ta fadawa badiyya),badiyya ta tabe baki tare da cewa 'sai me?,ba shi ya jiyo ba,idan tayi wari shi ma zai jiyo ,ya kuma hakura ya bar wa yarima matarsa ',bolaji ta kara sautin kukanta ,badiyya taja wata doguwar hamma tare da yin mika ,sannan tace 'idan kin gama kukan tarawa kai zunubi,sai ki tashi kije mijinki na kira ',bolaji a fusace tace 'me kuma zanyi masa ?',badiyya tace 'ko ma me zakiyi masa ,ki tashi kije ,domin amsa kiransa yafi wannan kukan da kikeyi lada ",bolaji tayi mursisi tace babu inda zata ,ganin badiyya bazata kyaleta ba ,yasa ta tashi ta fice ba dan ranta yaso ba ! A bangaren sultan kuwa goma da ashirin ne suka hadar mai ,domin bayan bolaji ta fita ta kyaleshi a kitchen,jiki a sanyaye ya fice shima ,a hanyarsa na zuwa dakinsa , fulani ta tareshi tayi masa wankin babban bargo ,harda ce masa 'kaji kunya wallahi ,ni dana hada walima domin murnar samun lafiyar d'ana ,saika maida min walimar wajen aikata abinda ka koyo daga gun yahudu wa nasara ,ina d'an bahaushe kuma musulmi da proposing ,abinda ba al'adarmu bane balle kuma addininmu ',sultan murmushin takaici kawai yayi tare da wucewa dakinsa yana cewa a ransa 'daman umma ta san da Allah ,ta aikata abinda ta aikata ga bolaji'! ☆☆☆ Da sallama tashiga dakin ,a kwance ta iskeshi akan gado ,yana sanye da kayan bacci ,akan stool ta zauna tare da cewa 'gani !',hashim ya tashi ya zauna sannan ya dubeta tare da cewa 'sai yanzu ?',ganin bazata tanka masa ba yasa ya cigaba da maganarsa kamar haka'abinda kika aikata dazu a gun walima baki kyauta ba mujiba ,meyasa zaki yi denying proposal din dan uwana? Why?',"saboda bana sonsa kuma bazan taba son sa ba',bolaji ta bashi amsa ,hashim murya a kausashe yace 'ya zama tilas ki so shi domin,ni dinnan da kike burin mallaka ,bazaki sameni ba domin zuciyata da gangar jiki na duk mallakin matata ne,kamar yadda na fada miki dazu cewa ni da aure...',bolaji ta katseshi ta hanyar cewa 'ka daina yaudarar kanka hashim ,kai ma bana sonka kamar yadda bana son dan uwanka ,kuma kai da kake ikirarin cewa zuciyarka da gangar jikinka mallakin matacciyar matarka ce ,haka zalika nima tawa zuciyar da gangar jikina mallakin.....',sai kuma ta kasa karasawa,idanunta suka ciko da kwalla ,hashim yayi dariya sosai tare da cewa 'mujiba kenan dani dake wanene yake yaudarar kansa ,in har ba kya sona meyasa kika bani kulawa da duk wani kula da mata take bawa mijinta?',sannan yayi dariya ya kuma cewa'idan da babu so ko kauna ,hakan ba zai taba faruwa ba',murmushi bolaji tayi mai ciwo tare da cewa "hashim kar ka dauka nayi duk wannan ne saboda so ,nayi ne kawai saboda ina son in cimma wani buri ne a rayuwata",'wani buri kenan?',hashim ya tambayeta ,bolaji tace 'wannan kuma bai shafe ka ba ,yanzu kawai bukatarka shine in auri sultan ko?',hashim yayi murmushi yace'zan fi kowa farin ciki da faruwar hakan',bolaji tayi murmushi irin na gatse ,sannan tace 'toh zan auri sultan bisa sharadi guda daya tak','wanne sharadi kenan?',hashim ya tambayeta ,bolaji ta amsa da cewa 'sharadin shine ina son ka rubutawa tsohuwar matacciyar matarka takardar saki',a hargitse murya a kausashe hashim ya katseta ta hanyar cewa 'how dare you ?',bolaji tace 'dakata malam in gama magana,saki uku zaka rubuta ,ni kuma na maka alkawari idan har ka cika wannan sharadi zan auri dan uwanka ( a zuciyarta tace 'hisham kenan') ,hashim ransa a bace yace 'mujiba da ace ina iya tafiya da wallahi babu abinda zai hanani tasowa in zo sharara maki mari,kin haukace ne ,matar tawa kike son in saka ,never over my dead body wallahi',bolaji ta tafa hannunta tace 'aww ho ,matacciya kenan,ka kasa sakar matacciyyar matarka ,ta ya kake son ni kuma in rabu da rayayyen masoyina ,ka ga kenan ba zata sabu ba ',hashim ya dubeta idanu jajir tare da cewa'wai shin mujiba ,me cece alakarki da matata da kike alakanta ta a cikin sharadinki',bolaji ta tashi tsaye tare da cewa 'wannan kuma baza kaji daga bakina ba ,sai da safe ',tana gama fadin haka ta fice ,ta bar hashim da bacin rai ,ji yake tamkar ya tashi ya sha'kota ya sha'ka mata kamshin lahira! * * * Written by : ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 11:47 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~59~ Washegari da safe bayan an gama yin karin kumallo,mai martaba yayi wa sultan fada sosai game ga dabi'ar yahudu wa nasara dayayi a gun walima a daren jiya,sannan kuma ya ja masa kunne akan cewa kar ya kuskura yace zai takurawa yar mutane wajen tilasta mata ta aureshi ,ita ma fulani tazo da bukatar ta na son a hada auren mujiba da hashim,mai martaba ita ma yace mata baya son fa a tilastawa wani ko wata in dai maganar aurene idan har suna son junansu ,su zo su fada masa ba wai itace zata yanke hukunci ba ,don haka magana ta mutu kar a kara tada ita! A bangaren ummu kuwa tunda asuba ta bugawa MD waya tare da bashi umarnin ya je ya shaidawa bamidele da nawwara su zo sokoto a yau dinnan domin warware wani boyayyen al'amari game da bolaji! Ko da MD yaje gidansu bamidele ya shaida masa sakon ummu,babu bata lokaci ,yace nawwara ta shirya zasu wuce sokoto! Misalin karfe 11:00am ummu ta nufi dakin fulani ba tare da rakiyar ko wacce hadima ba ,ko da ta shiga dakin,fulani ta tarbe ta da fara'a tare da tambayarta dafatan lafiya ,ummu tace 'wata muhimmiyar magana nakeson muyi ,amma ina son ki sallami hadimanki',cikin 20secs gaba daya hadiman suka fice daga dakin, Bayan sun fice , sai ummu ta murzawa kofar dakin key ,tare da karasawa gun fulani ,fulani kuwa tuni tasha jinin jikinta ,amma bata gama shan jinin jikinta ba sai da ummu tace 'fulani ki dubi girman Allah da manzonsa sallallahu alaihi wa salam,ki fada min gaskiya ,meye faru a ranar da muka fita rangadi da mai martaba ?",fulani bakinta na rawa tace 'naja'atu wacce irin tambaya ce wannan,ni ban gane abinda kike nufi ba ,meye faru kuwa ',ummu ta ja numfashi ,murya a tausashe tace 'abinda nake nufi shine ina son sanin gaskiyar abinda ya faru game ga al'amarin batan bolaji ?',fulani duk sanyin a.c da ya gauraye dakin,sai da zufa ya fara keto mata ,a fusace ta fara cewa'haba naja'atu wacce gaskiyar kike nema bayan guduwar da yarinyar nan,dalilin haka ta riski mutuwarta na kuma tsinto gawarta a asibiti',ganin yanayin fulani yasa ummu ta fara yarda da cewa zancen mujiba akwai alamun kamshin gaskiya ,sanin cewa fulani ba kanwar lasa bace yasa tace 'zan kara tambayarki a karo na karshe ,ki gayamin gaskiya....',cike da masifar wanda hausawa suke cewa tabarmar kunya.....,fulani ta juyawa ummu baya tana cewa 'wai shin me kike nufi ne naja'atu ,wani irin titsiye ne wannan,kina nufin nice nake da sa hannu game da bacewarta daga fada?',ummu ta amsa mata da cewa 'ba wai ina nufi bane ,ni ina da tabbacin cewa kece ki kulla duk wani kulle kullenki game ga bacewarta daga fada ',a zafafe fulani ta juyo tana cewa 'amma naja.....', ji kake TAS! wani wawan marin bazata ummu ta zabgawa fulani ,wanda hakan yasa fulani ta katse maganar da zatayi tare ta dafe kumatunta tana kallon ummu cike da mamaki,'ni kika mara ?' Fulani ta jefeta da tambayar,ummu tace 'eh na mareki ,kuma zan cigaba da marinki idan har bazaki fada min gaskiya ba,domin babu mutuncinki da kuma darajarki na kasancewarki uwargida da ya saura a cikin idanuna',fulani ta daga hannunta zata rama marin da ummu tayi mata,amma ina.... ta makaro ,domin ummu hannunta na hagu tasa tayiwa hannun fulani dam'kar karfi,tare da kuma zabga mata wani lafiyayyen mari da hannunta na dama ,fulani hawaye fal idanunta tace 'akan me zaki mare n....',ummu ta kara zabga mata wani marin tare da cewa 'zaki fadamin gaskiya ko kuwa ba zaki fada ba',fulani kuka ne ya kwace mata gashi kuma ta kasa kwatar hannunta ,murya a cunkushe tace 'wai wani gaskiya .....',kafin ta karasa furucin,ummu ta zabgeta da wani hadadden marin ,fulani fuska tayi jajawur kamar tattasai ,amma bakinta fadi yake 'ni fa wallahi babu sa hannuna ga batan gwolaji daga fada ',wasu maruka ummu ta kara zabga mata hagu da dama tare da cewa 'tunda bazaki fada min gaskiya ba ,.ni kuma bazan gaji da marinki ba',Tas ! TASS!! TASS! TASS! ,ummu ta cigaba da zabge kumatun fulani da lafiyayyun maruka ,wanda a kirge sunfi goma,fulani ganin ba sarki sai Allah,in ba tayi da gaske ba ,zawo da fitsari zasu iya kufce mata don azabar zafin mari,ba shiri ta fara labartawa ummu duk wani makirci da ta kulla game da batan bolaji ! Ummu kanta ne yayi mugun kullewa ,mamaki ne ya cikata domin ba ta taba zaton kiyayyar da fulani take yiwa YARE ya kai wannan matsayin ba! Cike da bakin ciki da takaici ummu ta cika mata hannu tare da nuna ta da yatsa tana cewa'tir da halinki fulani ,kin zama shaidaniya fulani,saboda mai imani ba zai taba aikata abinda kika aikata ba,fulani wallahi nayi dana sanin baki dana kyauta ,domin kin salwantar da rayuwarsa ta fuskoki da dama,kin sashi yayi sanadiyar mutuwar iyayen yarinya,ta Allah ta kasance yarinyar ta zama matarsa duk da haka baki kyaleta ba sai da kikayi sanadinta ,wanda hakan ya jawo ya shiga wani hali,haba fulani ,kar fa ki dauka bana kaunar d'ana ,kara da kawaici kawai nake domin ke ma ki na kaunarsa ,amma kaunar da kike masa makaho ne ,tunda ba kya sara kina duba bakin gatari ,kuma abin takaici shine yadda ki ka hada baki da nawwara da sultan wajen aikata wannan mugun aiki,mecece fa'idar ki na aikata hakan,shima sultan din da kika haifa da cikinki ba ki bashi tarbiya ba ,ashe ni ina gyara kina warwarewa ,fulani wallahi baki cancanci a kira ki da sunan uwa ba ko kadan,sannan kuma ko ba komai nawwara tata tayi kyau ,tunda har dan uwan bolaji ya zama mijinta i shikenan,wannan kadai ya isheta ishara ',fulani kuka take tana cewa'naja'atu bazaki ta ba ganewa ba....',ummu ta katseta ta hanyar cewa 'daman ba zan taba ganewa ba mana,amma ki kwana da sanin cewa ,za'ayi walkiya ,kuma xa'a ganki ,ke ma kuma zakiga bolaji',ummu na gama fadin haka ta nufi kofa ta murza key tare da ficewa daga dakin ,ta bar fulani tana rawar dari ,domin har wani zazzafan zazzabi ne ya dirar mata ,cewa kawai take 'na shiga uku ,oh ni 'yasu ,kar dai gwolaji tana raye ?',ba shiri ta haye kan gado ta kwanta tare da lullube kanta da bargo dalilin sanyi sanyin zazzabi da ya addabeta ,ga kuma fuskarta da ke yi mata zogi da radadin zafin marukan da bata taba shansu a rayuwarta ba!" Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 11:48 AM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~60~ Ko da hadimai suka shigo ,tsawa ta daka musu da cewa su fice su bar ta ita kadai! Ummu tana fitowa daga dakin fulani ,sai ta umarci hadimanta da suje dakin nawwara su kwaso duk wani kayan bolaji da fulani tasa akai wa mujiba dakin,su dawo dashi dakin hashim,ko da hashim ya ga ana shigowa da kaya ,sai ya nemi yaji dalili,ummu ta amsa masa da cewa'kayan matarka ne ,ummanka ta kyautar dasu ga mujiba,shine na ce a dawowa da matarka kayanta ,tunda mujiba ba ta cikin jerin mutanen da zasu ci gadonta",bata jira jin ta bakinsa ta fice daga dakin,bayan hadimai sun gama kwashe kayan daga dakin nawwara sai kuma ummu ta umarcesu da cewa ,su gyara dakin! A bangaren bolaji kuwa badiyya ce tasa ta a gaba da cewa 'ki bani adireshin gidansu hisham in je ni in warware masa zare da abawa,tunda naga kin damu kanki da batunsa'",bolaji ta bude bakinta da niyyar bawa badiyya amsa , shigowar wata hadima dakin ne ya katse mata zancenta,hadimar ta dubi bolaji tare da cewa wai taje ummu na nemanta,bolaji ta dubi badiyya ,sannan ta dubi hadimar tare da cewa 'gani nan zuwa',bayan hadimar ta fice sai bolaji tace 'badiyya don Allah tashi muje ki rakani','ke fa aka ce tana kira .....',bolaji ta katseta ta hanyar cewa 'da Allah na hadaki fa',badiyya babu yadda zatayi ba dan taso ba ta tashi suka fice ! Ummu ta dubesu tare da cewa 'mujiba magana nakeson muyi ni da ke game da maganarki da mukayi a baya",ummu ta gama fadin haka tana mai kallon badiyya ,bolaji ta ce 'kar ki samu damuwa ummu, badiyya ita ma ta san komai',ummu tace 'shikenan!' Sannan ta dubi badiyya tare da cewa ' badiyya tashi ki rufe kofar da mukulli',bayan badiyya ta aiwatar da haka ,cike da nutsuwa ummu ta fara labarta musu yadda ta kasance tsakaninta da fulani ,sannan kuma ta dora da cewa'a gaskiya bolaji zuwan d'ana cikin rayuwarki ne ya jawo miki duk wani tsanani da kika tsinci kanki a ciki,amma ki sani duk hakan ya faru ne dalilin fulani,kuma bawa a kullum ba ya gujewa kaddararsa,ina son ki dauki komai ki daura akan mizanin kaddara,wanda nake fatan hakan ya rinjayi kiyayyar da kike wa hashim ,ki hakura ki cigiba da zama dashi a matsayin mijinki ,domin a gaskiya baki da masoyi da ya wuce shi',bolaji idanunta cike da hawaye tace 'ummu kar ki ga laifina ,kuma bana son ki dubi maganar da zanyi miki a yanzu a matsayin rashin kunya ,a gaskiya bana miki kallon suruka face kallon uwar da ta haifeni,ummu zuciyata bata taba son hashim ba,ni kaina tsoron kaina nake ,har ga Allah na yafewa hashim abunda yayi min a rayuwa ,amma har yau bana jin soyayyarsa ko kadan a cikin zuciyata,wallahi da ace babu auren hashim akaina,da wallahi babu abinda zai zaunar da ni a fada har zuwa wannan lokacin,domin zuciya da so na gun hisham...',badiyya ce ta mintsineta tare da zabga mata harara,ummu tace 'kyaleta badiyya ,har ga Allah ban ga laifinta ba,domin zuciya tana son wanda ya kyautata mata ,kuma hisham ya kyautata mata a rayuwa ,bai cutar da ita ba ,ya bata sabuwar fuska,sabuwar suna ,sabuwar rayuwa ,ya hadata da zuri'arsa,sun koya mata sabuwar YARE,su ne suka samar da mujiba ,kinga kenan hisham ya cancanci abinda ya fi haka daga gun mujiba ,domin mujiba kike a garesu ,mu kuma bolaji kike a gare mu ,ya kamata ki gane bambancin haka..',sannan kuma ta cigaba da cewa'bolaji ni ba zan tursasa miki ba,rayuwar so da aure ,rayuwace da kike da ikon zabar wa kanki wanda ya dace kiyi wannan rayuwar dashi,amma a yanzu abinda ya kamata muyi shine mu san yadda zamu tara hujjoji da shaidu domin gabatarwa da mai martaba,hashim da kuma dan uwanki',bolaji da badiyya suka sauke numfashi ,ummu ta cigaba da cewa 'a yanzu haka dan uwanki da matarsa suna hanyar isowa sokoto,sannan kuma a yanzu zan nemi doctor ayuba a waya ,domin samun shaidar da zamu gabatar na cewa fulani ta samu gawa ta dalilinsa !', Misalin karfe 2:00pm Dr.ayuba ya iso fada dalilin neman da ummu take masa ,palace guest parlour aka saukeshi ,ummu ,badiyya da bolaji suka iskeshi a parlour din,bayan ya gama gaisawa da ummu ,sai ya dubi bolaji yace 'my patient yau idonki nake gani ,it's been long ',bolaji tayi murmushi kawai ,ummu ta dubi dr.ayuba tace'na kira ka ne saboda muyi wata muhimmiyar magana ',dr.ayuba ya russunar da kai tare da cewa a ladabce 'ranki ya dade Allah yasa ba matsala aka samu game da lafiyar yallabai ba...'',ummu ta katseshi ta hanyar labarta masa komai dangane da fulani, bolaji,hashim da hisham! Dr ayuba duk ya bi ya jike da zufa ,jikinsa sai kyarma yake ,idanunsa suka firfito sukayi jajir,ba shiri ya fara rantse rantse yana cewa 'wallahi tallahi har ga Allah da niyyar taimako na bawa umma gawa tare da creating fake DNA result ,amma wallahi babu sa hannuna ga duk wani abu da ya shafi cutar da matar yallabai,ni asali ma ban ma santa ba ,kuma ko da hisham ya kawo ta asibitin ban san itace ba ,wallahi tallahi.....',,ummu ta dakatar dashi ta hanyar cewa 'kar ka damu ayuba ,na yarda da kai,abinda nake bukata daga gareka shine ,zan bukaci shaidarka a duk lokacin da bukatar hakan ya taso,ka tashi ka tafi ,sai na kara nemanka',jikinsa na tsuma ya amince tare da kuma yin alkawari bada hadin kai dari bisa dari in har asirinsa zai rufu ,da kyar ya tashi ya tafi yana mai mamakin makirci irin na fulani,amma ko ba komai kwadayi da son abin duniya ne ya jaza mishi,kuma yasan muddin wannan labarin ya yadu a gari toh babu shakka bankwana da lasisinsa na zama cikakken likita ya zamar masa tilas! Misalin 6:00pm bamidele da nawwara suka iso fada ,ummu ce ta tarbesu domin ita fulani zazzabi yayi mata mugun kamu ,kuma ko da lafiyarta kalau ,bamidele da nawwara bazasu samu arzikin kallo daga gareta ba balantana kuma tarba,a dakin nawwara da ummu tasa a gyara aka saukesu,bayan sun kimtsa tare da samun hutu ,misalin karfe 9:00 pm bayan angama cin dinner kowa ya watse ,domin mai martaba ya wuce turaka ,sai ummu ta bukaci ganin bamidele da nawwara,a guest parlour suka hadu har da bolaji da badiyya tare da baturen likitan da ummu ta bukaci matar gwamna ta turo mata shi,bayan kowa ya zauna,ita bolaji sai kallon bamidele take ,yadda yayi kyau yayi haske yayi fresh kamar bashi ba,tabbas nawwara tana bashi kulawa wato ta maye mai gurbin iyaye da kuma yar uwarsa ,shi kuwa bamidele tun da suka zo ya dora idanunsa akan mujiba(bolaji) yaji gabansa na faduwa ,kuma idanuwanta na masa kama da idanun marigayiyyar yar uwarsa ,ummu ce tayi gyaran murya tare da yin nuni ga mujiba (bolaji) tare da labartawa bamidele komai dangane da ita cikin harshen turanci,nawwara idanunta na zubda hawaye ta gasgata zancen ummu ta hanyar labarta musu abinda duk sukayiwa bolaji tin ranar data shigo fada a matsayin matar hashim,sannan ta dora da cewa a gaskiya ita tayi nadama domin ta dawo daga rakiyar fulani ne a ranar data kawo gawa a matsayin gawar bolaji ,kuma sanin kansu ne gaba dayansu basu da tabbacin masaniyar makomar bolaji a wannan daji',bamidele idanunsa na zubda hawaye ya dubi mujiba(bolaji) tare da cewa 'bolaji is that really you?',bolaji kasa amsa masa tayi saboda kukan da ya ci karfin ta ,domin ita da kanta tana tausayawa kanta,domin rayuwa ta gara ta tun daga ranar da hashim ya shigo mata rayuwar ,ummu ce ta yiwa likta umarnin diban jinin bamidele da mujiba(bolaji) domin gudanar DNA test ,saboda DNA test result dinne zai tabbatar da cewa mujiba itace bolaji ,duk da a yanzu babu shakku ko tantama ita din ce ,a take doctor ya aiwatar da umarnin ummu ylyare da yi mata alkawarin zai kawo mata result washegari ,bayan likitan ya tafi ,sai ummu ta tashi ta wuce turaka domin yau kwananta ne , badiyya ta mike tare da riko bolaji suka fice daga parlour ,nawwara kuwa hankalinta duk ya gama tashi ganin irin kallon da mijinta ke jifanta dashi ,hakan yasa ba shiri ta bi bayan su bolaji dakinsu ,bamidele ya tashi shima kanshi a cunkushe da tunani ya zarce dakinsu da aka musu masauki a ciki! Nawwara ta kama hannun bolaji tana cewa 'wallahi tallahi babu kaffara ke ce dai bolaji,daman jiki na yana bani cewa kina raye kuma zaki dawo",nawwara ta durkusa kan gwiwowinta tana mai cewa'bolaji ki dubi girman Allah ki yafe min,nasan mun zalunceki ,mun aikata miki mafi munin cutarwa,pls nd pls find it in ur heart to forgive me',bolaji ta tayar da ita tsaye tare da cewa'nawwara har ga Allah na yafe miki,domin kin cancanci in yafe muki ko dan kasancewarki matar brother dina,ki sani kin xama yar uwata ,we r nw family,na yafe miki nawwara,Allah ya yafe mana gaba daya",cike da farinciki nawwara ta rungume bolaji tana mai zuba godiya,sannan ta kara dubanta tare da cewa 'Allah mai iko ,bolaji yau ke ce kike jin hausa kuma kikeyin hausa tamkar dama can bahaushiya ce ke '',badiyya tace 'ke ma dai kya fada,Mujiba bahaushiya ,bolaji bayarabiya",nawwara tace'tabbas bolaji a yanzu is potraying 2TRIBES(YARE BIYU )!",a haka suka dan taba hira inda nawwara ta ciro wayarta ta nemi alfarmar bolaji da ta taimaka tayi mata wani abu,sai da badiyya tasa baki sannan bolaji tayiwa nawwara wannan abun,nawwara murna fal cikinta ta yiwa su bolaji sai da safe tare da wucewa dakin fulani domin aiwatar da abinda zuciyarta ke bijiro mata! Fulani ta gama kurbar shayi tare da ahan maganin da jakadiya marakisiya ta kawo mata ,bayan ta gama sha ,sai ta kwanta tare da bawa jakadiya umarnin kashe mata wutar dakin idan zata tafi! kamar a mafarki fulani taji muryar bolaji tana cewa 'mummy folani.....here i come....oduduwa has given me the will and power to scatter your life.....',suman kwance fulani tayi domin ko yatsarta ta kasa motsawa,sai zuciyarta dake bugawa pat pat pat ,a zuciyarta cewa 'oh ni sa'a naga ta kaina ,yanzu 'yar mutan oduduwa fatalwa ......",muryar bolaji ce ta katse mata zancen zucin da take "mummy folani ,am going to scatter ur face just the way you did the same to my face ,sango will strike you to death....",wani irin ruwa mai dumi dumi da lami lami fulani taji yana fita daga kasan mararta bakinta na rawa ta fara jero duk wani addu'ar da yazo bakinta ,ga kuma dakin babu haske balle ta ga fatalwar bolaji ta kuma bata hakuri, nawwara kuwa gimtse dariyarta tayi lokacin da kunnawanta suka jiyo mata fulani tana neman gafara cikin muryar kuka da pidgin english tana cewa 'na una dey see me ,me i no dey see una,abeg bolaji forgive me na , na devil cos am ,abi u don forget sey me and u na 1 &2 ,abeg no scatter my life .....',nawwara ta kara danna play din recording din muryar bolaji da sukayi ita da badiyya ,''folani...your end has come.......',sautin fitar kukan fulani ne yasa nawwara ta sa stop domin fulani ta fara kuka mai kama da tashin mota,bayan ta yi kokarin gimtse dariyarta tare da boye wayarta cikin skirt dinta ,sai ta nemi switch ta kunna wutar dakin tana cewa 'umma lafiya na ganki haka hanci duk majina ?',fulani jiki na rawa tana raba idanu tace'nawwara mun shiga uku ,bolaji ce take min fatalwa wai she go scatter my life ....',nawwara ta hadiye dariyar daya taho mata tare da cewa 'kin dai shiga uku dai,daman in baki manta ba na gaya miki cewa in har bolaji tana raye zata dawo ....',fulani ta katseta ta hanyar cewa'haba nawwara wani irin zata dawo ,kar ki sa zuciyata ta buga mana ,bolaji ta dawo i nagama mutuwa,kidaina ma cewa zata dawo domin ina da tabbacin cewa bolaji ta riga tayi mushe tunda gashi har fatalwa take yi min ....',nawwara tace 'kika sani ko ita din ce ta dawo a gaske ,sai kuma ta zo miki ta sigar fatalwa .. ',sai kuma nawwara tace 'daman zuwa nayi mu gaisa dazu da yamma muka iso,ummu ce take ce mana wai baki jindadi ,kuma ga zahiri na gani ,Allah ya kawo sauki ,sai da safe ',fulani ta kama yi mata magiya tana cewa'nawwara kar ki tafi ,dan Allah ki kwana a dakin nan....',nawwara tace 'wato shi kuma mijina in barshi shi kadai ko?, wai shin ina hadimanki ne masu tayaki kwanaa? ....',"ni ce na basu umarnin tafiya ...",fulani ta bata amsa,sai nawwara tace 'bara in duba side dinsu ko marakisiya ce sai na turo miki,sai da safe ',nawwara ta fice ta bar fulani tana kyarma ta zazzare idanu tamkar berar da tirela ta dannewa bindii,nawwara tana fita ta kwashe da dariya ,sai da tayi mai isarta sannan ta je ta bawa jakadiya da sauran hadimai umarnin zuwa dakin fulani domin su tayata kwana! ko da suka iske fulani a daki ,babu kunya tace musu'kuyi min wanka dan Allah ,sannan kuma kuma ku wanke kayan gadon nan dana fitsare " Written by :ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 1:48 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~61~ Ko da nawwara ta koma 'daki ,bamidele ko juyowa bai yi ba,hakan yasa ta chanja kayan jikinta izuwa na bacci ,ita ma ta hau gadon ta kwanta a bayansa ,murya a sanyaye ta fara cewa 'i know you will be mad at me ,but pls & pls try and understand ,i'm scared of loosing you that's why i kept quite...',rai a bace bamidele ya dago ya dubeta tare da cewa'you're scared of loosing me? ,oh i can see ...just hear ur self out,how can u be so cruel and wicked ,i never thought a day like this will come so soon that i wont be able to trust you anymore,and you know what ?,just pray that all this is a dream,cause if it is'nt.....',kawai sai yayi kwafa ya juya mata baya ,hakan yasa nawwara ita ma tayi kwanciyarta ,a zuciyarta tana mai cewa 'nasan ko ba jima ko ba dade wannan ranar zatazo ,ranar da mijina zai sa almakashin saki ya datse duk wani igiyar aure da so a tsakaninmu,ya Allah ka bani juriya da dauriyar karbar ko wanne irin hukunci da mijina zai yanke min' Sultan shi ma yana dakinsa yana fama da jinyar zazzabin rashin samun mujiba a matsayin matar aurensa! Hisham ya rasa mai yake masa dadi a duniya ,amma ya fawwalawa Allah lamurransa ,hakan yasa ya fara samun kansa da nisanta zuciyarsa da soyayyar mujiba(bolaji) ,domin yana ji a jikinsa ya rasa ta har abada ,amma a haka ya bar wa Allah zabi ! * * * Washe gari misalin karfe 1:00pm ,ummu ta bukaci kowa (wato duk wanda lamarin 'batan bolaji ya shafa ) ya bayyana kansa a turakar mai martaba ,wanda tun a daren jiya ta shaida masa cewa akwai wata muhimmiyar boyayyiya a kasa da za' tono! ☆TURAKA☆ mai martaba ,ummu ,fulani,hashim,sultan,bolaji(mujiba),bamidele,nawwara ,badiyya,jakadiya marakisiya,kurtagu,barde ,dr.ayuba ,da kuma baturen likita mai suna dr.albert! Dukkansu sun hallara a turaka,masu mamakin wannan haduwa sunayi,wanda kuma cikinsu ya gama durar ruwa ,suma nasu cikin nayi,sai kuma wanda suka fara kuka tun kafin a fallasa suma sunayi! Ummu ce ta fara yin sallama tare da kuma cewa 'ina son kowannenku a nan wajen ya kasance mai fadin gaskiya a yayin da aka bukaci gaskiyar,domin gara aji kunyar duniya da akan aji kunyar lahira',sannan kuma ta umarci bolaji ta fadi abinda ya faru gare ta.......'bolaji murya a sanyaye ta fara bada labarinta tun daga ranar da hashim ya tafi liberia ,har izuwa ranar da hisham ya kawo ta fada a matsayin kanwarsa' ,mai martaba,sultan,hashim da fulani tare da su kurtagu mamaki ne ya kamasu kasancewar wai mujiba ce bolaji ,mussaman hashim da shi ya kura mata idanu yana mai ganin wawancinsa da sokoncinsa na rashin gane matarsa bolaji tun da take kula dashi ',ummu ta dubi sultan tace 'sultan abinda mujiba ta fada akan ka gaskiya ne?',sultan idanunsa cike da hawayen nadama yace 'gaskiyane hakan ya faru ,amma har ga Allah babu hannuna game da abinda ummu da nawwara sukayi mata ,domin ni da kaina a wannan daren na koma domin dauko bolaji,sai ban tarar da ita ba,amma a kullum addu'a ta itace Allah ya bayyana mana ita idan tana raye',ummu ta sauke numfashi sannan ta dubi nawwara tace 'ke kuma me zaki ce game da wannan al'amari',nawwara ta sadda kai tare da cewa 'gaskiya nasan na aikata babban kuskure ,amma ko ma menene duk makircin umma fulani ne,domin ta aikata komai bisa kiyayyar da takeyiwa YARE ....amma ni ina neman afuwa domin ni na riga na saduda kuma Allah ya riga ya nuna min ishara ta hanyar sanya min soyayyar dan uwan bolaji a zuciyata ,wanda a yanzu haka yake a matsayin mijina",ummu ta dubi su jakadiya ,kurtagu da barde tare da neman jin ta bakinsu,jikinsu na rawa suka amsa laifinsu tare da neman sassauci daga gun mai martaba da yarima hashim! Fulani ji take tamkar kasa ya tsage ta fada viki don tsabagen kunya ,mussaman hashim da yake mata wani irin kallo ta da ta kasa tantacewa ,ummu ce ta katse mata tunani ta hanyar cewa 'fulani muna son muji daga gareki ,ki kuma fayyace mana gaskiyar al'amari ga me da gawar da kika kawo a matsayin gawar bolaji',fulani na zubda hawaye ta labarta musu yadda ta je gun dr.ayuba ta amshi gawa!',ummu ta dubi Dr.ayuba tare da cewa 'ayuba shin abinda fulani ta fada gaskiya ne ?",Dr.ayuba jiki na rawa yace 'gaskiyane amma wallahi tallahi da niyyar taimako na bata gawar", nan ya kwashe yadda sukayi da fulani ya shaida musu ,tare da rokon dan Allah a rufa masa asiri ',ummu ta juya ta dubi mairmataba tare da cewa 'toh mai martaba kaji dai duk yanda abubuwa suka faru ,kuma hukunci ya rage gareka',sannan kuma ta umarci Dr.albert ya miko DNA test result ,bayan an mikawa mai martaba result din ,sai ummu ta labarta masa rawar data taka ,tun daga ranar da taje ta tadda mujiba(bolaji) kwance akan kirjin hashim har izuwa daren jiya da likita yazo ya debi jinin bamidele da mujiba (bolaji)! Maimartaba yayi gyaran murya tare da cewa 'a gaskiya na yi mamakin faruwar wannan al'amari ,duniya kenan ,kana naka Allah na nashi,kun cutar da baiwar Allah ,kun salwantar mata da rayuwa ,kun mata mafi munin makirci duk sabida ta kasance YARE",sannan ya dubi fulani yace 'fulani bazan taba mamakin ki ba domin kiyayyarki ga YARE a bayyane take ,amma ban taba zaton zaki je to the extent of doing all this',mai martaba ya bude DNA test result ya karanta sannan yace 'result dai ya nuna cewa jinin bamidele da mujiba yayi matching,wato kenan mujiba ce bolaji ,Allahu Akbar ,Allah mabuwayi gagara misali,wallahi ko da ba'ayi test dinnan ba,babu tantama ko kuma jayayya na kasancewa mujiba ce bolaji ",mai martaba ya dubi fulani yayi murmushi mai ciwo yace"kin fitar da ita da hannunki domin nisantata da hashim da sultan ,kuma da hannunki kika amsheta a lokacin data dawo,har kike kokarin hada aurenta da hashim,kuma sultan shima yake kokarin aurenta ,kinga kenan Allah ya nuna miki ishara da wannan kadai ',fulani kuka take har da majina domin bata taba zaton akwai ranar da dubunta zai cika ba ,a gaskiya wannan ranar tayi mata zuwan bazata domin batayiwa wannan ranar shiri ba! Bolaji kuwa kuka kawai take wanda ta rasa dalilin yinsa ,farin ciki zatayi ko kuma bakin ciki?,sautin kukanta ne yasa hashim ya mike tsam akan kafafunsa daga kan wheel chair, ya taho gareta ,ya kamota ya rungume tare da shafa bayanta cikin sigar lallashi ! Fulani jiki a sanyaye tazo gaban hashim da bolaji ta durkusa murya a raunane ta fara cewa 'ku dubi girman Allah ku yafe min ,nasan na cutar da ku ,na cutar da soyayya da aure,ban cancanci ku yafe min ba ,amma dan Allah in ci arzikin kasancewa musulma yar uwarku ku yafe min',idanu jajir hashim ya dubeta ,jijiyoyin jikinsa duk sun tashi ,kauda kansa yayi ya cigaba da rarrashin matarsa ,hakan yasa fulani ta cigaba da cewa "nasan zaku so sanin dalilin da yasa bana kaunar YARE a rayuwata,saboda komai yana faruwa ne bisa dalili da kuma sanadi ,kafin aure na da mai martaba na taba yin aure.... ♡ ♡ ♡ ♡ ♡ ♡ Soyayyata da PATRICK OKWONKWO ya samo asaline a lokacin da aka turoshi makarantar mu bautan kasa ,lokacin ina ss3,ina sonshi yana sona,lokacin da zancen yaje gaban iyayena,sam babana yace bai san zance ba ,haka zalika yangidanmu suka sani a gaba da cewa me zanyi da inyamiri kuma arne ,ni kuwa nace na ji na gani haka nakeson abuna ,anyi fama da ni sosai akan in hakura da patrick amma ina nayi nisa ,shi kanshi patrick din ya hakura amma ni ban hakura ba,na daura gaba da kowa da kuma abinci,ganin za'a rasa ni yasa babana ya amince da aurenmu ,bayan patrick ya amshi musulunci,a ranar da ya gama bautar kasa a ranar aka hadamin jakar kayana ,akace in bi mijina ,tare da cemin duk abinda ya sameni inyi kuka da kaina ,ni kuwa murna fal cikina na bi mijina garinsu abia state ,ko da muka a isa garin abia ,naga tashin hankali da masifa a gun mahaifansa domin uwarsa kuka ta dinga yi tana ihu kamar wacce akace mata gobe zata mutu ,a lokacin da ya shaida musu wacece ni,danginsa kuwa cewa sukayi basu san zance ba ,kawai su dai ya sakeni ya maidani garinmu faqat ,wai ina shi ina auren bahaushiya kuma musulma ,patrick shima yayi musu kunnen uwar shegu tare da yin rantsuwar cewa babu abinda zai rabani dashi sai mutuwa ,a haka ya kaini dakinsa ya ajje ni ,ya nemo min abinda zanci,tare da kwantar mini da hankali ,ni kuma a lokacin ina mamakin ganin yadda suke tada jijiyoyin wuya don kawai ya aureni ,idan kuma sun san cewa ya musulunta fa me zai faru ,domin sarkin yankinsu har gida yazo ya sami patrick game da batuna ,shikuma patrick yace shi fa yana kan bakansa,a haka suka kyaleshi,cikin dare bayan munyi sallolin mu ,mun kwanta kenan,sai kawai ciwon ciki ya murdeshi ,kafin ace me ,ya fara aman jini ,ina ji ina gani patrick ya cika da kalmar shahada ,nayi kuka sosai a wannan daren,gashi kuma ina tsoron in fita in shaida masu ,sai washe gari da safe ,na fito daga dakin idona zuru zuru ,duk na fige ,a zuciyata ina mai cewa shikenan na rasa patrick a daren dana tare a matsayin matarsa ,lokacin dana shaida musu cewa patrick ya mutu,naga bala'i,cewa sukayi ni na kasheshi,duka suka min mai sunan duka ,sannan suka min askin kwal kwal , suka kulle ni a wani daki mai shegen duhu ,da gani sai daurin kirjin bakin yadi ne a jikina,sai dana shafe kwana bakwai ina shan ruwan wankar gawar patrick,basa bani abinci ,kullum sai an tambayeni in fadi gaskiya ni na kashe patrick ,ni kuma sai na dinga rantse musu da cewa bani ba ce ,a rana na takwas da rasuwarsa,wasu manyan mata guda shida suka zo dakin danake ciki a kulle ,ina ji ina gani ,suka kwantar dani tare da waremin kafafuna ,suka zambada min dakakken barkonon su (alligator pepper) a gabana ,ji nayi tamkar an zare min rai a lokacin ,a sume suka fice suka barni,sai danayi kwana biyu suna zuwa suna zuba min barkonon a gabana su fita su barni a sume, cikin wani dare bayan na farfado, duk na bi na fita hayyacina ,dani da tababbiya babu banbanci,wata mata ce tashigo ta sameni jikinta na rawa ,ta bani kaya na saka ,sannan ta bani abinci naci ,ta bani umarnini in tashi muje ,ko da muka fito ko ina tsit , haka ta rike min hannu ta kaini wajen mararrabar yankin nasu ,ta bani kudi tace in mike wata hanya har tasha zata kaini in hau motar garin mu in tafi ,saannan ta juya ta tafi ta barni ,na ci bakar wahala kafin in iso garin sokoto ,ko da na iso gida babu wanda ya ganeni an dauka mahaukaciya ce,sai daga baya suka gane nice ,asibiti aka kaini sannan aka hada da bani rubutu inasha ,sannan na dawo daidai ,sai da kowa ya tausayamin a lokacin dana basu labarin abinda yafaru ,ni kuma tun daga lokacin na tsani duk wani YARE ,in har ba hausa fulani ba ,...... ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Fulani cikin muryar kuka ta dubi mai mai martaba tace"kai kanka ka aureni ba tare da kasan wannan labarin ba ,kawai dai kasan na taba yin aure mijin ya mutu",sannan ta dora da cewa"wannan dalilin ne yasa na tsani YARE...! Written by : ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL=YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~61~ Ko da nawwara ta koma 'daki ,bamidele ko juyowa bai yi ba,hakan yasa ta chanja kayan jikinta izuwa na bacci ,ita ma ta hau gadon ta kwanta a bayansa ,murya a sanyaye ta fara cewa 'i know you will be mad at me ,but pls & pls try and understand ,i'm scared of loosing you that's why i kept quite...',rai a bace bamidele ya dago ya dubeta tare da cewa'you're scared of loosing me? ,oh i can see ...just hear ur self out,how can u be so cruel and wicked ,i never thought a day like this will come so soon that i wont be able to trust you anymore,and you know what ?,just pray that all this is a dream,cause if it is'nt.....',kawai sai yayi kwafa ya juya mata baya ,hakan yasa nawwara ita ma tayi kwanciyarta ,a zuciyarta tana mai cewa 'nasan ko ba jima ko ba dade wannan ranar zatazo ,ranar da mijina zai sa almakashin saki ya datse duk wani igiyar aure da so a tsakaninmu,ya Allah ka bani juriya da dauriyar karbar ko wanne irin hukunci da mijina zai yanke min' Sultan shi ma yana dakinsa yana fama da jinyar zazzabin rashin samun mujiba a matsayin matar aurensa! Hisham ya rasa mai yake masa dadi a duniya ,amma ya fawwalawa Allah lamurransa ,hakan yasa ya fara samun kansa da nisanta zuciyarsa da soyayyar mujiba(bolaji) ,domin yana ji a jikinsa ya rasa ta har abada ,amma a haka ya bar wa Allah zabi ! * * * Washe gari misalin karfe 1:00pm ,ummu ta bukaci kowa (wato duk wanda lamarin 'batan bolaji ya shafa ) ya bayyana kansa a turakar mai martaba ,wanda tun a daren jiya ta shaida masa cewa akwai wata muhimmiyar boyayyiya a kasa da za' tono! ☆TURAKA☆ mai martaba ,ummu ,fulani,hashim,sultan,bolaji(mujiba),bamidele,nawwara ,badiyya,jakadiya marakisiya,kurtagu,barde ,dr.ayuba ,da kuma baturen likita mai suna dr.albert! Dukkansu sun hallara a turaka,masu mamakin wannan haduwa sunayi,wanda kuma cikinsu ya gama durar ruwa ,suma nasu cikin nayi,sai kuma wanda suka fara kuka tun kafin a fallasa suma sunayi! Ummu ce ta fara yin sallama tare da kuma cewa 'ina son kowannenku a nan wajen ya kasance mai fadin gaskiya a yayin da aka bukaci gaskiyar,domin gara aji kunyar duniya da akan aji kunyar lahira',sannan kuma ta umarci bolaji ta fadi abinda ya faru gare ta.......'bolaji murya a sanyaye ta fara bada labarinta tun daga ranar da hashim ya tafi liberia ,har izuwa ranar da hisham ya kawo ta fada a matsayin kanwarsa' ,mai martaba,sultan,hashim da fulani tare da su kurtagu mamaki ne ya kamasu kasancewar wai mujiba ce bolaji ,mussaman hashim da shi ya kura mata idanu yana mai ganin wawancinsa da sokoncinsa na rashin gane matarsa bolaji tun da take kula dashi ',ummu ta dubi sultan tace 'sultan abinda mujiba ta fada akan ka gaskiya ne?',sultan idanunsa cike da hawayen nadama yace 'gaskiyane hakan ya faru ,amma har ga Allah babu hannuna game da abinda ummu da nawwara sukayi mata ,domin ni da kaina a wannan daren na koma domin dauko bolaji,sai ban tarar da ita ba,amma a kullum addu'a ta itace Allah ya bayyana mana ita idan tana raye',ummu ta sauke numfashi sannan ta dubi nawwara tace 'ke kuma me zaki ce game da wannan al'amari',nawwara ta sadda kai tare da cewa 'gaskiya nasan na aikata babban kuskure ,amma ko ma menene duk makircin umma fulani ne,domin ta aikata komai bisa kiyayyar da takeyiwa YARE ....amma ni ina neman afuwa domin ni na riga na saduda kuma Allah ya riga ya nuna min ishara ta hanyar sanya min soyayyar dan uwan bolaji a zuciyata ,wanda a yanzu haka yake a matsayin mijina",ummu ta dubi su jakadiya ,kurtagu da barde tare da neman jin ta bakinsu,jikinsu na rawa suka amsa laifinsu tare da neman sassauci daga gun mai martaba da yarima hashim! Fulani ji take tamkar kasa ya tsage ta fada viki don tsabagen kunya ,mussaman hashim da yake mata wani irin kallo ta da ta kasa tantacewa ,ummu ce ta katse mata tunani ta hanyar cewa 'fulani muna son muji daga gareki ,ki kuma fayyace mana gaskiyar al'amari ga me da gawar da kika kawo a matsayin gawar bolaji',fulani na zubda hawaye ta labarta musu yadda ta je gun dr.ayuba ta amshi gawa!',ummu ta dubi Dr.ayuba tare da cewa 'ayuba shin abinda fulani ta fada gaskiya ne ?",Dr.ayuba jiki na rawa yace 'gaskiyane amma wallahi tallahi da niyyar taimako na bata gawar", nan ya kwashe yadda sukayi da fulani ya shaida musu ,tare da rokon dan Allah a rufa masa asiri ',ummu ta juya ta dubi mairmataba tare da cewa 'toh mai martaba kaji dai duk yanda abubuwa suka faru ,kuma hukunci ya rage gareka',sannan kuma ta umarci Dr.albert ya miko DNA test result ,bayan an mikawa mai martaba result din ,sai ummu ta labarta masa rawar data taka ,tun daga ranar da taje ta tadda mujiba(bolaji) kwance akan kirjin hashim har izuwa daren jiya da likita yazo ya debi jinin bamidele da mujiba (bolaji)! Maimartaba yayi gyaran murya tare da cewa 'a gaskiya na yi mamakin faruwar wannan al'amari ,duniya kenan ,kana naka Allah na nashi,kun cutar da baiwar Allah ,kun salwantar mata da rayuwa ,kun mata mafi munin makirci duk sabida ta kasance YARE",sannan ya dubi fulani yace 'fulani bazan taba mamakin ki ba domin kiyayyarki ga YARE a bayyane take ,amma ban taba zaton zaki je to the extent of doing all this',mai martaba ya bude DNA test result ya karanta sannan yace 'result dai ya nuna cewa jinin bamidele da mujiba yayi matching,wato kenan mujiba ce bolaji ,Allahu Akbar ,Allah mabuwayi gagara misali,wallahi ko da ba'ayi test dinnan ba,babu tantama ko kuma jayayya na kasancewa mujiba ce bolaji ",mai martaba ya dubi fulani yayi murmushi mai ciwo yace"kin fitar da ita da hannunki domin nisantata da hashim da sultan ,kuma da hannunki kika amsheta a lokacin data dawo,har kike kokarin hada aurenta da hashim,kuma sultan shima yake kokarin aurenta ,kinga kenan Allah ya nuna miki ishara da wannan kadai ',fulani kuka take har da majina domin bata taba zaton akwai ranar da dubunta zai cika ba ,a gaskiya wannan ranar tayi mata zuwan bazata domin batayiwa wannan ranar shiri ba! Bolaji kuwa kuka kawai take wanda ta rasa dalilin yinsa ,farin ciki zatayi ko kuma bakin ciki?,sautin kukanta ne yasa hashim ya mike tsam akan kafafunsa daga kan wheel chair, ya taho gareta ,ya kamota ya rungume tare da shafa bayanta cikin sigar lallashi ! Fulani jiki a sanyaye tazo gaban hashim da bolaji ta durkusa murya a raunane ta fara cewa 'ku dubi girman Allah ku yafe min ,nasan na cutar da ku ,na cutar da soyayya da aure,ban cancanci ku yafe min ba ,amma dan Allah in ci arzikin kasancewa musulma yar uwarku ku yafe min',idanu jajir hashim ya dubeta ,jijiyoyin jikinsa duk sun tashi ,kauda kansa yayi ya cigaba da rarrashin matarsa ,hakan yasa fulani ta cigaba da cewa "nasan zaku so sanin dalilin da yasa bana kaunar YARE a rayuwata,saboda komai yana faruwa ne bisa dalili da kuma sanadi ,kafin aure na da mai martaba na taba yin aure.... ♡ ♡ ♡ ♡ ♡ ♡ Soyayyata da PATRICK OKWONKWO ya samo asaline a lokacin da aka turoshi makarantar mu bautan kasa ,lokacin ina ss3,ina sonshi yana sona,lokacin da zancen yaje gaban iyayena,sam babana yace bai san zance ba ,haka zalika yangidanmu suka sani a gaba da cewa me zanyi da inyamiri kuma arne ,ni kuwa nace na ji na gani haka nakeson abuna ,anyi fama da ni sosai akan in hakura da patrick amma ina nayi nisa ,shi kanshi patrick din ya hakura amma ni ban hakura ba,na daura gaba da kowa da kuma abinci,ganin za'a rasa ni yasa babana ya amince da aurenmu ,bayan patrick ya amshi musulunci,a ranar da ya gama bautar kasa a ranar aka hadamin jakar kayana ,akace in bi mijina ,tare da cemin duk abinda ya sameni inyi kuka da kaina ,ni kuwa murna fal cikina na bi mijina garinsu abia state ,ko da muka a isa garin abia ,naga tashin hankali da masifa a gun mahaifansa domin uwarsa kuka ta dinga yi tana ihu kamar wacce akace mata gobe zata mutu ,a lokacin da ya shaida musu wacece ni,danginsa kuwa cewa sukayi basu san zance ba ,kawai su dai ya sakeni ya maidani garinmu faqat ,wai ina shi ina auren bahaushiya kuma musulma ,patrick shima yayi musu kunnen uwar shegu tare da yin rantsuwar cewa babu abinda zai rabani dashi sai mutuwa ,a haka ya kaini dakinsa ya ajje ni ,ya nemo min abinda zanci,tare da kwantar mini da hankali ,ni kuma a lokacin ina mamakin ganin yadda suke tada jijiyoyin wuya don kawai ya aureni ,idan kuma sun san cewa ya musulunta fa me zai faru ,domin sarkin yankinsu har gida yazo ya sami patrick game da batuna ,shikuma patrick yace shi fa yana kan bakansa,a haka suka kyaleshi,cikin dare bayan munyi sallolin mu ,mun kwanta kenan,sai kawai ciwon ciki ya murdeshi ,kafin ace me ,ya fara aman jini ,ina ji ina gani patrick ya cika da kalmar shahada ,nayi kuka sosai a wannan daren,gashi kuma ina tsoron in fita in shaida masu ,sai washe gari da safe ,na fito daga dakin idona zuru zuru ,duk na fige ,a zuciyata ina mai cewa shikenan na rasa patrick a daren dana tare a matsayin matarsa ,lokacin dana shaida musu cewa patrick ya mutu,naga bala'i,cewa sukayi ni na kasheshi,duka suka min mai sunan duka ,sannan suka min askin kwal kwal , suka kulle ni a wani daki mai shegen duhu ,da gani sai daurin kirjin bakin yadi ne a jikina,sai dana shafe kwana bakwai ina shan ruwan wankar gawar patrick,basa bani abinci ,kullum sai an tambayeni in fadi gaskiya ni na kashe patrick ,ni kuma sai na dinga rantse musu da cewa bani ba ce ,a rana na takwas da rasuwarsa,wasu manyan mata guda shida suka zo dakin danake ciki a kulle ,ina ji ina gani ,suka kwantar dani tare da waremin kafafuna ,suka zambada min dakakken barkonon su (alligator pepper) a gabana ,ji nayi tamkar an zare min rai a lokacin ,a sume suka fice suka barni,sai danayi kwana biyu suna zuwa suna zuba min barkonon a gabana su fita su barni a sume, cikin wani dare bayan na farfado, duk na bi na fita hayyacina ,dani da tababbiya babu banbanci,wata mata ce tashigo ta sameni jikinta na rawa ,ta bani kaya na saka ,sannan ta bani abinci naci ,ta bani umarnini in tashi muje ,ko da muka fito ko ina tsit , haka ta rike min hannu ta kaini wajen mararrabar yankin nasu ,ta bani kudi tace in mike wata hanya har tasha zata kaini in hau motar garin mu in tafi ,saannan ta juya ta tafi ta barni ,na ci bakar wahala kafin in iso garin sokoto ,ko da na iso gida babu wanda ya ganeni an dauka mahaukaciya ce,sai daga baya suka gane nice ,asibiti aka kaini sannan aka hada da bani rubutu inasha ,sannan na dawo daidai ,sai da kowa ya tausayamin a lokacin dana basu labarin abinda yafaru ,ni kuma tun daga lokacin na tsani duk wani YARE ,in har ba hausa fulani ba ,...... ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Fulani cikin muryar kuka ta dubi mai mai martaba tace"kai kanka ka aureni ba tare da kasan wannan labarin ba ,kawai dai kasan na taba yin aure mijin ya mutu",sannan ta dora da cewa"wannan dalilin ne yasa na tsani YARE...! Written by : ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 1:49 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~62~ Fulani ta cigaba da cewa 'ban baku wannan labarin ba domin kuji tausayi na....",murya a sanyaye ummu ta katseta ta hanyar cewa " a gaskiya kin cancanci tausayawa domin kafiya da kuma jayayya da iyaye ne ya jaza miki halin da kika tsinci kanki a ciki a baya ',mai martaba ya dora da cewa'kuma wannan labari naki bai kamata ya zamo sanadin da zakiyi wa ko wanne irin YARE wannan mugun kiyayyar ba,ita bolaji me tayi miki da zaki dauki fansar abinda mutanen tsohon mijinki sukayi miki,bara in gaya miki gaskiya YARE baya taba zama mizanin da zaka auna halin mutum dashi domin kuwa YARE daban halin mutum daban ,ko da zaki koma baya cikin labarinki patrick mijinki bai cutar da ke ba ,kuma naga shima inyamiri ne kamar yadda sauran mutanen garinsu suke,haka zalika matar da ta taimake ki ita ma inyamirar ce ,kin ga kenan YAREn su daya halayyarsu daban daban ,inaso ki yi nazari da tunani ki gane cewa YARE kalma ce kawai domin nuni ga harshen da mutum yake ji,kin ga annabinmu muhammad sallallahu alaihi wa sallam ya kasance balarabe amma hakan ba wai yana nufin duk larabawa amnabawa bane kamarsa,asalima ba gabadaya larabawa bane suka kasance musulmai ba,kinga kenan YARE ba zai kasance ma'aunin auna halayyar dan adam ba ',ko da mai martaba yazo nan a zancensa sai ya dubi hashim da bolaji yana cewa"ina mai baki hakuri bolaji game da abubuwan da aka aikata a gareki ,ba dan ni ba dan Allah kiyi hakuri ki yafe musu ,domin Allah yana son bayinsa masu yafiya ',bolaji idanunta na fidda hawaye tace 'har ga Allah na yafe musu',mai martaba yacigaba da cewa "madallah bolaji,kai kuma hashim nasan cewa an cutar da kai da matarka ,amma ka daure ka cije ka danne ,kayi hakuri ka yafe musu ,domin muma muna yiwa Allah laifi kuma yana yafe mana',hashim idanu jajir yace 'Allah ya yafe mana gaba daya',mai martaba ya dubi su jakadiya yace 'toh jakadiya ,kurtagu ,da barde inason ku tattara ina ku ina ku ku bar min fada salin alin babu duka babu zagi,kuma ina fatan wannan yazama na farko kuma ya zamo na karshe ',jiki a sanyaye suka tashi suka fice tare da yin godiya da kuma neman gafara,mai martaba ya dubi Dr.ayuba yace 'kai kuma kaje in halinka ne ka cigaba ,zakaga sakayya in kuma ba halinka bane Allah ya kare maka zuciyar ka ga aikata aikin dana sani',Dr ayuba idanunsa na zubda hawaye yayi godia sosai tare da daukan Alkawarin zai kasance mai yin aikinsa bisa doron gaskiya da tsoron Allah! Mai martaba ya dubi sultan da ke kuka shabe shabe yayi masa nasiha mai ratsa jiki tare da kuma ce masa ya fidda mata yayi aure,bamidele yatashi ya rungume bolaji bayan mai martaba ya bashi hakuri ,tare da rokon alfamar ya yafe wa nawwara ,ita ma bolaji ta rokeshi da ya yafewa nawwara ,bamidele ya yafe mata ita da fulani ,domin komai ya faru mukaddari ne kuma rubbutacen al'amari ne ! ☆ ☆ ☆ ☆ *GIDANSU HISHAM* Misalin karfe 4:30pm su mai martaba suka isa gidansu hisham,da gudu su zuhra da zahra suka rungume bolaji,haka zalika hajiya ,bayan an zazzauna ,sai mai martaba yafara da yi musu godia ,sannan ya basu labarin bolaji tun daga aurenta da hashim izuwa yau da komai ya zamto bayyananne,hisham kwalla ce ta cika masa idanu ,shikenan ya rasa mujiba a karo na biyu,tashi yayi ya bar falon,hashim ne yayi wa bolaji nuni da idanu da cewa ta bishi,a study room bolaji ta iske hisham,idanunta cike da hawaye tace 'hisham ka kwantar da hankalinka ,mujiba taka ce ,baka rasa ni ba ,insha Allah zan kasance mata a gareka...',hisham ya katseta ta hanyar cewa 'mujiba ki daina yaudarar kanki ,stop getting ur hopes high,and stop giving me false hope ,kar ki manta ke fa matar hashim ce ,u can never be mujiba ,u r bolaji ,so kawai go back to ur husband",bolaji jikinta na rawa tace 'ni kuma bana sonshi ,ban taba sonshi ba ,kuma bana tunanin zan so shi a rayuwata ',hisham yayi murmushi mai ciwo tare da cewa 'ki koyawa kanki sonshi ,kuma so da yawa a rayuwa yana da kyau ka auri wanda yake sonka ba wai wanda kake so ba,hashim yana sonki ,he deserves you ,ya cancanci zama miji a gareki ,nasan kina tunanin cewa rayuwarki ta shiga garari saboda shi ,amma ina son ki bashi chance please yayi making things up to u,idan har kika bari hashim ya subce miki ,wallahi kiyi asarar masoyi na gaskiya .....',bolaji tace"wai shin meyasa ba zaka dubi halin da zuciyata take ciki ba.....",hashim ne ya katseta ta hanyar cewa 'bolaji kar ki damu ,farin cikinki shine nawa ,bakin cikin ki shine nawa ,zanyi iya yin komai domin dawwamar da zuciyarki cikin farinciki na har abada ,kuma ni mai son duk abinda kike so ne,don haka zan sawwake miki in har yin hakan kadai zai sa ki mallaki hisham a matsayin mijin aurenki',hisham ya dubi hashim yace 'kar ka kuskura ka aikata wannan mafi munin gaganci,bolaji taka ce ,you couples are meant for each other.....',hashim ya katseshi ta hanyar cewa 'nagama magana dasu maimartaba ,na ce musu i'm willing to let bolaji free ,in har ta bukaci hakan,domin so ba'a yi masa dole,ba a hada kiyayya da so ,she dont love me and she will never ever love me',hisham ya dubi bolaji dake zubda hawaye yace 'bolaji i dont love you ,i only love mujiba ,and you are not mujiba ,mujiba ta riga ta tafi ,na riga na rufe shafinta a rayuwata,so for once ki budewa hashim zuciyarki,for once ki kalleshi a matsayin masoyinki ,for once ki yi masa kallon mijinki ,ki bashi dama ya koya miki sonsa .... in har kika bari hashim ya sake ki wallahi tallahi bazan taba yafewa kaina ba ,kuma ke ma bazan taba yafe miki ba ",yana gama fadin haka ya fice daga studyroom din ya barsu ! Hishan yana fita ya tsaya passage din din da zai karasa parlour ,kuka ya kama yi kamar karamin yaro yana mai cewa 'ya Allah ina mai mika godiyata a gareka a duk halin da na tsinci kaina ,kai ka samin so a zuciyata ,kuma ina mai rokon ka saka min dangana , hakuri da juriyar da zai maye gurbin so a zuciyata ",cike da tausayawa zahra da zuhra suka zo suka tsuguna kusa dashi ,zuhra tana cewa 'yaya sham ka daina kuka haka ,kar kasa bolaji ta karaya itama ,sadaukarwa a so sai jarumi',zahra tace 'i'm very proud of you bro",ahaka suka lallashe shi ,suka tashi tare da komawa parlour ,hira ce ta barke tsakaninsu (mai martaba,ummu,hisham,dad,hajiya,zuhra,zahra da badiyya),ana kuma jiran shigowar bolaji da hashim!" Hashim ya mikar da bolaji tsaye tare da goge mata hawayenta ,rungumeta yayi kamkam tare da cewa "my better half can you feel my heartbeat ,kinji yadda soyayyarki ke wahalar da zuciyata ,ban san da wacce kalma zanyi amfani ba wajen baki hakuri tare da gaya miki irin dimbin son da nake miki amma i guess this will explain it better', ba shiri jikin bolaji ya mutu murus domin kafafunta kasa daukarta sukayi ,ji tayi kamar ba 'a duniya take ba,sai da hashim ya gaji dan kansa sannan ya dakatar da kiss din tare da cewa "my better half ....',kwantar da kanta tayi akan kirjinsa ,ko motsin arziki ta kasa yi ,balle yasa ran zata tankashi ,murmushi yayi tare da cewa 'OUR LOVESTORY IS SO UN-USUAL'! Written by : ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL [10/19, 1:49 PM] ‪+234 806 079 4214‬: =YARE BIYU= [ 2tribes ] na ILILEE ~63~ Hashim Rungume da bolaji suka shigo parlour,ko ba'a fada ba daga ganinsu kowa yasan cewa sun sasanta junansu.....! ♡♡♡♡♡KOMAI YAYI FARKO...♡♡♡♡♡ *BAYAN WATA DAYA* Fulani tana mu'amala da kowa a fada tsakani da Allah ta watsar da duk wani makamin kiyayya da ta dauka ta sawa zuciyarta,ta rungumi hanyar Allah,alaka tsakaninta da maimartaba ,hashim da sultan ya ja baya ba kamar yadda suke da ba ,bolaji da ummu ne suke kokarin janta a jiki a kullum ! Hisham da Sultan sun bawa bolaji wuka da nama game da zabin matayen da zasu aura ,babu bata lokaci aka sanya ranar auren badiyya da hisham ,wanda kowa yayi murna da amanna da wannan hadin da bolaji tayi, domin badiyya mace ce abar so ,batada makusa a halayya da kuma sura,kuma su kansu hisham da badiyya sunyi na'am! Bayan auren hisham da badiyya ,nawwara da mijinta bamidele sukayi haramar komawa erin,inda bolaji da mijinta zasuyi masu rakiya,shima sultan ba 'a barshi a baya ba! Ko da suka isa erin,kowa yayi mamaki da aka ce bolaji ce da fuskar mujiba,tabbas babu ta yadda Allah baya tsarawa bawa lamarinsa! Kwanan su uku a erin ,sultan da funmilayo soyayya mai karfi ta kankama tsakaninsu,wanda babu bata lokaci,hashim ya shaidawa mai martaba ,mai martaba da tawagarsa sukazo suka nemawa sultan auren funmilayo ,basu bar yankin erin ba sai da aka daura auren sultan da funmilayo! ☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆ Bolaji ce zaune a gaban dressing mirror tana cire earrings dinta ,hashim ne ya fito daga bathroom,kugunsa daure da towel ,rungumota yayi ta baya ,murmushi kawai tayi tare da cewa 'oga hitler when are getting back to work tunda yanzu everything is settled ',hashim ya cusa kansa a wuyanta yana cewa 'what work?',bolaji ta amsa da cewa'aikin sojanka mana',hashim yayi dariya tare da cewa 'ni da aikin soja har abada my better half,bana son abinda zai kara nisanta ni da ke,nagama magana da mai martaba ,i will join sultan in the family business so that we can manage it together',bolaji tace 'shikenan,Allah yasa hakanne ya fiya maka alkhairi',hashim ya amsa da 'amin',tare da cewa "bolaji i know u r trying to force ur self to love me by trying all the best u can to please me....',bolaji ce ta katseshi ta hanyar juyowa tare da dora hannunta akan bakinsa tace 'ka daina fadin haka oga hitler,ni dai kawai ka cigaba da kyautata min,ka cigaba da nuna min so da kulawa,da izinin Allah sonka zai yiwa zuciya mugun kamu wanda kai da kanka sai kayi mamaki",sai kuma tayi murmushi tare da cewa 'wuyarta in ganni da babynka',hashim idanunsa cike da kwalla yace 'my better half i love you with all my heart,Allah ya nuna min ranar da zaki haifa min babies masu kama da asalin fuskarki',kankameta yayi a jikinsa ,tare da cewa 'i will love my kids to learn the 2TRIBES from you",bolaji ta maida masa martani da cewa "ni da kai zamu koya musu YARE BIYU"............... "Indeed hashim and bolaji's love story was very un usual.... " 'ililee' ♡♡♡KARSHE♡♡♡ Created &written by : ABDULAZIZ ILILEE ISMA'IL ☆☆☆☆☆☆☆ Godiya ta tabbata ga ALLAH daya bani ikon kammala labarin YARE BIYU ! ina kuma mika godiyata ga duk wanda ya karanta wannan labari (YARE BIYU),da kuma wadanda sukayi supporting dina financially and emotionally,godiya gareku ga wadanda suka taimaka min wajen koya min yaren (yoruba) tare da fada min duk abinda ya shafi (yoruba land), bazan manta da ku ba! Duk wani mai sharhi,,jinjina ko kuma comment game da labarin,pls ya tuntubeni via whatsapp :08125363328 ,ina jiran sakonninku ! Love you all #ILILEE

Post a Comment

0 Comments

Contact Form

Name

Email *

Message *

Translate

LATEST POST